Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 6
gidan cike yake da samari bata wani rufeshi ba saboda kowa da lokacin dawowarsa ga uwa uba shi kansa malam din tunda shima bashi da taka mai man lokacin shigowar sa gida kasancewa akoda yaushe ya na masallaci. Mrs Alokacin da ya shiga farfajiyar gidan tsintar kanshi yayi yana mai faduwar gaba sakamakon ganin motar Fahad da yayi, a farfa jiyar gidan. Tabbas kuma hakIka babu tantama shine ya dawo hakika daw warsa ba kara min bajet ta ke neman ruguza masa ba. Yasan halin fahad sarai, duk abinda yasa a gaba sa yaga Karshensa hankalinsa yake kwanciya. lokacin da Auwal din ya shiga gidan alokacin baifi minti goma da dawowa ba, saboda kai tsaye ya nufo masa gida saboda yasan babu kowa aga shi sai mai gadi da 'yan aiki dan haka babu wanda zai tadawa hankalin tunda kowa yasan halin tafiya. Auwal nan take ya daure fuska ba bu wata walwala a tare da shi ya shiga buga kofar shi ma haka Fahad din a kule yake, cike da zargin shin daga ina Auwal yake? Zuciyarsa ta tsaya kyam a babu tantama daga gurin Humaira yake, to me ta kaishi, amsar da bashi da ita ke nan. A nan suka zauna a falon cike da zargin juna bayan sun gaisa ne Auwal yake tambayar sa dalilin dade war sa a Abuja Fahad ya ce, wallahi zuwa nayi na tarad da aiki gagarumi a gabana wato wata baiwar Allah ce ta zo haihuwa munfi awa biyar a kanta amma ta kasa haihuwa har muka gaji muka kaita dakin tiyata da akayi mata ne 25 LUBABАН aka samu ashe 'yan biyu ne a cikin nata sai dai kansu a hade yake kuma cikinsu ma a hade haka muka fito mata dasu kai lallai Allah mai ikone wato Auwal baka san wani abuba ana fito dasu, su kama kuka gaba daya duk abinda daya zaiyi sai kaga tare sukeyi shiyasa muke zargin an ya kuwa ba da kwakwalwa daya suke aiki ba kuma abin haushi matar ba musulma bace amma hakan bai sa, ta yadda da Allah ba, dan bata da addini kwata-kwata. Auwal ya ce e ai kasan shi Allah haka yake, sai ya ga dama zai shiryar dakai irin wadan nan isaharorin sunfi faruwa a gurarensu amma hakan bai sa sun fargaba Allah dai ya kyauta kuma ba ka sani ba Auwal ni kadai nayi mata wannan tiyatar hakIka na sami yabo ta fannoni da dama nan take decta asibitin ya bani hutu na sati biyu amma dan danace masa ina da uzuri na sam bai amince ba, har raina ya 6aci raina sosai na kwanta da nufin garina wayewa zan taho wata sai dai in rassa aikin gaba daya. Allah cikin ikonsa sai gashi an kawo matar a wannan daren wallahi tausayin yaran naji shi yasa har na zauna na dan kula dasu na 'yan kwanakin nan in banda hankalina ya kasu kashi da dama, kuma itama matsalar da na bari a gida tana da amfani sosai a kaina to kiwa da babu abinda zai hanani zama da su har sai wantannin da zasuyi a asibitin ina kuma basu kulawa ta musamman. Auwal ina ka nufane? na dawo ban samekaba yayi masa wannan tambayar ne dan ya kara tabbatar da zarginsa duk da cewar baya raba dayan biyu burinshi daya kawai yaji amasar da ga bakinsa dai yanayin sa kawai zai lura da shii ya bawa kansa amsar tambayar sa ta farko Auwal ya wangale baki gaba daya ya ce, wallahi matuniyar na kawai ziyara tunda ka tafi sai yau Allah ya kaini ni kaina nayi mamaki, inajin karfe tara na wannan 26 WANDA YACE NAMIJI UBA NE 3 dare tare ta ruskemu da ita amma gashi har sha daya ta wuce ta shiga farfajiyar cakon karfe goma sha biyu amma muna tara amma ai kazo a dai dai da ma gobe ake shirya tafiyar mu kano har itan, dan kai an jiraka shiru da malam yace in ka dawo kaje ka samemu a can amma tunda Allah ya dawo da kai ai anyi a dade, kaga sai a dauki hanya da sanyin safiya. A zahiri da tika-tikan kankara ya samu yayi inasa zuban ruwan sama da su, hakIka da yafi so da wannan annurin fuskar da yake nuna masa wanda hakan shi ya nuna masa firi falo cewar ya shawo kan matar shi, tabbas da sake an bawa mai kaza kai abinda Fahad ya fada ke nan a ranshi dan kuwa babu yadda za'ayi ya amince da wannan shirin nasu tabbas ya zama dole ya tsinkayi gidansu da Asubashin farko don yayi wa Humaira dirar ungulu shin me ma Humaira ta ke nufi da shi. A sanda zai bar garin zamfara ta amınce da kanta cewar babu wani a gaban ta face shi to yaya za'ayi kuma kan ya dawo ta nemi dainkewa da tsohon mijinta. Dole yasan abinyi, dan haka nan take ya daure fuska. Abinda Auwal ya lura ke nan shima ya maida tasa fuskar ya dinke ta tsaf da rashin walwala dan haka a nan suka tsayar da hirar, kowa ya kwanta cike da tunanetunane gami da tsananin kuncin rai su duka in badda juyi babu abinda sukeyi shi kawai Auwal ji yake kamar ya kashe Fahad, badan bashi da mafutaba. Dan me zai ringa nuna son matar shi uwar 'yayan shi a gaban shi, wanda yake ganin in anbi diddigi ma yanzu haka sakin bai sakuba, tunda cikin 6acin rai yai sakin Allah kuwa baya aiki da tunanin marar hankali mutumin da ya shiga baçin rai ko dede yake da mutumin da baya cikin hayyacin shi 27 LUBABАН koma dai menene, wannan kuma ya, wuce, sai dai a kori gaba a kuma shiryawa abinda za'a tarad da shi a goba. A wayewar ranar lahadi karfe bakwai a kofar dakin su ta yiwa Fahad abinka da dan gida babu shamaki amma tabbas duk da haka da ya karasa ya gaida su Hajiya ko mutan gidan kuwa da ya gamu da shamakin da ya daka tar dashi har Humairar ta shiya dan kanta, ta fito hakika bugun kofar ya rudar da su Shafa'atu ce ta taso cikin sauri ta nufi kofar dan ta bude a zatanta Hajiya ce dan haka daga irta sai daurin kirji ta leko saboda tuni Humaira ta shga wanka itama jiranta take tayi ta fito, itama ta shiga cikin sauri ya kauda kanshi gami da tambayarta ina Humaira duk da cewar shi maharrraminta ne amma sai da taji kunya dan tana ganin ta wuce munzalin da zai ganta a haka. A hankali cikin nutsuwa tace dashi Humaira tana wanka ya danja tsaki kadan nuna alamun ba haka yasoba ba watiu ita tama kagu ta tafin shi ne har ta shga wanka da wduri, amma yasan abanyi ya dan zura hannayensa ciki ajjihun sa yace okey in ta fito kice da ita tayi sauri ta tarad dani a mota ina jiranta. A yadda Shafa'atu ta lura da fuskarshi tabbas tasan a matse yake dan haka sai ta shiga bugawa Humaira kofa tana ce da ita dan allah tayi sauri ya ya Fahad na jiranta a motarshi, dan ko wanka bai yi ba, dagashi sai rigar bacci. A gurguje ta gama wankan ta fito dan tasan tabbas, babu lafiya to yaushe ma ya dawo tambayar da tayiwa Shafa'atu ke nan shafatace wallahi ni ma ban sani ba na dai so in tambayeshi, to amma sai naga sam ba fuska, ke dai kiyi sauri kije ki sameshi kyaji a bakinshi cikin sauri ta hanzarta ta shiryawa ta ficè ta sameshi a mota, ya buga uban tagumi gaba daya gwiwoyin hannunsa akan sitiyarin 28 3 WANDA YACE NAMIJI UBA NE 3 motar suke idan shi yai jajir kai ka rantse kuka ya sha'ain ka fahimci yanayinsa ne kadar zai tabbatar maka da cewa tabbas bai runtsa idanun shi, daren jiya ba, wanda hakan ne ya hadda sa masa canjin launin kalar idanshi. A hankali tamkar motsoraiyar da tayiwa masifaffe Ôarna, ta shiga gaida shi bayan sallamar da ta sakar masa da 'yar muryarta mai ki dimashi a duk sanda ya jita baiyi niyyar murmusawa ba amma kawai sai ya tsici kanshi ga me sakin fuskar da tun jiya take a tsuke tamau, ya rasa abinda zai kwaçe masa ita yaji dadi a ransa amma a yanzu tashi daya zinariyar muryar masoyiyar tashi ta gama mareta tasa acikin yan fakikan da basu taka kara sun karya ba ya bude kofar motar ya umarceta da ta shiga ganin yanayin da yake ciki ya hanata musa masa, ta shiga a hankali ta zauna shi da kansa ya ratso hannunshi ta gaban ta ya rufo kofar sannan ya dan kalleta na dan lokaci ya shiga jan motar, ba tare da yace da ita ko ta tafasa ba.dan kuwa ko gaisawar da ta masa bai amsaba. A hankali ya ringa jan motar itama batace dashi komai ba, dan ita a zatanta gidanshi zai nufa da ita gurin Auwal. Amma sai labari yasha ban bam, da taga yanufi inda bama ta taba zuwaba tun iya zaman ta a zamfara balle ta san sunan inda suke nufa daji ya keta da motar yahau wata 'yar hanya sai da sukayi tafiya mai nisa sannan ta kasa jurewa ta tambayeshi inda yake shirin yi da ita. A hankali ya dago kai ya dan waiga ya kalleta yai naida ganinshi ga banya yace da ita na Humaira LUBABАН har yanzu tana wasiwasin gun wanda zata tsaya to da naga kan in dawo har kun shirya tafiya a yau ke da tsohon mijinki to sai naga abinda ya kyautu damu shine gara in kaiki a raba mana ke a biyu kowa ya dauki kasan shi mai tafiya kano ya tafi mai zaman garin zamfara ya zauna ina ganin hakan zai fiye mana sauki ko ba haka ba?. A'yadda ya nuna a fuskarsa tabbas babu alamun wasa hakan kuma bai nemi ruda taba sai da taga ya ratsa hanya ya keta cikin daji sosai inda sam babu hanya koda da ta mutum balle keke ko babir, har ta tsalla ja da hanyar mota to a nanne gabanta ya fara faduwa kaddai ace Fahad baya cikin hayyacinshi? tabbas da yana cikin hanklinshi to kuwa da bai ringa tura kan motarshi cikin dajin nan, ba tare da tunanin zai iya taka abinda zai hadda masa fashewar tayar motar sa ba, sai da ya-yi tafiya dai dai iyawarsa sannan ya sami gindin wata katuwar bishiyar tsamiya ya tsayar da motar a dede lokacin da wani murti keken maciji ya fito da gudu daga cikin surkukin wasu ciyayi ya cilla yai gaba a guje kamar yadda ya gani tabbas yasan itama taga macijin dan haka sai ya dago kai a hankali ya dunbeta suka hada ido. A hanka!i ta sunkiyar da kanta yayin da idanunta suka cika da hawaye ya danyi murmushi karfin hali yace "Humaira lallai ruwan idan ki zai tsiyaye, tunda Allah ya hadaki soyayya da mahaukaci, dan wallahi Humaira nakan zama mahaukaci akan soyayya dan ni bana sa abu a raina in hakura in barwa wani balle son mace daya da daya kamar ke, Humaira ina kaunarki, kauna mai tsanani ina sonki so marar musaltuwa na tabbabta a lokacin da Auwal ya shiga neman auren ki na farko na tabbabta ya kayar da masu sonki, da dama. To a wanan karon Allah ya hadashi takara da mayen karfe. 30 3 WANDA YACE NAMIJI UBA NE 3 A gaskiya Humaira na riga na dafe milki to kuwa ban 6areni zaiyi wuya ya kamo hannunta ya dora kan kijinshi duk da yasan haramcin hakan, yace da ita "Humaira ki ji yadda zuciyata take bugawa kuma bata taba bugawa face sai da tsananin sonki yadda zuciyata take bugawa da sonki Humaira haka kuma kwakwalwata take aiki da sunan ki Humaira rashin ki kusa dani a matsayin matata zai iya jawowar, katsewar amfanina kwata-kwata a daniya ina sonki, so mai tsanani Humaira shin kin taßajin wanda ya kashe kansa ya kuma mikawa wani ran da hannunshi to in kuwa har za'a iya haka a doron kasa to kuwa Fahad zai iya barwa Auwal ke. A gaskiya Humaira nariga na tanjama nayi nutso mai tsanani wand na tabbata kamoni sai gwanin iya ruwan gaske, dan haka bazan iya fita daga kogin soyayyarki ba, hatta sai da igiyoyin auren ki a hannuna Humaira na riga na gama shirya mana rayuwar mu ta aure, kai har rayuwar ‘yayan mu dama yadda zamu tafiyar jikokinmu in Allah ya bamu to Humaira ta yaya za'ayi in iya daukan wannan littafin ka co kan in mikawa wani, bakya ganin nayi gangancin wargaza babin rayuwata da kaina? Humaira bazan iya hakura ina ji ina gani ki guje min zuwa ga wanda da zai iya wulakantaki kamar yadda ya wulakantaki a baya ba. ni kuwa Humaira da a wulakantamin ke gara in sami makiyin da zai kacalcalamin rigar mutuncina a tsakiyar kasuwa Humaira ganin kine yasa na tsani kadaita ka tsakanina da duk wata mace koda kuwa du bata zanyi a asibiti. Humaira gaskiya bazan iya rabuwa da ke ba da in rabu da ke gara in tunkari macijin nan da ya fito yanzu ya sassareni in mace ya fimin dadī da saukin jin radadi akan radadin da zuciyata zata tsinci kanta yayin da ta rasaki, kunuwana kuma suka jiye 31 LUBABAН ki ga wani, balle ace har min jin fatihar daurin auren ki ga idona ya ganemin zaman ki da wani a matsayin masoya ma aurata, tabbas dole in shiga rudani marar musaltuwa. Amma Humaira ina son ki tabbatarmin da halin da na ke ciki a gurin ki, kuma wanne matsayine nawa a zuciyarki?" "shiru Humaira tayi ta rasa inda zata sa kanta tabbas gaskiyar Fahad da yace ta kasa tsayar da zuciyarta guri daya, to ya zatayi Allah ya hadata da masoya biyu sara kuna a fagen iya soyayya kala man su da iya soyayyar su yana iya jan ragamar duk wata 'ya mace duk taurin kanta to yanzu ita me zata ce da shi. A nanne ya kara juyowa gurinta gaba daya ya ruko hannunta duka biyun ya zura ya tsunsa a daya daga cikin hannuwan nata ya ruke su sosai ya matse hannun na dan lokaci sannan ya lumshe idanshi ya doshi bakinshi da hannun ya sakar mata dafin dake manne a la66ansa hakan kuma ya jawo mata shiga wani yanayiın da in bata yi karya ba zata iya kiransa da bata taba shigar shi ba, in kuwa ta ta6a shigar to kuwa ta manta iya kanta ta yadda da cewa Fahad yafi Auwal iya soyayya ta ko wanne fannni to amma me bata da ta cewa barawo a hannun mata ya ringa matsarta yana cewa Humaira me kikace ne? Humaira kinyi shiru kin barni ina ta zuba. A nutse cikin sanyin murya gami da kaifafa ta, ta yadda zata doki zuciyar mai sauraro tace dashi yaya Fahad, amma kana sane da haramcin da muke aika tawa a yanzu ko? Ina ganin saurin so bazai iya janmu zuwa fadar azabar Allah ba ko? In kuwa har kana tunanin cewa shaukl so ba zai iya janmu wajen aikata aikin saboba to kuwa zai kyautu a ce ka matsa daga kusa da ni, zuwa mazaunin ka gyara ga abin kuwa ka sakar min hannun 32 WANDA YACE NAMIJI UBA NE 3 cikar kyautatuwar imaninmu kuwa mu zamto masu ambatan istigifari, na dan lokaci. A gaskiya yaya mu barwa Allah zabi shi yafi, kada muje mu zabawa kanmu abida zai zo ya dagula rayuwarmu baki daya sanin kanka ne ina sonka so mai tsanani, ina kaunarka kauna marar musaltuwa. Ga tsarin kunya da kawaici irin na 'ya mace bazai iya barina in zai yane maka irin tsannin san da nake maka ba in har ka kyaleni in ji da radadin da zuciyata take ciki to kuwa da sai ince kamin adalci marar musaltuwa ina mamakin kace ka matsamin kò ka ta kuramin akan in sanar dakai irin san da nake maka. A gaskiya bani da kalaman da zan zaiyana maka irin san da nake maka face in nuna maka a zahiri a kuma aikace. Hakan kuma na iya sawa in jawo mana azabar Allah mai tsanani a kanmu yaya kamin adalci a bar maganar zaifi, zafafa son kaji irin son da na ke maka saboda in har hankalinka bai tafi da nisa ba to sai in iya tunasar da kai cewa mu biyu ne a gurin nan, amma muna da cukon na ukun mu wato shaidan, sai kuma Allah da ya haliccemu da yake kallonmu. A nutse ya shiga, shigar da kwayar idansa ciki-ciki a zahiri kalamta sun rudarshi sun kuma kAra tsananta sonta a ranshi ya kalleta yayi murmushi yace, lallai kalamanki sun ceto ki daga shirrin mayanka, kinsan kuwa tafe nake da zabgegen, takobina mai suna gayawa jini na wuce, to amma Humaira bazakimin adalci ba a sanar dani irin son da akemin ko a hanyá mafi saukl ce, wato mudan tsotsa minti domin in tsotsi zakin zumar son da akemin. Amma ka bani mamaki yaya meye amfanin tsotsar minti ga wacce ba muharrramar ka ba, kaje garin ka tsotsi zaki kaci karo da daci marar musaltuwa shi kansa 33 LUBABАН ma'adanar mintin me makon kaci karo da sanyi da ni'i,amtaccen kamshi kaje, kaci karo da tsannin wari, mai tafe da matsannancin zafin da ka iya kuna matsotar minti yaya a gaskiya ni nawa mintin, ban tana darwa manemiba face sai mijin aurena. Amına baka da laifi yaya, sai naga laifin nawa ne da har na sakar maka fuskar da har zaka iya tambayata mintin da zaka tsotsa. Tabbas kuwa in har zamu dore da haka to kuwa nan gaba zaka tambayi abinda yafin tsotsar minti a gurina. Dan haka yaya ka duba lokaci, ka gani tára har da minti hamsin da shida kasan fa a yau aka shirya za'a mai dani gurin iyayena, wadanda basu bani fuskar tsotsar minti a kofar gidan su ba, suka kuma nusar dani aikata hakan a gidan da suka kaini a matsayin matar sunna ga mai gidan saboda haka ka mai dani inda ka ďauko ni. Amma duk cikin tsananin 6acin rai take wadannan maganganun wanda hakan ya nutsar da Fahad a matsananciyar kunya tabbas bai san maganar zata ja wo masa wannan martanin ba kuma shi bai fadi hakan da nufin yasan zai samu koda kusantar ma'adanar mintin ba to amma fa da za'a masa tayi da ya gaggauta, koda lasar ma'adanar mintinne dan haka sai ya dago kai cikin rahsin kwarin jiki ya dubeta cike da dan munacikin murmushinsa da ya yi nufin 6oye tsananin kunyar da ya tsinci kanshi a ciki, yace da ita. Amma Humaira in har kika gaggauta dauke wutar annufin fuskarki a gareni, to kuwa da sai in iya cewa ba'a min adalci ba Humaira in kika duba ai kinsan sam ni ba haklina bane in da za'a min afuwa in furta manufata to kuwa da na ce dake wasa nake miki. Haba Humaira nifa musulmine gaba da baya kuma ina tutiya da adddinina, ba kuma najin kunya ko shayin a nuna ni a matsayin musulmi 34 WANDA YACE NAMIJI UBA NE 3 to dan me zai sa in kasance daya daga ciki mayaudaran mutane masu yaudarar al'umma da cewa su musul mai ne alhalin kuma sunfi kowa kwarewa wajen saban Ubangiji Humaira nasan kusan tar matar da ba muharramar kaba, da sumba ma kawai (kiss) haram ne to kuma, ina ga mai tsotsar minti (romance) kuma na san tsananin azabar masani tafi ta jahili shi jahili Allah zai kama shi da laifin, kin zuwansa ya nema shi kuwa m,asani fa ya je ya nema ya kuma samu amma sai yasa kafa ya take, yace shi haka bai masa ba, sai dai ya gudanar da son ranshi Ayimin afuwa dan Allah, in sha Allahu bazan kara ba shaukin so ne ya dauke ni har na yaba gurfatacciyar maganar cikin mayen so da kauna. Amma hakIka zan gargadi kaina ko dan gaba in san irin maganar da zata fito daga bakina. Har kunnuwa su kaiwa zuciya yasa amsa mai faranta raina. Humaira ina sonki fushin ki dani zai iya jefa ni cikin halin kaka nakayi." "Amma yaya kai kanka kasan bai dace ka furta haka a gareni ba amma shi ke nan, wannan ya wuce sai mushirya wa tarar abinda ke gaban mu yaya ya dace ace mun bar garin nan kasancewar, mukadai ne a dokar daji sannan irin wannan maganganu na shiga tsakaninmu, mu koma gida kada a neme mu, kaga har goma ta wuce duk abinda zuciya ko rai suka raya a akanmu abin nufi duk abinda aka zargemu da shi yaya bamu da bakin futar da kanmu face Allahn da ya haliccemu, shi kadai zai shedemu shi kaďai zai shedemu dan haka dan Allah Yaya ka taimake mu ka fitar damu daga cikin zargi musamman ma ni. Tunda kai dansu ne sun dade da kai sun san halinka ni kuwa fa su yi tunanin 6oye halina nayi sai da naji zan koma ga iyayena sannan na fito dashi fili tunda baza su kara ganina ba. Amma bai dace kiyi wannan tunanin ga iyayena ba Humaira ina alfaharin sanar dake cewa iyayena masu fahimtane sai dai ban gane dai nufinki ba cewa daga yau ba 35 LUBABАН zasu kara ganinki ba kina nufi dama yaudarata kike sai munje Kano kice ke gidan ki zaki koma? To wallahji baki isaba ki dauki zamfara a matsayin gida Kano kwa ki rikekwa ki rike a ranki tamkar zaki ganin gida ne, in kuwa kin canja gari to kuwa Abuja kika nufa da mijinki na har a bada aure na dake kuwa babu gudu babu ja da baya can jin ra'ayinki a kai na ya kan iya jawo miki dana sani mai tsanani a rayuwa. A cikin zafin rai ya fizgi motar ba tar da ya kara sauraranta ba kuma har suka karasa gidan babu wanda ya Kara cewa wani koda ta tafasa. A kofar gida suka tarad da malam, da wanı kanan Fahad da ake kiransa isah da kuma Auwal tsaye a kofar gida babu tantama akwai abinda suke tattaunawa, wanda tatsuniyar gizo bata wuce koki, dan gane ga yadda suka zuba musu ido cikin mamaki shi ya bashi tabbacin akan su suke maganar. Alokacin da suka fito daga motar babu abinda ya ruda Humaira ya kuma kidimata face irin matsananciyar a zababbiyar hararar da Auwal ya jefo ta da ita nan take jikinta ya daukar karwa ruda ni kuma ya durar mata a dai-dai lokacin da ya fiskanci irin kallon da fahar ya tsareta da shi gaba dayan su durkusawa suka yi a gaban malam cikin Kunar rai Malam ya hausu da fada ya shiga zazzagin Fahad yace wai shin yaushe ka dawo? Da mu bamu san da dawo warka ba kazo ka dauki 'yar mutane kuka fice gidan uwar wa ka kaita? A kasa ya zame dishan ya zauna yace jiya na dawo cikin dare malam shi yasa banz I ba ita kanta Humaira tambayar da ya dace tayi masa ke nanan amma sam ta manta sai a yanzu ta san lokacin da ya dawo sannan yaci gaba da cewa malam jiya Auwal yake sanar dani cewa yau za'a tafi Kano shine na dauketa na kaita gidan abokaina sukayi sallama a yanzu haka akwai guraren da bamu je ba saboda lokaci ya kure.. 36 WANDA YACE NAMIJI UBA NE 3 Abin ya bawa Humaira mamaki ganin yadda tashi daya ya iya shirya karya, irin wannan alhaliko karkarwa baiyiba, irin ta nuna alamun makaryaci Nan take Malam yace, in haka ne ka kyauta to amma me yasa baka fada ba?" malam nayi kuskure kayi hakuri ato nan gaba in har zaka fita da wani a gidan nan ka ringa sanar da ni ko baka sami gani na ba ka sanar da mahiafiyar ka, "To" yace da malam din wacсe ba ta karya wuya. An koma falon abban aka zauna na mai da yadda magana take malama yayi shiru yace ato shi dai aure na Allah ne. dan haka ni yanzu addu'a ita zan shiga yi muku Auwal dan Allah a kori gaba dan sha'anin mata sai a hankali kasan mace sai ta shekara tana 6atawa namiji rai yayi shiru ya jure walau saboda yay\anta ko dan irin san da ya ke mata ko kuma gudun tonawa gidan shi da 'ya 'yanshi asiri amma banda mace yanzun nan kana sata mata rai duniya zata ji su kuma 'yan uwan ta a ara a yafa kaji ana ta ambatan maza da munayen sunave sai a manta da cea ba duka aka taru aka zama daya ba kamar yadda suma matan ba duka ne ana gari ba to mudai maza da hakuri aka san muy dan an ya kansace mauna da hakuri kuwa gida zai gyaru Allah dai a kyauta don Allah Fahad a ringa hakuri da rayuwa su mata sune hatun mu da jin dadin mu kuma sune futu ninmu mafi tada hankali da na miji, dan wallahi duk yadda kuke da mae, duk ranar da tsiyarta ta tashi, in ta rikice maka sai ka rasa in da zaka sa kanka har gara a hadaka da kana nan yara ina ka daka musu tsawa sayi shiru kuma duk namijin da ya sakarwa mace ta rmashi to kowa ya shiga uku duk irin san da kukewa maceе kar ku bari ta raina ku duk inda ya dace kuyi mata fada kuyi mata. Amma fa Auwal yau sai dai kayi hakuri da tafiyar nan ka bari sai jibi saboda got e za'a fara taron limamai na kasa, domin mu shawo kan matsaloli da ake fuskanta musammam akan kaddamar da shari'ar nan gashi dai dama tun zuwan 37 LUBABАН alkur'ani mai girma sahria ta baiyana amma har yau kokarin kafuwar ta akeyi bil hakki da gaskiya, amma abin na neman ya gagaга. A nan ne kwakwalwar Auwal ta tsaya cak da aiki me kuma malam yake nufi? Ko dai yana nufin daurewa dansa baya nae kiri krirn. Dan me bazai masa fada ba akan ya hakura tunda dai yasan abinda ke wakana yana cikin tunaninne wannan maganar ta doki dodon kunnen Auwal wato malam ne yake ce da Fahad yau da yamma sai ya karasa mika Humaira tayi sallamar da sauran jama'a, har yana kara nanata cewar sallamar tana da amfani tunda anyi zaman mutunci da su, bai dace kawai suji ta ta fi ba, hakan bazai musu dadiba daga karshe ya gargadeshi da kada su dade don kada ya yarda sukai magariba. A gaskiya hakan ba karamin dadi ya hadda sawa Fahad a zuciyarsa ba ya kuma haifarwa da Auwal mummunan Gacin rai a zuciyarsa ba hakika ya tabbatarwa kansa mahaifin Fahad bashi da nivyar kwantanta adalci a al'amarin gaba daya dan hakIka yasan in har shi za'abawa damar

Chapter 3 of 6