Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 6
ya tsare kayi tafiya da kula." Ya ji dadi sosai da ba ta nemi takura shi ba, amma ta tsare shi sai da ya yi kalaci, sannan ya fita. ta Tun safe Naja'au aikin gyaran dakin Inna take yi, sai da ta fiddo kayan dakin kaf waje, ta share lungu da sako, sannan ta maidasu ciki. Dakin yayi tsari fes-fes da shi, sai yamma ta yi wanka ta yi sallar la'asar sannan ta ci abinci ta shirya cikin wata shadda ja siket da riga, jikinta yana kamshin turare mai sanyi ta fito tsakar gida ta zauna tana karatun wani. Littafin Hausa, wani yaro ya shigo ya ce "Wai an ce ana sallama." Ta dago kai tana kallon dan makwabtansu ne, ta ce "In ji wa.?" Ya ce "Wani mutum ne anan waje." Ta ce "Wa yake nema?" Ya ce "Bai fadi mani ba ya ce dai in shigo lu ce ana sallama." Та се "To ka tambayo wa ake nema." Inna ta fito daga cikin daki ta ce "Kina nan dai da gardamarki ki leka da kanki mana ki gani kilama bakon Babanku nc, ba sai ki fadi mashi aaya wurin aiki ba bai dawo ba, amma ai babu dadi, babban mutum ayi mashi irin wannan aiken." Sai ta mike rike da littafin ta fita cikin zaure bata ga kowa ba sai da ta leka suka yi ido hudu da Daddy ya na tsaye rungume da hannayenshi ya jingina da mota. Ta 45 ji zuciyarta ta na bugawa da Karfi, duk wam kuzarin da take da shiya katse, ta sarda kai ba ta ce komi ba, ta dawo cikin zauran don haka shima ya biyo bayanta, ya tsaya kawai ya na kallonta sai yaga ta kara yi mashi kyau, muryarta duk ta sarke ta ce mashi "Ta na zuwa." Ta koma cikin gida. Inna ta na tambayar ta "Wayc.?" Ta ce "Daddy ne." Ta dube ta cike da mamaki, ta ce "Ba dai angon ba.?" Ta ce "Shi ne." Ta cc "Ina fatan lafiya ko." Та се lafiya lau, ina makullin dakin su Mas'ud in shiga dashi ciki." Inna ta mika hannu ta dauko mata maku!lin kan taga ta bata yayinda zuciyarta ke raya mata abubuwa da dama, amma ta barma Allah komi. Naja'atu ta dawo zauren, yana nan tsaye ta bude dakin, sannan ta yi mashi magana ya shiga dakin samarin, ya zauna sannan ta juyo zata fita, a hankali ya kirata "Naja'atu.?" Ta tsaya cak tana kallonshi, ya ce "Zo zauna, ina za ki? Ta ce "Ruwa zani kawo maka." Ya girgiza kai ya ce "Bar shi zauna muyi abin da ya kawo ni." Yanayin da yake maganar ya tabbatar mata ya na cikin damuwa, sai ya bata tausayi, duk ya fada yayi duhu, babu kwanciyar hankali da walwalar da ta san shi da ita. Ta koma ta zauna ya tsare ta da ido, akwai rikici sosai a cikin su, sai dai yana kokarin danne damu'varshi A hankali ya saukar da ajiyar zuciya ya ce "Yanzu abin da kika yi Naja'atu kinyi mari adalci kenan? Kin f son ki jagoranci rugujewar rayuwatə ko? Sai naga ina bakin kokarina wajen ganin na kauce ma damuwarki, amma duk wannan bai yi maki ba, shi ne kika tsallako ki ka 46 taho, saboda ba ki so na, ba ki son kwanciyar hankalina, ba ki damu da damuwata ba? Naja'atu kin fi son kanki ba ki tunanin halin da zani shiga? Yanzu look at, me, kalle ni sosai, haka ki ka baro ni?" Ya jinjina kai ya ce "Shi kenan kin samu yarda kike so, ga shi na biyo ki Katsinar sai mu zauna tare." Kuka ya kubce mata, ta zame gabanshi ta na bashi hakuri, ta ce "Ka yi hakuri Daddy, ba nufina kenan ba, na yi haka ne don in samu kwanciyar hankali, zuciyata ba zata iya jure ganin wannan lokacin ba." Ya ce "Amma kinsan nima ba zani iya jure ma rashin ganinki ba, sannan akwai abubuwa da dama da kika yi mani saboda su yanzu nayi nissing din su ko abinci yana yi mani wabalar ci, kina tsanımanin da haka mima zani samu kwanciyar hankalin.?" Sai ya bata tausayi, ta kwantar da kai tana ba shi hakuri. Zuciyarshi ta yi sanyi ya ce "Ki rinka hakuri Naja'atu, duk abin da kayi hakuri akanshi wata rana zaya ba da baya, idan kika duba wannan abun ba yinmu ba ne, nufin Allah ne, to sai ki bar komi a hannunshi mu ci gaba da addu'a sai kiga ya zame mana alkairi, to amma kin kwaso kin taho, na yi Imanin ba za ki samu kwanciyar hankalin da kike cewa ba, haka nima can ki tada mani hankali, yaya kike so in yi.?" Ta jinjina kai ta amsa laifinta, ya ce "Yanzu yaya ki ke son ayi.?" Ta zuva mashi ido, ta ce "Yadda kace." Ya ce "Kin yarda za ki bi ni mu tafi gobe da safe.?" Ta sarda kai tana tunani, ya ce "Idan kuma ba za ki tafi ba, to rima ina nan ba in 47 du zani je zan yi waya in sanar da Mummy su dakatar da bikin sai sadda kika shirya." Ta rinka girgiza mashi kai, ta ce "Shi kenan na yarda zani bika mu tafi." Sai lokacin ya saki fuska yana murmushi, ya ce "Don Alah Naja'atu ba yanzu ba ko can gaba, kada ki sake yi mani irin wannan horon kin wahalar dani, cikin kwana biyu kina ja yunwa tana shirin kama ni." Sai ta kara jin tausayinshi, ta taso ta shigo cikin gida ta shiga kicin yau Inna dashishin shinkafa tayi fari sol, da miyar kifi sadin, tasha attarugu tana kamshi. Ta zubo mashi cikin kwano mai tsabta da filet ta kawo mashi, sai ta fita da kanta ta sawo mashi ruwa da lemu masu sanyi, tazo ta zauna tana zuba mashi, ai kuwa ya ci abincin kamar ba zaya rage ba, ya ji dadin girkin, ga kuma yunwar kwana biyu tana cinshi, don haka ya ci sosai sai da ta yi mamakinshi ya ce ai duk laifin ta nc." Farida ta kira shi tana yi mashi korafin taji shiru ba ta ganshi ba, gashi suna ta shirye-shiryen mother evening. Ya ce "kiyi hakuri, ni yanzu ma ina Katsina, amma insha Allahu gobe da wuri zani taho, na bar ma abokina Aliyu sallahun yazo wajenki, duk wasu hidimomin ku za ya yi." Farida kamar zata fasa kuka, zuciyarta ta raya mata cewa kila Naja'atu ya kai Katsinar, tunda ba ta san cewa bata nan ba, amma sai ta kyale shi a ganinta aski yazo gaban goshi, a dai gama bikin yazo hannu zata raba shi da tunanin duk wata diya mace. 48 Da ya rufe wayar ya na kallon Naja'atu sai tayi nurmushi kawai, Daddy ya jinjina kai ganin kokarin mazan da ke tara mata har hudu yake yi, suna fama. Та wani Gangaren kuma, dole su zama makaryata, saboda kowace da irin tata rigimar, yanzu shi duka su biyu ne, amma kamar su haukata shi, mata shu'umai ne kowace da rigimarta. Awa biyu ya shafe da Naja'atu, ya cika ta da kalaman soyayyarshi, yana kara jaddada mata kaunarshi gare ta, sai ta ji zuciyarta ta dake, ko don ta faranta mashi rai, zata bishi su koma Abujar, itama tasan kusanta kanta dashi, shi ne kwanciyar hankalinta, har yamma ta yi Malam Abdu ya dawo, ya rinka mammakin katuwar motar fa ya gani kofar gidanshi, sai da ya shigo ya wuce su Naja'atun cikin zaure, ya shiga cikin gida, Inna ta yi mashi bayanin cewa Abubakar ne dan Hajiya Halima yazo. Malam Abdu ya jinjina abun a ranshi, bai ce komi ba ya shiga dakinshi. Ba'a jima ba Naja'atu ta yi ma Daddy jagora har cikin gida ya fara gaisawa da Inna ta na tambayarshi mutanen gida, ya ce "Kowa lafiya, suna gaishe ku." Inna ta ce "To madallah mun gode, su ka wuce dakin Malam, ya shiga har ciki su ka gaisa a mutunce, Malam ya ce "Malam Abubakar ga hidima kuma ka taso ka taho.?" Ya yi murnıushi ya na kallon Naja'atu, sai ya kalli Malam ya na shafa kanshi ya ce "Ga wadda nazo biko nan." Malam ya tsura ma Naja'atu ido, shi dama ya zargi wani abu dangane da tahowarta cikin lokacin, alhalin su na ta shirin biki. Ya ce "Wani abu ya faru.?" Daddy ya 49 yi murmushi ya ce "Laifi nayi mata Baba, to sai dai na fadi mata ba laifina ba ne, nufin Allah ne, duk abin da ya faru da bawa rubutacce ne, abin da ya ke faruwa shi ne an yi maganar aurcna da ita wanna yarinyar da zani aura, yanzu to kuma Allah cikin ikonsa, sai ya kawo mani Naja'atu cikin dan lokaci Allah ya jarabe ni da Kaunarta, dor haka mu duka muna son juna, namiji ne ni mijin mace hudu don haka na yi ma ta alkawarin cewa ko bayan na auri wannan yarinyar itama zani aure ta in hada su su biyu, to yanzu da ake ta shirye-shiryen auren, shi ne duk ta damu, ba tare da sanina ba ta taho, don haka na biyo sawunta." Naja'atu ta sarda kai tana jin nauyin Malam, yayin da shi kuma ya jinjina maganar a ranshi, tabbas wannan magana ce mai dadi, to sai dai ina zancen wancan yaro, da ta kawo mashi har yayi mashi alkawarin cewa zaya jira shi har sai ya dawo ba zaya matsa ma Naja'atun ba, da maganar aure.?" Ya saukar da ajiyar zuciya ya ce "Na ji bayaninka Abubakar, kuma na yi farin ciki, babu abin da zance tsakanina da ku sai addu'a sai dai akwai wani abu guda, ke Naja'atu ina maganar yaron da kika kawo mani nan ki ka ce zaya tafi karatu sai ya dawo zaku yi aure.?" Guyawunta su ka yi sanyi, ko dama abin da take gudu kenan, tasan halin Babanta magana daya tal ya ke yi, tunda kau ta fara kawo ma shi maganar Khalid to kuwa yana nan bisa ita, sai dai in dama Allah ya kaddara Khalid din ba mijinta ba ne. Malam ya gyara zama yana kallonta, ya ce "kin gane ko, a harka ta aure babu zancen 50 kunya a ciki, saboda kace mai yi kuma keke tara da mutanen nan, don haka ki buďa baki kiyi mani bayani." Naja'atu ta kasa cewa komi sai Daddy ya yi murmushi ya cc "Baba ni kaina nasan da maganar Doctor, to sai dai shi aure nufin Allah ne, mu duka Allah ne ya jarabe mu da son Naja'atu, kuma shi ya san mijinta a cikinmu mu bar wannan lamarin hannun Allah, mu ci gaba da addu'a Allah ya warwarc mana lamarin ba tare da kowa ya kwaru ba, yayi mana zabi ma fi alkairi." Malam ya rasa abin da zaya ce, Daddy ya daure shi da igiya, tun da ya sanya Allah a gaba ya gama komi, don haka yayi masu fatan alkairi Daddy ya ce zaya zo da safe su tafi safko ya ke so su yi." Malam ya ce "Babu komi." Su ka fito tare ya yi ma Inna sallama, suka fita, cikin zaure ya ci karo da su Badiyya sun taso daga Islamiyya don haka ya ja su wajen motarshi ya bude but, ya rinka fiddo masu tsarabar da yayi ma Malam suna shiga da su, dankali ne da doya, sai kayan miya da na marmari. Naja'atu ta zuba mashi ido tana tuhumarshi hidimar tayi yawa, shima ya yi mata kyar da ido, tana hango matsahanciyar Kaunarta cikin idonshi, sai ta yi murmushi ta dan cije lebe ta ci gaba da kallonsu, har yaran su ka gama kwashe kayan ya cika masu hannu da kudi sabbi fil su ka shiga gida s murna. Ya jingina da mota, ya na jiíarta da mayataccen kallonshi, baya son tafiya ya barta, sai dai ya gaji sosai, so yake yi ya isa gida ya dan watsa ruwa, da wuri yake so ya kwanta saboda daren jiya bai rumtsa ba. Ya zuba hannayenshi cikin aljihu yana kallonta, ya ce "kinsan 51 wani abu.?" Ta girgiza kai ta ce "Sai ka fada." Ya cc "Na gaji da yawa so nake yi in tafi in huta, sai dai Kwayar idona bata gaji da ganinki ba, ina son in rinka sauraren muryarki, ki shirya mu tafi can gida mu kwana da safe kawai sai mu wuce." Naja'atu ta bude ido tana dariya ta ce "Dady kasan abin da kake fada kuwa.?" Ya ce "Ina sa ne." Ta girgiza kai ta cc "Gaskiya kayi hakuri, wannan ba kimar mu ba ce ina gudun sharrin shaidan kuma Baba ma ba zaya yarda ba, ni ma haka." Ya tsura mata udo, ya ce "Don kada dodo ya cinye ki?". Тa се "Mu bar maganar nan Daddy nema kake yi ka take. gaskiya ka bi son ranka, kaje ka kwanta ka huta, insha Allahu zani yi shiru da wuri, karfe nawa zan iso.?" Ya ce "Karfe shida da rabi, ki zama cikin shiri." Ta yi murmushi ta ce "Shi kenan Allah ya bamu alkairi." Ya shiga mota tana tsaye sai da ya bace, sannan tayi murmushi ta koma cikin gida, tana tunanin Daddy ya san kanta da yawa, abun har mamaki yake bata. Washe gari karfe bakwai daidai ya iso gidansu ta tsare shi sai ya yi kalaci, ya co "Tayi hakuri sun taushe hannu sosai, yana so ya isa da wuri." Don haka ta dauki abincin su ka tafi dashi, Inna ta yi masu fatan alkairi har waje Malam ya rako su, su ka tafi yana son isa da wuri saboda jiya ya sha korafi wajen Farida wai ya wulakantata, sun gayyato mutane yawancin kawayen Mama, nata son su ganshi amma baya nan, ya bata bakuri ya ce "Insha Allahu yau zaya halarci lunchen party din. Don haka ya ke son ya koma da wuri kada 52 lokaci ya kure, ya kara wani laifin, so yake yaga kyautata ma kowace cikinsu. Kan hanya ma ya rinka kokarin kwantar ma Naja'atu da hankali yana kwatanta mata yarda abubuwan suke, to babu laifi Naja'atu ta fahime shi tana tausaya mashi, don haka ta kwantar da hankalin ta tana kyautata mashi suka rinka tafiya cikin dadin rai, ya na nuna mata kauna da kulawarshi, ya tabbatar mata da cewa kada ta damu, insha Allahu ba za'a ďauki lokaci mai tsawo ba, zaya yi maganar aurenta ya ce "Ta fadi mashi lokacin da take son ya rinka zuwa suna gaisawa tunda ba zaya iya zuwa kullum ba, ko ba koni akwai nisa tsakanin gidanshi da wajen aikin shi baya da lokacin da zaya dawo daga aiki kuma har ya fito yazo gida akwai tazara sosai." Naja'atu ta yi murmushi ta ce "koda ka samu damuwa, duk lokacin da ka samu lokaci kazo ba komi." Ya zuba mata ido ya ce "Ba fushi kika yi ba ko.?" Ta yi murmushi ta ce "Wailahi ba fushi nayi ba, ai nasan yanzu rayuwa ta canza, dole ne ka ba iyalinka lokacinsu, idan nace sai kazo cikin lokacin ai na shiga hakkinta, tunda idan ka dawo aikin kana son hutawa, kuma lokacin kurarre ne, tunda ga waya ai babu matsala." Ya zuba mata ido kaďan, sai ya ci gaba da kallon gabanshi a hankali ya ce "Na gode Naja'atu, kinga daga jiya zuwa yau, kin kwantar mani da hankali, rabon da in ji zuciyata tayi mani sanyi irin yau har na manta, don Allah kada ki kara barin wani abu ya sake shiga tsakaninmu." Ta jinjina kai ta ce "Insha Allahu." Ya zuba mata ido ya сe 53 'promise' ta yi murmushi ta daga mashi gira sai yayi dariya har zikin zuciyarshi yana kara Kaunar yarinyar. Karfe biyu daidai suka isa gida, Zainab ta fio da gudu ta rungume Naja'atu tana murnar dawowarta yayin da ita kuma Mummy ta rinka yi masu fada, wai sunyi gudu don mi Naja'atun ta kyale shi ya yi gudu sosai irin haka.?" Naja'atu ta yi murmushi ta ce "Kiyi hakuri Mummy ya ce ana jiranshi ne." Gidan cike yake da mata 'yan biki, don haka basu da wani hutu Sallah kadai suka yi suka fita saloon gyaran gashi ita dada Amina diyar kanwar Babansu ce tana karatu a Danfodio University, tana da sakin fuska don da nan su ka shaku. Tun a saloon din su ka fara gardama, sabcda su Zainab sun ce da sun koma shiri zasu yi su je wajen lunching party din, yayin da ita kuma Naja'atu ta kafe kan cewa ba za ta je ko ina ba, haka kawai taje a wulakantata." Amina ta ce "To mu dai sai munje." Naja'atu ta ce "To ai dama ban hana ku ba, ku shirya kuje kawai zani zauna gida." Zainab ta Kule ta kasa ce mata komi, ta rasa irin Naja'atu tasan saboda Farida ue zata ce ta ki zuwa, to ina ruwanta da ita, ta shirya taje, idan yaso ita kada ta zauna ruwanta, amma sai ta rinka ware kanta tana takura ma kanta, alhalin shi Daddyn ya fi son yaga ta saki jiki ana yin komi da ita, ta yi imanin cewa zaya yi ſarin ciki idan ya ganta a wajen. Da su ka koma gida, su Zainab na a shirinsu, Naja'atu ta zauna tana shirya kayanta cikin wadrof Zainab ta gama shirinta ta fita. Daddy ya na cikin dakinshi yana shiri ta kwankwasa mashi kofa ya ba ta 54 izinin va shiga, sai ta murfa kyauren ta shiga ya ce Zainab lafiya dai ko." Ta yi murmushi ta ce "lafiya lau Rarar Naja'atu na kawo maka, ta zauna wai ba zata je Wurin lunching din ba, alhalin ga shi mu mun shirya lafiyá zamu yi." Bai yi magana ba, ya dauki wayarshi ya kirata, ya ce "Tazo yanzu yana sön ganinta a dakinshi." Zuciyarta ta rinka raya mata abubuwa da yawa, tunaninta ya tsaya kan cewá Zainab ce ta hafa ta da shi. a taso ta fito zuwa dakin, ta vi sállama ta shiga yana saye yana daura agogo, sanye ya ke da wani farin fallausan yadi, dan ubansu, bata san me zata kira shi ba, ya yi mashi dinkin zamani mai fadin hannu rigar ta saya mashi iya guiwa, da nmanyan atjihu kana ganin farar shimin da ya shimfida a jikinshi, kafin ya sa rigar. Farin mutum dogo AHah ya zuba ma Daddy-ruwan kyau, mai dauk ar hankali idanuwanshi makimanta farare ol masu tsananin haske da saurini daukar hankalin duk wanda ya kalka sajenshi mai kyau da tsari yasha gyaran zamani, sai ya kara mashi kyau na musamman. Ya zuba mata ido da wata irin siga ta nana kaunar Bshigare t ta yi murmushi ta sarda kai, tana kallon Zainab Zatonta ya zama gaskiya, sai ta dubi Daddyn tana sauraren abin da zaya ce mata. Va mika bannu ya dauko firarenshi yana fesawa sai ya cần koisita ya.co #Me svasa kika ce ba za ki je duncing oe?saboda ba ki son kWandiyar harikalina Ko? ta ce "Ha haka ba nejni bani Boninyi dbin da wani zaya ga banyi mashi daldai ba, bah son tashin hankali"Ya/zuba mata ido ya ce 'Dawa zaki yi tashin hankalin.? Ta darr cije lebenta ana kallon 55 wani sashin ba ta ce komi ba, ya ce "Kije ki shirya ku fito in tafi da ku." Bai saurare ta ba ya ci gaba da shirinshi, ta juya tana kallon Zainab sai dariyar mugunta takc yi mata, ita kam Daddy yana neman takura mata ne, da yayi hakuri sunyi tafiyarsu, ya fiye mata sauki. Zainab ta kama hannunta ta ce "Zo muje don Allah kina bata mana lokaci kin san fa ana jiranshi." Daga Zainab har Amina suka yi tsaye kanta sai da ta yi kwalliya sosai, da wani leshi lallausa, mai jinin kare riga da zani rigar 'yara karama daidai jikinta, tayi kyau sosai cikinsu, ta shafa jambaki kalar kayan abinka ga farar mace sai ta yi kyau kamar ita ce amaryar ta daura kallabin kayan ta kara haskawa, jikinta na kamshi na musamman su ka tito Daddy na jiransu, Zainab da Amina su ka zauna baya, yayin da ita kuma ta kame gaba kusa dashi ya dube ta sai ya ji nufashi ya na yi mashi wuyar dauka ta yi kyau kamar fure ina ma ace ita ce amaryar? Sun dace da juna, ya rinka satar kallonta ta madubi, da ya son ya yi mata wata magana gabansu Zainab su raina shi, Daddy akwai tsare gida. Harabar otel din da ake yin partyn ta cika makil da mutane 'yan biki wayayyun 'yan boko, ya dace ace an fara gabatar da komi amma rashin zuwan ango yasa aka dakata, Farida har ta fara cika, ta hango motarshi na shigowa, sai tayi murmushi yayin da motar ta shigo ta isa wajen da aka kebe don aje motoci ta tsaya ya bude aljihun motar ya fiddə bandiran kudi sabbi fil ya manna ma Naja'atu nata a hannu, ya mika ma su Zainab nasu ya ce "ku yi amfani dasu." A hankali ya sauke kwayar 56 ¡donshi akan Naja'atun sai ta sakar mashi murmushinta mai sanyi. Ya ji dadi a ranshi, ya cc "Takc care." Suka fito tare Zainab taja hannun Naja'atu, su ka kama gabansu, yayin da shi kuma ya tsaya yana gaisawa da wani abokinshi, sannan su ka nufi in da amaren su ke. lAkan idanuwan Farida duk abin da ya faru, sai ta ji kamar ya soke ta da mashi, ta rumtse ido cike da takaici. Zee da ke kusa da ita, ta dafa ta ta ce "Ga Angon nan ya iso fa, wadancan kannenshi ne.?" Farida ta dan cije lebе ta ce. "Akwai kanwarshi ciki, amma waccan da ta fito kusa dashi yarinyarshi ce, wai itama aurenta zaya yi." Zainab ta bude ido tana mamaki ta ce "Shi ne kuma ya taho mana da ita nan.?" Farida ta cije lebe ta ce "In haka aka ce mashi ba dole yayi ba, ai yarinyar cikin gidansu take, uwarshi ce ta jajibota ta kawo ta don kawai ta hana shi aurena, Allah ne bai nufa ba." Zee ta ce "kuma shi yana sonta.?" Та се "Ba ga alama nan kin gani ba, ki duba kwalliyar da ta yi mana, ko ita ce amary sai haka." Zee ta ce "Lallai kina da aiki ja a gabanki, ashi zaki yi tsaye ki raba shi da ita:" Farida ta yi dariyar mugunta ta ce "Daina wannan maganar Zee, ai kin dai sanni, ki bani 'yan kwanaki ki gani, ko ita uwar idan ba ta bi a sannu ba, raba su zani yi don ba za ta zame mani matsala ba. Su Daddy su ka karaso wajensu, yana fara'arshi lallai kam ya yi ma ta kyau shima ganin kyawunta ya ke yi, ya dan rusuna yana kallonta cikin idonta ya ce "kiyi hakuri na 6ata lokaci ko.?" Ta ji wani iri cikin jikinta, sai ta sarda kai ita dai tasan tana cikin mata masu 57 tsanamin sa'a a rayuwa, auren kyakkyawan mutum irin Daddy abun alfahari ne a gare ta, sai ta ji ya wanke duk laifin shi da take gani aka shiga hidima, ga abinci da na sha nan kala-kala, yayım da makadan rundunar 'yansanda su ka kayata wajen da kidansu mai dadi, kowa ka gani yana cikin farin ciki da annushuwa. Daddy na tarc da Amarya a wajen zaman da aka keße masu na musamman amma idanuwanshi suna kan Naja'atu, ta saki jiki suna ta hirarsu da su Zainab, sai dariya suke yi, ya rinka kallonta yana son ta kalle shi, amma ta ki kulawa dashi bata son taga abin da zaya bata mata rai. Ango da amarya su ka fita fili, su na taka rawa, su Zainab su ka fita suna liki, amma Naja'atu ta ce ba za ta je ba, ta yi zamanta tana kallonsu, fili ya kacare ana ta cashewa don haka yayi amfani da wannan damar ya kefe kanshi ya kira ta ta waya, da ta duba taga shi ne sai ta rufe wayar gaba ki daya, ta dago kai yana kallonta sai ta yi murmushi ta girgiza mashi kai, ta share shi ta ci gaba da kallonta. Ba zato sai dai ta ji kamshin turarenshi ya baibaye wajen da take. Ta fago idanuwanta a hankali tana kallonshi sai ta yi murmushi ta ce "Daddy abin da kake babu kyau fa, idan ni kayi ma haka ba zani ji dadi ba, kayi hakuri ka koma ku ci gaba da hidimar ku." Ya ce "Amma don mi za ki takura kanki ki zauna waje daya.?" Ta ce "Shi kenan ka tafi zani taso." Ya jinjina kai ya koma sai da aka dauki lokaci sannan ta tashi ta shiga fagen rawar bata takaba, amma ta rinka zubda Naira kamar ruwan banza. Farida na kallonta ta kara kulewa, amma Naja'atu ba ta je kusa da 58 jta ba, ta tsaya in da su Zainab suke su ka rinka yi ma junansu liki. Da aka tashi ba su jira Daddy ba, abokinshi Aliyu ya dauke su ya maida su gida, haka nan bata sake ganinshi ba, bai kwana gidan ba, saboda yawon mutane sai đai ya yi mata Text ya na godiya kan abin da tayi mashi. Washe gari tunda su ka tashi ba su da lokacin kansu ana ta hidimar yinin biki da daurin aure, gidan ya cika da mutane maza da mata yan faurin aure. Su. Naja'atu Hajiya ta fora ma hidimar ba baki abinci don haka gaba ki daya hankalinsu ya tafi wajen hidima da jama'a, da ke ta durarowa ta ko'ina 'yan'uwa sumyi ma Hajiya Halima kara sosai, bata yi tsammanin Inna zata zo sai gasu cikin bus, tare da sauran 'yan'uwan Hajiya, taji dadi kwarai, an ce kayi ma mai yi maka. Mummy ta cancanci ayi mata komi. Karfe daya saura tana cikin kicin tana fidda abincin baki maza da suka zo daga Katsina, Zainab ta shigo ta ce "Ba ri in ida zubawa kijc Daddy ya na kiranki, ya na dakin shi." Naja'atu ta dan yatsuna fuska, ta ce kai jama'a in yi yaya da wannan aikin? Yanzu idan naje ba zaya barni in fito ba, kije Zainab in abinci yake so ki zuba mashi. Zainab ta ce "Amma ai ya ganni kuma ya ce in zo in kira ki, sai dai in ba za ki je ba in koma in fadi ma shi don kar ya ga lailina" Naja'atu ta jefa mata harara, ta fito ta nufi dakin ta dan kwankwasa sannan ta shiga ya na kwance dai dai bisa gado ko alamun shiri bai yi ba, ga shi daurin auren na karfe biyu da rabi ne, 59 lokacı yana Karatowa. Ta yi mashi sallama ya fago kai a hankali yana kallon ta duk sai ya ba ta tausayi, ya yi wujiga

Chapter 4 of 6