Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 6
babu yarda za'ayi in ki daukar wayarta da gangan." Ya sa ki ranshi yana dariya, ya ce "Na yarda yanzu ina labari.?" Ta ce "Labari yana kannunka, tunda kaine idona." Yace "Ban yarda ba, kece idanuwan dai ni yanzu tamkar makaho nake kuma bani da dan jagora, me yiwuwa sai ranar da na dawo gare ki." Tа сe "To Allah ya nuna mana ranar zani fi kowa farin ciki, saboda nasan wani ci gaban mu ne dama kasar mu baki daya." Zuciyarshi ta yi sanyi, suka yi ira mai dadi ha baya son su rabu. Naja'atu nauyinshi ta rinka ji, da jina sauraren irin kalaman da yake fadi mota, tabbas kauna ce 'yar usuli, kuma a cikin zuciyarshi take tana sha'awar 15 halayyar Khalid zata so ta yi rayuwa dashi ta har abada sai dai kashi Kaunarshi Ďaddy tarinja. Ya zuciyarta ta yarda ita kanta bata son yarda zata sarrafa zuciyar ba har ta sama ma wani matsugunni a cikinta don haka lokuta da dama idan ta tuno Khalid din takan ji tausayinshi kamar ta yi kuka so da banne, ta kanyi mashi addu'a da fatan alkairi akan dukkan al'amurranshi. Har bayan sunyi sallama tana jin kalamanshi sunayi mata karakaina a kwakwałwa, da tunanin ta kwanta ta dan samu barci sai yamma ta tashi tayi wanka, ta sanya riga da sike na wani leshi blue dinkin dan kib-kib, daidai jikinta tana son yanayin rigar ta dace da tsarin hattar jikinta ta zauna bakin madubi ta dauki tsawon lokaci tana gyaran fuskarta ta fitofresh, ta yi kyau jikinta yana kamshin body spray masu kamshin, kayan marmari, Daddy ne ya zaba mata ya ce favorite dinshi kenan, yau da gobe har sun kama mata jiki. Ta daidaita daurin kallabinta, fuskarta ta fito ta tsaya tana kallon kanta ta madubi ta yi kyau daidai gwargwado, sai ta yi murmushi zuciyarta na kan Daddy ya ci ace zuwa lokacin ya dawo gida. Ta saba duk asabar yana fita ya bada motarshi wajan wanki ayi mashi 'yan gyare-gyaren da take bukata, da wannan damar ne yake yi amfani yaje wajen Farida, babu shakke yana can tare da ita. Sai ta rufe idanuwanta ta jin watar kishin tana ruruwa zuciyarta, daidai lokacin taji shigowa motarshi cikin harabar gidan, sai ta saukar da ajiyar zuciya, wani sanyi yana ratsa ta Daddy da banne a ranta, Ta daga 16 labule tana kallonshi ya bude sit din baya ya fiddo wata katuwar jikkar Ibrahim ya dauko suka shigo tarc. Da ta fito Ibrahim ya shi da jikkar cikin dakin Mummy ta zuba ma fuskar Daddyn 10o, har yanzu ba ya da walwala, bai ce mata komi ba, ya rabata ya nufi fakinshi, sai tayi murmushi ta zauna falo tana jiranshi ya fito cin abinci, amma shiru bai fito ba, tasan duk fushin ne a kalla minti talatin da shigarshi, ta dauki waya ta kirashi shiru kamar ba za ya dauka ba, sai ta ji babu dadi, bata san abin da Daddy ya ke nufi ba, dan abu karami sai ya dauki fushi da ita. Kafin ta tsinke ya dauki wayar ta ce "Ka fito ka ci abinci mana." Ya ce "ki barshi kawai na koshi bai jira ba ya katse layin." Ya aka yi, sai kuma ta sake kiranshi ta ce "Daddy ma kaci da zaka ce ke koshi.?" Ya ce "Abincin me zaki matsa mani inci tunda baki son kwanciyar hankalina." ta ce "Don Allah Daddy kayi hakuri ka aje maganar nan gefe daya, kai fa musulmi ne riko baya da kyau, daga ni har kai babu wanda yasan abin da zaya faru sai Allah, to mu duka mu ci gaba da neman zabinshi, ba wai son zuciyarmu ba, Daddy idan ban damu da kai ba, ba zani rinka shiga harkarka ba irin haka." Ya saukar da ajiyar zuciya ya ce "Shi kenan kawo mani abincin nan." Та се "Gaskiya Daddy kayi hakuri bani son in rinka shiga dakinka, ba kima ba ne, idan muna irin haka sai mu shiga zargi." Ya ce "Babu wani zargi ai ba zama zaki yi ba, ba ni jin dadi ne, zazzabi ya ke neman matsa mani, Mummy kike gudu, to ta fi kowa sanin halin na tasan 17 abin da zani yi tasan wanda zani yi ba, ki shigo ni na baki izini. Ta rufc wayar ta shirya mashi abincin ta dauka ta kai mashi. Ta same shi kwance ya sanya suwaita tabkekiya, kuma ga AC ya kunna, da sauri ta aje farantin bisa tebur ta rufe AC din tana yi mashi fada. "Haba Daddy, ba ka da lafiya shi ne zaka kunna AC kuma." Ya dube ta idanuwanshi sun kada sunyi jajir, ya cc "Ina son in samu saukin zafin jikin ne." Ta cc "Amma ba da haka ba." Ta yi mashi sannu, ta matsa mashi sai da ya danci abincin, sannan yasha magani ya koma ya kwanta jikinshi yana rawar dari, ga alama yana jin jiki, yau 'yan maza balafiya. Duk sai ta ji tausayinshi ta damu kwarai, ta fito ta shiga daki ta sanar da Mummy Daddy ba lafiya. Tare su ka shiga dakin tana tambayarshi abin da ke damunshi ya sanar da ita zazzabi ne kawai, ya ce "To kaje asibiti.?" Ya daga mata kai, jikinshi na rawa, Mummyn ta sanya Naja'atu ta warware bargo ta lullube shi su duka sun shiga damuwa. Har zuwa dare babu wani sauki Naja'atu ta shiga damuwa sosai ta kasa ta tsare ta kasa samun natsuwa, har dare jikin da zazzabi Mummy ta matsa mashi sai ya sake komawa asibiti, shi kuma ya ki yarda ya ce tunda ya ce babu wani dalilin da zaya sanya ya sake koma masu tunda bai gama shan maganin da aka bashi ba. Kafin dare ya galabaita sosai, saboda amai da ya rinka yi akai-akai Mummy ta shiga damuwa sosai, don haka ta yi waya gidan kanin mahaifinsu aka turo Likitan 18 dake dubansu yazo ya duba shi ya yi mashi allurai ya canza mashi wani maganin. To babu laifi ya dan samu sauki har ya tashi ya yi sallolin da ake binshi, jikinshi babu karfi, bakinshi babu dadi ya tashi ya zauna bakin gado. Naja'atu ta shigo dauke da faranti kayan marmari ne da abinci akai, ta aje gefc daya tana kallonshi, shima kallonta yake yi, yana kara jinjina mata tana bakin kokarinta akanshi, sai ya ji ya kara sonta ta taimaka mashi sosai, ya danyi murmushi.ya ce "sannu Naja'atu." Ta ce "kai zani yi ma sannu. ka wahala sosai ba ka gani ba ka dan fada." Ya yi murmushi ya ce "Wallahi kuwa." Ta ce "Allah ya kara sauki, ga abinci nan Mumny ta ce ka daure kaci." Ya zuba mata ido ya ce "Ba ni jin dadin bakina ba zani iya cin wani abu ba." Ta ce "To ga fruits nan idan kasha zaka ji dadin bakin, zuwa anjima sai ka ci abincin." Ta dauki farantin ta mika mashi ya dauki kamu yanka dayan yana sha, sai yaji dadi ya ci gaba da sha. Naja'atu ta tashi zata fita ya dago yana kallonta, ya ce "ina zaki.?" Ta ce "Falo zani koma." Ya ce "Don Allah ki zauna bani jin dadin zama ni kadai kuma kinsan ba zani yi barci ba yanzu." Ta kasa yi mashi musu duk da cewa bata son zama dakinshi, amma yau lalura ce ba zata iya tafiya ta barshi ba. Don ta koma ta zauna a hankali suna hira. Wayarshi dake aje gefen gadonshi ta yi kira,. mika hannu ta dauka Farida ce ke kiran saj ta mika mashi ta tashi zata fita ya zuba mata ido, yana girgiza sai ta koma ta zauna ya bude wayar ya amsa mata, tana yi 19 Korafi kan rashin zuwanshi, yau ya bata hakuri ya mat da ita lalurar da ya samu ta rashin lafiya, a hankali ya ci gaba da kallon Naja'atu yana yima Farida bayanin rashun lafiyar yayin da yake nazarin Naja'atun ta canza sosai yana ganin tsabar kishinta duk sai ta bashi tausayi yarda ta damu dashi take kula dashi yayin Imanin Farida ba za ta iya yi mashi irin haka ba, dole ne ta ji kishinshi, don haka ne ma yanzu baya yin waya da Farida a gida, sai da ofis ko kuma idan ya fita, idan ya kama a gidan sai dai ya shiga dakinshi ya yi maganar shi, ya tsini abin da zaya bata ma Naja'atu rai yarda take tattalinshi take kokarin kyautata mashi bai kamata shi ya rinka yin abin da ya sán bata so ba. Da ya gama magana ya rufe wayar ya aje, sai ya zuba mata ido yana nazarinta a hankali ta sauked kanta, bata ce komi ba, ya jinjina kai ya ce 'Don Allah Naja'atu abin da nake so da ke shi ne, ki rinka hakuri da wasu abubuwa, na sani da ciwo, to amma duk abin da kika gani nufin Allah ne, ba wai yina ba ne, Allah ya hada ku dani sannan ya kaddara kaunarku gare ni, kowacce da matsayinta a cikin zuciyata, don haka bani son in ga kina nuna 6acin ranki don kinga ina magana da Farida ki sanya ma zuciyarki hakuri, wani abu ne da ya zama dole tunda wata rana ma tare zaku zauna." Ya sassauta muryà ya ce "kin fahimta.?" Ta jinjina mashi kai, suka ci gaba da hira. Washe gari da ya tashi babu laifi jikin ya yi sauki, sai dai rashin karfin jiki, don haka bai fito ba ya ci gaba da kwanciya cikin dakin, yayin da Naja'atu ta yi tsayin 20 daka akanshi. kai kwannan kai wancan ita dai so take vi taga ya warwarc. Ta gyara mashi dakin fes, yana kamshin Airfreshner. Sannan ta dawo dakinta, tayi wanka ta yi kwalliya ta daidai gwargwado, karfe goma ta fita ta shirya mashi kalaci mai rai da lafiya, ta dauka ta kai mashi yana zaune bakin gado, yayi wanka ya yi fresh alamar lafiya ta fara samuwa, ya dube ta ya yi murmushi itama ta maida mashi martani ta ida shiga ta aje bisa tabur ya. zuba mata ido yana sha'awar halayyarta, kwalliyarta ta yi mashi kyau ya ce "Naja'atu ba ki gajiya da hidima dani ko.?" Ta yi murmushi kawai. ya ce "Na gode, Allah ya bani ikon rike ki da kyau bisa amana da gaskiya, Allah ya kara mana kaunar junanmu." Ta saukar da ajiyar zuciya, duk sai yasa ta ji nauyinshi, ta sarda kai kawai bata ce komi ba, yayin da shi kuma ya bude filet din, filentan ce da kwai aka soya. sai kamshi suka yi da miyar kifi 'yar kadan, ya yi sha'awarsu, don haka ya saki jiki yana ci, suna hira. Aka kwankwasa kofa aka shigo, Mummy ce gaba sai Farida da wata kawarta suka shigo, idanuwan Farida na kan Naja'atu, sai taji kishi matsananci ya dauke kanta tana kallon Daddy, ranta ya dan taba sai dai lura da yayin da Daddyn ya ke ya dan fada sai hankalinta ya koma kanshi. Tana yi mashi sannu. Naja'atu ta mike ta basu waje, kawar Farida kadai ta yi mata magana su ka gaisa, amma ko kallon arziki Farida bata yi mata ba, bata yi magana ba, ta fita ta basu waje to itama Mummy bata zauna ta fito. Farida taja 21 wani stool ta zauna gaban Daddyn, tana tambayarshi jiki, ya dan lumshe ido, sannan a hankali ya bude su yana kallonta ya ce "Da sauki Farida, yau kam na tashi da sauki, amma jiya naji jiki, da da karar kwana sai dai kiji bakin labarin ance maki babu ni." Ta dafe kirji ta ce "Da na shiga uku, idan ka tafi ka barni yaya zan yi.?" Ya yi murmushi ya ce "Sai ki samu wani ko.?" Та zuba mashi ido da wata irin siga mai daga hankali, ta ce "Ai ba ka san wani abu ba, kai kaďai zuciyata take so, bani tsammanin idan wani da namiji zaya yi tasiri akan zuciyata, idan har ka riga ni mutuwa, kila sai dai in mutu ban yi aure ba." Daddy ya rinka yi mata dariya ta ce "Balle ma insha Allahu ba za ka mutu ba, sai ka tsufa, shima na fi son in riga ka mutuwa, saboda zuciyata ba zata iya jure rashinka ba." Daddy ya jinjina mata ya yi Imanin kaunarshi a zuciyarta cikin jiki take, su duka su na son juna, haka nan Allah ne ya dasa mashi kaunar Farida a ranshi, su duka ya na sonsu, ko wace tana da nata tasirin ga rayuwarshi. Su ka ci gaba da hira a hankali Farida ta rinka nazarin dakin, tsarinshi ya yi mata kya, ko ina fes-fes sai kace ba dakin namiji ba, koda ya ke tasan Daddy mutum ne mai tsabta, don haka ba abin mamaki ba ne don ta ga dakinshi da tsabta, cikin kalle-kallenta ne ta hango wani hoto jikin dan karamin frem bisa wata loka, ta zuba ma hoton ido daga nesa, bata gane wadda ke jikin hoton ba, a zatenta nata ne, don haka ta mike ta isa in da hoton yake, ta mika hannu ta daukoshi, hoton Naja'atu ne cikin kananan kaya a millium pack ta yishi wata rana da su ka 22 fita tare da Zainab da ibrahim da shi Daddyn, sun yi hottina da yawa, wasu tarc wasu daban-daban amma duk ciki Daddy ya fi son wannan saboda tayi kyau sai kace Balarabiya, don haka tunda su ka dawo ya fiddashi ya aje shi cikin firem din ya na kallon shi koda yaushc. Farida ta zuba ma hoton ido, zuciyarta na tafasa kamar zata fashe saboda azabar kishi, cikin wani irin tashin hankali ta juyo tana kalion Daddy shima kallonta yakc yi, yaga abin da take yi, ga mamakinta sai taga ko a jikinshi bai nuna damüwa ko jin nauyin abun ba, zuciyar ta ta kara tunzura muryarta na rawa ta jefa firem din kan gado kusa da shi, ta ce "Daddy wannan menenc? Me hakan takc nufi.?" Ya zuba mata ido, ya ce "Ba ki gani ba, Naja'tu cc fa.?" Ta ce "Na gani ina son in ji dalilin da ya sanya ka aje hotonta cikin dakin ka.?" Daddy ya sanya harshe yana lasar lebenshi da ya bushc, bai yi tsammanin tashin hankalin da ya lura ta shiga ba, to sai dai abin da ya ke tunani yasan dole ne dama tasan yana tarc da Naja'atu, ko da kuwa bayan aurensu ne, tunda itama Naja'atun aurcnta zaya yi, to sai dai a tsarinshi ba wannan ne lokacin da ya yi niyyar fadi mata ba. To sai dai bakin alkalami ya riga ya bushc, komi zaya fadi mata ba zaya yl tasiri ba, haka nan matsayin Naja'atu a zuciyarshi ya wuce ya боус та wani gaskiya, ba zaya iya karyata soyayyarta ba. Ya zuba wa Faridar ido, duk ta rikicc kamar zata saka mashi kuka, ya cc "ki kwantar da hankalinki zani yi maki bayani." Ta dakatar dashi, ta ce "Bayanin me zaka yi mani Daddy? Ga shi na gani da idona, dama abin da emui kenan? Yanzw sakayyar da zaka yi mani nDama Žuciyata ta karanta mani akwai abin da y ke faruwa ina mamakin canje-canjen da ka bullo dasu in wannan lokacin baka yi máni waya sai kaga dama, ka nan sai ka jera kwanaki baka leka in da nake ba, she dama wata ka samu, shi ne ka tsaya kana yaudara ta kana bata mani lokaci, to Allah ya fika, kuma na gode de abin da ka yi mani." Da sauri ta juya zata tafi, Daddy rinka kiranta, ko juyowa bata yi ba taja kawarta su ka Mummy da Naja'atu na zaune cikin falo, sai taji ta ane su baki daya, tafi ganin laifin Mummy, ita ce hbar manafukar, dama don ta hada Daddy da aja'atun ne ya sanya ta jajibo ta, Mummy ta dago kai yana kallonsu, ta ce "Farida har kun fito? Ta yi kokarin danne damuwarta ta ce "Eh Mummy tafiya zamu yi." Ta ce "To mun gode kwarai, ku gaida gida, ki gaishe mani da Mamanki." Su ka fice ko kallon Naja'atun basu yi ba, ama haka bata kula su ba tana kallonta har su ka fice ba ce masu'komi ba: Ta tsaida zuciyarta tana tunanin dalilin wannan na da Farida take nuna mata, alhalin bata ma san wa Daddy yana nemanta ba, ko idan ta sani yaya zata vi? Tun farko jininsu bai hadu ba, sai ta rinka ganin laifin shi kanshi Daddyn, ita bata ga wani abin so ba ga arida, mace sai kace kalmar daya, dan hasken ma na nan kanti ne, kila yatsunar da take yi ce yake so, ita kau dai sai ta yi irin wannan karuwancin za a so ta, to sai 24 dai in kar a so ta, wata wayewar in ta yi yawa abun har babu kyau. Ba ta sake komawa dakin Daddy ba, ta yi zamanta falo tana kallon kishi ne kome duk sai ta ji shima ya bata haushi ta rinka jin zafin ganinshi da Farida, waya san abin da ya fadi mata? Maza daban ne, tana mamakin yarda suke kokarin hada kaunar mata daban-daban a ransu, kuma wai su duka sonsu suke yi dole ne munafunci ya shigo, saboda duk yarda za'ayi sai ya yi ya fi son wata ko cikinsu ita da Farida wa yafi so? Idanuwanta suka yi jajir zuciyarta kamar zata fasha idanuwanta sunan neman tara hawaye ta tashi ta shige daki, sai ta kwanta kan gado, tana jin har wani sanyi sanyi yana kada ta, duk ta takura kanta kan gado har aka yi sallar azuhar bata sake fita ba. A can shi kuma Daddy ya yi shiru yana nazarin matakin da Farida ta dauka, bai ji dadin abin da ta yi ba, to sai dai yasan an Gata mata, matsalarshi da ita daya сe,. ya dace ta tsaya ta saurari abin da zaya fadi matga, koda kuwa ba zata amince dashi ba. Ya koma ya kwanta, yana tunanin yarda zaya shawo kanya yasan tana can cikin damuwa, yau akwai kuka kenan ya yi murmushi bai damu ba tunda yasan zaya sauko ne sai ya lumshe ido, yana tuno shagwa6ar Farida, amma koda wasa bai yi tunanin wai ya canza maganarshi kan Naja'atu ba tana nan daram, komi zasu yi zasu yi su sauko su daidaita, sai da ya tabbatar ta isa gida sannan ya kira ta waya, wayar ta rinka kara har ta tsinke bata dauka ba, bai damu ba ya 25 sake kira, nan ma shiru ya rinka kina tana katsewa ba ta Jauka sai ya rabu da ita. Ya kwanta yana tunanin rigimar da ya dauko ma kanshi, amma da ya ke yasan kan Faridar sosai, bai đamu ba đa zaran yaje gare zaya shawo kan yan kayanshi. Da wannan tunanin ya samu barci, har karfe biyu ya tashf va yi sallah, sannan ya zauna, to kuma sai ya rinka jin yuhwa gashi shiru bal sake jin Naja'atu ba, yasan itama damuwar ce, mata akwai kishi kowace da Kalan nata, Shi Rahar yanzu eikin daki take Kwance, ta dauki Wayal wr laRs fubawa kamar ta share shi, amna ta kasa ta ansa masti, muryarta ta yi kasa ya ce "Naja'atu kema pat bå za EšGo kitusayd manf ba, so kike yi ki bata mani SK9 ral. Ta се e nayi maka?Ya ce "Babú komi, kuzo yanzu MESSA ASUS ina jirankia 1 rufe wayar ta aje gefe daya sái ta taso ta fithia shiga ta same shi zaune bakin gado, yhhe 60 sb gics Vazub 88b dAkitaccen kallonshi, sal taji 55 sysb sti sh idare zuciyarta tay tai sani tafihea Kokarin boye damuwarlá. oK Bgaba da Kalioita ya te "Are you okey.? ta daga mashi K To e yasa kika tafi ki ka barni ni dayha.? 8Tlangabe kai tana kallonshi, ta ce "Daddy Kwanciva Hayi la.Vsankar da ajiyar zuciya, ya ee "To mebani in çi yunwa nake i.Ta ce "Me kaké so.?" b8 "Duk abin da kika bani ina so. Ta yi murmushi ta ce "Inaz Tito tana tmanin Daddy, tausayinshi ise stishish we a daga hi ta san akwai damúwa táre dashi fa alama basu rabu da dadi ba da Faridár, koda yake ta lura 64 60 UA iki Baci rar ta tati, 16 don mi itama zäta rinka bata mashi? Dole ne ta bi a hankali tunda yana 26 kokarin akanta, idan har yana tsoron Farida ba zaya sake kula ta ba, tayi Imanin rigimar ba ta rasa nasaba da zuwan da ta yi ta same shi tare da ita, sai ta jinjina kai. zuciyarshi ta yi sanyi. Cikin kicin ta shirya mashi salad fan kadan yasha hadi da kayan kara jini ta zuba mashi shinkafa kadan da peppe meat, ta hada mashi lemun abarba da kwakwa bata sanya sukari ba sosai, saboda yanayin bakinshi, ta dauko ta kawo mashi ya ji dadi sosai, ya saida ya kusa cinyewa. Don haka da dare tun wuri, ta fidda kaza daga firij ta yi mashi gashi na musamman mai romo-romo yasha attaragu da albasa da ya ji mai kayan kamshi tasha curry da reyco, gidan ya cika da kamshi Mummy ta yi mata korafin ta yi son kai, dole ta kara, ta gasa har da su. ya ji dadin gashin ya ci naman har baya son ya bari sauran da ya rage ya ce ta aje mashi sai da safe zaya kara çi. Cikin falo suka yi hira har darc ya mika ya hana Naja'atu tafiya ta kwanta wai ya kasa barci, saboda barcin da ya yi da rana, sai da Mummy ta sanya baki sannan ya sallame ta taje ta kwanta, to itama sai ta kasa barcin tana tunanin Daddy, shu'umin mutum kenan, ya daure ta sosai da igiyar kaunarshi, har mamakin kanta take yi ba ta taba tsamınanin cewa zata samu kanta cikin irin wannaı yanayin ba, a hankali ta fera tuna Khalid da irin muhimmancin da ya ba kaunarta, ko yaya zav iї idan yasan cewa ga halin da take ciki? Sai ta iumshe ido tana kissima wani abu dake kara shaukin kaunarshi cikin zuciyarta, shi ne wani abu mai tsananin tasiri da 27 take hangowa cikin kwayar idonshi tabbas wannan true rove ne, Daddy yana sonta ta yarda da kaunarshi gare ta to sai dai koda yaushe dan adam tara ya ke bai cika goma ba, sai ta rumtse ido tana addu'ar Allah ya mallaka mata Daddy." Da wannan addu'ar tayi barci. Cikin kwanaki biyu ya warke garas, kamar bai yi ciwo ba, ya jinjina ma Naja'atu sosai, ya sani har da taimakonta wajen kulawa dashi da bashi abinci mai kyau, don haka ranar da ya fara fita, ya shiga super market ya yi ma ta sayayya, tarkace iri-iri, ya kawo mata ya ce gift ne. Murmushi kawai ta yi ita dai tasan komi zata yi mashi ba ta fadi ba yanzu ma kenan idan su ka yi aure sai ya yi mamakinta, bata hada kaunarshi da komi ba a ranta, ita kanta bata san dalilin da yasa ta ke yi mashi irin wannan mugun son ba, ita dai tasan tana sonshi, so kuma mai tsanani. To takura shi ma Daddyn ya na kara daukar lamarin da muhimmanci. Kwana da kwanaki yana neman layin Farida, amma fir ta ki yarda ta saurare shi, idan ya kira ba ta dauka ya yi mata text babu amsa, abun ya kan dan taba zuciyarshi, baya son yaje wajenta cikin. halin da take ciki, ya fi son ta tsaya ko magana daya su fara yi ta waya, idan ya so in ya jai su ida warware matsalolinsu, to-ta ki ba shi dama,yanzu har ya fara ganin laifinta, a ganinshi zafin kishinta ya yi yawa, bai dace ta dauki wannan matakin ba tashi daya ba tare da ta tsaya ta saurari abin da zaya ce ba, to ita kam Farida ta shiga damuwa, duk sarda ta tuno hoton Naja'atu dakin Daddy, sai taji kamar-zuciyarta zata fashe, musamman 28 ganin da tayi mata cikin dakinshi, babu irin zargin da ba ta yi masu ba, gani take yi babu abin da basu yi. kuka take yi sosai tana zarginshi da cin amanarta, don haka ta ke kokarin ganin ta fiddo sonshi kwata-kwata daga zuciyarta, hakan ya fiye mata sauki, to sai dai abun takaici duk irin yarda take tunanin abun ya wuce tunaninta, kullum rana kaunarshi kara zurfi ta ke yi cikin zuciyarta, don haka kishinshi ya ke karuwa, duk ta sukurkurce. Mamarta ta damu sosai, ta na sane da abin da ya ke faruwa, to sai dai ta fadi ma Farida cewa tayi hakuri wannan ba matsala ba ce, komi żaya warware ta се kuma daga ganin hotonta a dakinshi sai kice ala dole sonta yake yi? Tun yaushe ta ke gidan? Ai in har yana sontga ba zaya yarda ayi maganar aurenshi da ke ba, ki bi komi a hankali matsalarki ba ki da hakuri." Farida kuka ta rinka yi mata tana rantsuwa kan cewa Daddy son Naja'atu ya ke yi. Mama ta yi dariya ta ce "To idan ma sonta ya ke yi, sai me? Shi fa mijin mace hudu ne, kiyi hakuri in binciki lamarin a hankali, babu abin da zaya faskara, ni dai fatana ki shiga gidanshi, idan yazo hannu cikin ruwan sanyi za ki kama shi ta yarda ba zaya sake tunanin wata diya mace ba, balle har ya yi tunanin aurenta. Zuciyar Farida ta danyi sanyi, sai dai har yanzu ba ta huce da Daddy ba, sam ta ki daukar wayarshi. To bai damu ba, yasan dai babu fashi, duk idan komi ya karato ta tsaya ta saurare shi. 29 A bangaren Mummy shirinta ta ke yi, so ta ke yi Kaishen satin akai lefe ya zamto ta ture shi, sai sauran hidimomi. Ta hada lefenta akwatuna seti daya masu guda uku da kit dinsu, sai kuma na jikkuna suma guda hudu masu kyau 'yan yayi, lallai kam abun nayi ne Naja'atu tunda taga kayan sai jikinta ya yi sanyi, mamakin uwar dukiyar da aka nautsa take yi, an kashe kudi kamar banza, lallai abun nayi ne, sai lokacin ta gane wautar da ta ke yi, Daddy ba ajinta ba ne ya fi Karfinta, saboda duk in da za'a kai lefe irin wannan to tabbas suma zasu so a maido masu abun arziki wanda tayi Imanin cewa iyayenta basu da halin yi mata karya irin wannan an ce kwarya ta bi kwarya, Khalid shi ne ajinta ko ba komi,

Chapter 2 of 6