Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 7
ta tafi da dare ya iso gidan. Maigadi ya iso in da ya tsaya su ka gaisa, sannan ya je ya kira Naja'atu yasan dai wajanta ya ke zuwa. Su na zaune falo ya fadi sakon sai ta yi murmushi ta taso ta fito, ya na zaune cikin mota su ka gaisa ya yi murmushi ya ce "Ga ni na dawo, kuma na yarda da Sirrin Zuci.. 4 Sa'adatu Saminu Kankia shawararki ina fatan kinyi ma ta maganar?" Sai ta yi dariya ta ce "Ina zuwa." Ta koma cikin gida ta kamo hannun Zainab, ta na biye da ita har wajenshi, ta ce "o ga ta na kawo maka, kasan an ce waka a bakin mai ita ta fi dadi." Zainab ta zuba mata ido kamar zata yi magana, amma sai ta gaza cewa komi, a hankali ta sauke kwayar idonta akanshi, ta ji wani irin abu ya daki zuciyarta, sai ta sarda kai tana murmushi, Naja'atu ta dube shi sai ta yi dariya, ta saki hannun Zainab ta koma cikin gida. Su ka yi shiru su na jin nauyin juna, Zainab ta jingina da motar ta daga kai ta na kallon taurari, gabaki daya Khalid ya canza mata salon tunani da kallon da ta ga ya na yi mata, to shima kwarjinin yarinyar ya cika wajen har ya gaza ce mata komi, sai da ya lura ta saki jiki sosai, a kalla ta gama duk wani nazarin da ya ce ta yi. Sannan ya yi gyaran murya, ya ce "To ni Zainab na ma rasa ta ina zani fara, naso ace Naja'atu ta yi maki bayanin komi, kin ga da yanzu amsarki kawai zan ji to ta tattara aikin duka ta dora mani. Amma na sani zuwa yanzu da muke tsaye da ke za ki iya fahimtar wani abu a tattare da ni, kinga dai yarda tafiyar nan ta taho kuma kina sane da komi, naso Naja'atu sai dai ga yarda abun ya kasance, ta zabi wani a kaina, wanda ni ban ga laifin ta ba, so daban ne, don haka na sanar da ita cewa ta yi maki magana, idan kin amince mani in karkato akalar kaunata a gare ki, me yiwuwa haka ta ta cimma ruwa, kada kiji komi ki fadi mani gaskiyar abin da ke cikin zuciyarki, kin amince. Zainab ta ji wani irin farin ciki fal da zuciyarta, samun miji irin Likitan ba karamin alkairi ba ne, ta yarda da shi da halayyarshi, don haka ba ta tsaya Simin Zuci.. 4 Saʼadatu Saminu Kankia wahalar da kanta ba, ta amince mashi dari bisa dari, mamaki ya yi sosai bai yi tsammanin zaya same ta haka da sauki ba, a karshe ya yi ma Allah godiya, wani hanin ga Allah baiwa ne, cikin natsuwa ya ci gaba da yi ma ta bayanin kanshi da kuma manufarshi akanta, amma ya се zaya ba da lokaci yanda za su fahimci juna sosai, ta yarda ba za su rinka fuskantar matsala ba, a zaman auren su. Zainab ta amince, don haka suka saki jiki suna hira. Can cikin gida kuma, Mummy ta fito daga cikin daki, Naja'atu ce kadai zaune falon tana kallo. Ta zauna tana kallon Naja'atun, ta ce, "Ina Zainab din kuma?" Naja'atu tayi murmushi ta ce, "Tayi bako ne tana waje." Mummy ta ce, "Bako daga ina kuma?" Tayi dariya ta ce, "Mummy Khalid ne ya zo wajen ta." Ta ji maganar kamar daga sama, ta ce, "Bawan Allah, bai yi fushi ba dai? Ina son yaron nan, yana da hankali. Amma kiri-kiri kin kishi." Naja'atu tayi dariya ta ce, "Nifa Mummy ba kinshi nayi ba, Allah kuwa ina tausayin Daddy ne, yana bukatar kulawa. Kuma ba ga shi ya samu Zainab ba." Mummy ta ce, "Au shirin ku ke nan?" Naja'atu ta се, "Mummy za'a ba shi ko?" Tayi dariya ta ce, "Me za ya hana, idan dai ita tana so? Allah dai ya shige mana gaba." Gaskiya Mummy, ta ji dadin wannan lamari, tayi ma Allah godiya. Don haka da Zainab ta shigo ta hadasu su duka ta rinka yi masu nasiha. Sannan ta tabbatar masu da cewa, in dai ta samu yanda take so, nan da wata uku, su duka aurar dasu za tayi. Khalid da kanshi ya mai da Zainab makaranta. Yayin da suka bude sabon babin soyayya, abun har mamaki yake ba Naja'atu, yanda suke tafiyar da 55 Sirrin Zuci.. 4 Sa'adatu Saminu Kankia al'amuransu, sai kayi tsammanin sun dade tare. Yanzu hankalin ta ya kwanta, ba ta jin tsoron komi. Amma shi Daddy da aka fadi mashi wannan tsarin, cewa ya yi shi sam ba za ya iya jira sai nan da wata uku ba. Don haka ya matasa ma Mummy sai da ta je Katsinar da kanta, gidansu Naja'atu. Malam ya yi farin ciki, ya yi godiyar Allah da fatan alkairi. Don haka ya ce, "Babu komi, Naja'tu tasu ce, don haka duk lokacin da suka ga ya yi masu, to sannan za'ayi." Daddy ya ji dadi, da kanshi ya debi sati hudu kacal. Ya ce, "Lokacin yake so." Da suka dawo Mummy ta shirya kudin neman aure da sauran kayan sanya buki aka kai gidan su Naja'atu. Cikin kwanaki magana ta kankama. Wannan karon Daddy da kanshi ya ke hada lefenshi, sayayyar har da marasa amfani. Amma idanuwan shi sun rufe, za ya iya yin komi saboda Naja'atu. Mummy dariya take yi mashi, al'amarin maza sai su. To itama Naja'atun, takan yi mashi korafi kan cea ya rinka yi abubuwa da kula, kada ya wahalar da kanshi. Amma ina, ya yi nisa baya jin kira. Itama Mummy ta bangaren ta, ta ce ma iyayen Naja'atu, ba ta bukatar komi, duk abin da ake yi ta dauka, ita ce za tayi. Haka nan Katsina za su taho ga baki daya ayi buki a gama, su ataho da amaryarsu. Ya rage saura sati biyu, Naja'atu ta ce, "Tana son ta fara tafiya Katsina saboda shirye-shiryen ta." Mummy ta ce, "Shirin me za ki yi'Naja'atu? kada fa ki je ki dora masu hidima? Kina gbani dai duk abin da za ki bukata nayi. To me kuma za ku nema?" Ta ce, "Allah kuwa Mummy ba saboda haka za ni tafi ba, ina son in dan samu lokaci in zauna dasu ne, ba wai da na je ba a shiga 54 Sirrin Zuci.. 4 Sa'adatu Saminu Kankia buki." Mummy ta ce, "Shi ke nan, sai ki shirya zuwa jibi sai Babangida ya kaiki, gobe in Allah ya kaimu za mu je Sahad Store ki za bi kayan kicin dinki da kanki. Na san na ture ki, sai sauran hidimomi." Da kyar da Daddy ya yarda da tsarinta, wai sai dai ta jira su tafi tare. Sai da Mummy ta sanya baki, sannan ya amincc. Da ya koma gida, Farida na zaunc cikin falo ko kallon arziki ba ta yi mashi ba, babu jituwa sosai tsakaninsu cikin kwanakin, tun ranar da ya zo bai same ta gida ba, wai sun je unguwa tare da wata kawarta. Da ta dawo ya rufe ta da bala'i, itama ta rufe idc, suka yi ta babu dadi. Tun daga lokacin ta tsiri fushi, shima bai damu ba, ya ci gaba da shareta. To amma yau ganin komi yana karatolwa, har yanzu ba ta san abin da ake ciki ba. Sai ya ga ya dace su zauna ya sanar da ita, su tsara yanda abubuwa za su kasance. Don haka ya zo ya zauna ya dube ta, itama kallon shi take yi cike da tsana. Ta sarı dai inda ya fito, yana like da Naja'atu, kuma kallon, shi kawai take yi ta ga yanda za'ayi ayi auren. Ko itar da suka yi ranar wajen wani boka ta je, kuma ya tabbatar mata da cewa babu wannan maganar, ta je ta kwantar da hankalin ta. Duk abubuwan da ya ba ta tayi amfani dasu tayi. Hatta karkashin gadonshi, akwai layoyi, haka kowace kusurfwa an daga kafet an saka laya, hayaki da sauransy duk tayi. Abu daya ya rage mata, shima dama take jira. Ya zuba mata ido fuskarshi babu walwala ya ce, "Kawo mani ruwa in sha." Ba tayi musu ba, ta je ta dauko da kofi ta kawo ta aje gabanshi, ta koma ta zauna. Ya fiddo Paracetamol cikin aljihu ya zuba ruwan ya sha, sannan ya gyara zama yana kallon ta ya ce, "Magana 57 Sirrin Zuci 4 Sa adatu Saminu Kánkia nake son muyi, kina da lokacin saurarena ko kuwa?" Tа yatsuna fuska tana kallon wani sashin ta ce,, "Ina saurare." Ya ce, "Magana ta da Najalatu ce, kuma dama na fadi maki auren ta zaniyi. Do haka maganar cc ta taso, duka bai fi sati biyu ya ragbe ba Don haka ki samu lokaci ki dadi mani dukkan bukatunn ki, da sauran abubuwan da kikc bukata, saboda Katsina za'ayi bukin, sai dai faga baya nan zata dawo kunzaunantare. Don haka, don Allah Farida, ki nutsu mu hada kanmu, mu zauna lafiya, ba ni son rashin jituwa irin haka tana shiga tsakaninmu." Wani irin duhu ta ji yana gitta mata ido, kanta yana sarfawa, ga baki daya bakinta ya mutu, ta kasa ce.mashi komi. Sai kawai ta mike ta bar falon Yabi ta da kallo yana cizon lebe, sai ya girgiza kai. Idan da sabo ya saba da rainin wayun Farida; amma lokacii nee zas ya yi maganin ta. Cikin daki ta fada kan gado tana kuka, gani take yi wulakanta ta kawai Daddy yake somyi don baya Kaunar ta. Ba ta ga duk irin abubuwan da take yi mashi ba na rashin kyautatawa. Hankalinta ya tashi sosai, idan akwai abin da ta tsana a rayuwarta, bai wuces Naja'atu. ba Yarinyar ta tsaya mata a rai. Kwana tayi tana tunanin abun yi. Don haka washegari yana fita, itama ta fita, ta san Mama ba ta gida, ta fita wajen-aiki: Don haka kai tsaye wajen aikin ta nufa. Mama na cikin ofis taз kwankwasa ta shiga. Ganin yanayin da Faridar takecciki ya ba ta mamaki, ta zuba mata ido ta cikin farin gilashin, sai ta sanya hannu ta cire gilashin tana kallon taş taace, "Ke kuma daga ina haka?" Farida tga ja kujera ta zauna, zuciyarta ta kare, sai 58 Sirrin Zuci.. 4 Sa'adatu Saminu Kankia ta fasa mata kuka. Mama ta girgiza kai, har ta fara gajiya da matsalar Farida, duk sanda ta zo da abin da za ta zo da shi. Ta kasa kwantar da hankali ta daidaita zamantakcwar ta da mijin ta, abin da ta kasa fahimta ke nan. Ita rayuwar aurc, halin mutum ke ceton shi, da za ta nutsu su fahimci juna, zamansu za ya yi kyau, amma fitinar ta, ta isa. Ta dube ta, ta cc, "Me kuma ya faru?" Ta cc, "Wai Mama, Daddy aurc za ya yi nan da sati biyu." Mama tayi murmushi ta cc, "To ya rasa? Ai na fadi maki, amma kin ki, tunda kin zama sakarya, kin kasa sama mashi kwanciyar hankali sai ya ki yin auren shi? Munyi waya da Hajiya Halima, tayi mani bayanin komi, don haka matsala ke ta duba yanzu. Wallahi kina zaune za ta shigo ta shiga gaban ki, ai ya yi hakuri dake. Kuma ni babu wani abun da zan iya yi maki. Duk wani gyaran da kike so yana nan a hannun ki, ai Daddy bai kiki ba, kuma ko gober yana sonki. To Farida, sai ya zauna yai ta wahala kanki, ke ba ki san ki kyautata mashi ba?" Kuka ta rinka yi. Mama ta ce, "Da gangan, yanzu ke ko kunya ba ki ji, duka wata nawa ke nan da yin aurem ku? Amma ke, ke nan kullum jan fitina, daga wannan sai wancan, kina biye ma kawaye. Ina gaya maki, su za su kaiki su baroki, kina ji kina gani za su kashe maki aure. Kuma wallahi ni babu abin da za ni yì maki, kwanciyar hankali daya, ko koma dakin ki, ki kama mijin ki ku zauna'lafiya. Ai ke kika ba shi damar yin auren, idan da kin tsaya kina kyautata mashi yayа za'ayi ya samu idon kallon wata diya mace? To nan ma dai babu taushin, don haka da ta fito ba ta zame ko'ina ba, sai gidansu Dije. Ta ja ta suka fice, sai Yanye gidan Sirrin Zuci.. 4 Sa 'adatu Saminu Kankia malaminsu. Ta fadi mashi komi. Ya cc ta kwantar da hankalin ta, ta dauka kamar an fasa auren ne. Idan ma ba'a yi sannu ba, za ya iya haukata yarinyar duka a huta, tunda dai au ba za ya auri mahaukaciya ba. Sai lokacin hankalin ta ya kwanta, ta balle jikka ta fiddo kudi ta ba shi. Ya ba ta wani magani ya ce ta je ta barbada kan shimfidar da Daddy yake kwanciya, za ta ga abin da za ya biyo baya. Haka nan ko da wasa kada ta kuskura ta sake ta dame shi maganar auri, da kanshi za ya zo ya се ya fasa. Suka taho cikin farin ciki. Lokacin Daddy ya koma gida, yana kwance falo ya gama cin abinci. Take away yayo a Restaurent. Ta shigoko kallon ta bai yi ba, ta wuce daki. Matsala daya ce, tuni sun raba dakin kwana, kuma kulle dakin shi yake yi idan za ya fita. Don haka babu hanyar da za ta shiga dakinshi. Ba ta ga fuska ba, balle ta bullo mashi da wani abu. Ya jima kwance falo, sannan ya shiga daki. Ta kasa kunne tana saurare sai da ta ji shigarshi kewaye. Tayi sanda ta shiga, cikin sauri ta aiwatar da abin da boka ya sanya ta, ta fito bai sani ba. Amma kuma kamar yana duba, lokacin da za ya kwanta da daddare, sai ya kwashe zanin gadon ya saka cikin kayan wanki ya shimfida wani ya yi kwanciyarshi. Ita kau duk a zatonta komi ya yi. Da safe tana kwance ya gama shirin shiya fita, saboda ranar Naja'atu za ta tafi Katsina. Ya biyata gida ya sallame ta, sannan ya wuce wajen aiki. Tunda ta tafi, shima ya fara shirin shi. Mummy ta tura lefen Katsina aka kai gidansu Naja'atu, kowa ya yaba ana ta sanya albarka. Daddy ya yi rawar gani. Nan kuma ana saura sati daya, itama Mummy ta tafi Katsinar, yayin da 10 Sirrin Zuci.. 4 Saʼadatu Saminu Kankia Daddy ya ce sai ranar laraba za ya taho. To ita kama Zainab jarabawa suke yi, sai ranar juma'a Khalid za ya biya ya dauke ta su isa Katsinar. Al'amuran buki sun kankama, Naja'atu ana ta hidima, ko da yaushe suna tare da Daddy a waya, yana fadi mata yanda abubuwa suke tafiya. Ranar talata, Aunty A'isha da kawarta Umaima, suka je gidan Daddy suka tsara ma Naja'atu dakinta, falo karami da daki daya, sai kewaye a ciki. Farida ba ta gidan. don haka har suka yi aikinsu suka gama ba ta nan. Washegari tare da Daddy za su taho Katsinar. Da dare ya shiga gidan, Farida na cikin daki. Ya zube kayan da ya shiga dasu bisa kujera, ya je ya kwankwasa mata kofa, sannan ya dawo ya zauna. Jim kadan ta fito, sanye da wando baki da riga body hug. A kule take saboda yaron da ke yi masu wanki ya sanar da ita an kawo kayan amarya, kuma ta ga alama. Ta tsaya jikin kujera ba ta ce komi ba. Ya dube ta, sai ya yi dariya, yanzu ta daina bata mashi rai. Ya ce, "Zo ki zauna mana, magana za muyi." Ta се, "Ba sai na zauna ba ina jinka." Ya jinjina kai ya ce, "To ga kayanan nayi karambani na sayo maki tunda na ce ki fada kin ki fadi, kuma gobe in Allah ya za ni tafi Katsina. Idan kuma za ki je, to ki shirya mu tafi, sai an gama komi za mu dawo." Ta zumburi baki ta ce, "Idan ka tafi kada ka dawo ka gani idan za ni fasa rayuwa." Ya yi murmushi ya ce, "Ni kuma me za ya sanya in zauna can? Sai dar ina son ki fahimci wani abu guda, wadannan abubuwan da kike yi ba za su sanya in ji tsoronki ba, sai ma rage ma kanki kima kike yi. Amma tunda kina ganin haka yha fiye maki, Allah ya ba ki sa'a. Wata rana ko an ce kiyi, ba za 61 Sirrin Zuci.. 4 Sa ʼadatu Saminu Kankia kiyi ba." Ya mike ya shige cikin daki ya barta nan tsaye. Sai ta zube kan kujera, zarginta guda, Naja'atu asiri tayi ma Daddy, don haka ya makance irin haka a kanta. Da safe har ya gama shirinshi tana cikin daki, ya fidda jikkar shi ya kai cikin mota. Sannan ya dawo ya kwankwasa kofarta ya bude ya shiga, ko'ina a hargitse, dakin ma ba ta iya zama ta gyara. Shigarshi ta tada ta, ta bude ido tana kallonshi. Sai ta ja tsoki ta mai da kai ta kwantga. Ya tsaya kanta hannayen shi zube cikin aljihu, sai kuma ya daga kafada cikin halin ko in kula, ya fiddo kudi ya jefa kusa da ita, ya ce, "Na tafi, sai ranar talata." Ya juya za ya tafi. Ai kuwa tayi tsalle ta diro daga kan gadin, sai dai ya ji ta fizge rigar shi ta baya. Та сe, "Wallahi ba za ka fita gidannan ba, sai ka sake ni. Mugu maci amana, butulu!" Ranshi ya yi bala'in baci, ba ta san yana kyaleta bane saboda Mummy ta ce kada ya kuskura ya yi fada da ita, duk abin da za tayi ya rabu da ita, za ta daina. Amma wannan karon ta kaishi iya wuya. A fusace ya fizge hannunta daga jikin shi ta fada kan gadi, sai kuma ta sake yunkurawa ta nufo shi, Wannan karon ya sharara mata mari, dole ta saduda, ta dafe fuska tana nadama. Bai kulata ba, ya sanyakai ya fice. Ko garin Abuja bai bari ba, itama tayi shiri sai gida. Karya da gaskiya ta shirya ta fadi ma Mama, sai rantsuwa take yi ta ce ba za ta koma gidan ba. Shi kuwa Daddy hankalin shi kwance ya biya ya dauki A'isha suka nufi Katsina. Hidimar buki tana tafiya lafrya, а tsarin Naja'atu, ba ta yi niyyar yin wata bidi'a ba, amma Daddy ya kafe kan cewa bai yarda ba, a ganin shi, Naja'atun za ta ga bai yi murna da aurenta ba, ganin yanda aka yi hidima lokacin Farida. To ita wannan bai 62 Sirrin Zuci.. 4 Saʼadatu Saminu Kankia dame ta ba, ta ce ta yafe. Duk da haka Mummy ta shirya masu walimar cin abincin dare, nan ciki gidan ta. Ranar juma'a, 'yan uwa da abokan arzuka suka hadu aka tayasu murna, Daddy ji yake kamar ya lashe ta, tayi kyau sosai, ga kumshi ya tsaru kan fatarta, tana wani irin kamshi na musamman, na Humra 'yar Maiduguri. Wannan kuma duk shirin Mummy ne, ta gama kimtsa diyarta, don haka tunda ya iso, ya ida rikicewa, duk inda ta sanya kafa yana biye. Ranar juma'ar da wuri Zainab ta iso tare da Khalid, har gidansu Naja'atu ya je ya gaida malan, ya yi mashi kyautar manyan riguna na farar shadda har da turare da kudade masu yawa. Malan ya yi godiya, ya sanya albarka, da fatan alkairi. Hidimar tayi armashi, basu zafafa abubuwan ba, anyi komi cikin nutsuwa, aka tashi cikin farin ciki. Mummy kau murna kamar ta zuba ruwa kasa ta sha, sai da godiyar Allah take yi. Itama Naja'atu, kasa yi mata godiya tayi, sai kuka tayi. Hajiya ta kwabe ta, ta ce ba ta so, da ita da Daddy duk daya, ta je ta rike mijinta da kyau. Allah ya basu zaman lafiya." Washegari karfe sha daya da rabi, aka daura aurensy a kofar gidansu Naja'atu. Kowa ka gani cikin farin ciki. Naja'atu sai godiyar Allah, har kuka tayi don farin ciki. Kaunar Daddy wani sirrin zuciyarta ne, ita kanta ba ta san dalilin da yasa take sonshi ba. Kaunarsu daga Allah ce, tayi ma Allah godiya da ya mallaka mata abin sonta, tare da addu'ar Allah ya basu zama lafiya, ya basu ikon rike juna bisa gaskiya da rikon amana, ya kau da fitina. Ranar da daddare aka dauke ta daga gidansu zuwa gidan Hajiya, nan za ta zauna zuwa ranar talata da za su tafi Abuja. Daidai gwargwado anyi shagali, amma Naja'atu ta 63 Sirrin Zuci.. 4 Sa'adatu Saminu Kankia ture duk watga bidi'a, kiri-kiri ta soke Dinner Party da Daddy ya tsara za'ayi. Zainab ta ji haushin ta, kamar ta doke tga. Wai ta cika son miji, don kada ya sha wahala. To ita kam wani ra'ayinta ne na daban, ba ta da murnar da ta wuce tayi ma Allah godiya. A 6angaren Malan, ya yi rawar gani, dai-dai karfinshi ya yi ma ango sallama da kudi dubu dari da buhunan abinci. Haka nan itama Inna ta ba da mai da sauran kayan gara. Da yayar Hajiya Halima ta karbi kayan cewa tayi, "Aikinta ne, ita ce ya dace tayi duk wadannan." An gama buki lafiya, ana ta sanya albarka, kowa ya kama gaban shi. Ita Zainab ranar litinin ta bi Khalid ya mai da ta makaranta ya wuce Abuja. Sai su kadai a gidan, Daddy ya rinka wayau, yana son ya kebe da amaryarshi. Amma fir Naja'atu ta ki yarda, ba ta yarda ko waya ta hadasu. Haka nan da dare tana rugan kowa kwanciya, kullum sai ya yi matga korafi ta waya, ba ta cewa komi sai dai tayi dariya. Basu bar Katsina ba, sai ranar laraba. Su suka fara tafiya, sannan Mummy ta bi bayansu. Bisa hanya ya rufe gilas ruf ya kunna A.C, ga kamshi ya cika motar. Naja'atu ta haye bisa sit barci yana dan fizgarta, ga shi Daddy yana matsa mata da mayen kallon shi. Sai ta rinka jin sanyi, don haka ta makure kanta. Tana jin shi yana murza 'yan yatsunta da suka sh kumshin lalle ya kama ya yi ja sosai. Haka nan zabban gwal da ta zuba, sun kara ma dogayen 'yan yatsun kyau. Tana jin shi ta yi shiru ta rabu da shi, ta san tsokana ce. Rana ta tafi za ta fadi, suka shigba garin Abuja, ya juya yana kallon ta ya ce, "Ba za mu biya gidan Mummy ba fa." Ta tsura mashi ido duk ta marairaice ta ce, "Nayi tsammanin za ka bari zuwa gobe, ko Aunty A'isha sai ta rakoni." Ya yi 64 Sirmin Zuci.. 4 Sa'adatu Saminu Kankia murmushi yana girgiza kai, sai ya sanya hannaye duka biyu ya dafe sitiyarin motar, sai da ya yi tafiy tsawo, Sannan ya ce, "Kin cika son kanki Naja'atu, ya ce ki tausaya mani, kwana biyu kina bani wahala, kiy hakuri mu tafi gida, idan an kwana biyu za ni kaiki wajen Mummyn." a Ya dan zuba mata ido, sai ya ba ta tausayi, tayi murmushi ta jinjina mashi kai. Don haka kai tsaye ya nufi gidanshi da ita. Bai yi mamaki ba da ya tarda gidan a rufe, ya san Faridar fushi take yi. Ya nemi layinta rufe yake, duk da ya tafi ba ta saurare shi ba. Suka fito tare ya yi amfani da makullinshi ya bude kofar suka shigba. Gidan ya danyi kura, hakan ya tabbatar mashi cewa, ta kwana biyu ba ta gidan, ba wai fita tayi ba. Ya je ya bude ma Naja'atu dakinta ta shiga, shi kuma ya je yana kwasu kayansu daga cikin mota. Naja'atu ta shigba cikin dakin, sai ta tsaya kawai tana mamakin abin da Mummy tayi mata. Ga baki daya setin'yan italiya ne, ko ba a fada ba, ta san an kashe naira. Kauna ce ko mai, sai kawai ta ji idanuwanta sun ciko hawaye. Ta zauna shiru tana gode ma Allah, tare da yi ma Mummy addu'a. Cikin yanayin Daddy ya riske ta, ya aje akwatin ya iso kanta yana kallon ta, ya c e, "Meke faruwa kuma?" Ta ce, "Daddy kalla ka ga abin da Mummy tayì mani, ko ita ce ta haifeni sai haka, da me za ni saka mata?" Ya yi murmushi ya janyota cikin jikinshi ya сe, "Kаada ki samu damuwa, Mummy taña kaunar ki Naja, fatana Allah ya bamu zaman lafiya da zuri'a mai albarka, kada ki damu." Ta ji yana neman zarcewa, sai ta janye jikinta ta shiga kewaye. Daddy daban ne, kaunar shi wata abu ce mai muhimmanci a 65 Sirrin Zuci.. 4 Sa'adatu Saminu Kankia cikin zuciyarta. Bayan sunyi sallah, ya fita sawo masu kaji gashin inji da lemo da madara fresh milk, ya kawo suka ci. Tana son ta tambaye shi Farida, amma ta rabu dashi. To shima rashinta a gidan ya tsaya mashi cikin zuciya, har Karfe tara suna hira ba ta dawo ba. Ta kasa daurewa ta ce, "Daddy banga Farida ba?" Shima ya zuba mata ido, sai ya rasa abin da za ya ce mata, baya son ya fadi mata wata matsala da ta shafi Farida, hakan ka iya janyo rashin fahimta tsakaninsu. Don haka ya ja bakinshi ya yi shiru. Itama da ta fahimci akwai wani abu a kasa, sai ba ta ja binciken ta ba, ta saki maganar suka ci gaba da hira. Karfe goma ta shiga daki, tayi wanka ta sanya kayan barci, riga da wando masu santsi jajaye. Ta tufke gashinta, ta sanya turare masu sanyin kmashi da humra, ta kara ma dakin kamshin air freshner. Sai ta kwanta tana karanto addu'o'i. Daddy ya murda kofa ya shigo, shima ya yi shiri da kayan barci cotton zalla masu taushi farare, yana rike da robar madara fresh milk. Ya zauna bakin yana jefarta da mayataccen kallonshi, sai ta ji zazzabi yana shirin lullubeta, ta kara makure kanta kan gado. Yayin da wani tunani ya dira a zuciyarta, sai ta lumshe ido a hankali, tana tuno abubuwa da dama. Ya aje robar madarar gefe guda, ya shiga kewaye, ya dauro alwala, ya dawo ya tada ta, ta je tayi alwala ta dawo, suka yi shirin yin nafila raka'a biyu, suna masu neman yardar Allah a cikin zamansu. Ta gaji sosai, ta koma kan gado ta kwanta, yana kallon ta ya ji wani abu ya daki zuciyar shi. Ya yi saurin shafa addu'a ya taso ya dawo kusa da ita, ya zuba mata madara, ya ba ta tana sha, ya rinka janta da hira yana yi 66 Sirrin Zuci.. 4 Saʼadatu Saminu Kankia mata nasiha dangane da zaman su. Ya ci gaba da janta da hira, yana ba ta labarai masu dadi na ban dariya. Don haka ya samu kanta yanda yake si, suka yi barci mai dadi, cikin farin ciki da annashuwa. Da safe barci yake yi sosai, Naja'atu ta janye jikinta ta shiga kewaye tayi wanka da ruwa mai dumi, ta dawo daki tayi shiri, cikin wata atamfa 'yar super fara, siket da riga

Chapter 5 of 7