Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
6 / 7
dai-dai jikinta. Ta fito cikin falon, yunwa take ji, ta hada shayi mai kauri ta sha. Amma shi maigidan ta dora mashi sanwar kalaci mai nauyi, ta san shima yana tare da yunwa. Ta inka tariyo wasu abubujwa da suka faru, sai ta rinka jin tausayin shi. Daddy ya nuna mata kauna 'yar usuli, kaunar da duk watga diya mace za ta so ta samu irin ta. Don haka ta daukarma zuciyarta za ta ci gaba da kula da rayuwarshi ta rinka kyautata mashi, insha Allahu ba za ta saba mashi ba, sai dai akan kuskure, wannan ku an ce dan adam ajizi ne. Kwana biyu sun samu nutsuwa da juna hankali ya kwanta. Daddy har wata shagwbaba yake yi mata, ita kuma don da nan sai ta marairaice ta shigba lallashin shi tana lallaba shi. Abinci akan lokaci mai dadi da gina jiki. Daddy ya kara shiga jikin ta sosai, sai suka zama kamar hanta da jini. Ko da yaushe suna like, baya ko son fita. Yanzu yanda yake jin Naja'atu a ranshi, ji yake yi baya iya yin tafiya ta kwana biyu ya barta. Yarinyar 'yar albarka ce, ga tsabta ga ladabi, ba ta gajiya da hidama da shi. Haka nan duk runtsi idan ya kawo uzurinshi za ta tsaya ta ba shi lokaci sosai, sai ya sallameta don kanshi. To itama ta aza ma zuciyarta son Daddy, 67 Sirrin Zuci.. 4 Sa'adatu Saminu Kankia musamman yanzu da ya shayar da ita zumarshi, ya karantar da ita yanda za ta soshi. Jin shi take kamar wani fangare na jikinta, idan ya fita sai ta ji gidan babu dadi, har zazzabi take yi. Amma da zaran ya shigo, ya ware mata hannaye ta shiga jikinshi, sai ta ji sanyi a ranta. Ba ta taba tsammanin ana yi ma da namijin irin wannan son ba, ashc da can duk shirme take yi, yanzu ne za tayi mashi na Karshc. Amma da zaran ta tuna ba ita kadai ke da Daddyn ba, sai hankalinta ya tashi. Musamman idan ta tuna fitinar Farida. Ko yaya zamansu za ya kasance idan ta dawo? Tana son tayi ma Daddy maganar, amma ta lura sam baya so, don haka ta zuba mashi ido kawai. Yau da yamma yana shirin fita, ya yi shiri cikin kananan kaya wando Bosch baki, da shat fara mai dogon hannu, yana tsaye gaban madubi yana taje kai, ta zuba mashi ido, shima ita yake kallon ta cikin madubi, ta ji tsakar jikinta tana tashi. Sai ta mike tana shirin fita, ya aje kum din ya ce, "Ina za ki kuma?" Ta zuba mashi ido tana murmushi, ta ce, "Ina jiranka falo idan ka gama." Ya yi dariya ya ce, "Dadina dake tsoro. Shirya mu je mu gaida Mummy, kullum idan na je sai ta tambaye ki, wai ta damu da kewarki." Naja'atu ta ji dadi, tana son ganin Mummy. Sai dai kuma za ta ji nauyin ta, yanzu ta zama sarakuwarta. Ta fiddo mayafinta da jikka, ta sanya takalmi flat suka fita. Sunyi yawo sosai cikin gari, har akayi magaruba. A National Mosque suka yi sallah,' sannan suka isa gidan Mummy. Tayi murna da ganin Naja'atu, sai taga ta canza mata, tayi kyau tayi kiba, alamar koshin lafiya. Naja'atu ta zauna gefenta suka gaisa. Daddy na zaune gefe daya yana kallon kaunar su, Mummy na son 68 Sirrin Zuci.. 4 Sa'adatu Saminu Kankia Naja'atu. Sai da suka nutsu sannan ya gaida ta. Ta dubi Naja'atun ta ce, "Zaman ku lafiya dai ko?" Naja'atu tayi murmushi kawai. Ta ce, "Don Allah, Naja'atu halinki da na sanki da shi, ki rike shi, ki zauna. lafiya da mijin ki da abokiyar zaman ki, banda fitina. Ina Faridar kuka barta?" Naja'atu ta zuba mashi ido. Shi kuma ya yi ma Mummy zuru. Ta ce, "Mc ke faruwa ne kake kallona?" Ya jinjina kai ya ce, "Tunda muka dawo ban same ta ba." Mummy ta fiddo ido tana mamaki, ta ce, "Amma baka kyauta ba, da ka dawon ka je gidansu?" Ya girgiza akai. Ta ce, "Kayi kuskure Daddy, na fadi maka ba sau daya ba, ba sau biyu ba, sai kayi hakuri, ita kantga Faridar yarinyar ce, kuma tunda ka tsiri yin aure da wuri haka, dole ne abuhn ya yi mata ciwo. Don haka sai kayi hakuri da irin abubuwan da za tayi. Kuma da ka zo ka tarar ba ta nan, me ya hana ka zo ni ka sameni kayi mani bayani? Zuwan ka nawa gidan nan, amma baka fada ba. Kaga yanzu sai suyi tsammanin dama kayi niyyar yi mata wulakanci ne, tunda ga shi ta tafi baka bi ta ba." Daddy ya yi shiru, ya san bai da gaskiya, sai dai abin da yake dubawa, itama Faridar tana da nata laifin, banda rashin kunyar da tayi mashi ta tafi, kuma taki saurarar shi ta waya, bai san yanda ta dauki abun a ranta ba. Haka nan yanda yake jin dadin Naja'atu yanzu har mantawa yake da wata Farida, baya son ta dawo ta rikita mashi gida. Yanzu hankalinshi ya kwanta, kaunar Naja'atu a zuciyarshi wani sirri ne na musamman, yarinyar tayi mashi halarci, ta san ciwon kanta, yanzu ne ya san ya yi auri. Tana da hakuri da juriya, ga ladabi kamar ta kwanta ya takata. Akwai wata baiwa ta 69 Sirrin Zoci.. 4 Sa'adatu Saminu Kankia musamman a tare da ita, wadda ke yin tasiri a kanshi. To sai dai idan ya tuno Farida, ya kan ji tausayinta, ya san tana cikin damuwa. Matsalarta daya, rashin wayau, a ganin shi ai ya nuna mata iya son da take bukata, don mi ita ba za ta kwantar da hankali ba su hada kansu, su zauna lafiya. Daga ita har Naja'atun yana son su, kowace tana da muhimmanci gare shi. Ya saukar da ajiyar zuciya yana kallon Naja'atu, tayi mashi zuru, da alamar damu a fuskarta. Tayi kokarin hade wani abu da ya tsaya mata a wuya, sai tayi mashi murmushi. Mummy ta ci gaba da yi mashi nasiha kan zaman shi da iyalinshi. Haka nan itama Naja'atun ta gargade ta, ta ce tayi hakuri su zauna lafiya banda rigima. Ta ce ma Daddy shi kuma, Daddy tace ya je, za ta je gidansu Faridar da kanta." Sai da dare ya yi sosai suka tafi. Naja'atu ta debi sauran kayanta dake gidan suka tafi. Da suka isa gida ta wuce cikin dakin ta, ta shirya kayan cikin loka. Yayin da shima Daddy ya wuce dakin shi. Tayi wanka tayi shirin barci, har ta kwanta tana karanto addu'a, shiru Daddy bai shigo ba. Ta ji wayarshi, ta dauka ta amsa mashi muryata tayi kasa, shima kasa-kasa ya ce maganar. Ya ce, "Kin kwanta ce?" Ta amsa, "Eh." Ya ce, "Tasowa za ki yi, ki zo nan ina jiran ki cikin daki." Ya rufe wayar. Itama ta kwanta shiru, me Daddy yake nufi? Ita -kam nauyi take ji. Ta kwanta shiru, amma ta dauri ta tafi. Tа kwankwasa ta shiga, yana kwance ya zuba mata ido. Sai ya yi dariya ya ce, "Wai koya maki zuwa turaka za ni yi? Kada ki saba, can gaba ki kasa zuwa." Ba ta ce komi ba tayi murmushi kawai. Ta mai da kyauren ta rufe, ya nuna mata waje ta kwanta. Cikin nutsuwa ya rinka yi 70 Sirrin Zuci.. 4 Saʼadatu Saminu Kankia mata nasiha akan zaman su. Ta ce, "Kada ka ji komi Daddy, na san kana da mata, kuma na aure ka. Ai kuwa dole ne in yi hakurin zama da ita, ni dai kawai abun da nake rokonka shi ne, ka zama adali a cikin gidan ka, kada ka karkata Gangare guda, daga cikinmu duk wadda tayi ba dai-dai ba, ka tsawatar mata. Haka nan sai ka zuba ido sosai dangane da zaman mu, ta haka ne za ka fahimci matsalolin cikin gidan ka. Allah ya baka ikon daukarf nauyinmu bisa gaskiya da amana." Ya ji dadi sosai, sai ya ji ya kara sonta, ya matsa a hankali kusa da ita ya rufe ta da soyayyarshi. Irin soyayyar dake saurin narkar da Naja'atu, take rikita ta. Don haka ta makance akan Daddy, ji take ruwa da iska babu abin da za ya raba ta da shi, sai fa wani nufi daga Allah. Wadda kullum take addu'a, Allah ya sanya ita da Daddy mutu ka raba. Washegari yana gida Mummy tayi waya tana neman shi. Don haka ya yi shiri ya fita. Ta ce, "Gidansu Farida za su je." Bai yi musu ba suka tafi. Mama na gidanb, don haka ga baki daya aka zauna teburin sulhu. Ita Farida ta dauki zafi sosai, ta ce dukanta ya yi. Yayin da shi kuma Daddy ya yi rantsuwa kan cewa, ya san dai ya mare ta, shima zagin shi tayi ta ci mashi kwala. To su duka anyi masu fada, an sasanta tare da gargadi. Mummy ta ba da hakuri. Don haka Hajiya Hafsatu, ta tsare Farida sai da ta shirya suka tafi tare. Kan hanya bayan sun sauke Mummy, za su tafi gida, ta rinka yi mashi korafi har da kuka, wai ya wulakantata don ya yi aure. Shi kuma ya ce ba haka bane, laifin ta ne, saboda ya neme ta a waya ya ba ta hakuri, amma taki saurarenshi. Yaya take so ya 71 Simin Zuci.. 4 Sa'adatu Saminu Kankia yi mata? Amma dai ya yi kokarin kwantar mata da hankali. Naja'atu na cikin kicin tana aikin abincin rana suka shigo gidan, don haka ta aje aikin da take yi, ta fito tana yi masu sannu da zuwa. Ko kallon arziki Farida ba ta yi mata ba, ta wuce ta bude dakinta ta shigbe. Daddy ya dube ta, sai tayi murmushi a hankali bakinta ya motsa, tana yi mashia sannu. Ya iso kusa da ita, ya sanya dan yatsa ya shafi kumatunta masu taushi, ta lumshe ido da sigar shagwaba, suka yi dariya ba ki daya, ko kadan ba ta bari ya ga damuwarta. Naja'atu ta koma kicin ta ci gaba da aikinta. Yayin da shi kuma ya shigar da kayan Farida dakinta, ya dawo falo ya kwanta yana kallo. Don haka da ta gama hada komi ta dawo falo ta zauna suna hira da kyalkyatar dariya. Farida na cikin daki ba ta fito ba, amma akan idonta tana ganin duk abin da suke yi. Da ta gama abinci ta hada ga baki daya, ta kawo falo ta shirya. Daddy na kallon ta, ta je ta kwankwasa kofar Farida, a fusace ta zo ta bude tana kallon Naja'atu. Naja'atu ta dan saki fuska ta ce, "Ki zo mu ci abinci." Ta ce, "Na koshi." Та turo kyauren ta rufe dakinta, Sai ta jinjina kai ta dawo falo ta zauna, ta dauki filet tana zuba ma Daddy. Ya zuba mata ido ya ce, "Kin yi ma Farida magana ko?" Ta се, "Тa сe ta koshi." Sai ya mike ya nufi dakinta, ba ta san yanda suka yi ba. Sai dai ta gansu sun fito tare sai cika take yi tana batsewa. Ba ta ce mata komi ba, ta aje ma Daddy nashi gabanshi, itama ta zuba nata, suka fara ci. Ita kau sai da ta zuba lemu ta fara sha, sannan ta zuba abincin dan kadan, tana ci kamar ba ta so. Naja'atu ba ta kula ba, ta ci gaba da cin abincinta tana kallol. Daddy ya rinka nazarinsu, shi kanshi ya san 72 Sirrin Zuci.. 4 Sa'adatu Saminu Kankia matsalar a wajen Farida take, ta cika daukar abu da zafi, idan ta sauko za suyi zaman lafiya da Naja'atu. Ya aje cokalin yana kallon su, ya ce, "Kun gane ko? Don Allah bani son irin wannan zaman da kuke yi, Allah ne ya hada ku zama cikin inuwa daya. Don haka sai kunyi hakuri, hadin kanku shi ne kwanciyar hankalin gidan dani kaina, don haka ku aje komi mu zauna lafiya, ku duka ina son ku, shi yasa na auro ku. Kc Naja'atu kece karama, don haka sai kinyi ma Farida biyayya, ba wai don ta girme ki ba, sai don ta riga ki shigowa gidan nan. Ku zauna lafiya, ku fahimci junam, bani son fiutina da tashin hankali, daga cikin ku duk wadda ta tada fitina cikin gidan nan ranta za yha бaci. Haka nan kema Farida, ki kama girmanki, kada ki dauka don bani sonki shi ya sanya na auro Naja'atu. Ba haka bane, aure nufin Alla ne, ku zauna lafiya, daga cikin ku duk wadda taga nayi mata ba dai-dai ba, ta same ni tayi mani magana. Haka nan tsakaninku ma, kada ku dauki mataki da kanku, duk abin da ya faru ni za ku yi ma magana. Haka ne za ya kawo zaman lafiya a gidan." Naja'atu ta jinjina kai, ta amince. Yayin da Farida ta buntsuru baki ta ce, "Ina saura kuma? Ai tun farko ba ka nemi a zauna lafiya ba cikin gidan ka, don haka in ta nemi a zauna lafiya sai a zauna. Idan kuma ba ta nema ba, duk wadda ta samu ita za'ayi." Ta mike yana kiranta ba ta kula ba ta shige cikin dakinta. Ya dubi Naja'atu ranshi ya baci sosai, amma sai ya danne ya rabu da ita, insha Allahu ba za ya biye mata ba ayi fitinar da take nema. Don haka ya ci gaba da kwatanta ma Naja'atun kada ta biye mata, komi za tayi, tayi hakuri, sai tayi kokarin kauce ma duk wani abu da za ya kawo rashin 73 Sirrin Zuci.. 4 Sa adatu Saminu Kankia jituwa tsakaninsu." Da daddare ba ta ci abinci ba. To daga Daddyn har Naja'atu sun zuba mata ido, harkar gabansu kawai suke yi. Haka nan bai fasa nuna mata Kauna da kulawar da ya saba ba ta ba. Har dare suna zaune falo suna hira, Daddy ya fara mikewa, ya dube ta duk da langabe ta marairaicc, ya iso kanta ya mika mata hannu tga mike, ya je ya kashe kallo ya rufe ko'ina. Ta nufi dakinta, har tayi shirin kwanciya ya kira tga. Ta fita ta same shi kwance cikin dakin shi. Ya ce, "Ta je ta kawo mashi coppee mai zafi." Ta fita, ta hado ta kawo mashi. Ya zauna yana sha, tana zaune gefenshi. Ba shiri Farida ta shigo cikin dakin, suk duka suka zuba mata ido, ta tsaya bakin kofa ta rike kugu, ta ce, "To, ka ce za ki yi adalci tsakaninmu, yanzu adalcin ke nan, da ta biyoka alhalin ka san yau aikina ne." Daddy ya zuba mata ido ya ce, "Amma kin san duka yau ne sati daya da aurena da Naja'atu, kuma bisa ka'ida sai gobe ne za ni cika mata kwanakinta. Don haka damuwar ki yau, ba za ta shafi kwananta ba. Gobe in Allah ya kaimu za ni fita hannunta shi ke nan, sai ki ci gaba da rabawa. Kuma kwana daya-daya za ku rinka yi." Ta rufe ido ta ce, "Sam ba ta yarda ba." Ga baki daya ma sai ata zagaya ta haye gadoa tayi kwanciyar ta. Da Naja'atu taga haka, sai ta mike ta fuce ta basu waje, ta shiga cikin daki ta kwanta, abun ya tsaya mata a rai. Matar nan 'yar rainin wayau ce, ba ta taba jin kishin Daddy ba sai yau da taga Farida kan gadon shi. Wani abu ya tukare ta a zuciya, sai ta rufe ido tana karanto addu'o'i, har ta rasa wadda za ta karanta. Kishi fitina ne, amma za ta gani idan Daddy za ya yi adalci. 74 Sirrin Zuci.. 4 Saʼadatu Saminu Kankia Shi kuma a can, bai ce mata komi ba, ya ci gaba da kurbar coppee dinshi. Da ya gama ya mike yana kallon Faridar ranshi bace, sai yaga babu dalilin da za ya sanya ya biye mata tana bata mashi rai, tunda ita sakarya cc. Don haka ya sanya silifas din shi ya fice daga dakin. Naja'atu na kwance ta ji shigowar shi, sai ta ji kamar an zuba mata ruwan sanyti. Ya murda key ya rufe kofar, ya iso ya ratsa jikinta, a hankali ta saukar da ajiyar zuciya, ya hana ta magana, ya shagaltar da ita. Suna jin Farida ta zo tana bugun kofar, sai bala'i take yi, su duka babu wanda ya kula ta har ta gaji ta tafi. Me yafi wannan takaici? Wasu matan kuskurfe suke yi wajen nuna wani abu da ya hadasu da miji har kishiya ta sani, a ganin Naja'atu idan ita ce ba haka za tayi ba, ko yanzu din nan da a ce Daddy bai taho wajen ta ba ya tsaya wajen Faridar, ba za ta je inda suke ba, sai dai cikin ruwan sanyi za ta dafa shi, ai ta gano sirrinshi. Da safe da fito, Farida na daki, har ta hada kalaci, Daddy na kwance cikin dakinta yana barci. Don haka ta shiga dakin shi tayi mashi gyara na musamman. Cikin sa'a ta share duk wasu tsubbace-tsubbacen Farida da ta zuba, ta san dai ita ke dasu. Don haka ba tayi mashi magana ba ta ja bakinta ta tsuke, ta zuba cikin shara. Karfe goma da rabi ta koma dakinta, barcin shi yake yi cikin kwanciyar hankali. Ta zauna kusa dashi a hankali tana murza yatsun kafarshi, ya bude ido yana kallon ta. Tayi murmushi ta ce, "Yau baka jin yunwa ne?'Rana tayi fa." Ya yi murmushi ya ce, "Ai laifin ki ne, ba ke ce kika sanya mani gajiyar ba." Tayi dariya ta ce, "Babu ruwana, kai ne fa?" Ta mike ta shiga kewaye ta cika roba da ruwan dumi, ta fiddo 7 tawul ta kawo mashi ya shiga wanka. Sirrin Zuci.. 4 Sa'adatu Saminu Kankia Tare suka fito falon, ya wuce zuwa dakin Farida. Yayin da ita kuma ta zauna tana zuba mashi kalaci. Farida na kwance abinta, ya shiga, ko kallon arzuki ba tayi mashi ba. Ya yi sallama ba ta amsa ba, ya tsaya kawai yana kallon ta. Sai ta dan ba shi tausayi. To sai dai ya san hakan da ya yi ba laifi bane, abin da ta kasa fahimta ke nan. Ya saukar da ajiyar zuciya ya ce, "Kin tashi lafiya?" Ba ta ce komi ba, ta rufe ido. Ji take yi kamar ta tashi ta rufe shi da duka, don haka ya rabu da ita ya fitc, ya zauna suka yi kalaci. Yana shirin fita ya ce ma Naja'atu, "Don Allah kiyi kokari komi Farida za tayi cikin gidan nan kada ki biye mata kuyi rigima." Naja'atu ta jinjina kai tana murmushi, ta ce, "Insha Allahu babu abin da za ya faru." Tayi mashi rakiya ya tafi, sannan ta koma ta ci gaba da gyaran dakinta, ta gyara ko'ina fes, ta wadata shi da kanshi. Ba ta fito ba tayi kwanciyar ta, har karfe sha biyu, sannan ta fito ta shiga kicin. Ita za tayi aikin abincin rana, amma daga shi ne za ta ba Farida aiki. Don haka tunda suka ci abincin rana ta fidda hannunta daga harkokin Daddy, wanda ta lura, sai daddafe yake yi dakin Faridar yana lallashinta. A duk iya tsawon rayuwarta ba ta taba jin kshin da namiji irin na ranar ba, musamman da dare ya yi taga Farida ta nufi dakin shi, sai taga kamar ta saka ihu. Kusan kwanan zaune tayi. Watau shi yasa dai wasu matan ke haukacewa akan kishiya, amma kuma da tayi wani tunani, sai ta jinjina ma Faridar, ganin ita ta dade da shi amma yanzu yana tare da wata. Itama ke nan da ta same shi ba da dadewa ba, sai da ta rinka addu'a, sannan ta samu nutsuwar zuciyarta, tayi alwala tayi 74 Sirrin Zuci.. 4 Saʼadatu Saminu Kanki.a nafila tana rikon Allah ya sassauta rnata kishinta, kada ya fito yanda kowa ma za ya gane. Sai da tayi sallar asuba, sannan ta samu barci ya dan debe ta. Karfe takwas saura, tana kwance ta ji shi tsaye a kanta. A hankali ta bude idanuwan ta tana kallon shi cikin shiri, yau ofis za'a. Tayi murmushi tana mamakin barcin da tayi, sai ta yunkura ta tashi ta shiga kewaye ta wanke baki, sannan ta dawó ta gaida slhi. Ya zuba mata ido, sai yaga duk ta canza mashi. Ya ce, "Za ni fita ofis sai zuwa yamma." Ta ce, "Kayi kalaci?" Ya yi murmushi ya girgiza kai, ya ce, "Bars hi kawai, idan na fita na samu abin da za ni ci." Ta ce, "Ba za ya yiwu ba, mu je sai kayi kalaci za ka fita." Sai ya ji dadi a ranshi, ya yi imanin Naja'atu ta damu da shi da dukkan al'amuran shi akasin Farida. Sai zafin kishin ba ta damu da kula da hakkinshi ba, yanzu haka tana can kwance kuma ya fadi mata fita za ya yi, ba ta yi maganar kalacin ba, ba ta damu da bai ci komi ba. Ya zauna falo, ita kuma ta shiga kicin ta soya mashi plantan da kwai, ta hado da tea ta kawo mashi. Yana ci suna hira kamar wani abu bai faru ba. Sai ga Farida ta fito a fusace tana zuba ruwan tijara, don me za ya zauna da Naja'atu har da ba shi kalaci, wai an shiga hakkin ta, tunda ranar aikinta ne." Naja'atu ta dube ta tsab cikin ido babu sauran tsoro, ta ce, "Bari ki ji in gaya maki, ni nafi karfin in yi wani abu da ya saba ma shari'a, saboda duk iya abin da zani nema jikin Daddy na same shi. Kinga ke nan wannan zaman ba za ya kareni da komi ba, sai dai ina son ki sani cewa, ni ba sakarya ba ce. Idan ke ba ki san ciwon shi ba, ni na sani. Kuma kin san aikin naki bane, amma kika zuba mashi ido za ya Srrin Zuci.. 4 Sa'adatu Saminu Kankia fita bai yi kalaci ba? To ni ba za ni iya barinshi ba. Idan kuma kina so a daina shiga hakkin naki da kike magana, to ki tsare hakkokin mijinki." Bakin Farida ya mutu murus. Itama Naja'atun ta sharc, ba ta kara magana ba. Sai ta mai da bala'in kan Daddy. To shima baya da lokacin ta, ya rabu da ita, ya ci gaba da kalacin shi. Ga baki daya suka mai da ta mahaukaciya. Sai ta kwasa fuu, ta shige dakinta. Har ya gama ya yi mata godiya, ya tafi, ita kuma ida cinye sauran da ya rage ya isheta, ta koma dakinta tayi kwanciyar ta. To haka zamansu ya kasauce, da wuya a yini ba'ayi cecekuce ba a gidan. Ita dai Naja'atu tayi tsayin daka akan mijinta, ko Farida ke da aiki, idan dai taga za'ayi abin da za ya kwari mijinta, to fa za tayi yanda za tayi taga bai takura ba. Yara jin dadin haka, yanzu hankalin shi ya kwanta, bai damu da fitinar Farida ba, tunda Naja'atu na kokarin kyautata mashi, har kagara yake yi ranar aikinta ta dawo. Yana samun sauki sosai da kwanciyar hankali. Naja'atu mace ce har mace, ta san kanta, ta san ciwon kanta, ta iya tarairayar miji, a bangaren shi ba ta da matsala, don haka ko da yaushe yafi karkata kan ta, abin da kullum Farida take tsegumi ke nan. Saboda kullum rana sai ta ji abin da za ya yi mata fada, amma da wuya Naja'atu ta kuskure shi, ta san kanshi sosai, kuma tana kokarin kauce ma fitinar. To ai dama haka abun yake, har kullum mace mai kwantar da kai tana lallashin miji tare da kyautata mashi, tana kauce ma fitina, ta fi farin jini ga miji. Amma ita 'yar bala'i, sai dai bakin jini ta zama karfen kafa, har ya zamto daga maigidan har kishiya sun raina ta. Kai ko 70 Sirrin Zuci.. 4 Sa'adatu Saminu Kankia 'ya'ya ke gare ta sai sun raina ta. Don haka 'yan uwa mata sai ayi hattara, ko da yaushe ki zama mai hakuri da juriya. Idan kika samu shaida wajen miji, shi ke nan kin gama sa'a. Amma da zaran ya fahimci ke fitina ce marar son a zauna lafiya, to wallahi ko kinyi ko ba kiyi ke dai za'a ce kin yi. Don haka 'yan uwa mata sai a kula. Lokaci ya ci gaba da tafi, duk irin yanda Daddy yaso ya samu hadin kan gidanshi abun ya faskara. Sai dai kawai yanzu ba'a samun yawan rigima kamar da, kowace tana 6angarenta, da wuya ka gansu zaune tare. To hakan ya dan kawo zaman lafiya a gidan, shima yana iya bakin kokarin shi wajen ganin ya ba kowace hakkinta, akwai jituwa sosai tsakaninsu da Naja'atu, yana alfahari da aurensu. Wata hudu da auren su, aka sanya lokacin auren Zainab da Khalid. Saboda Zainab din tana shirye- shiryen kammala karatunta, don haka aka shiga hidima. Dai-dai gwargwado ko wane bangare sunyi rawar gani. Naja'atu mamakin soyayyar Khalid da Zainab take yi, kamar dama can sun dade da son juna, idan ka gansu kamar ta gwaye. Sai ta gode ma Allah da ya sanya suka rabu lafiya, ga shi yanzu ya samu madadinta. Da lokacion bukin ya zo, aka sha shagali dai-dai gwargwado. Nan Abuja aka aje amarya, shi kuwa ango murna har kunne, kaunar shi da Zainab wani sirri ne na daban, har mamakin kanshi yake yi, bai ta6a tsammanin za ya so wata diya mace ba irin haka. Sai ya gode ma Allah da ya kaddara cewa itama Zainab din tana kaunar shi. Naja'atu ta sha hidima kamar ta tsinke ranta, kan haka ma Farida sai da ta nuna jin zafinta, tana ce mata 79 Sirrin Zuci.. 4 Saʼadatu Saminu Kankia zakakka, ba ta kula ba. Ta wahala sosai, don haka ana gama bukin ta rinka jin ciwon jiki, a hankali zazzabi ya taho, ga baki daya ta kasa gane abin da yake damun ta. Ranar kwana tayi kwarara amai, ga shi ranar Farida се ke da aiki. Da safe Daddyn ya shigo duba ta, ganin halin da take ciki ya sanya ya dauke ta suka tafi tare ya fara aje ta asibiti, ya ce za ya je wajen aiki ya dawo sai ya mai da ta gida. Ya barta nan likita yana duba ta. Sunyi mata gwaje-gwaje da aune-aune, sakamako ya basu tabbacin tana da shigar ciki. Abun ya yi mata dadi, ta san Daddy za ya yi farin ciki, kullum yana yi masu korafin rashin haihuwa. To yau ga shi Allah ya kawo. Daga ofis shi kuma aiki ya yi mashi yawa, ga shi za sy shiga meeting. Don haka ya yi waya gida ya cе Mummy ta tura direba ya dauko Naja'atun daga asibiti. Ita

Chapter 6 of 7