Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
6 / 6
yanzu duk ya yi missing din wannan shagwabar da ta saba ma shi. Ya saukar da ajiyar zuciya a hankali ya ce "To ai kinga irin abubuwan da suka sa nake kara nace maki har kike ganin laifina, nayi missing din ki sosai, amma ina nan ina ta addu'a Allah ya nuna mani ranar da za ki dawo kusa dani in rinka samun kulawar da kike magana." Naja'atu ta rumtse ido tana dariya sai ta yi mashi sallama ta rufe wayar Daddt nema yake yi ya shagaltar da ita. To bai fito ba ranar anma da daddare ya na kwance cikin falon gidanshi yayinda Farida ke zaune gefe guda ta dukufa karatun wani Novel abun yakan bashi haushi ba ta da lokacin kanta balle nashi daga karance-karance sai kallo kamar Ibada, da ta tashi abin ta take karyawa dashi kenan, haka nan barci ke raba ta da littafi. Ya juya yana kallonta ba ta ma san yana yi ba, sai ya girgiza kai ya dan lumshe ido na wani lokaci wani abu ya tsargu cikin jininshi, sai kawai ya lalubo wayarshi ya kira Naja'atu, tana cikin daki ta gama sallar Isha'i ta ji wayar, ta dauka tana ınamakin Daddy, sai ta bude ta amsa mashi da sallama ya ji muryarta har cikin zuciyarshi, ya sanya hannu yana shafa kanshi, ya ce "Ka da dai in ce har kin kwanta.?" Та се "A'a na gama sallaha ne." Ya ce "To yaya garin, ina labari? Ta yi dariya ta ce labari ai yana hannunku." Daddy 77 dan zolaya ya saki jiki ya rinka janta da hira, yana Kyalkyatar dariya. Farida da ta dukufa karatun littafinta ta rinkа jin muryarshi sama-sama, yana magana tasan dai a waya ne, ba ta maida kai ba ta ci gaba da karatun, a hankali zuciyarta ta fara raya mata wani abu, sai ta tsagaita da karatun tana sauraren maganar da yake yi, ya shagalta sosau hira ta yi dadi da Naja'atu, ya ce "Kina shakku a kaina har yanzu, ni kuma nasha fadi maki cewa zani baki mamaki, me yiwuwa ranar da kika zo gidana kin tabbatar da abin da nake fadi." Wani azababben kishi ya taso mata, da karfin ta ta taso ta nufo Daddyn niyyarta ta fizge wayar ta jefar ta fashe baki daya a huta, amma Daddyn ya daure fuska sosai, yana jifarta da wani mayan kallo, sai taja ta tsaya tana huci, yayi ma Naja'atu sallama, ya rufe wayar bai ce mata kanzil ba, ya mike zaya bar mata wurin, tasha gabanshi da sauri ta ce "Wai mahaukaciya ka dauki ne ko me? Da zaka zauna gabana kana magana da wata 'yar iska." Ya tsura mata ido ya ce "Amma kin san ke ba ki da iko dani, ba ki isa ba kuma ki hana ni yin abin da na yi niyya, wannan 'yar iskar da kike magana, ta fiki hankali da tunani, don ita ba sakarya bace, irin ki." Ya raba ta ya wuce cikin daki abinshi, ta fasa kuka ta fada kan kujera wulakancin Daddy ya isa, 78 duka sati daya da aurensu ba a yi ba, har sun fara rigima irin haka, sai ta tashi zaune tana tunanin mufita. A can cikin daki shima ya cika sosai, ya yi wanka ya fito ya yi nafila, shafa'i da wuturi, sannan ya fito ya shiga kicin da kanshi ya hado shayi ya dawo dakin yasha, yayi kwanciyarshi. Lokaci kankani barci ya debe shi. Can cikin barci ya ji Farida tsaye kanshi tana magana, ya ture bargon ya na kallonta ta ce "Watau ma ba kə damu da abin da kayi ba, shi ne kazo kayi kwanciyarka, ka maidani mahaukaciya, to wallahi ba zaka yi barci ba, sai ka fadi mani matsayina." Ya sa hannu yana shafar fuskar shi, ya ce "Matsayinki ai ga ya nan na nuna maki, tunda gashi na aure ki, kuma gashi kina wasa dashi, don haka nima ina da right din da zani yi abin da nake so ko kuwa ni bani da iko dake sai kece kike da iko dani? Ko ko kina tsammanin zaman da kike yi kina karance-karancen tsiya baki da lokacina baya damu na? To yarda kike ganin karatun ya fiye maki, nima abin da rayi ya fiye mani, kuma ban baki a boye ba don ma ki sani a duk lokacin da na gama shiryeshiryena zani auro Naja'atu, in kawo ta cikin gidan nan, in ba ki san yarda ake tafiyar da miji ba, sai ki koya wajenta. Farida ta rumtse ido tana jin zuciyarta kamar zata yi bindiga, ta tsani ko ji tayi ya ambaci sunan Naja'atu, balle har yana maganar aurenta, sai ta cije lebe tana kallonshi, a wulakance ba ta ce komi ba ta koma dakinta ta kwanta tana tunanin mafita, dole ne ta mike tsaya taga ta raba zuciyar Daddy da kaunar Naja'atu kwata-kwata sai ta zame mashi kamar dodo, ya ji ya tsani ko ganin ta ya yi. Shin zata yi nasara? To mu hadu cikin littafi na hudu kuma na karfe insha Allah. Taku; Anty Uwanin Kankia 80 An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 6 of 6