Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
har yayi bacci jalal be daina ba Kallon ummi yayi tare da kwantar dashi da kyau "gobe zanje kafancen" Allah ya kaimu, tashi kawai yayi ya fice Kallo mami tabishi dashi tare da yima Allah godiya........ [25/12, 14:04] Hassan Atk: 🤴🤴 JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 76-80 Tsawon lokaci ya dauka yana bacci kafin ya samu tashi daga bacci Kallonshi ummi tayi ta sakar mishi murmushi ya tashi ji yake kamar yayi wani aikin gajiya "Tashi kaje kayi wanka" ba musu ya tashi har mamakin lokaci yayi Washe gari jalal yasa mubarak yayi mishi rakiya zuwa kafancen sukaje Kallonshi kawai yake yana yana diba sayyun itatuwa Wai me zakayi dasu ne? Ummi ta sani nemansu mana Haka suka gama abinda suke suka dauko hanya suka dawo zariya Kallonshi mubarak yake yana hada sayun ya gama ya hada man shafawa Sayyun itatuwa da zaitun da habbatus sauda Zanje wurin ummi,,, harara yayi mishi ya tashi shima ya sanja kaya zuwa irin na jalal din Cike da girmamawa suka gaida ummi "jalal ka gama hada maganin? Eh kawai yace "toh muje ko? Part din mami suka nufa harda mubarak din Suka sameta kishingide ta tashi zaune suka gaidata Ummin jalal dazu ko na tura a kiraki akace bacci kike Ciyon kaine ya sani bacci Toh da sauki dai ko? Alhamdulillah gaskiya Abdul din fa? Bari na kirashi yanzu ya bar nan ta daga waya ta kirashi ya shigo da sallama "Ummi wannan zai riqa shane wannan kuma zai riqa shafawa ne idan ze kwanta" Toh meye matsalan? Sai bayan kwana uku zan gaya miki "Bros jalal na menene? Ko kallonshi beyi ba bale ya bashi amsa Bakaji me yake cewa bane? Kallon mubarak din yayi ya aiko mishi da saqon harara Murmushin dole yayi tare da kawar da kanshi Ummi zamu koma school Ummi kin soya nama? Mubarak jalilah ce ta cinye sauran saidai kazo anjima ko gobe Wannan yarinyar ta fiye kwadayi wallahi Kallonshi jalal yayi "toh meye damuwarka? Ba shiri jalal yayi dariya dan yanayin yanda mubarak din yayi magana ba kadan ya bashi dariya ba "Wai jalal idan ba mubarak ba ba wanda yake sanyaka dariya ne kome? Ummi dan Allah ki daina yanzu zaice saboda nayi mahaukaci dashi ne Dariya sukayi lokaci daya mubarak da jalal suka tashi har sun kusa fita daga dakin jalal ya juyo yana kallonshi alama yayi mishi da yazo Wuri ya nema suka zauna mubarak kam tashi yayi ya matsa yana amsa waya Kallonshi jalal yayi cikin ido "Ka riqa addua kafin ka kwanta ka daina sauraren waqoqi nan da kake saurare basu da amfani ga rayuwarka" CD plate ya bashi "ka sanyashi acikin motanka ka zubar da wadan nan" kai ya gyada mishi yana murmushi "Giya illa ce ga rayuwarka ka daina shanta kafin kayi dana sani" nan ma kai kawai ya gyada mishi Jalal ne ya fara tashi yana kallon mubarak "malam wayan nan ya isa haka mana" Kashe wayan yayi "jalal Allah yunwa nakeji" dariya yayi tare da kawar da kanshi daga kallon mubarak din "Toh muje" wai ka dafa wani abune da zakace muje,, part din ummi mubarak ya nufa Binciken food flacks din ya fara "yauwa ai da sauran naman" Jalilah ce ta shigo da alama daga school take ko kallon jalal batayi ba shige kawai Bayanta yabi ya sameta tsaye kusa da mubarak sai shagwaba take zuba mishi Tana ganin jalal kawai tayi ciki yabi bayanta Hijab dinta ya cire ya qaraso kusa dashi "jalilah fushi kike dani? Kyaleshi tayi "bazakimin magana ba? Ya qaraso kusa da ita har suna juyo numfashin juna "gayamin me kike yima fushi? Ba komi Amma kike fushi? Ya fada a raunane "toh meyasa jiya kazo na hangoka ina sauri kawai ka fice dan kada ka ganni" murmushi yayi "sorry ummi ce ta aikeni shiyasa kikaga ban tsaya ba" juyawa tayi da sauri ya juyo da ita "bazaki daina fushin ba? Toh zaka sayamin ice cream? Dariya yayi cike da qasa ita Zan saya miki,, dariya tayi ta fada jikinshi rabata yayi da jikinshi bari naga ko mubarak ya gama zamu tafi ne "ya jalal" juyowa yayi yana kallonta "hhhhhh yau kunyi kyau" murmushi kawai yayi ya fice daga dakin Zaune ta samesu ta zauna kusa dashi "ya jalal na samu qawa tanada kirki sosai" kinsan banason wannan shirmen ko? Maza ki rabu da ita Kwantar da kanta tayi ajikishi "ya jalal kayi haquri Allah tanada kirki sosai" Murmushi mubarak yayi ganin yanda suka kafe juna da ido gashi ta wani shigewa jikinshi kamar wata mage "Ya jalal kayi haquri? Kai ya gyada mata har lokacin tana jikinshi Ummi ce ta shiga kallonsu tayi ba wanda ya kula da ita cikinsu jalilah hankalinta yanaga chatting din da jalal yakeyi "jalal meye haka? Ummi menene? Harara tayi musu "ko yaushe sai fadan da nake maka bazai shiga kunneka ba ko? Jalilah Allah na qara ganinki jikin jalal rankin zai baci" kallon juna sukayi Tsawa ummi ta daka mata da sauri ta tashi ta nufi dakai tana kuka Tashi yabi bayanta ya sameta kwance tana kuka Dariya yayi "jalilah tashi kiji" ba musu ta tashi Share hawayenki kiji,,, Ta share hawayenta "banason kina yawan kuka kinsan banason wannan kukan ko? Toh me nayi takemin fada? Ya isa banason irin wannan surutun Jikinshi taje ta kwantar da kanta "yaushe zaka kawomin ice cream din? Tashi yayi "anjima zan kawo miki amma ki tabbatar kinje islamiyya Kai ta gyada ya fice ya sami mubarak sukayiwa ummi sallama suka fice.............. [25/12, 14:04] Hassan Atk: 🤴🤴JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 81-85 Sai mami tayi da gaske kafin cool AJ yasha maganin sai yace ba dadi tsawon kwana uku kenan ummi ta kira jalal "jalal ba yaune zakazo ba? Ummi muna hanya ai" Zaune suke a parlour'n mami ta kira cool AJ yazo suka gaisa Kallonshi jalal yayi da kyau "zo nan" ba musu yaje amma gaskiya ji yake kamar zuciyanshi zata fashe ga baki daya ji yake ya tsani jalal din "Mubarak zo ka gani" ba musu ya matsa kusa dashi "riqemin babban yatsanshi" haka ko akayi kallonsu kawai mami da ummi suke Wani magani ya fitar ya fara shafa mishi acikin kanshi ko ina kafin ya shafa mishi a face dinshi Hade face yayi yana yiwa jalal mugun kallo "wai me kakeyi ne haka? "Mubarak sakeshi kawai Karatu jalal ya fara yi ba tare da ya riqeshi ba da sauri ya tashi ya shiga zaga dakin jalal ko kallonshi beyi ba yaci gaba da karanto ayoyin al Quran Tsawon lokaci yana karanto ayoyin masu ratsa zuciya cool AJ sai faman zaga dakin yake Cike da razana suke dafe kunnayensu sakamakon qarar da yayi ya fadi Kusa dashi jalal ya matsa yaci gaba da karatun ahankali bakinshi ya fara motsawa Shuru jalal yayi yana kallonshi " 'yata ke sonshi ni kuma ba abinda zata nema na bari ta rasashi" A iya tunaninki akwai aure tsakaninsu? Wannan ba damuwata bace Idan na qonaki nayi laifi? Kada kayi haka Meyasa kika bata rayuwanshi? Bani bace,,, "qarya kike" dan murmushi yayi "Idan har banyi hakan ba duk mace ta gari zata soshi daga baya na gane hakan ba mafita bace sai na sanya tsanar mata acikin zuciyanshi" "Abu mai sauki ne na qonaki amma zanyi miki adalci" Kada kayi tunanin zan rabu dashi dan 'yata ko yaushe tana ganinshi tana kasancewa cikin farin ciki ni kuma bazan rabu dashi ba" Kinsan a ina 'yarki take yanzu? "Ka daureta acikin jikinka" Kinsan dalilin yin hakan? Aa Jikina tamkar garwashi yake a wurinta zan azabtar da ita kafin in qonata ne kamar yanda zan qonaki Amma kasan sauran 'ya'yana bazasu barka ba? Murmushi jalal yayi "ba abinda zasu iya dani dan ke kanki biki iya aikata komi ba" Kana ganin idan kayi hakan zaka zauna lafia? Murmushi yayi ya fara karanto wasu addu'o'i Nan take ta fara ihu "Zan barshi basai ka qonani ba" sam jalal be saurara mata yaci gaba da qonata Tsawon lokaci tana ihu har tazo ta daina ga baki daya Shuru yayi yana kallon cool AJ Sanyayar ajiyan zuciya ya sauke Dafe zuciyanshi yayi "ummi bani ruwa" da sauri mubarak ya miqa mishi yasha Duk idanunshi sun sanja zuwa ja kallonshi kawai suke "Jalal lafia? Kai ya girgiza sai faman gumi yake Lokaci daya kuma ya fara kakkarwa "jalal wai lafia? Ummi ta riqeshi "Mubarak tashi ka fita" Lafia? Tashi nace Tashi yayi yana tafia yana waige "Ummi dan Allah ki yafeni ba lallai bane na rayuwa kuma nayi hakan ne saboda abdul jabbar ya samu lafia nasan zasu ilkatani amma nayi miki alqawarin zan qonasu kafin nabar duniya, ummi dan Allah kada ki bari mubarak ya shiga wani hali akan rashina" Jalal meyasa kayi haka? Cewar mami duk hankalinta ya tashi "Ummi bani ruwa " karatu ya shigayi yana tofawa a ruwan tsawon lokaci kamar numfashinshi zai dauke Zubawa yayi ajikinshi wani zafi yaji duk ya fita hayya cinshi Daqyar yake numfashi Ahankali har ya fara samun natsuwa mami ga baki daya hankalinta atashe yake sai faman jera addua take Ahankali ya dago yana kallon ummi "ummi zai dauki tsawon kwana uku yana baccin nan a nemo wadan da zasu sanja mishi wurin kwanciya "Jalal kai kuma fa? Kallonta yayi "Ummi jinin da yake jikina kadan ya rage bazai wadaceni na rayu ba" nan take ummi ta gane matsalar saboda ta taba faruwa da baffa Da sauri ta kira mubarak "muje a kaishi asibiti da wuri a qara mishi jini kafin ya mutu" Jinin mubarak aka fara gwadawa cikin sauri aka fara qara mishi jinin Duk wannan abinda da ake mai martaba be sani ba haka baffan jajal Mami kam hankalinta be kwanta ba ta kira mai martaba ta gaya mishi halinda ake ciki Da sauri suka nufi hospital din har ya fara bacci mubarak kam har idanunshi sun kumbura saboda kukan da yake A&E ga baki daya cike take saboda zuwan sarki Mahmud Kallonshi baffa yayi yayi murmushi "Aisha yaron nan naki bayada jarumta fa" haba baffan jalal na'ima saida aka qara mana jini" toh meye abin roqon gafara? Murmushi mai martaba yayi "Allah ya bashi lafia" suka amsa da ameen Kallon mubarak yayi ya sakar mishi murmushi Zaune suke tare da baffan jalal "wannan shine na farko da yayi shiyasa kuma bata bayn gida yazo musu ba saboda zuciyanshi ta riga ta kawo kawai ya tunkaresu Murmushi mai martaba yayi Zaune suke gaban AJ sai faman bacci yake Kallon mai martaba baffa yayi "sun cutar da yaron nan ba kadan ba kuma matsalan basu zauna ajikinshi ba bale a gane da wuri" jinjina lamarin mai martaba yayi Washe gari jalal yana kwance ya juya yana kallon mubarak murmushi sukayi juna Mamin mubarak ce ta shigo suka gaidata tayi musu ja jiki Abinci ta zuba musu sai faman hararan jalal mubarak yake "malam lafia? Meye damuwarka dani? Kawar da kanshi yayi yana murmushi ********************************** Da salati ya bude bakinshi ahankali ya fara bude idanunshi ya qarewa dakin kallo Sannu mami tayi mishi jin zuciyanshi yake kamar an dake mishi dotse akanta Kallonta yayi "mami jalal fa? Murmushi tayi mishi Je kayi wanka kazo ka rama sallar kwana uku Ido ya zare "mami kwana uku fa? Kai ta gyada mishi Tashi yayi ya nufi part dinshi yayi wanka ya shiga reja sallolin da make binshi Ba yanda ummi batayi ba akan jalal yazo su tafi gida yace shi school ze tafi dole mubarak ya haqura yabishi suka tafi............ [25/12, 14:04] Hassan Atk: 🤴🤴 JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 86-90 _Allah ya gafarta miki aunty amina yasa aljannah ce makomarki_ *ameen* Kwance suke bayan sunyi wanka kowa da abinda yake tunani aranshi, wayan jalal ce tayi ringing ya diba yaga new number ne ya daga tare da kwarara sallama Ta dayan bangaren kuma cool AK ne ya amsa "bros jalal where r u? Shuru yayi kamar bezeyi magana ba "Hello" sai a lokacin yayi magana "am in d hostel" okay which room you guys r? "7" okay ya katse wayan Kallonshi mubarak yayi "waye? Abdul" Ni dan Allah ka hadamin kunu Allah shi nakeso nasha "Kai bazaka iya bane? Eh bazan iya ba Ko kallonshi jalal beyi ba bale ya tashi Sallama yayi suka amsa mubarak ne kawai ya tashi amma jalal sam bayada alaman tashi suka gaisa "Bros jalal jikin ne? Kai ya girgiza mishi alaman aa Murmushi yayi ya zauna kusa da mubarak suka dan fara taba fira "Jalal amma kasan inajin yunwa ko? Tsaki yayi ya sauko ya dora ruwan zafi ya dama mishi kunu ya zuba a cup saura kuma ya juye a flacks Qin dauka mubarak yayi "Allah idan yayi sanyi kamin magana zakasha mamaki" toh ka bani ne? Ya fada yana hararan jalal din Murmushi cool AJ yayi "you guys r very funny" Kwanciya jalal yayi abinshi mubarak yaqi daukan kunun tsaf jalal yasan mubarak ba dauka zeyi ba ya sauko ya dauka ya bashi "sai ka zubamin ajiki ne? Eh ya bashi amsa "Bros mubarak wai haka kuke fada? Bakasan waye cool jalal ba ai wallahi hurt jalal yafi dacewa dashi Aiko jalal saida yayi dariya dan mubarak din ya fiye rikici Haka mubarak da cool AJ suka sha fira abinda mubarak ya fahinta kusan halinsu daya kawai dai abdul din yafi jalal yawan magana Lokacin sallah ne yayi mubarak yace ba inda zashi a ciki zeyi sallah "Allah baka isa ba sai kaje" sai kamin dole "sai fa kaje" tsaki kawai yayi jalal yazo yayi tsaye gabanshi suka shiga kallon juna Jalal kasan dai baa wasa da sallah ko? Sai fa kaje masjid din Tsaki yayi ya janyo kaya irin na jalal din ya sanya yayi gaba jalal yabi bayanshi yana dariya Sosai cool AJ yaji sun burgeshi shida jalal ne a baya mubarak yana gaba suka qarasa cikin masjid din jalal yaje kusa dashi ya tsaya Sosai ya basu dariya ganin ya sanja wuri Jalal da AJ ne suka daidaita suka fara yin sallah AJ yan bin jalal har suka kammala Mubarak ya rigasu fita ya nufi hostel Lokaci daya suka dago dan satar kallon juna aiko suka hada ido jalal yayi sauri ya kawar da kanshi murmushi AJ yayi "Amm rakani mana" kallonshi yayi "akwai wanda nakeson gani" juyawa sukayi Kowa ya gansu baya buqatar tambaya yasan jini daya ne Wuri ya nema ya zauna yana jiranshi ya gama magana da AK ya juyo yana kallonshi tare da sakar mishi murmushi ya tashi kawai suka fara tafia Kallonta yake yana nazarin wasu abubuwa kallonshi ya maida ga hannunta ba alaman jin ciyo har ta kawo kusa dasu ba tare da kallesu ba ahankali ya sauke ajiyan zuciya wanda ya sanya jalal ya kalleshi Hanya jalal ya sanja yaje ya siyo coke guda biyu suka nufi hostel Kallon coke din mubarak yayi jalal yayi mishi harara ya cire kayan jikinshi Supergetti da kifi jalal ya dora sosai ya bawa abdul dariya ganin yanda yake girkin kamar mace ya kammala ya juye a food flacks ya tashi ya fita Be jimaba ya dawo da qanqara a hannunshi ya fasa ya ya zuba a cups ya dauko plate ya ajiye musu kawai ya nufi toilet yayi wanka AJ tunanin yanda zeci abincin yake dan ganin yake bazaiyi dadi ba haka ya zuba abincin yakai spoon daya a baki Sosai yayi mamaki test din abincin Kallon mubarak yyi yaga shi sam hankalinshi baya kanshi ci kawai yake Ba wanda ya kalla daga cikinsu ya sanja kaya da alama fita zeyi "Malam ina zaka? Meye damuwarka? Bafa inda zaka Tsaki kawai yayi ya mayar da kayan ya dauki ragowar abincin mubarak yaci kadan yayi kwanciyarshi Haka suka wuni a hostel din AJ sai faman dariya yake ganin fadane kawai tsakanin jalal da mubarak kuma ba wanda yake tsallake zancen wani Sun gama sallah isha cool AJ ya kallesu cike da murmushi "bros zan tafi bacci nakeji" dariya mubarak yayi toh muje muyi maka rakiya ko? Tafiya suke sai mubarak ne kawai yake zuba surutu Wurin da yayi parking suka tsaya ya bude motanshi ya shiga ya tada motan "bros abdul ka sayamin ice cream wa jalilah dan Allah" cewar mubarak Kallonshi yayi yana murmushi tare da gyda mishi kai sukayi sallama dashi suka juya Kallonsu yake suna tafia da alama jalal magana yake yiwa mubarak kuma serious magana ce Waya take har ta qaraso ta wurin da cool AJ yake Kallo daya tayi mishi ta kawar da kanta tayi taci gaba da tafia kamar ya tsayar da ita kuma yaji sam bazai iya yi mata magana ba har ya daina hangota Gida ya nufa cike da tunani a zuciyanshi Tsawo sati daya cool AJ ko yaushe a hostel yake wuni idan sunada lectures su tafi su barshi haka shima idan yanada zai tafi ya barsu Yau ta kama sunday jalal ya kalli mubarak "malam ya dace kayi aski fa" tsaki yayi Bros abdul muje dan Allah tunda ya fara zancen askin nan sai nayishi gara na tafi kafin ya batamin Dariya jalal yayi ya sanja kaya suka fito Duk yanda abdul AJ yaso su tafi a mota sam jalal yaqi haka suka taka da qafa suna tafia Tafe suke itada salma sai faman dariya salma take mata Tunda ya hangosu yanayinshi ya sanja tafia kawai yake Duk yanayin da yake ciki jalal yana kule dashi haka mubarak amma ba wanda ya nuna mishi Aski akeyiwa mubarak jalal yace acire gashin ga baki daya wani kallo yayiwa jalal "Allah baka isa ba" sai fa an cireshi duka Tsaki yayi yana kallon mai shagon "malam dan Allah cire duka sauri nake" dariya jalal yayi "kada ka cire duka yi mishi wanda ka saba yi mishi" kallonsu kawai cool AJ yake amma hankalinshi baya wurinsu har suka kammala suka nufi hostel Kwanciya yayi yana tunanin juwairiya shin dagaskene ya yanka mata hannu ko mafarkin hakan ne yayi? Wa zai amsamin? Tashi yayi ya dauki wayanshi ba tare da yayi musu magana ba ya fita ba wanda yayi mishi magana daga cikinsu Duk inda yake tunanin zai ganta ya diba ba alamanta har ya haqura ya nemo wuri ya zauna Tun kafin su qaraso ya ganeta yayi saurin tashi ya nufesu Sosai juwairiya taji zuciyanta ta buga dan tasan ba kirki ne da cool AJ ba Cak ta tsaya suka zubawa juna ido,,, cike da qarfin Hali ta fara yi mishi magana "malam lafia? Salma kam gaba tayi tana murmushi Tsaki taja tabi gefenshi zata wuce Cike da mamaki Salma take kallon ikon Allah ganin yanda cool AJ ya janyo juwairiya ya hanata da qirjinshi ahankali ya furta mata "am very sorry pls" Janye jikinta tayi da sauri tana hararanshi Da sauri ta nufi wurin salma Kallonta Salma take taja hannun Salma suka nufi hostel Kallonta salma take duk tayi wani iri "juwairiya kinga fa guy din nan ya cika da rainin hankali kamata yayi kasan abin yi tun da wuri" Kwanciya kawai tayi lokaci kadan tayi bacci har mamaki salma take Hostel ya nufa kallo daya jalal yayi mishi ya fahinci akwai abinda yake damunshi Sam AJ yace bazaici abinci ba wani kallo jalal yayi mishi Key dinshi kawai ya dauka ya nufi hanyar fita "abdul" jalal ya kirashi ya juyo yana kallonshi Something bothering you and your keeping it to yourself, right? Murmushi kawai yayi ya juya ya fice Kwanciya jalal yayi yaci gaba da aiki da system dinshi Kallonshi mami take tana nazarinshi "abdul meke damunka ne? Kamar zeyi kuka yake kallonta "mami kamar a mafalki na yake hannunta fa amma fushi nake dani kuma ni sonta nake" kai ta girgiza tana murmumshi Ya gaji da zaman da yake ya tashi ya fita sai faman fushi yake "Ya abdul fita zakayi? School zan tafi" jirani dan Allah zan bika Da sauri ta nufi part din ummi ta sanja kaya suka nufi school din "Bros jalal suna lecture fa" ba wurinshi zan tafi ba wurin sis juwairiya" da sauri ya juyo yana kallonta "jalillah kinsanta ne? Ya mubarak ne yake sonta " sosai yaji zuciyanshi ta buga wani tashin hankaline ya ziyarceshi............... [25/12, 14:04] Hassan Atk: 🤴🤴 JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 91-95 Kallon juna suke shida ita ganin tayi duk ya fita hayyacinshi har ya fara zufa "ya abdul lafia? Girgiza kanshi yayi "by 2 zan gama abinda nake sai ki fito" Sam AJ beyi attending lecture ko daya ba saboda baya cikin hayyacinshi Kasancewar mubarak yanajin yunwa ya sa jalal ya fito shi kadai yaje sayen kayan da suke buqata Kallonshi ya tsaya yi sam baya tare da natsuwa Kusa dashi yaje ya dafashi Kallon juna suke na tsawo lokaci kafin AJ ya sauke ajiyan zuciya "Meke damunka? Murmushi ya qaqalo wanda ya sanya jalal qara hade face dinshi "Gayamin meke damunka? Bros jalal abubuwa sunata zuwanmin kamar a mafalki ne kawai" tsaki yaja "Wai atunaninka bansan damuwarka bane? Juwairiya right? "No na haqura da wannan yarinyar kabar zancenta" meyasa? Amma kasan mubarak ne yake sonta ko? Dariya jalal yayi yana kallonshi "mubarak din ne ya gaya maka hakan? No jalilah ce tare ma mukazo da ita tana wurin juwairiya din" Sosai yake kallon jalal yana dariya "abdul meye abin dauka acikin zancen jalilah? Toh ba gaskiya bane dan baya soyayya idan kana sonta kaje ka gaya mata kawai "Bazata saurareni ba" why? Bayanin abinda ya faru yayiwa jalal Ka bata haquri kuma? Kai ya gyada mishi Tashi ka rakani Tafia suke jalal yanajanshi da fira ahankali yake amsa mishi jalal kam mamaki yake yanda soyayya take mayar da mutum haka Harara mubarak yayi musu "kawai daga zuwa sayen tulare sai kayi zamanka" meyasa bakaje nemana ba? Kai waramin yarone da zanje nemanka? Tsaki jalal yayi mubarak ya matsa kusa dashi "Bawan Allah ai yau zaka yi mana dan wake ko? Kakan wake zanyi" sai a lokacin AJ yayi dariya "sai fa kayi mana" Duk yanda yake cikin damuwa idan jalal da mubarak suka fara rikici dole ne yayi dariya "Bros jalal nifa zanci" sai ku girka,,, kwanciya AJ yayi tare fito da wayanshi ya bude email dinshi Zama jalal yayi ya janyo system dinshi ya shiga aikin gabanshi "Bros jalal wai bazaka yi mana ba? So kake yunwa ta illatamu ne? Tsaki yayi ya kashe system din ya dora ruwa suka shiga dariya Allah za kuyi girkin nan da kanku Ba wanda ya qara yin magana daga cikinsu sai faman dariya suke qasa qasa Zuba musu yayi a plate yaje yayi wanka ya dawo ya sami AJ sai faman sauri yake ya kammala "Ba kyau fa" jalilah jirana take kada tayi gaba" wallahi yafi komi sauki indai jalilah ce " Rakiya mubarak yayi mishi "kaga bari na koma banason fitina ka gaida su mami" Kallonsu yake har suka qarasa kusa dashi sai faman fira suke suna dariya "Ya abdul sis juwairiya tayimin dan wake" murmushi yayi "muje" Kallon juwairiya tayi "sai nazo muje wurin ummi ko? Kai ta gyada mata tana murmushi Ta shiga motan yaja jalilah na daga mata hannu *9:30pm* duk mubarak yayi bacci jalal ya shirya tsaf ya fita sai zuba qanshi yake ya nufi wurin da yasan zaiga juwairiya Cikin saa ya ganta ita kadai zaune tana rubutun project dinta yayi mata sallama ta amsa ya nemi wuri ya zauna Kallonta yayi tayi saurin sunkuyar da kanta "juwairiya right? Kai ta gyada mishi Murmushi yayi yana kallon system dinta "project kike typing? Zan turawa supervisor dina ne a email dinshi Karba yayi yana kallo tare da murmushi "Sorry zan iya yi miki correction? Kai ta gyada Janyo system din yayi ya shiga typing yana gyara mata cike da mamaki take kallonshi har ya kammala tanada yaqinin da itace ko rabi batayi ba Kallonta yayi cike da natsuwa "juwairiya nasan kinajin zafin abinda abdul yayi miki wanda nasan hakan ba dadi amma inaso ki fahinci abdul mutum ne mai kirki saidai matsalan rayuwa da ya samu nasan ke kanki kinsan ya sanja yanzu,, cike da natsuwa yayi mata bayanin abinda ya faru da cool AJ ba abinda ya boye mata ,,, "juwairiya abdul yana sonkine bawai da wasa pls ki bawa zuciyanki haquri for God sake" sam juwairiya batayi tunanin abinda jalal yazo mata dashi kenan ba Kallonta yake yana jiran yaji me zatace "pls say something" ahankali

Chapter 5 of 13