Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
7 / 7
kuma ya kirata ya sanar da ita halin da ake ciki. To ita dai taja bakinta ta yi shiru ba ta sanar da shi abin da ke nan ba. Da direban ya zo, ta ce su tafi gidan Mummyn, sai da yamma za ta koma gida, don haka ta tafi gidan Mummy. Gaisawa kadai suka yi ta shiga dakinsu ta kwanta. Mick ke tananen nama a cikin, ba ta son kamshin zuciyarta tashi take yi. Har yamma tana kwance, Mummy ta kawo mata wannan ta kawo wancan, da kanta ta fahimci ciki ne ke wahalar da Naja'atu, sai tayi ma Allah godiya. Farin ciki fal da zuciyarta. Daddy ya kira yana tambayarta jikin? Ta ce, "Da sauki, sai dai tana gidan Mummy." Don haka da ya taso ya wuce gidan, har cikin dakin ya shiga inda take kwance, duk tayi laushi. Ya dube ta a sanyaye, itama RO Sirin Zuci. 4 Sa'adatu Saminu Kankia haka take kallon shi. Sai ya zauna kusa da ita, ya rike hannunta yana yi mata sannu. Ya ce, "Me suka ce yana damun ki, kinga yanda kika rame kuwa?" Ta lumshe ido tana jin nauyin shi, to kuma kamshin turaren shi ma sai ya sha mata kai, ta ji tana neman yin amai. Don haka ta yunkura ta tashi ta shiga kewaye, nan ma ya bi ta ya tsaya kawai yana kallon ta, zuciyarshi na raya mashi wani abu. Amai take kwararawa sosai, sai da ta gama suka dawo cikin dakin. Ya tsare ta da ido ya ce, "Naja'atu ciki gare ki ko?" Sai tayi murmushi tana jin kunya. Shima murmushin ya yi, ya ce, "Sun fadi maki haka?" Ta daga mashi kai. Ai murna kamar ya goya ta, ya rasa inda za ya saka kanshi don murna. Naja'atu tayi lamo tana jinshi, nauyi take ji sosai. Mummy ta shigo, ko kunya babu ya yi ma Mummy bayanin Naja'atu ciki ne da ita. Mummy murmushi kawai tayi, ta ce, "To Allah ya ba ta lafiya, saiu ka barta nan ta huta ko kwana biyu ne, kaga jikinta babu karfi, idan ta tafi can wa za ya kula da ita?" Maganar tayi ma Naja'atu dadi, amma shi Daddy bai ji dadi ba. Amma Mummy ta kafe cewa, sai ya barta. Babu yanda za ya yi, ya barta ya tafi gida. Amma da dare sai da ya dawo, nan ya yi hira, sai marairaice ma Naja'atun yake yi. Ita kuma ta san matsalar shi, har ta rinka jin tausayin shi. To sai dai babu yanda za tayi, ta san dai za ya takura, za ya yi rashin abubuwa da yawa da ta saba mashi dasu. Shima abin tla yake tunani ke nan. Da kyar ta lallabashi ya tafi, Mummy na kallon shi, sai dai tayi dariya ta ce, "Kayi ka gama." Kwananta biyu gidan, tana samun kulawa sosai wajen Mummy. Zainab ta zo duba ta tare da Doctor Sirrin Zuci.. 4 Saʼadatu Saminu Kankia Dariya ta rinka yi ma Naja'atu. Naja'atu ta ce, "Ki bi sannu, ai kara ni na sha miya, wa ya sani kila ma har kin dauka, wannan rawar jikin da naga Doctor yana yi." Zainab tayi dariya kawai. Ranar Daddy ya zo ya matsa sai ta shirya sun tafi gida. Naja'atu ta marairaice ba ta son tafiya. Amma ita Mummy, lura da halin da yake ciki ya sanya ta ce Naja'atu ta shirya su tafi. Ba ta son yi mata gardama, don haka ta shirya suka tafi. Tun daga lokacin Daddy ya dauki duk wani burinshi ya aza kan Naja'atu da cikinta, ya rinka ba ta kulawa ta musamman, abun ya tsone ma Farida ido, duk da cewa ba ta san abin da ke damun Naja'atu, ta dauki zafin kishi ta aza mata. Ko kallon ta taga Daddy ya yi, sai sunyi rigima. Don haka Naja'atun ta ce ya yi hakuri ta yafe mashi ranar aikin Farida ya daina shiga dakinta, ita za ta fito ta gaida shi. Don haka ba ta samun zama da shi sai ranakun aikinta. Wata daya, biyu, na uku cikin Naja'atu ya fito fili. Ai kuwa Farida ta dauki zafi ta dora ma ranta, ta rinka yi ma Daddy bala'i. Ya ce, "To ai ba laifin shi bane, haihuwa ta Allah ce. Itama idan Allah ya kawo za ta samu." Duk da haka dai ba ta sauko ba. Ya zuba mata ido, amma ya gargadı Naja'atu ta bi sannu kada ta yarda ta biye ma ta suyi rigima. Don haka babu ruwanta da harkar Farida, ko da yaushe tana cikin dakinta, sai in Daddyn yana gida ne ya ke matsa mata ta fita falo suyi hira. Yau da safe Daddy ya leko cikin dakin za ya tafi wajen aiki, Naja'atu na gyaran dakinta har da goge, ta juya tana gaida shi. Ya zuba mata ido, tayi kyau sosai, dan cikin ya zauna daf a jikinta, sai ya kara bude ta, ta Sirrin Zuci.. 4 Sa'adatu Saminu Kankja cika sosai. Ya ce, "Wai ke ba ki iya ki huta ko? Sai k rinka jajibu aiki." Tayi dariya ta ce, "Yana da kyau in rinka motsa jikina, haka nan cikin bai yi girman da za ya hanani aiki ba." Ya jinjina kai yana kallon ta, ya ce, "Za ni tafi, babu wani abu?" Ta ce, "Babu, sai ka dawo, Allah ya ba da sa'a." Ya yi murmushi ya yi mata godiya ya fice Da ta gama komi, tayi wanka ta fito kicin ta hada shayi ta zauna falo tana sha, ba ta kula Farida ba, itama ko kallon ta ba ta yi ba. Sai da ta kunna T.V tana kallon tashar Nolly Wood, sai ga Farida ta zo ta kashe. Naja'atu ta bi ta da ido kawai, sai ta tashi ta bar falon ta shige dakinta. Ita dai ta san ba yanda za'ayi tayi fada ita daya, dole sai da abokin yi. To ba za ta biye mata ba. Da rana ma ya dace tayi girkin abincin, amma ba ta yi ba. Naja'atu ta rinka jin yunwa, don haka ta fito ta shiga kicin, ta fere dankali dai-dai jikinta, sannan ta kunna gas, ta zuba mai ta dora. Ya dauki zafi ba ta kai ga zuba dankalin ba, sai ga Farida ta shigo cikin bala'i ta ce, "Amma kin san yau ranar aikina ce, don mi za ki shigo kicin? Ko kinga ni ina yi maki haka?" Naja'atu ta ce, "Na sani ranar aikin ki ce, amma ai baki bamu abin da za mu ci ba." Farida ta ce, "To ai ba aje ni aka yi ba don in dafa maki abinci ki ci, idan kin samu shi Daddyn yana lallaba ki don kina dauke da cikin shege! Ni ba ki isa in yi maki wannan wahalar ba." Naja'atu ta'sha mamaki, ta ce, "Ni ke dauke da cikin shege ko? Babu tsoro ta amsa, "Eh." Naja'atu ta се, "Na ji ina dauke da shege, ai ke banga kin dauki dan halak din ba, kin tsaya kina fama da bakin ciki." Farida tayi shewa ta ce, "Don nafi karfinshi ne, kema din ai 83 Sirrin Zuci.. 4 Sa'adatu Saminu Kankia rufa maki asiri ya yi ya aure ki, tunda dama tun can gida tare kuke, meye ban sani ba?" Maganar tayi ma Naja'atu ciwo, abun har ya kai ga 'yar kazafi? Nan fa suka rinka yinta babu dadi. Farida ta zo za ta sauke man da Naja'atu ta dora, ita kuma ta hana ta. Ba ta yi aune ba, sai dai taga ta dauki frying pan din, ta watso man da nufin ta konata. Dai-dai lokacin Daddy ya shigo kicin din, saboda ya shigo ya jiyo hayaniyarsu. Da sauri ya ture Naja'atu gefe daya, don haka ga baki daya man ya wanke mashi hannu da jiki. Ai kuwa ya saki wata irin kara, Naja'atu rayo kanshi da sauri cikin tashin hankali. Duk da dauriya irin ta da namiji, sai da ya kwalla. Sai dai ya gode ma Allah da ya sanya ba Naja'atun ce ta Kone ba. Da sauri Naja'atu ta dauko ruwan sanyi tana zuba mashi, amma kamar kara zafin ake yi. Farida kuwa sai tayi tsuru-tsuru, sai dai duk da haka ta girgiza da ganin abin da ya faru. Kishi bala'i ne, ita kam nata ya ma zama hauka. Da dai ta samu ta lallaba ta fice, sai ta shige dakinta ta kulle. A zatonta dukan ta Daddy za ya yi. Тo shi ta kanshi yake yi. Naja'atu duk ta rude, tayi nan tayi can, ta rasa abin da za tayi. Sai ta dauki waya ta kira Zainab, ta ce, "Zainab Doctor na gida?" Ta ce, "Eh, gaya nan bai dade da shigowa ba. Lafiya?" Ta ce, "Da sauki Zainab, ku-kawo mana dauki Daddy ne ya kone." Zainab tayi salati, ta ce, "Garin yaya?" Naja'atu ta ce, "Abun ba dadi; ku zo dai yana cikin hali." Ta jefar da wayar kan kujera ta komo kanshi tana yi mashi fifita, yanda taga yana shan wahala, har kuka tayi ta rinka yi mashi fifita, daga wannan tasa wancan. Cikin dan lokaci wuta ta tashi, ba ta son ta fadi ma Mummy hankalin ta RA Sirrin Zuci.. 4 Sa'adatu Saminu Kankia ya tashi. Ranar ta sha haushin rashin iya tukin ta, babu yanda Daddy bai yi da ita ba kan ta yarda ya koya mata, amma ta kiya. A ganin ta ba dole bane. Ashe ko dan lalura irin wannan ka koya. Yanzu ga shi kiri-kiri, tana gani yana shan wahala, amma ta gaza yin komi, da ta iya kau da yanzu suna asibiti. Sai da su Zainab suka iso, Khalid yaga jikin, don haka ya ce su tafi asibiti. Shi ya dauke su suka tafi. Zainab mamaki take yi, ta cc, "To wai garin yaya haka ta faru?" Naja'atu ta ce, "Farida ce, ni ta zo konawa, sai Allah ya kawo shi tana watsuwa ya ture ni sai ta same shi." Zainab ta rinka bala'i. Suna isa asibiti ta kira Mummy ta ce ta zo taga abin da Farida tayi. To itama yanda taga jikin Daddy abun ya bata mata, dama ita ke kange Farida, amma yau ta tsane ta kwata-kwata, abin da tayi rashin imani ne. Yanzu da ta samu Naja'atu yaya ke nan? To ba Mummy ba, duk wanda yaga jikin Daddy sai da ya yi Allah wadarai da mata masu irin halin Farida. Haka kawai zafin kishi ya sanya ka rabu da imani? Lallai dole ne mata su hankalta, kishi ba hauka bane, yanzu meye ranar irin wannan? Kwananshi biyar asibiti, Farida ba ta zo ba. Ko da yake ta san ba ta da gaskiya, tana kiran layinshi, idan yaga ita ce baya dauka. Amma Mama ta zo duba shi sau biyu, har kuka tayi da taga abin-da diyar ta tayi ma mijinta, ta rinka tsine mata. Sai da Mummy ta ba ta hakuri, mutane da dama suna fadin raayinsu akan faruwar wannan abu. Amma shi Daddy jinsu kadai yake yi, a cikin zuciyarshi ya gama daukar matakin da ya dace da ita, lokaci kadai yake jira. Sai da ya yi sati daya, sannan aka sallame shi ya koma gida. 85 Sirrin Züci.. 4 Sa'adatu Saminu Kankia Basu tarda Farida ba ta fita yawon tga. Naja'atu ta shigab ta gyara mashi dakinshi itama ta gyara nata, sannan tayi wanka ta dawo falo inda Daddyn yake kwance, Ya dube ta ya yi murmushi yana kara jin kaunar a zuciyarshi, har tausayin ta yake ji, ba ta da lokacin kanta sai nashi. Kwana biyu da ya kone, yanda baya iya yin barci haka itama ba ta runtsawa. Ya mika mata hannu ta zauna kusa da shi, ya ce, "Wai ke ba ki iya zama ki huta kina wahalar mani da Baby da yawa?" Ya sanya hannu yana shafa cikin, sai ta rike hannun tana dariya, ta ce, "Wa ya bani hutu, maigida ba lafiya." Ya yi murmushi ya janyo ta cikin jikinshi yana jin dadi marar misaltuwa. Naja'atu mace ce ta gari, ta gama mamaye zuciyarshi da kyawawan halinta. A hankali ta shigo gidan, jikinta duk ya yi sanyi, ta raina gaskiya, amma da yake ba ta san kunya ba, sai ta shiga washe baki za ta cika shi da dumi. Ya daka mata tsawa, dole ta tsaya. Ya ce, "Ina kika fito yanzu?" Tayi shiru. Ya ce, "To koma, daga yau ki dauka baki san wani Daddy ba, na sake ki." Naja'atu ta bude baki cikin tashin hankali za tayi maganas, ya dora mata danyatsa akan lebe, tayi shiru tana tararrabin abun. Da ya yi hakuri ya rabu da ita, wata rana sai ta gyara. Bai sake magana ba ya ja hannun ta suka shige daki. Abun bai yi ma Naja'atu dadi ba, amma Daddy ya hana ta magana. Mummy ma da ta ji tayi fada sosai, ta ce sai a dawo da na. Yayin da shi kuwa ya yi rantsuwa akarn ba shi ba Farida har abada. Yanda tayi din nan, idan ta samu makasar Naja'atu za ta iya kashe ta. To haka ake kishi? Zaman lafiya da kwanciyar hankali ya samu cikin gidan Daddy, ya zama dan lelen Naja'atu, duk da tsohon 86 Sirrin Zuci.. 4 Sa'udatu Saminu Kankia cikin ta ba ta gajiya da yin hidimomin shi. Mummy kau dadi take ji, sai sanya albarka take yi. Rayuwarsu gwanin ban sha'awa, akwai fahimta sosai tsakaninsu. Cikin ikon Allah Naja'atu ta sauka lafiya, an samu da namiji. Tun a asibiti Daddy ya fara kiranshi Usman, watau sunan mahaifinsu, ya yi Daddy junior ke nan. Yaron kyakkyawa kato da shi kamarsu daya da Daddy. Zainab ta rinka santin shi, Naja'atu ta ce, "Idan kin sauka kema Allah ya baki kamar shi." Ta сc, "Ba ki sani ba, shi Doctor ya fi son Baby girl, har scamng ya sanya aka yi mani, kuma sun ce me yiwuwa ma in haifi 'yan biyu duk mata." Naja'atu ta ce, "To Allah ya raba lafiya." An sha shagalin suna lafiya. Suka ci gaba da renon junior. Da ta gama wanka Daddy ya kaistu Katsina, satinsu biyu, suka gaisa da 'yan uwa. Akwai ci gaba sosai ta bangaren s Malan, ya yi ritaya an ba shi kudin sallamar aiki, đơn haka ya ce Hajji za ya je ya sauke farali. To da Daddy ya ji haka, sai ya ce, "Itama Inna ta shirya sai su tafi tare, ya biya mata." Abun ya yi masu. Daddy ya co, Tta kurna Naja'atu sai ta yaye junior sai su tafi." Ko da yaushe Naja'atu kanyi alfahari da auren ta da Daddy, ba ta taba yin nadamar aurensu ba, kullum ci gaba suke samu sun hada kansu, zamansu lafiya. Babu irm naci da bin diddigi da Farida ba ta yi ba, dơn ya mei da ita, amma ya ce sam ba za ya yiwu ba. Ga shi zamim gidan nasu babu dadi, Mama ta juya mata baya fada take yi mata sosai. Ga shi auren ya fi samuwa, ko yam samarin da take dasu da, yanzu duk sun guje. Karatun ma ba ta ci jarabawa ba, bà tà komi sai yawon bin gidajen kawaye. Idan akayi buki ana can. Wannan shi ne Sirrin Zuci.. Sa'adatu Saminu Kankia santatta, don Allah 'yan uwa mata mu rinka kushe kishin mu, wani lokacin zafin kishi, shi yake kaimu ga aikata aikin dana sani. Allah ya kyauta. Zainab ta haihu, ta samu 'yan matanta biyu, kamarsu daya da babansu masu kyau. Naja'atu ta rinka santin su, Daddy ya cc, "Kiyi addu'a next time kema Allah ya baki irin su." Dariya kawai tayi. Sun ci gaba da zaman lafiya da kwanciyar hankali, da ci gaban rayuwa. Da shckara ta zagayo, Naja'atu da Daddy, har da su Zainab suka tafi kasa mai tşarki suka sauke farali. Shekara biyu tsakani ta sake haihuwar 'ya mace, aka sanya mata sunan Mummy, Halimatu Sa'adiya. Itama Mummy suke kiran ta, kamarsu daya da Naja'atu. Daddy ya hada kan iyalinshi yana nuna masu so, ko da yaushe yana alfahari da Naja'atu, ta zama 'yar halak. Good life irin wadda yake so. - Allah yasa sauran mata su dauki halaye na gari, su rinka hakuri da juriya irin na Naja'atu. Masha Allahu Sai mun hadu cikin sabon littafi na gaba. WANI AL'AMARI insha Allahu Mai Kaunar ku -AUNTY UWANIN KANKIA An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 7 of 7