Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 6
wujiga, akwai alamun gajiya tare dashi, sai ta dan saki fuska ta ce "Ango kasha kamshi." Ya zuba mata ido a wahale yana murmushi ya ce "Ko kuma na sha wuya ko.?" Ta ce "Bayan wuya ai sai dadi." Ya dube ta kawai, sai ta gaida shi ya tashi zaune yana kallonta ya сс "Yunwa nake ji me za ki bani in ci.?" Duk abin da kake so muna da shi." Ya ce "Kamar me.?" Ta ce "Akwai abinci sosai, sai wanda ranka yake so." Ya ce "Matsalar ba zani iya cin abinci ba, tun jiya nake jin yunwa da uta na kwana." Ta yi dariya ta cc "So ka yi ai da kazo ka ci nan gida, amma dai bari in zo." Ta fito ta shiga kicin ta shirya mashi kayan shayi, ta kawo mashi ya hada ya fara sha, sannan ta koma kicin din ta zubo mashi sunasur da waina da miyar ganye, ta şanshi da son abincin gargajiya, ai kuwa ya ji dadi don haka ya saki jiki sosai ya ci abincin. Ta na son ta fito, amma ya hana ta dole ta zauna tare da shi ta rinka kallon dakin duk kayanshi suna nan bai tattara komi ba, ta dube shi ta ce "To wai kai da ke shirin tashi gidan, amma ba ka yi niyyar tattara kayanka ba sai yaushc.?" Ya zuba ma ta ido da wata irin siga, ya ce "An fadi maki don nayi aure shi kenan na tashi daga gidan.?" Ta сe "To me zaka yi.?" Ya ce "Ni da ke da babbar ajiya, ai in har kinga na bar gidan nan to na dauke ki ne." Ta yi dariya, ta ce "Sai ka ce wata tsuntsuwa.?" Yay: dariya ya ce "Shiri na ba'mai wuya ba ne, idan na samu lokaci zani debi abubuwan da nake 60 bukata, amma don yanzu ba zani saki dakina ba, idan na zo maki yini, ina zani rinka hutawa." Naja'atu ta yi murmushi ta ce "Cika baki dai kilama daga gobe ba zamu kara ganinka ba sai hali." Ya zuba mata ido ya ce "Haka kike so ko.?" Ta ce "Ba haka ba ne, wai dadi amarci ya boye ka ko? Sai ya yi dariya ya jinjina kai ya ce "Tun da haka kika ce shi kenan sai dai ina mai tabbatar maki cewa yarda ke kike tsaımmani, ba haka kuma za ki gani aikin riga kin kasa mani zuciyar gida biyu." Naja'atu tayi dariya kawai ta duka tana tattara kwanonin ta cc "Bari in barka kayi shiri, kada ka makara lokacin yana karatowa." Ta dauko kwanonin ta fito. Kicinta koma su ka ci gaba da hidimominsu, sai da zaya fito ya leko ya na sanye da babbar riga ta farin yadi, da bakar hula, ya yi kyau sosai, yana kamshin turarc, ya ce mata zaya tafi. Ta yi murmushi ta ce "Allah ya ba da sa'a a dawo lafiya." Ya ce "Ashe tare da Inna aka zo baki fadi mani ba.?" Ta ce "Mantawa nayi, nima ban yi tsammaninta sai gasu sun iso dazu." ya ce "Mun gaisa da ita ne yanzu kin kara yi mani godiya, Allah ya bada ladan zumunci." Amina ta rinka yi mashi tsiya ta ce "Ka tafi kada a tashi daura auren baka kusa aba wani." Zainab ta ce "Ba bakin ba insha Allahu wannan auren anyi an gama ko bayanan ba 61 za'a fasa ba, don itama amaryar ba zata yarda ba." Ya dubi Naja'atu yana dariya ya cc "Idan ma an fasan ai ga wata nan sai in kwaso tawagata azo nan a daura da ita, shi kenan kowa ya huta." Naja'atu murmushi kawai tayi ita kadai tasan yarda take jin zuciyarta kamar ta dora hannu aka ta saka kuka, yayi mata sallama ya fice sai taji har wani jiri-jiri yana dibarta shi kenan dai Daddy ya kubce mata ta zauna bisa kular abinci, tan ajin su Zainab na ta gulmar Farida to ita kam komi za'a fada kan Farida yanzu ta gama da ita, tunda ta shiga gabanta, gani take yi daga yau ta rabu da Daddy. Zuciyarta ta kasa samun natsuwa don haka ta fito ta shiga dakinsu ta kwanta kanta yana ciwo kamar zaya tsage, cikin dan lokaci zazzabi ya lullube ta ta kudundune cikin bargo zuciyarta cike da tunani iri-iri dama a dawo ace an fasa daurin auren." Abin da ta rinka raya ma zuciyarta kenan, sai dai tasan da kamai wuya, dole ne ta natsu ta daina yaudarar zuciyarta ta tsaya ma gaskiya, "Anya ma Daddy ba yaudararta yake yi ba, ya na bata mata lokaci? Tun da ga shi ya na ta hidimar aurenşhi hankali kwance jiya ya zubda kudi sosai wajen party haka nan har cikin dare yana tare da Amaryarshi suna watayawa, yanzu ma gashi ya sheka wanka ya ci kwalliya sai rawar jiki yake yi ya tafi daurn aure, idan ba ya murna ai ba zaya yi haka 62 ba, koda ya ke dama bai taba gaya mata baya son Farida ba, ya sanar da ita su duka yana sonsu, amma yanzu da kanta ta fahimci cewa ya fi son Parida, tunda ga shi ya aure ta. Wasu hawaye masu zafi, su ka rinka fita daga idanuwanta, tana jin tausayin kanta. Zainab ta shigo ta same ta cikin wannan yanayin, da ta taba jikinta ta ji zafi, sai ta fita ta kawo mata magani tasha ta koma ta kwanta. Cikin ikon Allah da ta samu barci ta tashi sai ta ji karfin jikinta, don haka tayi wanka, su ka sha kwalliyarsu anko din shadda ita da Zainab suka sake ana ta hidimomin biki da su. Har dare Daddy bai sake shigowa gidan ba, yana can yana fama da jama'a đon haka ta rinka kokarin ganin ta circ damuwa daga ranta, so take yi ta dasa ma zuciyarta hakuri akan Daddy. Da yamma su ka yi waya da Khalid ya na tambayarta hidimomin biki, ta yi murmushi ta ce "Alhamdulillahi komi yana tafiya lafiya." Ya ce "To ki taya mu addu'a mu ma Allah ya nuna mana lokacin namu haka." Ta yi murmushi ta ce "Amin." Ya ce "kin fadi ma Daddy ina yi mashi fatan alkairi tare da murna. Ta amsa "To:", kawai amma ko giyar wake tasha ba zata fara sanar da Daddy sakon Khalid ba, kusan shi ya ma fita kishi idon har ta sanar dashi sai ya bata rai, shi yasa bata fadi mashi komi dangane 63 da lamarnta da Khalid abin da ya ke dauka ma kwata-kwata ba su magana ita kau abin da takc hange daban, ba zata yi kamun gafiyar baidu ba. Har yamma tana nan gida ba ta je ko ina ba, amma su Zainab sun tafi gidan Amarya tare da Anty Nafisa, babbar Yayarsu. Ita kau ta cc "Babu in da za ta je ta zauna tana taimaka ma Mummy da hidimar jama'a. Da daddarc ma, duk Jama'a ana gidan Amarya, wasu kuma sun tafi daukar Amaryar daga gidansu zuwa gidanta, don haka Naja'atu tayi shigewarta cikin daki, tayi sallar Isha'i ta zauna tana ci gaba da addu'o'inta har dare yayi su Zainab basu dawo ba, Inna ma suna can gıdan Amarya, ita kuma Mummy tare ta ke da bakinta, don haka ta zauna shiru ba ta da abokin hira, ta yi kwanciyarta tana duba wani littafin addu'o'i tana jin wayar Daddy ya na kiranta, amma ta ki dauka. Sai da su Zainab su ka shigo ta ce taje Daddy ya na kiranta waje. Ba ta yi gardama ba, ta taso tafi, yayin da su Zainab ke ta shirin tafiya dinner ita kam bata yi niyyar zuwa ko ina ba, ta gaji kwanciya zata yi. Ta fito ta same shi zaune cikin mota, ya zuba mata ido yana nazarinta, ya ce "Zainab ta ce mani baki jin dadi me ya ke damun ki.?" Ta yi murmushi ta ce "Kaina ne ya ke yin ciwo, da zazzaßi nasan gajiya ce kawai." Ya ce "Yanzu yaya za'a yi 64 cnan" Ta kafa mashi ido ta ce kamar yaya.?" Ya Korasibiti zamu je?" Pa yi dariya ta ce "Abun bai kai na asibiti ba, ai na sha magani na ji sauki." Ya ce "Ba wata matsala ko.?" Ta girgiza mashi kai, ya ce "To gasu Zainab nan sai ku shirya kuje wajan Dinner na basu ticket a hannunsu." Ta daga kai tana kallon wani sashin ita kam bata ra'ayin zuwa wata Dinner. Shima ya ci gaba da kallonta ya ce "Kada kice mani ba za ki je ba, don mi zaki yi ta zama gida, alhalin kowa ya fita.?" Ta dan yatsuna fuska ta ce "Na gaji ne so nake yi in zauna in huta." Ya ce "Ni kuma gaskiya in ba ki je ba baki yi mani adalci ba." Ta dan cije lebenta tana kallonshi, ta ce "Ni Daddy ba wai bani son zuwa ba ne, ko makacın haka matarka ba zata ji dadi ba, sai ta dauka saboda wani abu ne ko jiya kiri-kiri na yi mata magana amma ko kallon arziki bata yi mani ba, sai ta dauka ina shigar mata harka ne." Ya ce "To ai ba don ita kika je ba, ni na gayyace ki yanzu ma sabo da ni zaki je, sai dai in baki zuwa na san ra'ayin kanki ne." T'a zuba mashi idc kawai, bata ce komi ba, ta juya ta koma ciki babu yarda zata yi dole ne ya shirya su tafi, idan ba haka ba ta bani da korafin Daddy kilama ya yimata fushin ko da ya ked yanzu koma ya yi fushin ba za ta gani ba, haka nan abun ba zaya yi tsanani ba, tunda ba ya gidan sai yazo 65 amma dai yarda shi yake kokarin kwantar ma ta da hankali, ya na sanya ta cikin dukkan harkokinshi, yana da kyau ita ma ta rinka kyautata mashi. Su Zainab har sun shirya, don haka a gaggauce tayi shirinta su ka fito, motar Anty Aisha su ka shiga, su ka tafi. Sai da gwammace da bata je wajen ba, saboda shirin da aka yi ya bugi zuciyarta sosai, angon da Amarya anko suka yi na farin leshi iri daya, ban da wannan ma, manne da juna suka shigo cikin dakin taron, sai wani lallabata yake yi sai kace kwąi, Naja'atu ta kara raina kanta tabbas tana wahalar da kanta, ba ta san Daddy ya na kaunar Farida ba, sai lokacin, sun hada kansu sai kuskus dinsu suke yi su na dariya, ya shagalta ya manta da jama'ar da su ka tara, sai nuna mata soyayya yake yi, abun har kunya ya ba ta, fitsarar tayi yawa. Zuciya tazo ma ta iya wuya, ba ta ankara ba, ta ji hawaye sun cika mata idanuwa, ta yi dubara ta sanya mayafinta ta share saukinta guda shi ne da ya ke su Zainab ba su kusa da ita, ta kifa kanta cikin cinyoyinta tana nadamar zuwanta wurin, da ta sani ta yi zamanta, fushi ne dai yayi ya gama, idan ma ya ce daga yau din ya daina yi mata magana ta kwana gidan sauki, tunda tasan dole ma sun rabu kenan. Zuciyarta ta rinka raya ma ta cewa, dama dón ya wulakantata ne ya matsa mata, sai tazo gashi kau 66 ta gani ta tsani kanta ta tsani Daddyn kanshi, jdanuwanta suka rufe da tsananin kishi, sai taji ta fita tabar fakin taron ya fiyc mata kwanciyar hankali, idan ba haka ba kau, zuciyarta zata iya tarwatsewa, kara ta fito ko taxi ce ta samu ta maidata gida. Ta bude jikkarta ta duba tana da isassun kudi a ciki, sai ta maida ta rufe ta dan saurara ana ta cashewa Amarya da Ango na cikin fili, su Zainab ma ana ta liki bankalin kowa ya tafi can, don haka tayi amfani da wannan damar ta mike ta fice. Zuciyarta ta yi mata sanyi, ta rinka tafiya da kafa har ta fita daga harabar Otel din, sannan ta tsaya tana jiran mota. Hankalinta ya yi nisa sosai, wajen tunane-tunane, sai dai ta ji muryar mutum kusa da ita, ta dan razana taja da baya tana kallonshi a tsorace yanayin shi ya canza sosai, ya ce "Ina za ki.?" Ta daga kanta tana kallon Titi, ba ta ce mashi komi ba. Ya yi shiru ya na nazarinta ya fahimci matsalarta duk da cewa tana kokarin dannewa yasan kishi ne, sai ya ji tausayinta, ya jinjina kai ya na yi mata magana a hankali, ya ce"vi hakuri kizo mu koma." Ta girgiza kai ta ce "Na gaji ne so nake yi in je in kwanta." Ya ce 'To muje in kai ki" Ta се "Ка barshi kawai, zani samu tasi yanzu." Ya ce "Don Allah Naja'atu kada ki tayar mani da hankali cikin wannan lokaci. Ta zuba'ma shi ido cike da tsana ta 67 cc kai kaso, saboda ai na san kana wajen, amma don kada in takura maka ban ce kazo ka maida ni ba, na fito to sai ka rabu dani ka koma ka ci gaba da hidimomiu ka." A hankali ya saukar da ajiyar zuciya, ya се "Na ji ba ki kira ni ba, amma don Allah kiyi mani wannan alfarma, ki dawo muje, sai in yi ma Aliyu magana ya zo ya maida ki." Ba ta ce komi bai, ta juya tayi gaba shi kuma ya biyo ta, amma sai da ya riske ta suka jcra har cikin harabar Otel din. Nan su ka yi karo da Farida, cikin 6acin rai ta rufe Naja'atu da bala'i ta ce "To munafuka, gani na fito marar zuciya, yau dai ai kisan nayi tunda gashi ya nuna baya yi da ke, yanzu ya zama nawa, in kina son kanki da mutunci, to tun wuri ki fidda tunanin Daddy a ranki, idan ba haka ba zamu sanya kafar wando daya dake, banza bakauya." Zuciya tazo ma Naja'atu iya wuya, wai mace 'yar uwarta ce take wulakantata haka?. Ba ta gama wannan nazarin ba, taji Daddy da kansi ya na bata amsa, ya ce "Ba ita zaki yi ma rashin kunya ba, ni za ki yi mawa, tunda ni ne na ce ina sonta, kuma haka ya ke a raina har yanzu, kuma yarda ki ke takama na aure ki yau, itama ba da dadewa ba aurenta zani, meye nata a ciki da za ki tsaya kina fadi inata magana, to na dai gaya maki bani son irin wannan sakarcin, in har za ki 68 wulakanta Najo'atu a gabana, to kuwa nima zaki iya yi mani." Da sauri Naja'atu ta juya zata tafi, ya rike ta yana kallon cikin idonta, ya ce "Na fadi maki ba za ki bar wajen nan ba, sai an tashi." Ta rumtse ido tana girgiza kai, ta tsani tashin hankali ta ce "Don Allah ka rabu dani in yi tafiyata." Ya ce "Ba za ki je ko ina ba." Sai ta zame hannunta cikin nashi, ta koma ciki kan hanya ta hadu ta da su Zainab tana tambayarta abin da ke faruwa, anje an fadi masu gasu can suna fada da Farida, Naja'atu ta yi murmushi ta ce "Babu kumi." Su ka koma ciki. Sun jüna zaune sannan Daddy ya shigo tare da Faridar, to iia dai Naja'atu ko kailon sashin da suke ba ta sake yi ba, gaba ki daya ma zama wajen don dole take yinshi, idab bacin bata son su yi ta gardama da Daddy da tafiyarta zata yi. Da aka tashi da wuri ta fita suka yi tafiyarsu, tana sane da cewa wayarta a rufe take, tasan Daddy zaya neme ta, amma ta ki budewa ba ta bukatar jin wani abu daga gare shi, ba zata iya wannan bala'in na matarshi ba. A can shima Daddy cikir: falon gidan Aliyu ya ke kwance bisa kujera iri-kiri barci ya faskari idanuwanshi, ya rinka auna wannan al'amarin, sai ya rinka ganin ya rabu da Naja'atu kawai shi ne kwanciyar hankalinshi, yau kukan da Farida ta yi mashi kafin su rabu ya tayar mashi da hankali, ya tsani wani ya yi kuka da shi kan wani abu, tabbas 69 abin da Faridar ta ec yana yaudararta zaya iya zama gaskiya, to itama Naja'atun abin da tako hange kenan. To sai dai mda ya natsu ya rinka auna matsayin Kaunar Naja'atu a cikin zuciyarshi, sai ya ji sam ba zaya ıya rabuwa da ita ba, koma ya ce ya yi hakuri zueivarshi ba zata lamunce mace mashi. Ya lalub: way a ya kira layinta, kashen dai yake ya jima ya na nemanta yasan saboda shi ne ta rufe wayar, a hankali ya saukar da ajiyar zuciya, sai ya rufe idanuwanshi yana addu'ar neman taimakon Allah a cikin lamarın." Da safe yana kwnace, har yanzu dai bai samu yin magana da Neja'atun ba, ya kira Zainab yana tambayarta Naje'atun, ta ce ga ta'nan kwance ba ta tashi ba." Ya ce "Shi kenan." Ya rufe wayar, ya aje gefe guda, ya na tunanin yarda zaya yi da yariny. A can itams Naja'atın tana jin shi da Zainat, ta yi lamo ta kyale su, sai da tagaji da kwanciya doG kanta, sannan ta yi wanka ta fito, yawanci bakin de su ka zo daga nesa, su na ta haramar tafiya, har da Inna, ta shiga dakir da su Iunar su ka kwana, ta gaisa da wadanda ba su tashi ba. lokacin da ta sbiga. gaida Inna, sannan ta zeuma kusa da Ionar, Inoa ta rinka yi mata rasiha, tarr da gargedata akan ta ci gaba da zama da mutane lafiya, ba ta son rigima. Karfe daya da rabi seka tafi soi ta ji knar ta bisu, zaman Abujar dak ya gundure ta, to tasan 70 Mumny ba za ta bari ba, haka shima Daddyn, idan ya ji tasan wata rigimar zata dauko ma kanta. Da yamia ne ya shigo gidan amma bai ganta ba, har ya fita. Bai ji dadin hakan ba, to amma da ya ke ya lura gudunshi take yi sai ya sharc ta yaga iya guduntga, kwana daya, biyu, har zuwa na uku da gama bikin, duk baki sun tafi Zainab ma ta koma makaranta, su kadai ne a gidan daga Mummy sai Ibrahim sai kuma ta rinka kewa, babu Daddy ga shi Zainab tayi tafiyarta, idan Ibrahim ya tafi makaranta sai ta zauna ita daya Mummy saboda gajiyar biki ba ta cika zaman falo ba, kwanciyarta take yi cikin daki tana hutawa, don haka zaman ya dan fara takura ta, amma tana kokarin dannewa kada Mummy taga damuwarta. Da sanyin marece na ranar Laraba Mummy ta fita zata je duba wata Kawarta Hajiya Barira, bata jin daui taua kwance asibiti Ibrahim ma ya tafi lesson, bai dawo ba, sai ita kadai a gidan da mick yana aiki cikin kicin ta fito sanye da atamfa 'yar Holland ruwan kunun kanwa, ta zauna falo tana kallon wani film a tashar Nollywood hankalinta ya tafi sosai tana son ta ga yarda zaya kare. A hankali ya shigo cikin falon sanye da kananan kaya, shirt fara mai dogon hannu da bakin wanão, idanuwanshi manne da gilashi muryarshi kasa-kasa yayi sallama don haka ba ta ji ba har ya shigo cikin felon, sai dai 71 kawai taga mutum tsayc gabanta, zuciyarta ta rinka harbawa da sauri sai ta rumtse ido tana ncman taimakon Allah, yayin da wani abu ya tsargu a jininta, a bangare daya kuma kishi matsananci ya taso mata, sam ta tsani ganinshi. Bai ce mata komi ba, ya zauna yana kallonta kawai, itama ta kasa cewa komi, ta rinka kokarin hade wani da ya tase mata yana neman hana ta lumfashi "Me Daddy zaya ce mata yanzu, bayan ya nuna mata iyakartą, ya nuna bai damu da ita ba, ya sharc ta tsawon kwanaki. Sai ta ji tausayin kanta, tabbas son maso wani koshin wahala be, ita kam ta yarda tana tare da wahala. Ta rinka kokarin sassauta zuciyarta, sannan ta dube shi ya zuba ma ta ido ta gilashi ya sanya harshe ya lashi busasshen lebenshi sannan ya yi gyaran murya ya ce "Naja'atu har yanzu fushin kike yi baki tausayina ko.?" Zuciya ta tsaya ma ta iya wuya, rainin hankalin Daddy ya isa kenan ita zaya azama laifin? Ko da yake ba yinshi ba ne, giyar amarci ce ke gaya mashi karya. Ta jinjina kai amma sai ta kasa ce mashi komi, yayin da shi kuma ya zauna dai dai cikin kujera ya dauki remote ya nemo tashar kwallo, suka yi shiru na 'yan mintuna sannan ya aje remotc din ya na kallouta, ya ce shi ne ko kiyi jajena kwana biyu kuma kin kama waya kin rufe don kada kiyi magana da ni ko.?" Naja'atu ta 72 dan tabe baki cikin halin ko in kula ta ce "Aí na san lafiyar ke haifar da shiru, ko so kake yi in kira ka ko kuma kai ka kira matarka tayi ta tsira mani wani bala'in, maganar gaskiya Daddy ina gudun fitina, ina ganin mu hakura da juna kawai shi yafi." Ya yi murmushi ya ce "Idan ke kina jin za ki iya hakuri dani, to ni ba zani iya ba, kuma in kika fadi haka ni baki yi mani adalci ba, idan kika duba ai ba dani kika yi rigima ba, da Farida kika yi kuma dake da ita a karkashin inuwata zaku zauna, dole ne kubi tsarina, kinga kenan babu dalilin da zaya sanya kice saboda ita kin rabų dani, sai i da ma kinyi niyyar rabuwa dani din don ra'ayin kanki wannan ba zani takura maki ba." Naja'ati ta sarda kai ya daure ta sosai, da igiyar kaunarshi abin haushi sai ma taji ta kara kaunarshi ya yi wani kyau na rnusamman ya yi fresh, alamun koshin lafiya da kwanciyar hankali, ko don ta rabu da ganin shi ne, sai taga ya kara yi mata girma kwarjininshi ya cika falon duk irin yarda ta kudurta share shi abun ya çi tura. Yayin da shi kuma duk ya marairaice mata ya cikata da hirar soyayyarshi, ya kwanta kan kujera yana jifarta da mayen kallon nan, ai don da nan ya ida luguiguitar da zuciyarta, ta kasa tabuka ka komi, cikin ruwan sanyi ya shawo kanta ta saki jiki suna hira. Nan Mummy ta dawo ta same su sai dai kawai ta girgiza kai suka gaisa, ta shige diaki, wani lokacin haushin Naja'atun take ji ta na ganin rashin wayaunta akan biye ma Daddy da take yi yana Gata mata lokaci, idan ita ce tunda har yayi aurenshi wallahi ko kallo bai ishe ta ba, to ta biyc mashi bata san me yake fadi mata ba, da yake shagaltar da ita irin haka. Da aka yi kiran sallah, ya fita a tunaninta ya tafi kenan, amma sai ga shi ya dawo da iyayen sayesayenshi, ya yi mata na kayan kwalama har da IceCream. Nan ma su ka dasa wata hirar, yana kara jaddada mata irin kaunar da yake yi mata, sai ta rinka ganin kamar ba ya son wata diya mace idan ba ita ba, to wai ma yana da lokacin Farida kuwa? To in baya da lokacin ta meye amfanin ajetan da ya yi gidanshi, ga alamanan ma ta gani,sai wani kara budewa ya ke yi idanuwanshi sun bude yanayin kallon da yake yi mata ma ya canza sosai, har tsikar jikinta ta tashi take yi, to itama Faridar haka yake fadi mata? Abin da ta kasa tantancewa kenan, halin maza sai su, tana ganin kokarinsu wajen raba zuciyarsu da suke yi. Dare ya fara mikawa, yana kwance abinshi ba ya da niyyar tafiya, ya sanya ta kawo mashi abun, ya zauna ya ci hankali kwance. Karfe tara ta dan wuce Mummy ta fito daga cikin daki, tana kallon agogo ta ce "Wai Daddy kanka daya da zaka aje diyar mutane ka zo nan ka zauna.?" Ya dubi 74 Mummun yana shafa kai, sai kuma ya kalli Naja'atun kunya ta rufc ta, ta sarda kai tana jin nauyin Munuyn, Mummy ta ce "Tashi maza ka tafi bani son sakarci, ta harari Naja'atun da wasa ta се "Kema har da ke, kin zauna kin biye mashi yana ta tsara ki." Naja'atu kam ba baki, ita kam bata lura da lokaci ba, Daddy ya shagaltar da ita sosai, yayin da shi kuma ya aje remote din kan tabur ya mike yana kallonta, Mummy ta girgiza kai ta wuce kicin, ya zuba hannayenshi cikin aljihu, ya ce "Ba ri dai in wuce kada Mummy ta kai ga dukana, amma don Allah kada ki rufe mani waya zani kira ki kafin in kwanta." Ta amsa "To", kawai ya yi mata sallama ya tafi, ya na fita ta rufe wayarta, Ibrahim ya fito daga dakin karatu ya zauna su ka dasa hirarsu. Zuciyarta ta yi sanyi, dk wani 6acin rai da ta rinka fama da shi na 'yan kwanaki Daddy ya wanke shi fcs, har taje ta kwanta tana tunaninshi da hirarsu ta yau, wata sabuwar Kaunarshi ta kara mamaye zuciyarta tabbas yaudarar kanta take yi da take tunanin cewa zata iya rabuwa dashi, itama tasan ba zata iya ba, sai dai ta ci gaba da addu'a Allah ya yi mata zabi mafi alheri. Washe gari tana bude wayarta text dinshi ya shigo da kalamai masu dadi, ya na kara jadadda kaunarshi gare ta, tà gama karantawa ta ajc wayar 75 Ihushi farin ciki fal da cikinta, yanzu kam ta yarda Daddy yana sonta tunda ga shi ya yi auren bai canza ma ta ba. Ba'a ji ma ba ya sake kira su ka gaisa yana yi mata tsegumin jiya ta rufe mashi waya. Ta yi munnushi ta ce "Ni ban dauka wai da gaske zaka kira ni ba, naga ka koma cikin iyalinka koda yake laifin Faridar ne da ta baka damar yin wata waya cikin daren alhalin lokacin ta ne ko zaman da kayi nan fa jiya ka shiga cikin lokacin ka, don haka gaskiya ka daina kana shiga hakkinta, kuma kasan ance bulalar uwargida tana nan an aje ma amaryarta, ni kam ba zani dauki irin haka ba, kai ba zani baka damar da zaka saurari wani ba ma, in dai har kana tare da ni. Daddy dariya ya rinka yi mata, ya ce "Allah ko.?" Ta ce "Kana wasa da ni ne." Sai ya ji dadi a ranshi, matsalar da ya fara fuskanta da Farida kenan tun ba'a je ko'ina ba, ba ta damu da tsayawa kan al'amurranshi ba, yarda ya saba yi ma kanshi komi, yanzu bai samu wani sauyi ba, idan ta zauna tana kallo mantawa take yi da komi har shi din, haka nan da safe ma barci sai ta kai azubur kusan shi ke hada ma kanshi kalaci don haka ya yi kewar Naja'atu tabbas Naja'atu mace ce tagari wadda tasan ciwon kanta, koda yaushe tsaye take akan dukkan al'amurranshi, yana ganin kokarinta ya na jinjina 76 mata

Chapter 5 of 6