Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 6
tana gasa shi. Yana kallon matashin da akalla zai kai shekaru talatin ko fin haka ya ciro waya ya kara a kunne, ba ya jin abin da ya ke fada saboda akwai 'yar tazara tsakaninsu. Bai wani jima yana wayar ba, ya ga wannan mata mai sanye da nikab ta fito, ta iso wajen matashin ta rusuna ta gaishe shi, sannan ya ga matashin ya tayar da mashin din ta hau baya suka bar harabar gurin. Mamaki ya kama shi, kar dai a ce wannan shi ne mijinta? Lallai ya dace mata mai kaifin kwalwa, sai dai ita ta dace sa miji NAJNOOR 85 SADAUKARWAtalaka fitik! Abin da ya ayyana a ransa ke nan. Dama haka rayuwa ta ke, wani za ka same shi da kaifin kwalwa amma sai rashi ya tauye masa damar da ya ke da ita. Bayan sallar isha'i ne Larab ya zo gidan, suka nufi asibiti shi da' Hafiz. Yanayin da ya tarar da Bintu ta ba shi tausayi, don duk ta rame saboda yarinya ce mai kumari amma ciwo ya ramar da ita. Tausayin yarinyar ya kama shi, ko me ya ke damunta haka har ciwon zuciya ya kamata? Larab abokinsa ne, tare suka yi sakandire har jami'a, don haka akwai shakuwa tsakaninsu. Duk gidan su Larab ba wanda bai san shakuwar da ke tsakanin Hafiz da Bintu ba, domin tun tana yarinya idan zai zo gidan yana taho mata da alawa, kasancewarta yarinya mai son kayan zaki, shi LTELA yasa da zarar Hafiz ya zo gidan da gudu za ta nufe shi. Yadda ya ke zuwa gidan yasa kowa ya sanshi, suna kuma girmama shi, don duk NAJNOOR 86 SADAUKARWA-1 Kannen Larab da Yaya suke kiran Hafiz wannan koyarwa ce ta gidan, karami bai isa ya kira sunan babba gatsal ba. Yanayin shakuwar da ke tsakanin Hafiz da Bintu ba yana nufin soyayya ba, don shi bai dauke ta a matsayin macen da zai so ba, duk da ba wani muni ne da ita ba, bai dai taба jin haka a ransa ba, haka ba wanda ya taba hasashen haka a tsakaninsu, ita ma a gare ta (Bintu) babu watą alama ta soyayya da ta ke duban Hafiz da ita, sai dai sun shaku ainun. Lokacin da suka zo asibitin bacci Bintu ta ke, amma kafin su tashi tafiya ta farka, tana yin tozali da Hafiz fuskarta ta yalwatu da fara'a, ta се. "Haba Yaya Hafiz ai na dauka sai na mutu za ka zo shan gumba?" Ya yi murmushi ya ce. "Hmm, na yi tafiya ne, ban ma san ba ki da lafiya ba sai dazun Larab ya ke fada min... Ya karfin jiki? Ta ce, "Da sauki". NAJNOOR 87 SADAUKARWA-| Ya ce, "To Allah Ya kara afuwa, amma ya kamata ki rage sanya wa kanki pressure da yawa, koda-ya ke na ga alama sai an cire ki daga makarantar nan tunda na lura ita ke haifar miki da tunani har ga shi hakan ta soma faruwa da ke" Ta yi takaitaccen murmushi, ta ceuh "Yaya karatun ne da wuya wallahi, ga shi kuma ina so Ya ce, "Duk da haka sai ki rage, saboda lafiyarki". abin?" Ta maida dubanta ga Umma ta ce. "Umma Yaya Larab ya kawo min Umman tana murmushi ra ce "Ai ga shi nan gabanki ba sai ki tambaye shi ba?" Larab ya ce, "Wane abu kuma?"" Bintu ta ce, "Zogalan ko? Ya auna mata harara, ya ce: "An ki a kawo, sai ka ce wani ci ta ke". Ta dan sobare baki, ta ce. NAJNOOR 88 SADAUKARWA-1 "Shi ke nan na ma daina cin komai" Larab ya ce, "Yo wa kika yi wa? Ina ce cikinki za ki kai" Hafiz ya yi dariya ya се. "Hmm Bintu rigima, yau kuma an koma cin zogala?" Ta juyo da ba wa maganarsa muhimmànci ta ce. "Likita ne fa ya ce na yawaita cin zogala, yana kara jini da lafiya a jikin dan Adam" Hafiz ya ce, "To shi ke nan, bari gobe zan kawo miki, kyale wannan man din ya cika latsi da yawa i nsa Sun dan jima asibitin sannan suka taho. *** Bayan kwana biyu zuciyar Hafiz ta dan yi sauki daga damuwar da ya ke ciki.,vibBm Ya shigo falon gidan da niyyar ya amshi abinci, tsautsayi kawai sai idanunsa NAJNOORA89 SADAUKARWA-1 suka hango masa Hamdiyya ta ci kwalar Alhaji Atiku cike da masifa, tana cewa. "An fada maka ni ma irin matan da ka saba' aura ne? To wallahi ni na fi karfin duk wani iskancinka, rubuta min takarda ta na ce" Hankalin Hafiz ya tashi ainun, duka kwana nawa da yin auren har an soma wannan artabu? Alhaji Atiku ya ce. "Ba zan ce da ke komai ba, don na lura hauka da rashin tarbiyya suna tattare da ke" Kamar ya watsa mata ruwan zafi, ta sake dakumar rigarsa. "Idan ba ka san ni mahaukaciya ba ce, yanzu za ka sani, rubuta na ce maka!" Takaici ya ishi Hafiz bai san lokacin da ya karasa gurin da hanzari ba, ya dauke Hamdiyya da wani gigitaccen mari, wanda ya yi sanadiyyar daukewar kuzarinta. Alhaji Atiku ya dubi Hafiz ya ce. "Wa ya sanya ka?" NAJNOOR 90 1-0.04 002 SADAUKARWA-I si sast Kansa ya rusunanikasa ya kasa cewa omaiAlbaji Atiku ya ci gaha da gowabnua kent sBanasyoi kanashiga sabgar da ba laka svieA BviigH idub 661-6t uliA ijsdIA Kafin Alhaji Atiku ya gama fadan abin da ya ke son fada, tuni" HamdiyyaMa rarumo aniufarantida i kel|saman lebur la rotsawa AMhajiAtiku a ka, men da nat goshinsalya fashe, jini ya soma zuba. uensbiy s uikin tsananin bacin rai da zafin nama Hafiz va damko ta ya oi gaba da duka, Hajjya Asiyanda ke labe tun da a ka fara rigimar tana ganin ta'adin da Hamdiywalla yiaya Alhaji sAtikuta fito dansauridanudigurin Alhaji lAtikunyayin da shiikuma Hafiz ya oirgaba da dukan Hamdiyya har suka fito harabar giden, tana ihu da kururuwar neman taimakowowsh nevsy Maigadi da ke zaunqaken benoi ya taso a rikice yan kokarin Kwatar Hamdiyyardaga schannun Hafinushiurkumas yanellciv gaba da dukanta.isz isd sn sd ijimsa nimerodвг пілвг .swo2 sb sdisd sy sm udsH SONAJNQ0821491 SADAUKARWA-I Da kyar maigadin ya kwace ta tana ta kundumawa Hafiz ashar. ya juya ya koma cikin gida. Lokacin tuni jini ya yi wa fuskar Alhaji Atiku fata-fata, ya dubi Hajiya Asiya ya ce. "Mu je asibiti". Suka fito da Alhaji Atikun su duka ukun, lokacin tuni Hamdiyya ta gane hanyar gidansu. Suna zuwa asibitin suka samu a ka karbe su, don ba karamin buguwa goshin nasa ya yi ba sai da a ka yi masa dinki sannan a ka ba shi gado ya huta zuwa anjima. Karfe biyar na yamma-suka dawo gida, suka tarar da yayyen Hamdiyya maza guda uku da mata biyu suna zaman jiran dawowarsu. Suna ganin dirin motar, Hamza yayan Hamdiyya ya taso da sauri, ya ce. "Wallahi ka ba mu kunya, ba mu taba sanin sahoramin namiji ba ne kai sai yanzu!. Habu ma ya karba da cewa. NAJNOOR 92 SADAUKARWA-I "Ka dake ta, katon danka ya daketa? Ina ba zai yiwu ba". Alhaji Atiku ya yi murmushin vakaici, bai ce da su komai ba. Hafiz ya се. "Wata kila makafi ne ku'shi yasa kuka gaza ganin abin da ya ke goshinsa! To ku yi abin da zaku yi". Sa'uma ta ce, "Kana nufin Hamdiy ya ce ta fasa masa goshi? Ina wannan zuki ta malle ce, ina Hamdiyya ta ke da karfin da za ta yi kokawa da katti biyu irinku? Kun dai ji kunya". cc. Alhaji Atiku ya nuna musu hanya, ya "Ku fice min daga gida" Lauwali ya ce, "Takardarta za ka ba وو. mu, kuma ka saurari sammaci Alhaji Atiku ya ce, "Idan an je kotun na bayar". Ya sa kai zuwa cikin gida, su Hafiz suka bi bayansa, yayin da suka bar dangin Hamdiyya suna ta bambamin bala'insu. NAJNOOR 93 SADAUKARWA-1 Wannan shi ne karshen auren Alhaji Atiku da Hamdiyya, auren da duka-duka bai kulla sati biyu ba, ai fa masu jini a farce suka samu abin fada, wai lallai Alhaji Atiku NAMIJIN ZARA ne, tunda ga shi wannan auren ma ko tsawo bai yi ba har ya saki ámaryar. Shi kam yana mamakin yadda mutane ba sa yi masa adalci, duk lokacin da sakin aure ya faru tsakaninsa da matansa shi ake ba wa laifin, bayan an ce idan an ciza a hura. Yanzu ita Hamdiyya daga ta ce tana bukatar kudi za ta yi kasuwanci ya ce, bai amince da ta yi kasuwanci ba. Ta koma ta ce tana so ta ci gaba da karatu, shi ma ya ce bai amince ba. Shi ke nan abin da ya jawo tashin fitinar, wai dama ya aureta ne dan ya takurawa rayuwarta ya tauye mata hakki, to ita ba ta daga cikin matan da maza suke rainawa wayo, idan bai sani ba ya sani tana NAJNOOR94 SADAUKARWA-I cikin kungiyoyin mata masu karc hakkin. mata, don haka ita ba za a takura mata ba. Abin ya ba shi mamaki, ya zauna yana mata nasiha don su samu daidaito, amma fir yarinyar nan ta ki fahimtarsa, ta ce, alo tsiya alo danja sai ya barta ta yi yadda ta ke so, kuma tunda tana da matsayi a kungiyoyinsu na kare hakkin mata dole ya amince da yin taro a gidan. Shi kuma ya ce bazai yiwu ba, shi ya ke aurenta dole ta bi dokokin da ya kafa. To a nan me ye laifinsa? Amma saboda rashin adalci na wasu mutanen sun ara sun yafa wai halinsa ne auri-saki! To bai damu ba, su ci gaba, aure ne dama ya sanyawa ransa daga wannan zai hakura, ya kuma hakuran insha Allah. Hafiz ya fi kowa tausayin mahaifinsa, halin da ya ke ciki yana damunsa ainun, sai dai ya zasu yi da kudirar Ubangiji? Yau ma kamar kullum a kan idanunsa Matashin nan ya sauke dalibar akan mashin NAJNOOR 95 SADAUKARWA-1 dinsa, tun kwanaki biyu da suka wuce Hafiz ya tsirarwa kansa wata al'ada, da zarar ya shigo gurin bayan ya shiga ofis ya ajiye abubuwan da ya zo da su, zai fito waje ya tsaya gurin motarsa yana kallon masu shiga da fice a kamfanin. Abin da kullum ya ke ba shi sha awa bai wuce wadannan ma'aurata ba, domin suna táfiyar da rayuwarsu cikin sauki, idan za ta gaishe da matashin ka'ida ne sai ta rusuna, haka idan za ta hau mashin abin gwanin sha'awa don tana ba wa addini hakkinsa wajen baza hijabinta gudun kada wani ya ga tsiraicinsa. Allah Ya sa ni bada wata manufa ya ke kallonsu ba, sai don burge shi da suke. Lallai talaka yana dace da mace, ina ma shi ne ya dace da samun wannan mace haka? To yau din ma yana tsayen ya ga ta sauka daga kan mashin din, shi kuma ya buga ya fice daga harabar gurin. A hankali ta ke takunta har ta iso gab da inda Hafiz ya ke, ta NAJNOOR 96 SADAUKARU'A-I dan rusuna ta gaishe shi. Cike da jin dadin yadda ta ke girmamashi ya amsa mata, wannan halinta ne idan har za ta ganshi za ta rusuna ta gaishe shi a matsayinsa na malaminta. Bayan ya amsa gaisuwar ta mikc za ta wuce, yа се.. "Am ba ki ji ba". Ta tsaya ba tare da ta juyo ba. Ya ce, "Kin karbi handout din wajena י"?kuwa Ta dan juyo kadan, idanunta cikin nikab ta се. "Ban karba ba Yallaбai". Ya ce, "Ko me yasa?" Ta ce, "Zan karba ne". Sai ya ji tausayinta ya kama shi, wata kila ba su da karfin siya ne, karatun ma ya lura karfin hali ne kawai irin na talaka mai dogon buri, ba don haka ba ina za su sami kudi har naira dubu ashirin na rajista? NAJNOOR 97 SADAUKARWA-1 Ya ce, "To shi ke nan, idan na shigo zan taho miki da shi". Duk da a cikin nikab ta ke, hakan bai hana ya gano firgitarta ba, shi ma sai ya ji haushin kansa, me ya kai shi shiga shirgin matar aure? Ta ce, "Yallabai ka barshi, na gode" Ya tamke fuska tare da kawar da kai daga dubanta, da kuma kokarin gotar da zuciyarta zuwa tunanin da bai dace ba, ya ce. "Tsarin gurin nan ne, mukan ba wa. dalibai masu kokari tallafi ba da wata manufa ba, don haka zan shigo miki da shi". Ta сe, "To na gode Yallabai". Bai ce komai ba, ta wuce shi, ya dan juyo a hikimance yana binta da kallo har ta shige ajin da suke daukar darasin. Duka daliban ba su wuce su sha takwas ba, amma yadda ya lura yarinyar ba ta mu'amala da kowa, hakan na matukar burge Hafiz, yana son mace mai shariya domin irinsu sukan kula da mu'amala da mutanen da NAJNOOR 98 SADAUKARWA-1 a Iכ ba su dace da su ba. mace mai karadi an fi samun munanan halaye a gare ta. a د כ n 지 Lokacin da ya shiga ajin nasu, tana zaune a mazaunin da ta saba zama, kanta a sunkuye da alama wani abu ta ke dubawa. Ya dube ta a nazarce sannan ya maida dubansa ga sauran daliban da ke cikin ajin. Bayan ya gabatar musu da darasin da zasu gudanar a ranar, ya mike a hankali yana takawa tarc da duba kowanne benci har ya kawo kan inda ta ke zaune. Ba ta dago da kai ba, sai ya zagaya ta bayanta yana kallon abin da ta ke dubawa, wani littafi ne na koyon computer, ya jinjina kai, wato ta mallaki ma wasu littattafan bayan handouf? A hankali ya koma can gaban allon, sannan ya сe. "Ina ganin gobe za mu fara pratical tunda kuna cikin mako na biyu da farawa, ina fatan kun haddace duk abin da a ka koyar da ku?" Gaba daya suka hada baki suka ce. NAJNOOR 99 "Insha Allah yallabai". SADAUKARWA-J Ya lura ban da ita a ka yi magana, abin sai ya dan taba masa zuciya, ba wai ya ji haushin kin tankawarta ba ne, a'a a ganinsa ya yi jam'i akalla tunda ita ma tana cikin daliban ta amsa, koda ya ke kanta a kasa ya ke bai sani ba ko ta amsa a cikin lullubin nata. Ya jinjina kai, yana cije lebe ya ce. "Da kyau" Ya zauna yana duba record din sunayen da a ka ba shi, sannan ya ce. dinka" "Ina Usman Hassan?" Matashin ya mike tsaye ya ce. "Ga ni nan yallabai", Ya ce, "Yauwa, zo ka karbi handout Ya mika masa. "Ina Fadima Malam Abdullahi?" Ya fada yana mai zare idanu ya ga ta taso, tsam ya ga ta taso din kuwa cikin takunta na tafiyar hawainiya ta iso gabanshi ta rusuna yayin karbar, hakan ya kara burge shi, NAJNOOR 100 SADAUKARWA-1 duk da kokarin da ya ke na kwabar zuciyarshi da ta ke son kissima masa burgewar matar a gare shi hakan ya ci tura, shi kam aiki ya same shi, don bai san irin yadda zai kwatanta shigar burgun da ta yi wa zuciyarsa. Kafin ya sakar mata, sai da ya yi jim kamar ba zai ba ta ba, har ta dan dago kai idanunsu suka hadu. Tsau! Ya ji wani abu ya ratsa bargo da kashinsa, lokaci daya kuma ya ji gabansa ya yanke ya fadi, don haka ba shiri ya sakar mata, ta juya ta koma inda ta ke zaune, shi kuma ya zauna yana nazarin takardun dake gabansa. Daga karshe ya tattara yanasa-yanasa ya yi musu sallama ya fice. Yana zaune a ofis dinsa hankalinsa gaba daya ya rabu da jikinsa. Fadima ta tsaye masa a rai, abin da ke kular da shi yadda ya kasa sarrafa żuciyarsa ta daina siffanta masa taswirrar matar da ya ke tunanin matar aure ce. Sai ma azalzala shi da ta ke yi, wai ya samu matar aure! NAJNOOR 101 SADAUKARWA-1 Da tunani ya yi masa yawa, sai ya dauki makullin motarsa ya bar kamfanin gaba daya, bisa matakin da ya ke son daukarwa kansa tunda zuciyarsa ta ki amince masa daina tunanin Fadima, gwara ya bar kamfanin wata kila zai kubuta daga fadawa tarkon halaka. *** *** Tafe suke cikin mota Hafiz da Alhaji Atiku zasu je gidan Alhaji Mande akan maganar takardun gidan da Alhaji Atikun ya siya a wajensa. Hafiz ke tukin motar, shi kuma mahaifin nasa yana zaune a daya 6angaren, babu mai magana a cikinsu, kusan kowa da tunanin da ya ke. A gare shi (Alhaji Atiku) har yanzu yana tausayin halin da dan nasa ya ke ciki na rashin Rufa'atu, a ganinsa wannan shi ne dalilin da ya sa har yau Hafiz ya ke cikin rashin walwala ba kamar can baya ba. Yayin da shi kuma Hafiz zuciyarsa ta ki nutsuwa da tunanin Fadima, tun ranar da ya ba NAJNOOR 102 SADAUKARWAta handout ya ke kokarin gocewa ko da kallonta; bare kuma kintatar lokacin da mijin nata zai kawota kamfanin, amma hakan ya faskara, ta ki fice masa. Dalilin haka ya shiga damuwa ainu, ko baccin kirki ba ya yi, da ya ga hakan na neman zame masa babbar matsala sai ya tsiri duk dare zai yi alwala ya yi nafila, bayan ya sallame sai ya kama karatun alkur'ani don gusar da shaidan daga makotaka da zuciyarsa. To yana samun sukunin yin bacci idan ya yi haka, da zarar gari ya waye ya je kamfanin ne ta dinga zuwar masa a cikin tunaninsa, da fatan ganinta a zahiri. Tunaninta yana matukar tasiri a gare shi, duk da haka ya kan takura kansa ko da zuciyarsa na azalzalarsa ya fito daga ofis din don ganin isowarta cikin kamfanin yakan ki bin umarnin. Haka dole ya samu Yusha'u ya karbе shi daga darasin da ya ke daukarsu, har zuwa practical da suke yi ya daina don dai ya daina ganinta har Allah Ya sa ta kammala ta bar kamfanin. NAJNOOR 103 au ay an ail at SADAUKARWA-1 Yau da safe da tsautsayi ya sa suka hadu, yana shigowa kamfanin su 'ma suna shigowa, don haka kafin ya gama tsayar da motarsa inda ya dace tuni ta iso gareshi tana jiran ya bude kofar ya fito. Da farko ya yi nufin shareta, to amma tunawa da ya yi matsayin mace da darajarta har ta iso don ta gaishe shi bai dace ya watsa mata kasa a ido ba, wannan ya sa ya bude kofar ya zuro kafafunsa waje ba tare da ya fito ba. Ta gaishe shi a mutumce, sannan ta wuce gaba. To tun bayan tafiyarta sai ta fama mishi tabon mikin kaunarta da ke nukurkusar zuciyarsa, ya yarda haduwarsa da ita wata jarabawa ce da Ubangiji Ya ke nufinsa da ita, bayan ya tsallake siradin Rufa'atu' na yin biyayya ga mahaifinsa yanzu kuma ya fada tarkon halaka? Haka ya baro kamfanin cike da damuwa, yinin ma dai duk a damuwa ya yi shi, har lokacin da Alhaji Atiku ya kira shi a waya cewar ya zo su je gidan Alhaji Manden, har NAJNOOR 104 SADAUKARWA-1 kawo yanzu da suke tafiyar hankalinsa bai kwanta ba. Alhaji Atiku ya juyo da dubansa kadan ya kalle shi, ya girgiza kai, tukunna ya ce. "Jiya Kawunka Isma'il ya ke ba ni wata shawara, wai me zai hana a hada aurenka da 'yar wajensa Nusaiba?" Da sauri Hafiz ya dago kai, don maganar ta daki zuciyarsa, ina shi ina Nusaiba? Cike da tsananin mamaki ya ce. "Nusaiba kuma Abba?" Alhaji Atiku ya yi murmushi, ya cе. "Ni ma abin da na gani ke nan, ana gudun gara a fada gidan zago, don dai ban san kai naka ra'ayin ba ne, kar na zartar da hukuncin da zan dawo ina da na sani, na so matuka na nuna masa rashin amincewata a lokacin, amma na bari na ji ra'ayinka” Girgiza kai Hafiz ya yi, ya ce. "A'a Abba, ni kam bana son auren Nusaiba, saboda ina da labarinta tsab ba ta da nutsuwa, shi yasa ko gidan na je ba na kulata duk da yawan shisshige min da ta ke yi". NAJNOOR 105 SADAUKARWA-1 Alhaji Atiku ya tsura masa ido, cike da dai tausayin ya ce. "To shi ke nan haka za ka zauna babu lokaci?" Hafiz ya ce, "A'a, lokaci kam ai zai zo ko Abba?" Ya ce, "To Allah ya kawo mana shi, amma na kosa matuka na ga ka yi aure Hafiz, domin aurenka yana daga cikin burace-buracen da na ke wa kaina tanadi". Shiru bai tanka ba, yayin da Alhaji Atikun ya ci gaba da cewa. "Duk da cewa ba a gaggawa ga lamarin aure, amma don Allah ka sanya wa ranka za ka yi aure a wannan shekarar, kar don wannan matsalar da ta faru ka će ba za ka yi aure ba..." Da sauri Hafiz ya katse shi. "Ina! Wallahi ko daya Abba ban taba sanyawa raina wannan abin da ya faru a takurar da za ta sanya ni kin sunnar ma'aiki ba, ai Kaddara ce tunda na san na dace da mahaifin kwarai bana shakku akan duk wani hukuncinka. Duk abin da ka zartar a gare ni dai-dai ne, NAJNOOR 106 SADAUKARWA-I fatana kullum Allah Ya Kara raunanar min da zuciya na yi biyayya a gare ka, kar shaidan ya samu nasara a gare ni ko yaya ta ke kuwa". ce. Ya ji dadin wannan furuci na Hafiz, ya "Yauwa dana, haka na ke so, Allah Yai maka zabi na alkhairi, ni ma ina nan ina addu'a Allah ya ba ni wata macen mafi alkhairi a gare ni, don na kasa tauye zuciyata ga lamarin aure". Hafiz ya sake waigowa ya dube shi, amma sai bai tanka ba, akalla don ya ce yana son ya sake wani auren ba aibu ba ne idan a ka yi la'akarin da halin da ya ke ciki, to amma shi ke nan haka za a kare, da wannan ta fita sai wannan ta shigo? Dai-dai lokacin suka isa kofar gidan Alhaji Mande, Hafiz ya tsayar da motar a inda ya dace, sannan suka fito su duka biyun daga cikin motar. Alhaji Atiku ya ciro wayarsa ya kira Alhaji Mande ya sanar da shi sun iso. Babu 6ata lokaci Alhaji Mande ya fito yana murmushi ya tare su, suka gaisa, sannan ya ce. NAJNOOR 107 SADAUKARWA-1 "Bismilla, mu shiga daga ciki mana" Alhaji Atiku ya ce, "A'a ba sai mun shiga ba, mu tsaya a nan ma ya isa Alhaji Mande ya ce. "Haba dai, sai ka ce gidan bakonka ne?" Alhaji Atiku ya yi dariya ya ce. "Ko ba bakona ba ne, ka san ni mai laifi ne, na kwana biyu ban zo na duba Anboy ba, don haka idan muka shiga ya ganni rigima се kawai zai saka min". Alhaji Mande shi ma ya yi dariyar, ya ce. "Kamar kuwa ka sani, jiya-jiyan nan ya ke min rigimar wai sai na kai shi gidanka..." Hafiz ya dubi mahaifin nasa ya ce. "Abba, bari na duba wani abokina nan kafin ku gama, ai babu wata matsala ko?" Alhaji Atiku ya juyo yana dubansa. "Nan din ma kana da abokai ke nan?" Murmushi kawai Hafiz ya yi ba tare da ya tanka ba. Alhaji Atiku ya ce. "Babu matsala, sai ka hanzarta, don ba daďewa za mu yi ba". NAJNOOR 108 وو ne. SADAUKARWA-1 Ya ce, "To, da ya ke ma ba nisa nan baya Ya tafi, su kuma suka shiga cikin motar suka soma tattauna abin da ya hada su. Suna cikin tattaunawar ne kamar an ce daga idonka, Alhaji Atiku ya hango wata matashiya tana tafiya sanye da koriyar atamfa, ta saka hijabi da ya wuce gwiwarta. Kallo daya ya yi wa matashiyar zuciyarsa ta buga, har hakan ya yi sanadin yin shirunsa daga maganar da ya ke. Alhaji Mande ya bi shi da kallon mamaki, bai tanka masa ba har sai da matashiyar ta face wa ganinsu, sannan ya tabo shi yana fadi. cе. "Ya ya dai Alhaji?" Alhaji Atiku ya sauke ajiyar zuciya, ya "Wannan yarinyar ce ta burge ni, daga ganinta 'yar gidan manyan mutane се". Alhaji Mande ya yi dariya.ya ce. "Ka ji ka da wani shirme sai ka ce karamin yaro, shin daga ganin sarkin fawa sai miya ta yi zaki? Ka sani ko matar aure ce?" NAJNOOR 109 1 d SADAUKARWA-I syed nAlhaji Atikuyugigiza kar ya seY "Na san ma ba matar auren ba се Tsloru Alhaji Mandeya Gwl ve ) Y ВП? Ме yasa ka ce hakauee smor ekua snobAlhaji Atiku ya cck Gu ettst nidio snsi Jikina ne ya bani ka san matar aurel ko da ganinta za ka iya ganewanol sb ovnse svitst AlhajiMande ya yi dariyajsosai ya.ce.s "Wannan hasashenka ke nan, amma idan yarinya ta samu tarbiyya daga gidan kwarai ba lallai ne ka lantance matar aure ce ko akasin haka ba sd szsm skus) isd ikamsm odsiAlhaji Atiku ya ce/ 988 :61 evidastem "Duk da haka, yanayin da naji a jikina ya ba ni ba ta da aureiisdlA isb aY G Alhaji Mandayacey ulA isdlA "Wato maganar dai da ake fada za ta Labbata Tip atac syni Cikin yanayin tuhuma Alhaji Atiku ya cсe da shi. 00 εν σxiτch iv sy əbasM jediA ייף 9Wace magana ke nад? i К" in ewlhalMnde Ya sauya fuskaimdagä yanayin dariya daraya ya cod inse o SIREN İN BI BYim SADAUKARWA-1 "Da ake cewa kai namijin zara ne, da ka ga mace ba ka da kwanciyar hankali sai ka kaita gidanka. Da kuma ta shiga ba ta cika shekara za ka saketa ka rido wata". Iya Bacin rai Alhaji Atiku ya shiga. fuskarsa a tamke ya ce. "Amma ka ba ni mamaki Alhaji Mande da ka yi min wannan fassarar". Alhaji Mande da ya lura ransa ya бaci, sai ya ji bai ji dadin fitowar furucin ba, ya karyar da kai cikin yanayi na rarrashi ya ce. "Ba ni na yi maka wannan fassarar ba, mutane ne ke fada, kuma da na tsaya na bi kanun abin, sai na ga kamar suna da gaskiya Shiru na tsayin mintoci ya gilma a tsakaninsu, kafin daga bisani Alhaji Atiku ya magantu da cewa. "Wata kila maganar ne ba ta taba hada mu da kai ba, amma wallahi ka ji na rantse maka duk lokacin da zan yi aure ba ni da kwanciyar hankali, saboda gudun irin wadannan maganganun da ake fada a kaina, to abu ne babu yadda ka iya, idan Allah Ya rubuto NAJNOOR 111 SADAUKARWA-1 sai ka auri mace ka sake ta ko ba laifin komai sai hakan ta faru, bare kuma ni da dalilai mabanbanta ke sa wa na saki mata. Ban taba auren wata mace da niyyar wani lokaci na sake ta ba, illa idan na aureta sai mutuwa ka raba, amma da ya ke haka Allah Ya kaddara min babu yadda zan yi, su kuma mutane 'yan ba'ni'na'iya da babu ruwansu da rayuwarka su bi su tsangwame ni. Shin me ye laifina a kai?" Alhaji Mande ya ce. "Ko ba ka da laifi dole a dora maka laifi, domin kowa ya sani mata hakuri ake da su, bare kai. da ka ga jiya ka ga yau, izuwa yanzu ya dace a ce ka tsaya ka nutsu ka fuskanci alkibla daya. Idan har an ce ba don ka so ka ke sakin auren matanka ba, da wace hujja mutane za su yarda da hakan? Kar fa ka manta ba a kan mace daya ko biyu hakan ta faru ba, sai a се koda yaushe laifin matan ne?" Alhaji Atiku ya ce. "Ba za ka gane ba ne, kaddara ba yadda ba ta zuwar wa Bawa, duk kuma wayo ko hikimarsa bai isa ya tsallake mata ba, facele NAJNOÓR 112 SADAUKARWA-1 Allah Ya iyakance masa. Wannan auren na Hamdiyya da na yi, shi ne na sawa raina ba zan kuma wani, auren ba ko don.na gujewa wadannan Kananan maganganun, ba don Allah Ya haramta min ba, to amma kullum zuciyata tana muradin na auri mace wadda zan ji dadin aurenta, Yau sama da shekaru ashirin da takwas ke nan, tun bayan rasuwar marigayiya Halima, har kawo yanzu bani da kwanciyar hankali akan rayuwar aurena, shin don me ba zai so samun kwançiyar hankali ga rayuwar aurena ba kamar yadda kowane namiji ya ke samu? Wannan shi ne

Chapter 4 of 6