tashi ta bar wajen.
Zainab dariya take yi masu saboda tasan su duka suna
son juna, ko ita Naja'atun dake kokarin dannewa,
damuwarta ta fara fitowa yanzu ko jiya Khalid ya kira ta yana yi mata korafin ya rasa gane kan Naja'atun cikin
'yan kwanakin, sai ta kama waya ta rufe, haka nan idan
ma ya same ta ba ta sakin jiki suyi hira sosai kamar da,
27
Sirrin Zuci.. 4 Sa ʼadatu Saminu Kankia
wai don Allah me ya ke faruwa.?" A zahiri ta san cewa
matsalarta da Daddy ce ta jagula mata lissafi, sai dai
babu damar ta fito ta fadi mashi haka don haka tayi
karya ta ce "matsalar karatu ce kawai amma babu wani
abu.
Amma shi Dáddy tasan matsalarshi, tsabar kishi ce
sai dai bata ganin laifin Naja'atu ita kanta bata yi mata
sha'awar zama da Farida a matsayin kishiyarta, yarda
Naja'atun ba ta son fitina kwarar ta za'ayi. Haka nan
yarda tafiyar ta taho kama ta ya yi ace ya kwantar da kai
yana lallashin Naja'atun, ta haka zaya iya shawo kanta
tunda yasan tana sonshi, amma wannan fushin da yake
yi ba zaya yi mashi maganin komi ba. Idan tayi ma
Naja'atu maganar sam ba ta so ta ce "Don Allah ta daina
yi mata maganar Daddy." Don haka Zainab ta zuba ida
wani lokacin ta yi dariya wani lokacin ta tausaya masu,
ganin yarda soyayya ke wahalar dasu.
Da hotonta ya kare ta yi shiri ta yi tafiyarta
makaranta, Naja'atu ba ta ji dadi ba. Abu kamar wasa,
sun kasa sasanta kansu, ta kai matsayin da babu ruwan
kowa da kowa, haka ya fiye ma Naja'atu kwanciyar
hankali, ta ci gaba da karatunta har Allah ya taimaka ta
gama, lokacin Khalid ya ke shirin dawowa. Sun yi waya,
ya sanar da Naja'atu, ya na tambayarta, abubuwan da
take so, a zuba mata cikin lefe, saboda so yake yi da
zaran ya dawo a sanya lokacin auransu." Ta yi dariya ta
ce "Ba ni da zabi, duk abin da ka sawo zani yi murna
dashi, ni dai fatana Allah ya dawo da kai lafiya, ya
sanya an dace da abin da abin da aka je nema." Ya ji
dadi ya ce "Na gode Naja'atu, na yi Imanin addu'ar da
kike yi man ce take yin tasiri a kaina don haka nake
28
Sirrin Zuci.. 4 Sa'adatu Saminu Kankia
ganin hasken abun na yarda wata baiwa ce Allah ya yi
mani da ya hada ni da ke ko kinsan cewa samun mace
tagari irin ki yana da wahala, wata babbar baiwa ce
Allah ya yi mani. Ta yi murmushi kawai.
To kuma ranar su na zaune cikin falo tare da
Mummy, Daddy ya yi sallama ya shigo tun da ta juya
taga shi ne, ta maida idanuwantga akan akwatin talabijin
ba ta sake kula shi ba. Yazo ya zauna su na gaisawa da Mummy, itama nazarinsu ta ke yi, ta na sane da halin da
suke ciki, zuba masu ido ta yi taga iya gudunsu, amma
yanzu da abun ya fara tsanani, sai ta ke ganin bai dace
ba, kusan abun ya farfa zama gaba tsakanin su babu
ruwan kowa da kowa. Naja'atu ta mike tana shin tashi, Mummy ta dube ta ta ce "Ina za ki Naja'atu? Zauna
muyi wata magana." Naja'atu ta koma ta zauna, yayin da Daddy ya zuba mata ido, zuciyarshi na harbawa da sauri, don haka ta sarda kai ba ta ce komi ba. Mummy ta
dubi Daddy ta ce "Wai me yake faruwa ne tsakaninku.?" Daddy ya watsa hannayenshi ya ce "Ga ta nan ta fadi maki." Ta dubi Naja'atun, yayin da zuciyar ta ta kare, а
hankali hawaye su ka cika mata ido, sai ta kifa kanta
cikin jikinta.
Ta juya kan Daddy ta ce "To wai duk meye ya jawo haka?" Ya yi murmushi ya ce "Ba wata matsala ba
ce ba, na yi mata magana ne kan cewa ina son ta amince
mani a fara maganar aurenmu, to kanshi ne fa ta dauki
fushi, kuma ni na fadi mata babu dole, itdan ta ce bata yi
ba zani matsa ma ta ba, a kan haka ne ta ke ta wannan
abun idan na shigo sai ta tashi ko kallon arziki ba ta yi
mani." Mummy ta yi murmushi ta ce "To gaskiya ba ni
son irin wannan abun, abin da nake so ka dauka, shi
Sirrin Zuci.. 4 Sa adatu Saminu Kankia
aurc nufin Allah ne, idan Naja'atu matarka ced zaka ga
an yi haka nan in ba matarka ba ce sai dai ka dauki
hakuri, don haka a bi komi a sannu." Ta juya kan
Naja'atu ta ce "Kin ji dai abin da na fada, bani son irin
zaman da kukc yi kc da dan'uwanki, kuma in ban da
abin ki, yaya za ki yi da Daddy? Ko shi yaya zaya yi da
ke? Duk me yake wahalar da ke cikin 'yan kwanakin nan
idan ba shì ba, ga shì nan ku sasanta kanku, bani son
sakarci."
Ta mike ta shige cikin daki, su ka zauna shiru, ga
shi Daddy ya tsare ta da mayataccen kallonshi, duk ya
takura ta sai ta ji kamar ta tashi ta bar wajen. Ya yi
gyaran murya ya na kallonta, ya ce "Yanzu ba ki ji
kunyar abin da ki ka yi mani ba.?" Ta girgiza kai ta ce
"Ko daya, saboda nasan ba ni ce na yi fushi da kai ba,
kaine ka fara." Ya ce "ko da nayi fushin nayi ne don ki
gane cewa kin yi mani laifi, amma ba don wani abu ba,
sai kika nuna mani ni ba wani abu ba ne, ga baki daya
ma za ki iya rabuwa da ni." Ta yi shiru ba ta ce komi ba,
yayin da shi kuma ya ci gaba da yi mata korafi, to ita
kam bata ga laifinta ba, kawai dai yana son ya yi
tabarmar kunya ne, don haka ya ke kokarin dora mata
laifi.
Ya gyara zama yana kallonta ya ce "Yanzu ina
magana ta kwana, shin kina jin za ki amince da ni ko
kuma kin share ni in rabu da ke? Tambayar tayi mata
nauyi, ba ta san yarda zata yi da rigimar Daddy ba,
alhalin shi kanshi Khalid cikin huro mata tashi wutar ya
ke, cikin sati mai kamawa zaya iso kuma ya ce da ya
dawo maganar aurensu ce abu na farko da zaya fara yi.
Abum ya sakata tsakiya, yayin da Daddyn ya marairaice
Sirrin Zuci.. 4 Saʼadatu Saminu Kankia
mata yana kokarin shawo kanta, tun yana magana da zafi-zafi har ta kai ya kwantar da kai yana lallashinta, tausayi ya bata da ya rinka fasa mata sirrin zaman aurenshi, ya cc "Na sani zake yi tunanin ko ina daya daga cikin maza 'yan sha'awa, masu zara wadanda da
sun ga macc zasu cc suna so, musamman ganin ban
dade da yin aure ba gashi, nazo ina magiyarki amince da
aurcna. Na sani sirrin gidana biyayya ne wajenki da
kanki kinga irin rayuwar da nake yi har yanzu ban samu
kwanciyar hankalin da nake so ba, bani samun kulawar
da ta kamata don haka kika ga na makance kanki, na
sani kina da kyakkyawar tarbiya da zaki san hakkina ki rinka kyautata mani. Ina kaunarki Naja'atu, zani so ace kanki na dora dukkan jin dadin rayuwata na yi Imanin
ba za ki bani kunya ba, zaki yi mani halarci, don haka ki amince dani ki yarda dani in baki amanar kaina."
"Kaunata gare ki wani nufi ne daga Allah, lokacin da muka fara haduwa, ba ki sanni ba, ban sanki ba, sai aka samu akasa muka fara da rashin fahimta, Allah ya sani raina ya baci, lokacin da kika rinka fadi mani bakaken maganganu alhalin gashi nayi nadamar abin da ya faru, har na tsaya don in baki hakuri: Duk da cewa raina ya 6aci kina gani saina kasa ce mani komi, saboda
wani abu daga gare ki da ya rinka fizgeta don haka na tafi na baki wurin saboda ba zani iya gaya maki magana ba, amma tunda na iso gida tunaninki ya tsaya mani cikin rai, har ta kai na ba Hajiya labarin abin da ya faru, har dare na kasa samun natsuwa, idan na rufe ido ina ganin kyakkyawar fuskarki gaba ki daya sai na daina ganin laifinki, naji ina son in sake ganinki kuma cikin yardar Allah sai Allah ya sa jininmu daya gashi muna
zaune tare."
Sirrin Zuci.. 4 Sa'adatu Saminu Kankia
"Nasha fama da zuciyata akan tunanin abin da
yake damu na dangane dake har mamaki nake yi yarda
na cika damuwa dake, a karshe da kaina na gane cewa
ba komi ne ka wahalar dani ba, face kaunarki, amma sai
na rinka kokarin danne zuciyata domin ganin na cika
alkawarin da na daukar ma kaina tsawon lokaci dai
haka, ina són ki dauka aurena da Farida rubutacce ne,
kuma kema ina fatan mun zama daya, zani yi farin ciki
idan har kika amince ki ka dauki ragamarta, Naja'atu
kina da halayc managarta da nayi Imanin zani ji dadin
zama dake, kuma kinsan ciwona, zaki yi tattalina ki
wadata ni da kulawar da na rasa."
Naja'atu ta zuba mashi ido tana kallon damuwarshi
karara, abin da ya fada gaskiya ne yana bukatar kulawa
a kullum takan tausaya mashi bai yi dacen mace ba, idan
har ya ci gaba da zama haka rayuwarshi ba zata kai ko
ina ba zata rugurguje, meye amfanin mace irin Farida?
Irinsu ne suke zama cikin gida su na fama da zafin kishi
ba a damu da tsare hakkokin miji ba, balle a kirkiri abin
da zaya faranta mashi rai, idana akayi sa'a da mai
karamar zuciya sai ya fita waje wata ta same shi ta rike
shi tana yi mashi dukkan abin da ya ke so, shi kuma ya
na biya mata bukatunta, idan ba ai hankali ba sai ta
janye shi baki daya, sai kuma ta samu canji hankali ya
tashi ta rinka damunshi da fitina iri-iri wanda in ba sa'a
ba, sai ya gwammace yaʼrabu da ita. Kin ga nan sakaci
da rashin kula ya jawo, Allah yasa 'yan'uwa mata su
rinka kula irin wadannan matsalolin da su ka shafi
zamantakewar yau da kullum ta aure.
Ta saukar da ajiyar zuciya tana kallon Daddy, sai
Sirrin Zuci.. 4 Saʼadatu Saminu Kankia
ta yi murmushi ta ce "Ni ba wai ban damu da kai ba ne, Daddy idan na ce bani sonka nayi karya, sai dai
abubuwan ne sun taso ni gaba ka sani nayi ma Khalid
alkawarin idan ya dawo za'ayi maganar aurenmu, to
yanzu haka ya sanar dani cewa yana nan isowa cikin sati
mai zuwa me zani fadi mashi idan ya iso? Ban da
wannan ina hangen yarda zamana zaya kasance da
matarka Daddy, bani son fitina ka sani, kada in amince
maka ya zamto ba a samu kwanciyar hankalin da ake so
ba." Ya dan zuba mata ido, amma sai ya yi murmushi ya
ce "Insha Allahu ma samu za'ayi, kuma idan kina ganin
zaman naku tare akwai matsala, sai in nemi wani gidan
ki zauna ke daya." Naja'atu ta yi murmushi tana girgiza
ta.ce "Ni ba ne ba zani iya zama da Farida ba, komi zata
yi zani iya dauka tunda ba ita ce ta aje ni ba kaina abun
yi kasan wani lokaci, ku maza kuke kawo rashin zama
lafiya a gidanku, ta hanya fifita daya, ko kuma kasa
tsawata ma duka mu bika, sannan kasa tsoron Allah da adalci a tsakaninmu."
Ya jinjina kai ya na yaba tunanin yarinyar, sai ya ji
ya kara sonta, ya ce "Duk wannan ba matsala ba ce, ni dai fatana ki amince da ni, in har muka samu fahimta
tsakaninmu, to insha Allah, ba zamu rinka samun
matsala ba." Naja'atu ta jinjina kai, sai tayi murmushi ta
ce "Shi kenan sai mu ci gaba da addu'a, Allah ya yi
mana zabi mafi alkairi. Amma ina son kayi mani wani
abu guda." Ya zuba mata ido yana saurarenta, ta ce "Ina
so kayi mani hakuri zuwa lokacin da Khalid zaya dawo,
ina son inga mun rabu lafiya dashi." Ya watsa
hannayenshi yana kallonta, ya ce "Babu damuwa, ai kin
gama kwantar mani da hankali." Ta yi murmushi kawai,
33
Sirrin Zuci.. 4 Sa'adatu Saminu Kankia
Daddy daban ne, ita kadai tasan yarda take jinshi a
ranta.
Cikin dare ta kasa barci tana tunanin hanyar da
zata bullo ma Khalid da ita, maganar gaskiya ba zata iya
ci mashi fuska ba, haka nan ba za ta iya yaudarar shi ba,
ta yi tunanin ko ta fito fili ta sanar da shi? Nan ma da
nauyi, ba za ta iya tunkararshi ido da ido ba, ta ce ba ta
son shi Daddy take so, alhalin ita kanta shaida ce tasan
shi ita kadai yak e so, sai ta rinka jin tausayinshi. Har
safe bata jin dadin zuciyarta, ta na kwance cikin daki ta
dauki waya ta kira Zainab, su ka gaisa tana tambayarta
karatu. Zainab ta ce "komi lafiya lau dama nayi niyyar
yau in yi maki text in yi murna, munyi waya da Doctor
ya ce yana tafe nextweek, ya tambaye ni size dinki na
underwears da takalmi, to na dai ba shi nawa, tunda ina
ganin size din mu daya, ya ce ya tambaye ki kin ki fadi
mashi."
Naja'atu ta saukar da ajiyar zuciya ta ce "Abin da
ya sa na kirawo ki kenan Zainab, abubuwa sunyi mani
zafi, jiya har dare ya yi sosai muna tare da Daddy gidan
nan, Zainab yaya zani yi da Dadd? Ina tausayin
rayuwata, don haka gaskiya na amince da aurenshi don
haka nake so ki bani shawarar yarda zani bullo ma
Khalid, mu rabu lafiya." Zainab ta ce "Amma Naja kin
yi saurin yanke hukunci."
Naja'atu ta runtse ido ta na sauraren Zainab, ta ce
"To Zainab ya na iya da rayuwata? Ba zani iya jure
ganin bacin ranshi ba." Zainab ta yi dariya ta ce "ki fito
fili kice kin fi son Daddy kawai, in haka ne ni ba zani
cusa maki ra'ayi ba, sai dai idan nice ke ba zani zabi
Daddy mai mata ba, ina kallon saurayi." Naja'atu ta ce
34
Sirrin Zuci.. 4 Saʼadatu Saminu Kankia
"Auren Daddy ba ya gabana Zainab, abin da nake
dubawa shi ne, Daddy ya na sona, kuma nima ina sonshi, sannan yana bukatar Good wife wadda zata kula
da rayuwarshi, kuma ke kin san halin da yake ciki,
hankalina ba zaya taba kwanciya ba, idan ina ganinshi cikin wannan yanayin."
Zainab ta kyalkyale da dariya, ta ce "karatun da ya yi maki kenan.?" Ta ce "Ba zancen karatu ba ne, ki fahimce ni Zainab." Zainab ta ce "Ai na gama fahimtar ki, yanzu meye matsalarki.?" Naja'atu ta ce "Khalid." Zainab ta ce "Ina ruwanki da Khalid kuma? Kina
tunanin shi me zaya sa ki yi ma shi haka? Ki share shi
kawai, idan ya iso ya yi kukan ra shin ki, ya hakura ya
samu wata, ko kuwa za ki auri mutum biyu ne.?" Naja'atu ta ce "Sai in bashi kanwata ko.?" Zainab ta ce
"Wace kanwar, Badiya ko Fatima.?" Naja'atu tayi dariya ta ce "Ke ko.?" Wuta ta dauke ma Zainab, yayin da Naja'atu ta kwantar da murya tana tsara ma Zainab yarda abubuwa za su kasance.
Zainab saurarenta kawai take, ko da yake ta jima da shawarar wasu halaye na Khalid din, shi kanshi ya na kula da ita, ta su tazo daya yana yawan yi mata waya su gaisa, haka nan sai dai ta dauki wannan yanayi ne saboda 'yar'uwarta Naja'atu. Ta yi dariya ta ce "Wai ke
me kika dauki soyayya ne? Shi fa so daban yake, koda- kike ganin muna gaisawa da shi, ba wai dole ne ya so ni ba." Naja'atu ta ce "Insha Allahu ma zaya so ki, na fara addu'a tun jiya, kuma ke ma kiyi tunani, ya dace ki fara tunanin yin aure, ai karatu ba ya hana aure, Allah kuma Mummy na yawan magana kanki, to ke na lura ba ki ma da lokacin samarin balle ki natsu ki zabi wanda ya dace
da ke.
Sirrin Zuci.. 4 Sa’adatu Saminu Kankia
Zainab ta yi shiru tana wani tunani, wani kuduri ne
da daukar ma ranta cewa, ba zata sake yarda da wani da
namiji ba, tun akan wani saurayinta Abdullah, da ya
nemi bata mata rayuwa, farkon zuwanta Jami'a." Та
saukar da ajiyar zuciya, ta ce "Nima tana yawan yi mani
maganar Naja, to sai dai akwai wani abin da ya faru a
kaina da ya sanya na daukar ma kaina alkawarin ba ni
ba da namiji, zan ci gaba da karatuna, har masters, idan
ya so lokacin na mallaki hankalin kaina, kuma nasan
yarda halayyar jama'a ta ke sauyawa, lokacin zani iya
samun wanda halayyarmu tazo daya in aura. Abin da ya
faru shi ne, shekarata ta farko a nan Jami'a na hadu da
wani saurayi Abdullah Sani, shekara daya muka fara
karatu dashi, sai dai ba kwas din mu daya ba, wata rana
muka hadu a capteria, ya zauna in da nake zaune, shi ne
ya biya mana kudin abincin har da nawa, mu ka fito
yana tambayata sunana, na fadi mashi, shima ya fadi
mani nashi, da kuma tarihin rayuwarshi, mahaifinshi
dan kasuwa ne hamshakin mai kudi su na zaune
Kaduna."
Cikin dan lokaci muka kulla abota mai karfi, kafin
daga baya mu birkice ta koma soyayya. A duk iya
tsawon rayuwata ban taba son wani da namiji ba irin
Abdullah saboda wannan ne karo na farko da na fara
soyayya cikin natsuwa muka rinka tafiyar da
rayuwarmu, mun shaku sosai, haka nan mun damu da
juna, Abdullah mutum ne can gayu, kuma dan karya
yana da kankamba da barazana da son nuna shi wani ne,
haka nan Allah ya zuba mashi ruwan kyau don haka ya
yi fice cikin makarantar.
36
Sirrin Zuci.. 4 Saʼadatu Saninu Kankia
Rayuwar mu ta ci gaba da tafiya, cikin kwanciya hankali koda yaushe maganar Abdul ita ce idan mun shiga shekara ta biyu da karatun mu, zaya yi ma
mahaifinshi magana akan aurenmu, idan ya so da
aurenmu sai mu ci gab ada karatun. Da irc-iren
wafannan maganganun ya jani jikinshi, na yarda dashi
da amincewa dashi, ban taba tunanin yana da wata
manufa ta daban ba a kaina, saboda ya na nuna tsananin
kishi akaina, ko ganina ya yi ina magana da maza, sai
mun yi rigima, don haka na rinka taka tsan-tsan bani son
abin da zaya bata mashi rai. Abu guda ne ke hada ni da
Abdullah, yanayin mahaukaciyar soyayyar da ya ke
nuna mani, ko a gaban wa, sai ya nemi ya rike ni, ni
kuwa bani so. Ranar da yayi kissing dinta na rufe idona
kai mashi mari, sai ya rike mani hannu ya na kallona bai
ce komi ba, ya saki hannuna ya juya ya tafi. A zatona ya
yi fushi ya rabu dani kenan, sai dai ko kadan ban yi
nadamar abin da na yi ba, saboda nasan 'yancin kaina na kwata, matsawar zani barshi yana yin irin haka to wata
rana abin da ya fi haka ma yi mani za ya yi."
Abun mamaki washe gari ina zaune cikin inuwa,
sai gashi yazo ya zauna kusa dani yana dariyarshi kamar
wani abu bai hada mu ba, lokacin ne na dan ji nauyin
abin da na yi mashi amma ban tada maganar ba, muka ci gaba da hira. Lokaci ya ci gaba da tafiya, rannan ya ce in
zo muje cikin gari yawo, ban yi musu ba na bishi mu ka
tafi, mun dan yi yawo ya ke bani labarin yana da kanin mahaifiyarshi da ke zaune nan Zaria, za mu biya mu
gaisa. Na ce mashi babu damuwa, muka is agidan
madaidaici, flat House, ginin zamani tare muka shiga
cikin falon, dan madaidaici, kujeru ne kadai ciki da
37
Sirin Zuci.. 4 Sa'adatu Saminu Kankia
kayan kallo, sai Allon kwamfuta, da sauran tarkacen ta.
Na zauna bisa kujera yayin da shi kuma ya shiga wata
kofa, sai gashi ya fito da lemu cikin kofuna biyu, ya na
shan daya ya miko mani dayan na karba nayi godiya
yayin da shi kuma ya aje nashi kofin bisa tebur ya ce
mani ina zuwa. Ya bi ta wata hanya ya shiga daki haka
nan sai hankalina bai kwanta da lemun ba, don haka na
aje ban sha ba, yayin da na ci gaba da bazarin falon
tsarin gidan bai dace da gidan mace ba, ko yaya ne da
bambanci.
Ban gama wannan nazarin ba, na ganshi ya fito
daga shi sai gajeren wando ya na yi mani wani irin dan
banzan kallo, gabana ya fadi na rufe ido ina neman
taimakon Allah, Allah ya bani sa'a bai iso in da na ke ba,
aka kira wayarshi don haka ya koma ya dauki wayar.
Ban yi wata wata ba, na fizgi jikkata na fice da gudu.
Ranar nayi nadama, na ji haushin kaina da na biye ma
Abdullah, a karshe na gode ma Allah da ya kubutar dani
daga sharrinshi, mafarin rabuwata kenan da shi, ya yi
bin, ya yi daddofa, amma ko kallo bai ishe ni ba, na ce
bani ba shi har abada, kin ji dalilin da ya sa nake gudun
maza, Naja lamar da ban tsoro, ke kam kin dace daga
Khalid har Daddy nayi imanin da zuciya daya suke
sonki, kuma su duka zuciyarsu mai kyau ce, sai dai abin
da ke kike nufi da kamar wuya Naja'atu ba ki san abin
da Khalid ya gani gare ki ba har yazo ya ce ya na sonki,
me yiwuwa ni bani da shi, kuma gaskiya bani zon auren
hadi irin haka, ana fuskantar matsaloli daga baya."
Naja'atu ta ce "Haka ne, to yanzu yaya zan yi ma
Khalid? Ina jin naushinshi Zainab." Zainab ta kyalkyale
da dariya ta ce "Sai ki aure su su duka, tunda ai kin san
38
Sirmin Zuci.. 4 Sa'adatu Saminu Kankia
kina son Daddyn, kuma kika yi mashi alkawari." Naja'atu ta ce "Kina daukar maganar nan wasa Zainab, ni kuma so nake yi ki taimaka mani in warware matsalar." Zainab ta ce "To ai abun ne da rikitaswa Naja, Khalid ya na sonki kuma yasha fadi haka, ko jiyan mun yi wannan hirar dashi, gaskiya ba karamar damuwa zaya shiga ba, idan ya ji wannan abun kuskure daya kika yi da kika boye mashi abin da ke tsakaninki da Daddy, da kamar ya sani to kin ga dama yasan dole cikin biyu akwai daya, ko ya same ki, ko kuma ya rasa, yanzu kau bai da wani tunani akanki.n
Naja'atu ta saukar da ajiyar zuciya, ta ce "To yanzu Zainab, yaya kenan?" Zainab ta ce "Sai dai addu'a, kici gaba da addu'a, kina neman zabin Allah ba wai son zuciyarki ba, insha Allahu kafin lokacin da zaya iso an
samu mafita." Su ka yi sallamea rufe wayar sai ta lumshe ido tana jin tausayin Khaku, ko wace irin dauka zaya yi mata.?
Kwanaki biyu ta kasa samun natsuwa, koda yaushe tunanin yarda zata yi da Khalid ta ke yi, abun ya tsaya mata a rai, duk lokacin da su ka yi waya, takan yi tunanin ko ta fadi mashi, amma sai ta kasa, don haka ta dukufa addu'a ba dare ba rana, har zuwa ranar da ya yi mata waya ya sanar da ita ya na filin jirgi su na shirin tasowa, taji kamar kada ya dawo, amma ita kanta abubuwan sun yi ma ta yawa, kara ya dawo ayita ta kare, hakan ya fiye mata kwanciyar hankali, ta yi ma Zainab waya ta ce, "Don Allah Zainab kizo wannan satin, nasan za ki taimaka mani wajen warware matsalata." Zainab ta kyalkyace da dariya ta ce "kina
bani mamaki Naja, wai ke da gaske auren Daddy za ki
39
Sirrin Zuci. 4 Sa'adstu Saminu Kankiz
yi? Ya na da mata fa." Naja'atu ta ce, "Nì dai ki rabu da
ni shan koko bukatar rai." Zainab ta ce "Shi kenan zani
z0, hankzlinki ya kwanta." Ta ce "To na gode."
Karfe goma na dare jirgin su ya sauka filin saukar
jiragen sama na Nnamadi Azikiwe, in da abokinsu Jabir
da Sulaiman kaninshi su ka tarbe shi, ya ji dadi sosai, ya
rinka mamakin girman Sulaiman, ya zama babban
mutum yanzu ya na 300 level a Jami'a. Su ma mamakin
yarda yą canza suke yi, ya yi haske da girma akwai
alamar koshin lafiya tare da shi. Su ka rinka murna da
dokin ganin juna yana tambayar Sulaiman sauran
kannenshi ya ce su duka lafiya lau, yasan za su kira su ji
idan ya sauka. Da wayar Jabir ya yi amfani ya kira
Naja'atu ya sanar da ita sun sauka lafiya, sai dai ya bata
hakuri saboda a jiya ba za ta ganshi ba sai gobe, ga shi
kuma dare ya mika. Ta yi ma shi sannu da hanya, tare da
nuna farin cikinta, ya ji sanyi a ranshi sai ya rinka
Kiyastawa a ranshi ko yaya itama ta koma? Yasan akwai
ci gaba sosai a tare da ita. Ya fidda kayanshi su ka
rankaya sai gida.
Washe gari har rana ta fito ya na kwance da ya
tashi ya fito falo ya zauna ya na yaba ma Sulaiman, ya
rike ma shi gida da kyau, bai ga wata barna ba, sai 'yan
sauye-sauyen da ba'a rasa ba, to wannan kuma yasan har
da yau da gobe. Ya tura Sulaiman ya sawo mashi sabon
layi na Glo da kudi ya zuba ma wayarshi ya kira
Naja'atu su ka gaisa ya na tsokanarta ya ce "Ba ki da
kirki Naja'atu, shi ne ba za ki zo ki yi ma maigida barka
da zuwa ba.?" Ta yi dariya ta ce "Kayi hakuri don Allah,
amma Mummy ba za ta barni ba." Ya yi dariya ya ce,
"Dadina da ke saurin karaya, nima tsokanarki nake yi,
40
Sirrin Zuci.. 4 Sa'adatu Saminu Kankia
insha Allahu ina nan fitowa zuwa yamma, abun ai da gaske za'a yi shi, babu wani hutu, sai naga na same ki, don haka ki zama cikin shiri, don nima da shirina na iso
zani zo mu tsara komi kafin hutuna ya kare ayi abun nan