Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 7
har cikin ranta ba ta son zamanta gidan Daddy yarda taso, Mummy ta barta ta tafi Katsina ta zauna can sai ta dawo, to ta hana ta ce ta bari idan ta dawo sun je tare. Don haka ba ta da zabi sai yarda aka yi da ita, amma alkawari ne ta daukar ma kanta, komi Farida zata yi, ba zata biye ma ta su yi rigima ba, insha Allahu lafiya za su rabu. Da su ka isa, Daddy ya na gaba su na biye da shi har saman benen, hawa na uku suke ya murda kofar ya shiga su ka bi bayanshi, Farida na kwance falo sanye da wata riga body hug, ja, da bakin wando kanta babu kallabi ta daure kitson da ribon zaune take tana gyaran akaifa, suka yi mata sallama ta dago kai ta na kallonsu, ko shi maigidan bata yi mashi kallon arziki ba. Su ka yi tsaye sororo, Zainab taja hannun Naja'atu 14 Sirrin Zuci.. 4 Saʼadatu Saminu Kankia su ka zauna ta ce mata "Anty Farida ina yini.?" Ta amsa ma Zainab lafiya lau, amma da Naja'atu ta gaida ta ko kallon arziki ba ta yi mata ba, taja tsoki ta tashi ta yi shigewarta daki. Daddy ya jinjina kai cikin damuwa, amma sai ya share ya ce "Ga daki nan, sai ku shigar da kayanku, ku zauna ciki." Zainab ta amsa mashi "To." Amma ita Naja'atu kamar ruwa ya ci ta, kasa cewa komi ta yi mamakin halayyar da Farida ta nuna mashi take yi, ai matsayin miji ya wuce wasa a kalla komi ya hada su ya zama na su kadai su ka sani ba wai har gaban mutane ta nuna ba, matsalar wasu matan kenan basu iya boyc damuwarsu ko kuma matsalar dake tsakaninsu da mazajensu, sai sun fiddo fili har wanda bai san anyi ba ya gane masu, lamarin sai dai du'a'i. Ta saukar da ajiyar zuciya, tana kallon Zainab, cikin halin ko in kula Zainab ta ce "Taso mu shiga daki mu huta." Su ka shiga dakin lafiya lau da katon gado, Zainab ta kunna AC ta fada kan gado da alamun gajiya, yayin da Naja'atu ta zauna a sanyaye take kallon Zainab, ta ce Zainab kina ganin zamanmu da matar nan zaya yiwu? Ni gaskiya bani son fitina, tashi ki kaini gidan Anty Aisha in zauna can, in ke za ki iya ki zauna." Zainab ta yi murmushi ta ce "Kema din ba in da za ki je muna nan, idan ba ta iya zama damu ta tafi, ai ba gidan ubanta ba ne." Naja'atu ta ce "Amma gidan mijinta ne." Ta ce "Mu kuma na dan'uwanmu ne, ke ba ri fa kiji in gaya maki, wallahi duk matar da kika ga ana kuka da ita kan cewa ta buwayi dangin mijinta, ta hana su zuwa gidan dan'uwansu, samu tayi, sai in shi mijin ya bata dama, kuma ta yi sa'a ta samu 'yan'uwan da ba su san abin da suke yi ba, ai dama da irin haka ne suke fara 15 9 Sirrin Zuci.. 4 Sa'adatu Saminu Kankia samun dama, su rinka yi ma mutane iskanci, to mu ba zamu ba ta wannan damar ba, ai ko shi Daddyn da ya ce mu zo nan din mu zauna yasan za'a yi haka, amma don ya nuna mata.matsayin 'yan'uwanshi da shi kanshi matsayinta, shi yasa ya ce muzo ju zauna din, don haka ki saki jiki, muna nan sai ranar da Mummy ta dawo." Naja'atu ta jinjina kai ta mike ta shiga kewaye ta dauro alwala, sai da ta yi Sallah sannan ta kwanta. Ba su fita ba haka nan itama Farida ba ta zo in da suke ba, har yamma tayi Zainab ta sauko taje ta fiddo masu kayansu dagą cikin mota, su ka shirya cikin daki, sannan su ka fito falo su na jiran fitowar matar gidan ta fito ta fadi masu abin da za su kama mata na aikin buda baki, amma shiru ta yi zamanta cikin daki, suna zaune cikin falo suka yi tsuru, ga magaruba na karatowa, amma ko sanwar ruwan zafi ba a dora ba, sau uku Zainab na kwankwasa mata kofa amma ta ki fitowa. Don haka ta ce su shiga kicin su dafa abin da suke so. Naja'atu ta се "A'a, Zainab kada ki farfa, idan muka yi haka mun shiga hakkinta, kuma duk abin da ta yi ba mu da gaskiya, ba ki san tsarinta ba don haka mu bari ta fito ai dai ko don cikinta ta fito ta dafa." An kusa kiran Sallah Daddy ya shigo gidan ya dan zuba ma Naja'atun ido, tana kwance kan kujera tana jin shi ta lumshe ido kamar tana barci yanzu ita tausayinshi ma take ji ya dubi Zainab wadda har ta fara kulewa, ya ce ma ta "Yaya.?" Ta ce "Lafiya lau." Ya ledka kicin bai ji motsin komi ba, ya fito yana kallon Zainab ya ce "Ya ya ku ke zaune ba a dafa komi ba, yamma ta yi fa." Zainab ta ce "To ai ba ta fadi abin da za'a dafa ba." Ya ce "Ta na ina.?" Ta ce "Tun da ta tashi ta shiga daki har 16 P 4 Sirrin Zuci.. 4 Saʼadatu Saminu Kankia yanzu ba ta fito ba." Da saurinshi ya nufi dakin, ba su san yarda ya yi da ita ba, sai gashi ya fito ya ce "Shi kenan bari in fita in kawo maku abin da zaku ci, amma zani tsaya in yi Sallah, akwai lemu cikin firij, sai ku fara amfani da shi." Ya juya ya fita. Naja'atu ta bude ido tana kallon Zainab, su duka suka jinjina kai, lamarin sai du'a'i. Suna cikin daki sun gama sallah, Farida ta fito ta shiga kicin ta hada tea din ta mai kauri ta soya kwai ta dauki abin ta ta shiga dakinta. Lamarin sai ya daina 6ata ma Naja'atu rai a ganinta har da rashin wayau ke damunta, in har tana da wayau mijinta ba abin wulakantawa ba ne, to ita da shi take tunkaho ba ta san cewa duk irin son da yake yi mata matsawar ta ci gaba da bata ma shi rai sai an wayi gari babu son sai ma tsana tsakaninshi da ita?. Da ya dawo yayo masu takeaway, abincin na Restaurant mai dadi, Zainab ta fita ta karbo masu nasu su ka zauna cikin dakin nan suka yi buda bakinsu. Da Asuba kuma tea su ka fito su ka hada su ka sha su duka, abin mamaki ya ke ba su Zainab ta ce "Za ta kira Mummy ta fadi mata halin da su ke ciki, amma Naja'atu ta hana ta ce "Ba'a shiga cikin harkar aure, yanzu idan kin fadi mata ranta 6aci zaya yi, ta tsane ta alhalin mijinta kuma yana sonta, kinga daga nan sai rashin jituwa ta shigo, mu yi hakuri kawai, duka kwana nawa ne zamu fita mu bar ma ta gidanta?" Zainab ta cе "Amma Naja'atu kina ganin abubuwan da ta ke yi fa.?" Ta ce "Na gani, kuma daga ni har ke 'yan kallo ne, wanda ya aje ta abun bai dame shi ba, sai ke.? Zainab ta cije lebe cike da takaici shi kanshi Daddyn ganin sakarcinshi take yi, kamar Farida ace tana 17 Sirrin Zuci.. 4 Sa'adatu Saminu Kankia neman gagararshi? Karfe sha daya su ka yi wanka, so su ke suje gidan Anty Aisha daga can su karbo dinkunansu, sun gama shiri su ka fito falon Daddy na kwance kan kujera da Jarida a hannunshi, yana dubawa ya sauke jaridar yana kallon Naja'atu abun har ya bata kunya ta yi mashi kyau yarda yake sonta, to sai dai ya dauki alkawarin ba zaya shiga harkarta don a zauna lafiya, amma Farida ba ta yarda da haka ba, har tana ikirarin matsawar Naja'atu ba ta bar gidan ba to kuwa ita zata tafi ta bar mata gidan akan haka sunsha rigima daren jiya, da ya biye mata sai ya kai ga dukan ta. Ya dan lumshe ido har yanzu akwai damuwa tare dashi Zainab ta zauna yayin da Naja'atu ta jingina da kujera gaba ki daya su ka gaida shi, ya saki fuska ya na amsawa ya zuba ma Zainab ido ya ce, sai ina kuma? Ta ce gidan Anty Aisha zamu je daga can mu biya wajen Tela idan ya gama dinkunanmu mu karbo. Ya jinjina kai sai ya dubi Naja'atu a hankali da sigar sadar da wani sako gare ta. Ta fahimce shi sarai, amma ta janye fwayar idonta akanshi tana kallon akwatin talabijin, ana wasan kwallon kafa, ta yi murmushi ta na jinjina kai, Daddy daban ne har yanzu yana nan da kwakwar kallon Kwallon, ga kuma karatun Jarida ya na yi, duk a lokaci daya ko wane ya ke yi?. Ya dubi Zainab, ya ce "Amma ba za ku dade ba ko.?" Ta yi murmushi ta ce "Da wuri zamu dawo, amma sai ka bamu kudi, an kara mai a mota, ya yi kasa sosai." Bai ce komi ba ya aje jaridar ya tashi ya shiga cikin daki bai dade ba ya fito ya ba su su ka yi mashi sallama su ka fice. Su na tafiya bisa hanya Zainab ta rinka korafin yanayin zaman gidan, sam ba ta gamsu da shi ba, Daddy Sirrin Zuci.. 4 Sa'adatu Saminu Kankia bai dace mata ba, ko da ya ke an ce dama abin da ka fi so ya fi wahalar da kai, me yiwuwa son da ya nuna ma Faridar ne ya janyo wannan rainin tsakaninsu, daren jiya tana jin rigimar da suka rinka yi, sai dai ta ji dadi kwarai da ta ji Daddyn ya rufe ido ya yi ma ta bala'i ya kuma jaddada mata matsayinshi to amma yarda abubuwan suke tafiya rayuwa ba ta da wani tasiri tunda babu mutunci, mutum irin Daddy da ke da son jama'a musamman 'yan'uwanshi kamata ya yi ace ya aje macen da ra'ayinsu yazo daya ta haka ne zasu yi rayuwa mai dadi ba wai sakarci irin Farida ba. To ita dai Naja'atu 'yar kallo ce bata saka abun a ranta ba, haka nan ba ta da niyyar saka kanta cikin lamarin ba, gidan Aisha suka sha yininsu suna bata labarin abubuwan da ke faruwa, Aisha ta ce "Ai ni dama nasan a rina wai an saci zanin mahaukaciya, matsala ce babba namiji ya fidda sonshi ga mace har ta fahimce shi kamar yarda yake matsala ga matan su fidda nasu, to shi Daddy komi Farida komi Farida, yanzu ga abin da Farida ke neman saka shi nan." Zainab ta ce "Amnıa fa ba laifi yana tsaya akanta insha Allahu zaya yi nasıra." Aisha dariya kawai ta yi ta ce "To Allah yasa, idan kuma ya zama mijin tace ba shi kenan ba." Suka yi dariya baki daya. Sai da aka yi sallar La'asar suka nufi gida, abun mamaki gidan a rufe shima Daddyn ba ya nan su ka zauna bakin kofa su na mamaki, Zainab ta te su koma gidan Aisha kawai, Naja'atu ta ce "A'a, a kira Daddyn aji." Don haka Zainab ta fidda waya ta kira shi, ya ce "Yaya Zainab.?" Ta ce "Lafiya lau, mun dawo ne gidan a rufe babu kowa." Ya се "Babu Kowa? Kuma kun 19 Sirrin Zuci.. 4 Sa'adatu Saminu Kankiа Kwankwasa.?" Ta ce "A rufe yake gama kwado an sanya." Ya dan yi shiru, sai ya ce "Shi kenan ku yi hakuri gani nan isowa." Zainab ta rufe wayar tana kallon Naja'atu ta ce "kin ji bai ma san ta fita ba, Allah kuwa idan yarinyar nan tayi wasa, sai nayi mata dukan tsiya." Naja'atu ta yi murmushi ta ce "Me ya yi zafi na duka? Ki rabu da ita tsakaninta da mijinta." Su na nan tsaye Daddy ya kawo masu makullin, Zainab ta sauka ta karbo bai tsaya ba ya fita. Da su ka shiga, su ka aje kayansu cikin faki su ka dawo falo, Zairab ta ce "To wai zaman mu kenan, kullum sai dai a sawo mana abinci?" Naja'atu ta yi murmushi ta ce "To me zamu yi.?" Ta ce "Tashi zaki yi mu shiga kicin kada mu ma mu zama sakarkarin." Naja'atu ta ce "A'a Zainab kada ta ce mun yi mata ba daidai ba." Zainab ta ce "To ita daidai din ce take yi yanzu? Tashi zaki yi kawai mu shiga kicin Naja'atu ta zauna tana jinjina abin a ranta, ita dai ta tsani wani ya ce ta yi mashi ba daidai ba, balle wannan zaman da suke yi dangwalolo kuma tasan duk a kanta ne take yin haka me yiwuwa da babu wani abu tsakaninta da Daddy ba zata yi masu ba. Zainab ta mike ta shiga kicin ta bude firij ga komi nan a wadace ta leka store nan ma babu matsala, don haka ta zage ta shiga aikinta. Shiru-shiru Naja'atu na zaune, don haka itama ta shiga su ka-ci gaba da aiki, Zainab ta yi ma Daddy waya, ta ce kada ya yi wahalar sawo abinci gashi nan su na dafawa." Hankali kwance su ka ci gaba da aikinsu, Zainab ta dora farfesun kaza ta zauna tana fere dankali yayin da Naja'atu ke tsaye tana yankan kayan marmari zata hada fruits salad. Babu sallama ta shigo cikin gidan, ta tsaya cikin 20 Sirrin Zuci.. 4 Sa'adatu Saminu Kankia falo tana waige-waige, hancinta ya cika da kamshi alamun girki ake yi cikin gidan, sai kuma ta kara harzuka, da saurinta ta nufi kicin din, ta tsaya bakin kofa ta ce "Waye ya baku izinin shigar mani kicin kuyi sanwa?" Gaba ki daya suka juyo suna kallonta, Zainab ta yi karaf ta ce "Ai ba sai an ba mu izini ba, mu ma muna da 'yancin yin yarda mu ka ga dama cikin gidan tunda ba na ubanki ba ne." Naja'atu ta yi sauri ta dafa ta, ta ce "Ba a haka Zainab." Farida ta ce "Ke tafi can munafuka, rufe mani baki ba da ke nake yi ba don ba ni da lokacinki, kuma ke da kike ikirarin don kin isa ki ka shiga kicin din, don kina takamar gidan dan'uwanki ne zani yi maganinki, ai zaya dawo gidan sai ya zaba ko ni ko ke, ko kuma wannan banzar bakauyar, kuma wallahi da ni mu ke magana, yanzu a fita a bar mani kicin." Zainab ta yi murmushi ta ce "Wannan kuma ne ba ki isa ba, ba kuma ki da hurumin da za ki fidda mu, don ba duwatsu ne a gidan ba da zaki fita yawonki na banza ba ki tsaya kin yi ma mijinki abincin da zaya ci ba, balle mu ma mu samu, sannan kuma kice ba zamu girka ba, wallahi kinyi kadan, kuma dul iya wulakancin da kike jin kin iya, kiyi wata rana ko an ce kiyi ba za ki yi ba, shashashar banza." Farida ta ce "ka da ki kuskura ki sake zagina." Ta ce "An zaga, kiyi abin da za ki yi." Rigima ta yi sama tsakanin su, Naja'tu duk ta rikice ta shiga kwakkwafat Zainab, kan ta yi hakuri ta rabu da ita, yayin da ita kuma Faridar ta rufe ido ta rinka dura masu ashar, zuciya ta kashe Zainab ta mike su ka rukume dambe, cikin yanayin Daddy ya shigo gidan da saurinshi ya saki ledojin da ke hannunshi ya nufo kansu 21 Simin Zuci.. 4 Sa'adatu Saminu Kankia yana kokarin raba su, amma Farida ta ki tsayawa, sai ma ta maida fadan kanshi, tana cewa "Don mi zaka basu izinin shigar mani cikin kicin ya ce "Na ba da, an fadi maki yarda kike sakarya su ma sakarkarin ne, ko kua yarda kika kasa tsayawa kiyi girki cikin gidanki, so kike su zauna da yunwa? Idan ba su girka ba me za su ci? Kuma sannan gidan ubanwa kika je? Wa ya ba ki izinin fita.?" Nan kuma sai ta yi sakwat, ya dubi Zainab ya ce kuje ku ci.gaba da aikinku." A fusace ta wuce daki shima ya bita Naja'atu na tsaye gefe gudam jikinta har rawa yake yi, ba ta son fitina, "Wannan wace irin rayuwa ce.?" Zainab ta gyara jikinta su ka koma suka ci gaba da aikinsu. Da daddare da suka yi waya da Mummy, Naja'atu ta rinka kwabarta, amma sai da ta fadi ma Mummy komi. Mummy ta ce "Abin da za'ayi, zani yi magana da Daddyn,ku koma gida kuyi zamanku." Zainab ta ce "Kiyi hakuri kawai Mummy Daddy yana bakin kokarinshi idan muka tafi kenan ta samu yarda take so ki rabu da ita sai naga iyakarta, muna nan zama daram, idan muka tafi ta yi galaba kanmu kenan, kuma shima zaya a ba'a yi mashi daidai ba." Mummy ta ce "Shi kenan amma ki kiyaye kada ki kuskura in ji an ce kun kara yin dambe da ita, ku zuba mata ido kawai tunda ba dukanku take yi ba." Zainab ta ce "Wallahi ko yanzu Mummy ita ce taja, don mi zata tsaya tana zaginmu kamar kananan yara.?" Mummy ta ce "Na ji, koma menene ku rinka hakuri." Su ka yi sallama ta rufe wayar. To kwana biyu ba a sake rigima ba, sai dai Farida 22 Sirrin Zuci.. 4 Saʼadatu Saminu Kankia ta tsame hannunta cikin harkar gidan, su ke gyaran falon, kicin da dakinsu, haka nan da yamma su yi aikin abincin buda baki, daga su sai Daddy ke ci. To su ma ba su shiga harkarta, iyakarsu da ita gaisuwa wani lokacin ta amsa wani zubin kuma ko kallo ba su ishe ta ba, Zainab haushi take ji sosai, sai dai Mummy ta ce kada su kuskura su kara yin rigima da ita, don haka ba ta biye mata. Duk aikin da ya kamata suyi, cikin gidan suna yi Naja'atu dai 'yar kallo ce, bata cika zama falo ba, idan ba wani aiki su ke yi ba, ko kuma Daddy ba ya gidan amma in dai yana nan cikin daki zata yi zamanta shima yana kokarin kauce ma duk wani abu da zaya janyo fitina tsakaninsu, cikin zuciyarta ta rinka tausaya mashi, duk ya bi ya rame ya sukurkuce kuma ta san ba wani abu bane illa rashin kwanciyar hankali, yarda take nazarin zamantakewarsu sai taji kwata-kwata ta daina sha'awar zaman gidan shi, yanzu haka ji take yi kamar tana kan kaya, to ina ga ya auro ta tazo gidan, ai tasan ta bani, yarda ba ta son fitina wuyarsu zata sha, don haka ta dukufa addu'a ba dare ba rana, akan Allah ya yi mata zabi mafi alkairi." Lokuta da dama idan tana auna zamanta da Daddy da kuma zama da Khalid sai taga auren Khalid ya fiye mata kwanciyar hankali, a kalla tasan babu wanda zaya tsangwame ta, kuma shima ba ya da hayaniya, zaya bata rayuwa mai kyau fiye da gidan Daddy, saboda matar to balle kuma ita. Sai dai idan aka yi maganar so, ta yi Imanin Daddy kadai zuciyarta take so, abin da ke wahalar da ita kenan. Don haka ta mika dukkan lamarinta a wajen Allah, tana neman zabinshi kuma babu laifi tana samun sauki. Idan suka yi waya da 23 Sirrin Zuci.. 4 Sa'adatu Saminu Kankia Khalid yana fadi mata matsayin kaunarta a zuciyarshi, ita kam addu'a take yi mashi da fatan Allah yasa ya dace da abin da ya tafi nema. Rayuwarsu ta ci gaba da tafiya, da dadi babu dadi sun dai dake, yau Naja'atu na makaranta, Daddy ya kirata a waya ya ce ta fito ya na jiranta waje. Zaune ta ke tana wani aiki dole ta aje ta fito, ta same shi zaune cikin mota ya zuba mata ido sai ta ji wani iri. A hankali ta sauke kanta, ya ce "Zagayo ki shigo mana." Ta bude dayan gefen ta zauna, ya dafa sitiyarin motar ya na kallon titi, kamar yana nazarin wani abu, sai kuma yг juyo yana kallonta ya ce "Wai laifin me na yi maki? Yanzu ba ki sakar mani fuska idan na zauna in da kike sai ki tashi abun ya na yi mani komi ba ina yin haka ne don kauce ma fitina." Ya zuba mata ido sai ya jinjina kai ya ce "Na fahimce ki sai dai ina son ki sani, har yanzu kaunar ki tana cikin zuciyata, kuma ina nan kan maganata, don haka idan Allah ya kaimu Sallah ta ba da baya, Mummy ta dawo, zani samu lokaci mu zauna da ita, a fara maganar nan." Naja'atu ta zuba mashi ido, ta ce "Daddy kana ganin abun nan zaya yiwu? Ni fa ina gudun fitinar matarka, ba za tga barni in zauna lafiya ba." Shi ma ya ci gaba da kallonta, ya ce "Amma ni za ki aura ba Farida ba, haka nan ba ita ke iko dani ba, ina da 'yancin yin duk abin da zaya yi mani dadi, don haka wannan ba hujja ba ce." Ta yi'shiru tana sauraren shi, ita kadai tasan abin da take hangowa, to tasan idan zata kwana tana kwatanta mashi ba zaya yarda ba, don haka ta rabu dashi din ya fiye mata kwanciyar hankali, rigimar Daddy yawa ne da ita, dayar ma yaya ya kare da ita balle ya hada biyu.?" 24 Sirrin Zuci.. 4 Saʼadatu Saminu Kankia Ya saki maganar ya ce "Yanzu me kike so in yi maki?" Ta zuba mashi ido ta ce "kamar yaya.?" Ya cе "Wai na hidima sallah." Ta yi murmushi ta ce "Na yafe maka, Mummy ta yi mana dinkuna kala biyu, kuma ga na biki bamu sanya wasu ba." Ya ce "Na sani amma ni ganina ke yi kina da hakki a kaina." Ya mika hannu sit din baya ya dauko leda da shaddoji guda biyu dinkakku, masu kyau dinkin senegal da leshi dfaya baki da adon duwatsu ya ce "ke da Zainab shima leshin naki ne." Ta karkace kai tana kallonshi yarda yake so ta ce "Daddy hidimar ta yi yawa." Ya ce "Ba ki tunanin cewa nan da dan lokaci gaba ki daya hidimominki kaina za su dawo, to ki dauka ina yin rahasal ne in gani in zani iya." Ta yi dariya ta ce "Sai ka ce wasa.?" Ya ce "Duk yarda kika ce." A hankali ya rinka janta da hira, don haka su ka dauki lokaci sosai, duk wata kewar da suke da ita ta tafi, sai begen junansu, Daddy kamar kada ya tafi ya shiga cikin wani irin nishadi, duk wata damuwarshi ta yaye, ya yi Imanin cewa Naja'atu rahama ce gare shi, mamakin yarda aka yi yarinyar ta shiga ranshi irin haka yake yi. Ya na shirin tafiya ya ce "Ba ki gama abin da kike yi ba? Kizo muje in saukeki gida." Naja'atu ta yi dariya ta ce "Rufa mani asiri, kada ran uwargida ya baci, ina gudun rigima kayi tafiyarka kawai idan na gama zani-dauki taxi in koma." Ya yi murmushi kawai bai ce komi ba, don haka ta fita daga motar ta rufe mashi tana kallonshi'ta ce "Na gode." Ya ce "Korata kike yi ko.?" Ta ce "Ba kora ba ce ina son in gama wani aiki kafin lokacin tashi yayi." Ya yi mata sallama ya ja ya tafi, itama ta koma ciki tana dariyar Daddy simple man, amma bai yi dace da mace ta gari 25 ba. Sirrin Zuci.. 4 Sa'adatu Saminu Kankia Ranar Sallah su ka tashi cikin farin ciki da annushuwa, na murnar zagayowar ranar suna fatan Allah ya sa su ga ya badi cikin koshin lafiya da kwanciyar hankali. Da wuri su ka yi shirinsu za su tafi gidan Anty Aisha karfe goma an sauko daga masallacin Idi, su ka fito falon masu gidan na zaune cikin falo, Daddy na cikin manyan kaya shadda fara sol, yayin da Farida ke sanye da atamfa 'yar (Super Exaisive) fara, duba daya Naja'atu tayi mashi ta kauda kai sannan gaba ki daya su ka gaida su. Cikin zuciyarta ta rinka mamakin ranar Daddy, farat daya zaka lura da hakan. Ba su zauna ba Zainab ta ce, Gidan Anty Aisha zamu je me yiwuwa sai dare zamu dawo." Ya ce "Ba damuwa itama Farida gida zata je, don haka nima zani yi babu wani abu ko.?" Ya zuba ma Naja'atu ido ta yi kyau cikin shaddar amma ita sai ta share kamar bata san yana yi ba. Zainab ta ce "Zamu zuba mai sai kuma barka da sallarmu." Yayi dariya ya ce, "kun yi girma da barka da Sallah Zainab ba ku tausayina ne.?" Ya fiddo kudi sabbi fil daga aljihunshi ya fidda ya bata su ka fice, gidan Aisha su ka sha yininsu har da Ibrahim sai yamma suka fita su ka je gidan Babansu, nan su ka sauke Ibrahim su kuma su ka wuce gida. Kwana biyu da yin sallah, suka yi waya da Mummy ta ce suna shidda suna shirin tasowa. Naja'atu tafi kowa murna, don gaskiya tana takura sosai da zaman gidan, ba wani sakewa, don haka su ka shiga hada kayansu, gabaki daya da kayansu, su ka tafi filin jirgi tarbar Mummy su na sauka sai gida. Yanci ya samu su duka addu'a suka yi kada Allah ya kara kaddara masu 26 Sirrin Zuci.. 4 Sa'adatu Saminu Kankia irin wannan zaman. Zainab ta rinka ba Mummy labarin irin rayuwar da suka yi, Naja'atu ta rinka kwabarta, to ita ma Mummy ba ta dauka da zafi ba. Ranar da daddare Daddy yazo gidan ya tsare Naja'atu sai ta amsa mashi cewa ta amince a fara maganar aurensu, Naja'atu tayi tsuru, ita kan abin da take hangowa daban, ya kada ya raya amma taki amsa mashi ta ce, "Sai dai ya jira idon ta gama nazari zata sanar dashi." Ya ce "Wane irin nazari zaki yi akaina Naja'atu? Sai dai in ba ki yi kin fito fili ki sanar dani." Ba ta ce komi ba, yayin da shi kuma ya cika sosai a karshe fushi ya yi ya tafi. Kwana biyu ko ya zo gidan ba ya kula ta idan ta gaidashi ba ya amsawa. Tun tana daukar abun da wasa har dai taga da gaske ya ke, don haka itama ta share shi kowa ya ci gaba da harkarshi. Zainab ta rinka kokarin daidaita tsakaninsu amma abun ya ci tura Daddy ya dauki zafi sosai, gaba ki daya ma ya dan daga ma zuwa gidan. Sati biyu da dawowar Mummy, ta shirya masu tafiya, Katsina. Naja'atu ta yi murna kwarai ta samu iyayenta da 'yan'uwanta lafiyar kwanansu biyar suka dawo Abuja, ko da yazo gidan suna zaune falo tare da Zainab da su ka gaida shi ciki-ciki ya amsa, ko kallon Naja'atu baiyi ba, ya tuna Zainab ta yima Mummy magana, don haka itama Naja'atu, ta

Chapter 2 of 7