ki."
A zuciye na miƙe cikin ƙeƙeshewar zuci da kaiwa maƙura na ce. "Wallahi ba zan iya auren duka ba, ba jaka aka kawo maka ba, don haka kar ka sake taɓa ni." Wancakalar da ni gefe ya yi ya ce. "Idan an kuma me za ki yi? Me za ki iya yi? Ko wannan gurgun matsiyacin uban naki zai ɗauki mataki ne?"
"Kar ka ƙara danganta shi da tsiya!" Na faɗa cikin ƙaraji da ihu. Yana kusanto inda nake ya ce. "Mene a tattare da ku ban da tsiyar? Na taimaka na tsamo ki daga cikin talauci na kawo ki cikin arziƙi amma ni za ki mayar ɗan'iska saboda ke butulu ce?" Babu tsoro ko razani na ce. "To ka sake ni ka ga idan zan rasa gurin kwana ko abincin ci, ka sake ni idan ka cika ɗan halak! Na gaji! Na gaji da wannan ƙaddararren auren da babu komai a cikinsa sai bala'i da masifa." Na ƙarashe maganar tare da dafe bango ina jin kamar zan faɗi, numfashina na fita da sauri da sauri. Yana wani ciccizewa kamar ɗan tauri ya ce. "Ni kike faɗawa haka?" Cikin ɗaga murya kamar yadda ya yi na ce. "Eh, na ɗaga ɗin." Mari ya kawo mini na goce cikin sa'a tare da ja baya, nuna ni ya yi da hannu ya ce. "Ki tattara kayanki ki bar mini gida, na sake ki!" Wani irin abu na ji ya daki zuciyata, ban tsaya tantance mene ba na fara ƙoƙarin haɗa kayana bayan na zira doguwar riga da hijabi. Ban san me nake zubawa saboda tsabar ruɗani, da ƙyar na lalubo wayata na saka a jaka na fice parlour. Ina fita na ji Hajiya tana ce masa. "Saki ɗaya ai za ta dawo ne ma da ƙafafunta." Ban tsaya sauraren sauran maganar tata ba na yi gaba. Dare ne amma ban san ko ƙarfe nawa ba ne, sai da na fita na ga unguwar ɗif na gane ya fara ja kenan, ba ni da ko ficika hakan ya sa na saɓi ƙafata na fara tafiya ba tare da na san inda nake jefa ta ba. Bana gane komai, tafiya kawai nake ina hawaye tare da tunanin halin da Kawu zai shiga idan na je masa wannan karon ma da batun mutuwar aurena a karo na uku. Na yi tafiya sosai amma ban gamu da kowa ba, sai haushin karnuka da yake amsa kuwwa a cikin kunnena. Na shiga wani layi kenan na ji kamar ana bin bayana, ina juyawa na ga wasu mutane guda biyu, wanda ruɗanin da nake ciki bai saka na tantance mata ne ko maza ba. Ƙoƙarin gudawa na yi na ga wasu daban sun sha gabana.........✍️
*Zeey Kumurya*✍️
[5/11, 12:13 PM] Bahaushiya👍: *YI WA KAI*
MIKIYA WRITERS ASSOCIATION
*BRIGHT PENS*
(FREE BATCH)
*33.*
Tsayawa na yi cak cikin saddaƙarwa da sarewa. Ko kaɗan ban ji wani tsoro ko razani ba, saboda yadda na gaji da rayuwa da duniyar ma gabaɗaya. Hannu ɗaya daga cikinsu ya miƙo mini tare da faɗin. "Kawo jakar nan." Miƙa masa na yi a dake na ce. "Don Allah ku taimake ni ku kashe ni, ku karɓi har raina ba iya jakar kaɗai ba!" Bai karɓi jakar ba ya cewa sauran. "Daga gani wannan ragowar tabahuwa ce, mu samfe kawai babu uwar da za mu samu." Hauri ɗaya daga cikin na baya ya yi na tintsira kamar zan kifa, Allah ya taimaka ni ban kai ƙasa ba. Cikin muryar ƴan'daba wani a cikinsu ya ce. "Mu dai laluba ko da mamora. Fizgar jakar suka yi kamar za su haɗa da hannuna, ya tattaɓa ya cillo mini. Wayata tana cikin rigata, da na san zai sun ƙwace ta. Kamar walƙiya suka falfala suka ɓace wa ganina, ajiyar zuciya na sauke na tsugunna na ɗauki jakar. Cikin bushewar zuciya na ja ƙafa da ƙyar na ci gaba da tafiya kamar zan kifa, saboda gajiya da tsananin galabaita, ga ciwo ga yunwa. Sai da na ji ina shirin yanke jiki na faɗi sannan na tsaya a wani titi na tari napep na shiga. Har ƙofar gida ya kai ni, na ce ya jira na shiga na karɓo masa kuɗin. Lokacin kusan sha biyu saura, har an rurrufe gidaje.
Jikina babu ƙwari na fara bubbuga gidanmu, na shafe wasu mintuna kafin na jiyo tafiya, ajiyar zuciya na sauke.
"Waye?" Na ji muryar Gwaggo ta faɗi haka da ƙarfi.
Muryata ba ta fita sosai na ce. "Ni ce."
"Ke wa?"
"Gwaggo ni ce Hafsah fa." Na faɗa ina ƙara volume. Ba ta kuma magana ba ta buɗe ƙofar tare da haske ni da fitilar hannunta. Cikin mamaki ta ce. "Lafiya? Waye ya rasu kika fito a wannan tsohon daren?" Kaina a ƙasa na ce. "Lafiya ƙalau, don Allah ki ba ni duba ɗaya na ba wa mai napep ɗin can." A tsiyace ta ce. "Ban da ita." Magiya na shiga yi mata amma matar nan ta ƙi ba ni, ƙarshe ma ta juya ta yi shigewar ta ciki ta bar ni nan tsaye, mai adaidaita kuma yana ta yi mini masifa na ba shi kuɗinsa, dare ya yi zai tafi. Na ba shi haƙuri na ce masa bari na shiga cikin gidan, da niyyar na tambayi Kawu ya ba ni, amma ina shiga na tarar ɗakinsa a kulle, na leƙa ta window na ga bacci yake. Sai na ji ba zan iya tashin shi ba, kawai sai na koma na ƙara ba wa mai napep haƙuri. Wani kallo ya yi mini ya ce. "Kya ba ni a can." Tare da jan machine ɗinsa ya yi gaba. Jiki a saɓule na koma na zauna a tsakar gida na fara rizgar kuka, abin da ban taɓa ci ba haƙƙin wani, amma yau ta sanadin auren Sani an yi mini Allah ya isa. Ko kallo na Gwaggo ba ta yi ba, ta je ta mayar da ƙofar gidanta ta rufe ta dawo ta shige ɗakinta ta banko ƙofa.
Kamar an ɗora mini bulalluka a kaina haka nake ji saboda nauyi da ciwon da yake yi mini. Ƙafafuna ma duk sun sage saboda uwar tafiyar da na ci. Kwanan zaune na yi a inda nake, sauraye suka yi watanta da bushashar su a jikina. Da wani zazzafan zazzaɓi na wayi gari, don duk iya satar bacci ko runtsawa ban yi ba. A inda nake na kwanta saboda zaman ma ya soma gagara ta.
Bayan gari ya fara haske Kawu ya fito zai tafi soro inda yake kwanciya ya gan ni, ina jin shi yana yi mini magana amma bana fahimtar abin da yake cewa. Ba komai nake ganewa ba a wannan lokacin, sai farkawa na yi na gan ni a kwance a gadon asibiti, wata maƙociyarmu na jinya ta. Ita ta faɗa mini Kawu ne ya kira mijinta suka kawo ni asibiti, don Gwaggo ta ce abincin sana'arta za ta yi. Kwanan mu shida aka sallame ni muka dawo gida. Ban ɓoye komai ba na faɗa wa Kawu duk abin da yake faruwa ina kuka. Cikin jimantawa ya ce. "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!" Sau uku. Daga haka bai kuma magana ba ya ja ƙafarsa ya tafi, don ba ƙaramin jin jiki yake ba, maganar ma da ƙyar yake yi, kuma duk ya rame. A ranar Inna Habi ta zo, tai ta masifar yadda ta gan ni duk na lalace. Wannan karon ba ta tafi da ni gidanta ba tunda ta ga babu mamora. Kwana biyar bayan sallamo ni na ɗan warware, don ba zan ce na warke ba, tunda ciwon da yake zuciyata yana nan a danƙare. Da yamma na je gurin Kawu mun gaisa ya dube ni ya ce. "Hafsah anya kuwa abin da kika faɗa mini akan rabuwarki da Anas gaskiya ne?" Gabana ne ya faɗi, na ɗan daure na ce. "Gaskiya na faɗa maka Kawu."
"Ban yarda ba, saboda babu yadda za a yi yaron nan ya shafe tsawon wannan lokacin bai zo ya gaishe ni ko ya kawo miki yaranki ba, kuma rashin dacen auren da kike yi na fi zargin ke kika zalunce shi haƙƙinsa yake bibiyarki." Da sauri na kalle shi tare da yin ƙasa da kaina a lokaci guda. Idona cike da ƙwalla na ce. "Ƙaddara ce kawai Kawu, amma ba haka ba ne." Jinjina kai ya yi tare da runtse idonsa alamun yana jin jiki, cikin tausayawa na ce. "Sannu Kawu." Ya gyaɗa mini kai tare da gyara zaman ƙafar tasa mai ciwon sannan ya ce. "Ki ji tsoron Allah! Ki tuna Ubangiji ba ya yafe haƙƙin wani akan wani, ki nemi bawan Allah nan a duk inda yake ki nemi gafarar shi, ko za ki samu sassauci a rayuwarki. Ki dubi yadda kika lalace kika bushe kika rame, ko ba ki faɗa ba duk wanda ya kalle ki ya san ba kya cikin kwanciyar hankali, Allah da kansa ne fa ya faɗa, idan mata da miji suka rabu, zai yi wa wanda aka zalunta sauyi da mafi alkhairi, duk da akwai ƙaddara, kuma Ubangiji yana iya jarrabar bawansa a duk lokacin da ya so, amma wannan abubuwan da suke faruwa da ke akwai ayar tambaya." Share hawayen da yake zuba a kan kuncina na yi, nauyin da zuciyata ta mini kamar an ɗora dutse ya sa na kasa magana, na ci gaba da kukana mara sauti kawai. Ganin haka ya sa ya ce na tashi na tafi. Kamar jira nake na miƙe da sauri na shige ɗakin da nake na faɗa kan tarbarmar da nake kwanciya. Sosai nake jin tarin nadama da, da na sani suna ƙara lulluɓe ni. Da ina gidan Anas har yanzu da hankali kwance zan ci gaba da rayuwata, da ban shiga cikin wannan tashin hankalin da nake ciki ba yanzu, da ban yi shekara guda cur babu ƴaƴana ba, da ban sha wannan baƙar azabar da nake kan sha ba, da ban saka Kawu siyar da kadararsa don yi mini magani ba. Don kwanciyar nan da na yi a asibiti sai da ya siyar da machine ɗinsa da yake ajiye tun bayan fara cutarsa sannan ya samu kuɗin dawainiya da ni. Na yi kuka sosai na rashin mafita da madafa, da ina da tabbacin dangin mahaifiyata za su yi mini tarɓa mai kyau da can zan tafi, ko zan samu sassauci idan na samu kulawa. Don aure kam na haƙura da shi har abada, gara na yi ta zama a haka. Na dinga tuno rayuwata ta baya, lokacin da ban taɓa tunanin zan tsinci kaina a matsayin bazarawa ba, amma ga shi ni ce yanzu har da aure uku. Ji nake kamar mafarki nake yi, zan farka na ga mun ci gaba da rayuwa da adalin mijina tare da ƴaƴana cikin walwala da aminci. Tuno lokacin da ina asibiti Sani ya dinga masifa na yi ciki na yi, ya ce dole na yi tsarin iyali don shi bai shirya haihuwa yanzu ba, na kuma tuno Anas yadda yake son ƴaƴa da son ganin na ƙara haihuwa, kullum addu'arsa Allah ya ba ni ciki na haifa masa mace mai kama da ni. A fili na ce. "Allah ɗaya gari banban."
Haka rayuwa ta ci gaba da yin tamolan ƙwallo da ni, kwata-kwata bana jin daɗin zaman gidan, ga Gwaggo da a kodayaushe burinta ta muzguna mini. Ga jikin Kawu da kullum ciwon gaba yake yi, duk ya siyar da komai nasa saboda magani. Gidan da muke ciki ne kawai ya rage masa. Da taimakon maƙociyarmu da ta yi jinya ta a asibiti na kwaso kayana daga gidan Sani kaf na sigar, ɗan abin da zan yi amfani da shi da kayan sakawa kawai na bari, na siyar da wayata na siya ƙarama daidai ni, don duk wani abu na ƙawa da burgewa yanzu ya fita daga kaina. Na tattara kuɗaɗena masu kauri na ce zan ja jari na fara sana'a, don idan aka ci gaba da tafiya a haka da matsala, tunda ni nake ciyar da kaina, Gwaggo ko ƙwayar shinkafa ba ta ba ni, sai dai na siya idan ta yi na siyarwa. Kuma ko da wasa ban bari Kawu ya sani ba. Na yi tunanin Inna za ta ce na koma gidanta a wannan karon ma, amma ko zuwa na yi ta dinga cewa ki tashi ki tafi kar dare ya yi miki, alamun ko kwana ba ta son na yi. A haka na kammala iddata a karo na biyu, wanda nake fata ya zamo mini na ƙarshe.
Yau da safe ina zaune ina sana'ar tawa ta tunani na ji wayata na ringing, cikin mamaki na ɗauko na duba, don yanzu babu wanda yake kira na babu wanda nake kira. Number na gani, ɗan jim na yi har ta kusa katsewa sannan na ɗaga tare da sallama, bayan mun gaisa na ji muryar mace ta ce. "Ba ki gane ni ba ko? Maman Humairah ce ƙawar Maman Nasmah." Na ce. "Maman Humairah da ma ke ce? Ya kike ya kwana biyu?" Ta ce. "Lafiya ƙalau Alhamdulillah, sai kuma muka ji ki ɗif kwana biyu kamar mutuniyar taki." Na ce. "To ya za a yi? Ya kowa da kowa ya ƴan group?" Don ni tun kafin na baro gidan Sani rabo na da hawa online. Ta ce. "Kowa lafiya ƙalau Alhamdulillah, da ma na kira ki ne don ina son mu haɗu urgently, idan da dama yau ko gobe." Cikin mamaki na ce. "Too! Lafiya kuwa?" Ta ce. "Lafiya ƙalau wallahi, kawai wani abu ne mai muhimmanci ya taso, kuma ya shafe ki, amma idan kina ganin da damuwa ki turo mini address ɗinki ni na zo gidanki mu haɗu." Haka kawai na ji zuciyata ta ɗokantu da sanin ko mene ne, hakan ya sa na ce mata. "Bari zan zo anjima, ki turo mini naki address ɗin." Ta ce. "Yawwa, hakan ya ma fi da ma, amma kar ki ɗaga hankalinki fa, ba wani abun damuwa ba ne." Na ce. "To." Tare da kashe wayar. Maman Humairah ƙawar Maman Nasmah ce tare suka yi secondary school, tana cikin group ɗinmu ita ma, amma ba ta wani participating sosai. A gaggauce na shirya, da ma zaman kaɗaici ya ishe ni, na san idan na fita ko hira na yi da mutane zan samu relief a cikin zuciyata. Na zumbula hijabi da niƙab na cewa Kawu zan je gidansu Naja, don a zaman nan da na yi sai da ya tambaye ni tana ina duk zaman gidan da na yi bai gan ta, ta zo ba? Na yi masa ƙaryar an tura ta aiki wani state ɗin ne shi ya sa. Gidan Maman Humairah babu wahalar ganewa, hakan ya sa ban wahala wajen ganewa ba. A shirye na tarar da ita, bayan mun gaisa ta kawo mini ruwa ta ce. "Ba zama za mu yi ba, gidan Maman Nasmah za mu je." Da sauri na ce. "Me za mu yi kuma? Da ma shi ne kiran? Gabana yana ta faɗuwa na ɗauka wani abun ne ya faru fa." Wani kallo ta yi mini ta ce. "Mene ma bai faru ba, ke dai kawai ki zo mu je." Bin ta na yi da kallon ayar tambaya ban ce komai ba. Ta dafa kafaɗata tare da faɗin. "Maman Nasmah fa ƙawarki na ce miki za mu je gidanta ba wata ba, mene abin damuwa a ciki? Ba cutar da ke zan yi ba kin sani ba, kuma ina mai tabbatar miki babu abin da zai faru sai alkhairi." Ajiyar zuciya na sauke na ce. "Toh shikenan, amma....."
"Amma me? Ki ajiye tambayoyinki, da mun je duk za ki samu amsoshin su a sauƙaƙe." Ta katse ni da faɗin haka. Ban ce komai ba na miƙe muka tafi.........✍️
*Zeey Kumurya*✍️
[5/11, 12:13 PM] Bahaushiya👍: *YI WA KAI*
MIKIYA WRITERS ASSOCIATION
*BRIGHT PENS*
(FREE BATCH)
*34.*
Ji nake kamar na koma gida na cewa Maman Humairah na fasa zuwa, saboda gabaɗaya daga group ɗin har ƴan group ɗin sun fice mini daga rai, tunda a sanadiyyar su na tsinci kaina a cikin halin da nake ciki a yanzu. Sai dai kuma ban san me ya sa wani ɓangare na zuciyata yake son mu haɗu da Maman Nasmah ba, ko don a lokacin da na auri Idonnera na so mu gana na faɗa mata halinsa ne?
Cikin mintuna ƙalilan muka ƙarasa, gidan da take ne wanda na taɓa zuwa, amma kuma an sake yi masa gyara da canje-canje da ya fi na da kyau. Sai dai ko kaɗan bai burge ni ba wannan karon, don duk da an yi masa gyaran bai kai wanda na zauna a gidan Mansur ba kyau da tsaruwa ba. Tana gaba ina bin ta a baya har muka tsallake faluka muka shiga wani bedroom, wata mata na hango a kwance ta yi ruf da ciki. Ganin Maman Humairah ta zauna a bakin gado ni na na zauna ina bin ɗakin da kallo.
"Hafsat Alƙali ga Maman Sultan ɗin na kawo miki." Da sauri na ga ta juyo kanta inda muke ta kalle ni. Waro idanuwana na yi waje kamar za su faɗo saboda mamaki, Maman Nasmah ce, duk da matuƙar canzawar da ta yi na gane ta, amma yadda ta rame ba ta fi rabin da ba ya sa ko kusa ban kawo ita ba ce da farko. Idanunta duk sun jeme sun yi wani iri. Tun daga fuskarta, wuyanta, hannunta da duk inda ake gani a jikinta wasu irin ƙuraje ne baƙaƙe marasa kyan gani sun yi mata dama-dama.
"Kin gan ni haka ko Hafsah?" Ta faɗa a raunane idanunta cike da ƙwalla. Ban iya magana ba saboda tsananin kaɗuna, ga tsikar jikina da take tashi tunda na ɗora idona a kanta. Ba ta damu da shirun na yi ba ta ci gaba da faɗin. "Ban san ta inda zan fara ba ki labarin abubuwan da suka faru bayan rabuwar mu da kafin rabuwar mu ba, abin da na sani kawai na cuce ki, na yi wa rayuwarki illa, amma duk da haka ba su kai waɗanda na yi wa kaina ba. Na ga illar zalunci da kauce wa hanyar Allah Maman Sultan." Ta yi shiru tana jan numfarfashi tare da yin tari sannan ta ce. "Hafsah tun ranar da na je gidanki na kamu da mugun son mijinki, duk zuga kin da na dinga yi ki yi masa rashin mutunci da gayya na yi, saboda ina so ki fito ni na aure shi ne!" Ban san ya aka yi na miƙe ba sai kawai gani na, na yi a tsaye, jikina na wata irin kyarma. Cikin rashin fahimta na ce. "Ban gane ba me kike nufi ba, Anas ɗin nawa kike so ko wa?" A galabaice ta yi mini alamar na koma na zauna. Ban bi ta kanta ba na kuma daka mata tsawa da tambayar da na yi mata. Maman Humairah da ke kallo da sauraren mu ta miƙe ta zaunar da ni tare da faɗin. "Ki yi haƙuri, ki zauna ki gama saurarar ta." A fusace na buɗe baki zan yi magana ta hana ni ta hanyar rufe mini baki tare da girgiza mini kai. Huci na saki na ƙura wa Maman Nasmah ido cikin tafarfasar zuci. Tana yamutsa fuska alamar ba ƙaramin jin jiki take ba ta ce. "Na yi ina yi na, da duk ƙoƙarin da zan yi, da duk wata hanya da zan bi don na ganin na auri mijinki amma Ubangiji bai ba ni nasara ba, ke ko ƙara ganin shi ma ban yi ba, sai an ce mini yana guri kaza ina zuwa sai a ce yanzu ya tafi. Na san halin mijinki Alhaji Mansur da sana'arsa saboda tare suke komai da mijina, duk halinsu ɗaya. Mugunta ce kawai ta saka na haɗa ku. A lokacin da ya kira ni ya ce mini kun rabu da hanyar da kika bi ya sake ki ba ƙaramin jinjina miki na yi ba, don ba ƙaramar sa'a kika taka ba. Na yi takaici ba ɗan kaɗan ba saboda ina tsoron kar ki koma gidan tsohon mijinki. Duk alwashin da ya ɗauka a kanki ya faɗa mini, na ƙara ƙarfafa masa gwiwa, muka bar abun a idan ya dawo daga wata tafiya da zai yi sai mu san abin yi a kanki, sai dai bayan sun je garin da suka tafi, sun sauka a airport, driver ya ɗauke su zai kai su masauki suka yi accident suka samu muggan raunuka a jikinsu wanda ko inda kansu yake ba su sani ba. Har yanzu suna kan jinya, wadda ba na tunanin za su tashi daga ita sai dai wani ikon Allah, don ba ƙaramin azaba suke sha ba, saboda a yadda aka ce daga accident ɗin har jinyar da suke saka musu hannu abokan hamayyar su suka yi, an kai su ƙasashe sun kai biyar, an yi magani har na gargajiya amma ba wani ci gaba, dole aka dawo da su ake jinyar su a nan gida.
Ni kuma a rana ta ƙarshe da na je neman Anas na dawo na tarar mijina ya dawo, na yi farinciki da hakan saboda ina so ya sake ni, sai dai hakan bai samu ba a sakamakon da ciwo ya dawo, sai hankalinmu ya yi kan neman magani, don wasu irin tsutsotsi ne suke fita ta duburar shi, ga kashi ba ya notice kawai zuba yake, kuma ya ƙi zuwa asibiti sai wani aminintaccen likitansa ne yake zuwa gida ya duba shi, da na buƙaci a fita da shi waje sai ya ce ai kafin ya dawo sai da ya je aka duba shi a haka. Duk da wannan halin da yake ciki amma yake amfani da ni ta baya kamar yadda muka saba da ma idan yana gari, saboda idan bai yi ba ya ce tsutsotsin wani irin yawo suke yi masa a jiki, sai ya yi amfanin da ni yake samun sauƙi. A nan na kwashi ciwon ba tare da na ankare ba, na shiga matuƙar tashin hankali wanda ba zai misaltu ba, na yi ƙoƙarin yin rigafi na tari ciwon kafin ya kar ni amma sai da ya kar ni, ni ma na koma kamar yadda yake. Ga cutar HIV da na kwasa a jikin mazan da nake hulda da su. Wannan ƙurajen kuma ban san dalilin su ba, kawai sun fito mini ne, ko magani ban nema musu ba saboda na gaji da rayuwar, so nake kawai Allah ya ɗauki raina ko zan huta da wannan wahalar. Daga ni har mijina yanzu ba mu isa mun zauna ko mu kwanta rigingine ba, saboda azabar da muke sha da yadda tsutsotsin suke fitar da mu daga hayyacinmu. Daga kwanciyar gefe da gefe sai ruf da ciki. Wanda hakan ma wata izayar ce ta daban, don ko'ina a jikinmu kullum cikin ciwo da ƙagewa yake. Shi ya sa na nemi Maman Humairah na roƙe ta, ta nemo mini ke ta kawo mini na nemi yafiyarki ko zan samu sassauci a rayuwata, na yi nadama, na yi da na sanin aikata abubuwa da dama saboda son abin duniya, yanzu ga dukiyar mun tara, ga uban kuɗi amma ba mu da damar ci, kuma dole watarana muna ji muna gani mu tafi mu bar ta, mu je lahira a tuhume mu akan ta yadda muka tara ta." Ta ƙarashe maganar cikin matsanancin kuka kamar za ta shiɗe.
Ajiyar zuciya kawai nake saukewa, ina jin wani imani da tsoron Allah yana ƙara shiga ta, Maman Nasmah ƴar'gayun nan mai fantamawa son ranta yau ita ce a haka? Kuma duk zaman da take yi da mijinta ta ce komai shi, ya yi mata kaza duk ƙarya ce ashe? Tunda ba ya nan ma a ina za ta gan shi. Sai abin da ya ƙara ɗaure mini kai da ta ce a jikin mazan da take bi ta samu cutar ƙanjamau, kenan da auranta take bin wasu mazan a waje? Ƴaƴanta yaya matsayi su yake to? Ban san lokacin da na furta. "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!" A fili ba, sai na ga ma ashe ni tawa ƙaddarar nafila ce a kan tata. Cikin kuka ta ce. "Don Allah, ba don halina ba ki ce kin yafe mini, na san na cutar da ke da yawa, sannan na yi silar raba ki da mijinki, hatta kayan da na ba ki da za mu yi taro
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 21 Chapter of 24