An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels
SIRRIN
ZUCI
NA
SA ADATU SAMINU KANKIA
(Mrs. Sani Abbas
Hakkin Mallaka (M) Sa'adatu Saminu Kankia
Copy Right (c) Sa'adatu Saminu Kankia
An Rubuta A Shekara Ta:
2008
ABUN ALFAHARI NA
Mahaifiyarmu H. Sa'adiya Samiru Kankia, Uwa ta
gari abin alfaharin mu, muna godiya da irin kyakkyawar
tarbiyar da kıka gina mu da ita, da kuma wadda kike
bamu a halin yanzu. Hakika kin cancanci yabo, Allah ya
ja da rai, ya yi maki sakayya da Aljanna Firdausi, amin.
Hakika addu'arki gare mu mai amfani ce muna ganin
albarka a dukkan al'amurranmu.
ALLAH YA RAYA MIN KU:
'Yayana Umar, Ahmed da Fahad, Sani Abbas,
Allah ya albarkace ku, ya sanya masu jinkan mu ne,
amin.
2
SIRRIN ZUCI..3
ati biyu bayan tafiyar Dr. Khalid, Naja'atu har Sta saba da kewar shi, sai dai sukan yi waya, ya
na sanar da ita halin da ya ke ciki, tare da kara jaddada
ma ta matsayin kaunarta a cikin zuciyarshi, yakan roke
ia cewa ta rinka yi mashi addu'a, Allah yasa ya yi
karatunshi lafiya ya dawo gare ta." Ita ta rike shi a ranta,
ta kanji kewarshi, haka nan idan ta natsu ta na tuno irin
kalaman da ya ke fada ma ta masu ma'ana, da tasiri a
zuciyarta, wadanda tayi Imanin cewa gaskiya ne babu yaudara a ciki. Wani lokacin kuma tausayinshi ta kanji ganin yarda ya dauki kaunar da muhimmanci ya sanyata
a ranshi alhalin ita kullum kokari take yi taga ta sama
mashi mazauri na din-din-din a cikin zuciyarta, amma
kullum abun kara rikice ma ta yake yi, musamman cikin
wanna lokacin da Daddy ya kara rikicewa a kanta. Zainab ta koma makaranta, sai ita daya kullum
rana tana tare da Daddy, ya na bullo ma ta da salo iri-iri
na takun soyayyarshi, amma har tsoro ya ke bata, sai dai
ta lura shi ko a jikinshi ya rufe idanuwanshi, ba ya shakkar kowa, a gaban Mummy nuna kaumarshi yake yi
garc ta tun tana jin nauyin Mummy har ta kai itama ta daskarc. Duk irin yarda taso ta danne zúciyarta game da shi, abun ya faskara, kaunar da ya ke nuna ma ta kaunace da ta jima ta na mafarkin samu daga gare shi sai ya zamto, ta kasa sarrafa zuciyar. Cikin ruwan sanvi
ya same ta yarda ya ke so, idan su na hira sai su dauki
3
Naiokaci ba tare da sun sani ba, duk wani jin dadin
ray awarta ta ta'allaka shi ga Daddy.
Abun da ban tsoro ita kanta ba zata iya cewa ga
abin da ya ke faruwa ba, illa dai tasan tana son Daddy,
son da ita kanta ba za ta iya fassara shi ba, akan kaunar
Daddy ya sanya ta raina duk wani da namiji, idan yana
kallonta ya kan tsuma ta da wata irin mahaukaciyar
soyayya, hakan ya sanya ba ta iya ketare maganarshi,
matsawar ya ce ya na son kaza, ko kuma ba ya son abu
kaza, to kuma duk runtsi tabarshi, haka nan idan ya ce
yana so, zata jure ta yi ma shi, idan har suka yi fada da
Daddy ta kan shiga damuwa, ba za ta samu natsuwa ba,
har sai sun daidaita. Ta na yin taka tsan-tsan akan
dukkan lamarinshi, abu guda ne ke saurin tada ma ta
hankali game da Daddy, shi ne idan ta tuno cewa wata
zaya aura ba da dadewa ba, sai taji ranta ya 6aci, tana jin
matsanancin kishi, har sai ta gwammace ta rabu da shi
kawai ya fiye ma ta kwanciyar hankali, tunda tasan dai
duk irin kaunar da zaya nuna mata ba ta kai wadda zaya
yi ma Farida ba, matsawar ya fara aurenta, tausayin
kanta take ji sosai, idan ta tuno har kuka take yi takan
shiga damuwa.
Amma kuma idan ya zauna yana fadi mata
matsayin kaunarta a zuciyarshi, sai ta amince da shi,
idan ta kalli kwayar idonshi ta kan hango wani abu a
ciki, da ita kadai tasan ma'anar hakan, da bakinshi ma ya
fadi mata yana sonta, son da shi kanshi ba za ya iya
cewa ga lokacin da ya dasu cikin zuciyarshi ba, sai dai
aka wayi gari ya samu kanshi dumu-dumu cikin kogin
kaunarta, kaunar da ke barazanar raba shi da abin da ya
dade ya na so." Zuciyarta ta shiga rikici sosai, saboda
shima Khalid idan ya kirata abin da ya ke fadi mata
kenan koda yaushe, to amma da ya ke shi Daddy tare
take dashi koda yaushe, ya rinjayi zuciyarta sosai.
Mummy na lura dasu, abun ya na damunta, ta fi
ganin laifin Naja'atun, ba ta ga dalilin da zaya sanya ta
biye mashi ba, yana 6ata mata lokaci, to sai dai ba ta son
ta cika takura mata, don haka yau da safiyar ranar
Asabar, Naja'atu ta yi shiri ita da Ibrahim su ka fita zata
je saloon ayi mata gyaran kai. Har su ka fita Daddy bai
fito ba, don haka da ya fito cikin falo, ya rinka zuba ido
yaga in da za ta fito, ga shi ya kira layinta a rufe ya ke,
sai ya zauna falo ya na kalaci shi daya duk kuma sai ya
ji babu dadi, Naja'atu ta saba mashi, duk sarda zaya ci
abinci ko ba zata ci ba, zata zauna kusa da shi har ya
gama hakan yana yi mashi dadi.
Cikin yanayin Mummy ta fito daga cikin dakinta
ta zauna falon sai ya dauko filet dinshi ya dawo cikin
falon, ya na saurarenta tana waya da wata Hajiya Ladi
da ke zuwa Dubai, ta ba ta sautun sawo mata wasu kaya
cikin na lefe. Da ta gama ta rufe wayar ta dube shi tana murmushi, ta ce "Ni da Hajiya Ladi ce ta ce kaya sun
iso, don haka in anjima idan ka fita ka biya ta gidan ka taho dasu, so nake yi a hada komi cikin sati mai zuwa
akai, yau duka saura sati uku ya rage fa." Ta dan saurara taji ko zaya ce wani abu, shiru bai ce komi ba sai ya dai
ya jinjina kai ya ci gaba da kurôar shayinshi.
5
Hajiya ta yi murmushi ta ce "Ko da yake na lura ni
daya ke fa shirme na, kai nema kake yi ka saki
maganar." Ya zuba ma ta ido, bai fahimci maganarta ba
sosai, ta yi murmushi ta ce "Ban san shirin da kake yi
ba, naga jana neman canza sheka, kafi daukar maganar
Naja'atu da muhimmanci akan ta Farida." Ya yi
murmushi ya ec "Mummy ba haka ba ne, kii sani ina
son Farida, kuma aurenta zani yi." Ta ce "Naja'atun fa.?"
Ya ce "Itama haka." Hajiya ta yi dariya ta ce "Daddy
rigimarka ta yi yawa, ina kai ina tara maia har biyu?
Gaskiya bani jin dadin abin da kake yi, ka rabu da
Naja'atu ka ci gaba da harkarka, gaba ki daya ua yarda
ka dauki soyayyar da zafi yana damuna, yair zako ame
ta ko gobe? Wanhan sakarci ne, kuina abin da ke cikin
zuciyata ne na fadi ma ka, bani son yaudara, yarinyar
nan amana takc a hannuna, bani son wani abu ya faru da
ita, yanzu ji ba yarda ka jata jikinka, ka dauki hankalinta
a karshe ba aurenta zaka yi ba, to meyc amfanin abin da
kake yi.?"
Daddy ya rinka girgiza kanshi, ya ce "Muuiat ina
son ki dasa ma zuciyarki cewa har abada ba zani taba
yin wani abu don in 6ata maki rai ba, ko don in son
zuciyata haka nan har abada babu yaudara tsakaniua da
Naja'atu, Mummy ina sonta, sonta nake yi son dani
kaina ban san adadinshi ba, Mummy ki yarda da ni idan
har zani iya cin amanar Naja'aiu to zani iya cin ta Zainab
da muka fito ciki daya, sonta nake yi úa zuciya daya,
kaunar ta a cikin jinina take, kuna insha Allahu zaui
aure ta ba da dadewa ba."
Mummy ta jjina kai ta san halin Daddy duk abin
da ya yi rantsuwa akanshi tayi Imanin cewa haka ne, ta yarda yana son Naja'atu da kanta ta lura da haka, sai dai
abin dubawa, abin da ya ke shirin yi an ya mai yuwuwa
ne? Tara mata ba sauki ba nc, shi kanshi ya kwari kanshi, sannan itama Naja'atun yaya zata yi da maganar Khalid idan ya dawo alhalin ita kanta ta daukar mashi alkawarin cewa zata tsaya mashi taga cewa Naja'atun ta jira shi har sai ya dawo, to wane irin bayani zata yi mashi idan ya dawo?"
Ta sake jinjina maganar a ranta, ta ce "Daddy ban ki ba, kuma kada kayi tsammanin ko bani sonka da Naja'atu ne, zan fi kowa yin farin ciki idan har haka za ta faru na sani Naja'atu alkairi ce gare ka, kuma idan zaka tuna da kaina na yi maka magana akan ka neme ta, kaga kau idan bani sonta hakan ma ba za ta faru ba, to
sai dai abin dubawa a nan shi ne, Daddy rayuwa
canzawa take yi, yanzu ka yi mata alkawarin cewa za ka aure ta, ta amince da haka, sai azo daga baya idan ka yi
aure kaji ba ka da ra'ayin kara auren yaya zaka yi da ita? Sannan ni kaina bani goyan bayan a shekarunka ace ka aje mata biyu a gidanka, yanzu ba zaka fahimci ain da nakc nufi ba, sai nan gaba., Don haka ka samu lokaci ka nutsu kayi nazari, idan ba kai ba babu mai kashe wannan wutar don Allah ka janye ta." Shiru ya yi ya na juya kofin da ke hmunshi, zuciyarshi ta natsu da tunanin abin da ya dace a yi, sai dai duk irin yarda ya so ya ce ya rabu da Naja'atu abin ba mai yiwuwa ba ne, ba zaya iya ba, koda wasa zaya
7
iya yin hakuri da komi amma ban da ita, ya sani sarai
Mummy ba ta son tarayyarsu, kuma tun lokacin yana
Kokarin yaga bai yi abin da zaya bata mata rai ba, sai dai
zuciyarshi ta gaza hakure mashi, ya rinka juya abun a
ranshi yana tausayin Mummy ba ya son damuwarta,
tunda ta yi mashi magana yasan abun aranta yake to sai
dai ya ya iya da rayuwarshi.?
A hankali ya saukar da ajiyar zuciya yana kallonta,
ya ce "Mummy kiyi hakuri, amma wallahi ko nace maki
zani rabu da Naja'atu, wallahi karya nayi maki, a karshe
ba za ki ji dadi ba, idan kika ganni tare da ita, Mummy
idan ba za ki damu ba, zan iya hakura da auren Farida,
in auri Naja'tun shi kenan." Cike da mamaki take
kallonshi, yayinda shi kuma duk ya marairaice mata, sai
ta ji tausayinshi ta ce "Daddy idan aka yi haka ai an
zama kananan mutane, kuma kai ma ba ka yi mata
adalci ba." Ya ce "To Mummy yaya zani yi, ni dai
gaskiya na fadi maki kiyi hakuri kici gaba da yi mani
addu'a, Insha Allahu komi zayazo da sauki."
Mummy ta rinka jinjina maganar a ranta, don so
kam tafi son ace Naja'atun ya aura, to sai dai abin
dubawa shi ne yarda aka dauki tsawon lokaci ana
wannan maganar, yanzu da rana tsaka azo ace an fasa ba
tare da wani kwakkwaran dalili ba, an yi karanta, ita
kanta ba za ta ji dadin irin daukar da Hajiya Hassatu
mahaifiyar Farida zata yi mata ba, haka nan idan ta duba
yarda shi Khalid ya dauki maganar Naja'atun da
muhimmanci, ba girma ba ne ya dawo ya tarda wannan
abun? Yanzu su duka tausayi suke bata, shi Daddy ga
halin da ya ke ciki, kuma tayi Imanin abin da ya lada
gaskiyarshi kenan, tafi kowa sanin halinshi. idan ba at:
da ya damu dashi ba da wuya ka ji yana magana
akanshi, itama Naja'atun ta lura ta rufe idanuwanta ta
makance akan kaunar Daddy abun har tsoro ya ke bate
ganin yarda abun ya ke ta kara ta'azara, ba ta son ta bat
mashi rai, idan ta ga ranshi a bace, shi kenan hankalinta
ya tashi, ba zata sake samun natsuwa ba har sai su
daidaita, komi zata fadi mata ba zaya yi tasiri ba yanz
ta damu dashi idan suna hira har bata son wani abu
gifta, bata son abin da ya ke fadi mata ba.
A bangare daya kuma tana jin dadin yardu
Naja'atun take kula da Daddy, abubuwan da take y
mashi ya nuna ma ta cewa ita ce mace ta gari, tasan duk
wata hanyar da zata bi ta kyautata mashi don haka cikin
ruwan sanyi ta yi saurin saye zuciyarshi ta karkat: akalar kaunarta gare shi tabbas kyautatawar da take
mashi ta yi matukar tasiri akanshi tunda ga halin da aks ciki, wai yau Daddy ne da bakinshin ya ke fadin cewa "Zaya iya yin hakuri da Farida akan Naja'atu, abin da ban mamaki, to sai dai itama Faridar abin dubawa се,
kowa ya sani Farida tana kaunar Daddy fiye da komi, ita kanta. wani lokaci mamaki take yi akan mahaukaciyar
kaunar da ta lura Faridar tana yi ma Daddyn, ta yi Imanin matsala ce babba a halin yanzu ace an wayi gari Daddy ya rabu da ita, idan ya yi mata haka bai yi adalci ba.
"To meye mafita.?" Matsalar da Mummy ta kasa
warwarewa kenan, don haka ta tattara komi ta bar ma
Allah, su ka yi sailama su ka shigo Ibrahim na gaba
tana biye da shi, hannunta rike da 'yar Karamar jaka da
ta zuba kayan gyeran gashi. Idanuwanta fes akan Daddy,
sai ta sakar mashi wani sassanyan nupnushi, shima ya
maida mata martani. Mummy ta dube ta taba murmushi
ta ce "Naja'atu ha kun dawo? Amma kunyi sauri." Ta
zauna bisa kujera a gajiye, yunwa tana damunta, ta ce
"Da yake mun fita da wuri ba mu samu layi ba."
Mummy- ta yi murmushi ia ce "Gashi nan kau kinyi
kyau." Sai ta sunņe kai tana rauriaushi, duk ta ji nauyin
Mummyn, ga shi Daddy yr tsare ta da idanuwa. А
hankali ta sauke kwaym idora akanshi, ya jefe ta da
wani mayen kallo, ta ji wani ii a jikinta, Daddy da
banne ya iya saurin narkar mata da zuciya, ba za ta iya
jure kallon da ya ke yi riata ba a gaban Mummy sai ya
sanya ta ji kunya.
Muryarta ta dan sarke ta ce ma shi "Ina kwana.?"
Sai ya yi murmushi, sannan a hankali ya dago kai ya na
kallon Mummy, itama kallon su take yi, ta ce "Naja'atu
kin biye ma Daddy ko? To yaya zaki yi da Khalid idan
ya dawo.?" Daddy ya zuba mat ido ya na sauraren amsar
da zata ba da, to itama tambayar ta yi ma ta nauyi, ne za
ta ce? Ita kam ta riga ta maida dukkan al'amurranta a
hannun Allah, addu'a take yi ba dare ba rana, Allah ya yi
mata zabi mafi alkairi, saboda daga Daddy har Khalid su
duka ba na yarwa.
Ba ta ce komi ba, ta yi murmushi ta tashi ta nufi
daki, ta aje jikkarta ta cire hijabinta, sannan ta fito falon
suna nan in da ta barsu, sai ta nufi teburin cin abinci
10
ji
suma ci ia da Ibrahim idan ta dago idanuwanta sai taga
Daddy yana kallonta, yayin da su ke magana akan wani
abu da ya shafe su ita da Mummy, nauyin Mummy takc
shi kuwa bai damu ba, ya rinka yi mata nuna da tazo
su ci tare, ta yi shiru kamar ba ta ji abin da ya ke fada
ba, sai ya buda baki ya kirata don kunya, Mummy ta ce
"Rigimarka ta yi yawa Daddy, ka matsa ma yarinyar
nan, ba har zama kayi zaka yi kalacin ba, amma ka fasa,
taso."
Ya zuba ma Naja'atun ido daga in da yake sai ya yi
murmushi ya ce, "Kada kiga laifina Mummy, duk
laifinta ne, ita ta saba mani, ba ni iya cin abinci sai a
gabanta." Mummy ta yi murmushi kawai lamarin Daddy
ya fara zarta hankali, amma a cikin zuciyarta sha'awarsu
take yi, suri hada kansu inama ace Naja'atun ce zaya fara
aura, ta yi Imanin zasu hada gina rayuwa mai albarka da
za su yi alfahari dasu. Bata yi magana ba ta mike ta nufi
kicin wajen Mick, ta ji abubuwan da ya ke bukata ya je kasuwa ya sawo.
Daddy ya sake sosai, ya maisa mata sai da ta taso
ta dawo cikin falo, tare cuka yi kalacin, ya rinka yi mata korafin wal ta cika kunya ta ce "Deddy a gaban Muminy
ne la.?" Ya zuba mata mayatattun idanuwansbi ya ce "To meye? Na fi. son itama ta fabimci irin kaunar da
nake yi maki, yarda zata aje maganar kowa ta rungumi
tawa. Har yanze dauker maganata wasa kike yi, b san
me zani fadi maki ba ki yarda dani." Ta yi murmni ta
ce "Ba maganar rachin yarda ba ce, Daddy ni abin da nake dubawa kada in shagalta akan kaunarka, kazo
11
bayan kayi aure ka manta dani, Daddy ina gudun halin
ku na maza." Ya ce "Da muka yi me.?" Baku da tabbas."
Ya ce "Ki fadi mani abin da kike so in yi maki ki
abbatar da cewa da gaske nakc har abada ba zani iya
udararki ba."
Bai rufe baki ba, wayarta dake aje bisa tebur tayi
kira, ta zuba ma wayar ido, tana kallon sunan mai kiran
octor ne, ita kuma ta tsani tayi waya dashi a gaban
Daddy, takura ta yake yi da kallo, tana ganin
matsanancin kishi cikin kwayar idonshi kafin ta kai
annuntaa wayar Daddy ya yi sauri ya dauki wayar, sai
kawai ya daure fuska, sai ta kasa ce mashi komi, bata
an yarda zata yi da fitinar Daddy ba, ashe haka maza
suke da tsananin kishi? Akan Daddy ta shaida haka, duk
m yarda suke zaman dadi matsawar Khalid ya kirata to
wa sai ta kai zuciya nesa, idan ba haka ba ka, sai sun
yi rigima.
Ba ta gama wannan tunanin ba, wani kiran ya sake
shigowa, ta zuba mashi ido, zuciyarta na bugawa, duk da
cewa tasan yanzu kaunar Daddy tafi komi muhimmanci
2 gare ta, amma bata son ta yi saurin sakin Doctor
halid saboda ba ta da tabbas akan Daddyn, to shi abin
va ke so wai ta kira shi ta sanar da shi cewa ta yi miji,
n haka ya yi hakuri kada ya sake yi mata waya. A
ninta wannan cin fuska ne, Doctor bai cancanci haka
ga gare ta ba, ta fi son ko rabuwa zasu yi su rabu cikin
erziki, tunda dama mutunci ne ya hada su.
Idanuwanta sun dan canza launi, ta rinka girgiza
mashi kai bata son ya bude wayar, shi kuwa niyyarshi
12
sana da tunda ita, ba za ta iya yin magana ba, shi zaya
shi da bakinshi ko ya samu sanyin zuciyarshi, saboda a
halin yanzu idan da akwai wani abu da ke yi mashi
barazana ga rayuwarshi bai wuce Khalid ba, ya tsani ya
ga ya kira Naja'atu ya na kishin hakan, saboda haka ne
ya sa duk lokacin da su ka yi waya da Khalid da ta gama
zata goge shi daga cikin lambobin da aka kirata, hakan
ya fiye mata sauki, saboda idan ya gani sanya ta yake yi
a gaba ya tsare ta sai ta fadi mashi duk abin da ya се
mata, ko ta fada ba a zama lafiya, sai ya ce ta boye
mashi wani abu, duk irin yarda zata yi mashi rantsuwa
ba zaya yarda ba, ya rinka fushi kenan. Daddy matsala
ce kishinshi har ya fi na wata macen.
Gaba ki daya ya rufe wayar ya aje ma ta bisa
tebur, ta ci gaba da kallonshi yanayin shi ya canza tana
ganin azababben kishin a cikin kwayar idonshi sai dan
cije lebentà ta ce "Daddy menene.?" Ya ce "Yaya kike
so in yi, na fadi maki bani son wayar da guy din nan ya
ke yi maki, ki fito ki fadi mashi gaskiya, ya yi hakuri ni
zaki aura, don mi za ki rinka bata mashi lokaci, alhalin
kin san ba aurenshi za ki yi ba, na lura har yanzu ba ki
yarda dani ba." Ba ta ce ma shi komai ba, ta saba da
rigimarshi, sai dai zancen wai ta fito fili ta ce ma Khalid
ba ta son shi ma bai taso ba, ba za ta yi sakin na hannu
kamun na waje ba, dole ta jira taga abin da Allah zaya
yi, shi kuwa laifinta ya ke gani, a ganinshi yana iya
bakin kokarinshi wajen ganin ya nuna mata tsantsan
kaunarshi, ta yarda don kanta zata iya fahimtar matsayin
kaunarta a zuciyarshi, amma ta ki fahimta ta tsaya tana
13
sawaven Khalid. Kila ta fi son shi ne. Kishi ya ke ji sosai
a cikin zuciyarshi.
Bai sake kula ta ba, ya share ta ya ci gaba da
kallon wasan kwallon kafa a talabijin, to itama sai ta fita
harkarshi. Idan ya sauko don kanshi zaya neme ta. Su ka
ci gaba da zama shiru, idan ta dube shi sai ya hararc ta
ya kusa sanya ta dariya, sai ta kwashi filet din ta nufi
kicin, shima bai jima ba ya dauki makullanshi ya fice
daga gidan baki daya.
Ta gama sallar azuhur tana zaune bisa abun sallah,
tana lazumi lamarin ya zauna mata a rai, ta rinka
kissima yarda zata warware matsalolinta, a karshe sai ta
karkata adda'arta akan Allah ya yi mata zabi mafi
alkairi, matar mutum Kabarinsa, Allah shi kadai yasan
daidai bata da zabi sai abin da ya za6a mata. Ta saukar
da ajiyar zuciya tana tuno Daddy yanzu haka yana can
yana fama da fushinshi, tasan halin shi idan aka bato
mashi rai, laifin sai ya shafi kowa. Sai tayi murmushi ita
tasan kan 'yan kayanta.
Wayarta tayi kira, ta duba taga Doctor ne, sai ya
bata tausayi ta dauka tana murmushi ta amsa mashi da
sallama, shima cikin damuwa yake, ya ce "Naja'atu ki
fadi mani me yake faruwa.?" Ta ce "Da aka yi me.?" Ya
ce "Meye ba'ayi ba? So kike yi sai kin fasa mani zuciya
ko? Ko kuwa so kike yi in tsallako karatun nan in
taho.?" Ta sassauta murya da shigar lallashi ta ce "ka yi
hakuri naji nayi laifi, amma idan ka saurari bayanina
zaka san cewa ba laifina ba ne, tun safe na fita saloon,
wanke kaina, sai yanzu na dawo naga miscall din ka har
14
biyu, saboda na bar wayar tana caji na duba wayar naga
babu kudi. na ba maigadi ya sawo mani don in
kirawoka, bai dawo ba yanzu na gama sallah na ji ka
sake kira."
Tana jinshi ya saukar da ajiyar zuciya sai ta
lumshe ido tana kara jin tausayinshi, bata san wando ya
fi sonta ba tsakanin shi da Daddy, su duka suna da
isananin kishi, ko' yaya zaya ji idan ya san Daddy yana
nemanta? Ko giyar wake tasha ba zata iya fadi mashi ba, ta bar komi a hannun Allah."
Muryarshi ta yi kasa-kasa "Hankalina ya tashi sosai, da na ga na kira har sau biyu baki dauka ba, wallahi babu irin zargin da bai zo mani a raiba, sai naga kamar kina yi mani kora da hali ne, har Zainab na kira
na tambaye ta ta ce mani. Iya sanin ta babu komi sai dai
in baki kusa ne abin da ya sanya na dan ji sanyi kenan." Naja'atu ta yi murmushi ta ce "Ka yi hakuri, kasan dai