Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
haka" me kakeso ka gayamin yanzu wanda bansani ba? Murmushi mubarak yayi "haquri nakeso kayi" "Mubarak kaje dan Allah" "jalal hamma kasan ni bana mana hakan ko? Cike da zafi jalal yake mishi magana "me kake nufi ne? Me kuma kakeso ka gayamin? Tsawon lokacin da na hadu da kai ban taba gayama ummi damuwana kaine mutum na farko da yake fara sanin duk wani abu da ya shafeni bana boye maka komi har nida family dina ba abinda nake boye maka amma kai sam ba haka bane a wurinka me kakeso yanzu ka gayamin? Kallonshi yayi cike da rauni "jalal abinda nazo kenan in gaya maka sai kuma naga alaman akwai gajiya tare dakai shiyasa kawai ban gaya maka ba dan sanan zaka shiryane kace zakaje ka sami mami" Banzan kallo jalal ya aika mishi "ka ajiye wannan tarihin kuma kasa aranka ko a wurin wani bazaka qarajin damuwa na ba" "Jalal wai kai kenan ko yaushe cikin doramin laifi meyasa bazaka fahinceni ba " "Dan Allah kaje a gajiye nake inaso na huta" Tsaki yayi kawai ya fice jalal ya bishi da kallo yana murmushi Kallonshi ya mayar ga jalilah "jalilah gobe zamuje Neman family din mubarak a bauchi "Ya jalal yanzu duk wannan gajiyan sai kuma ka qara debo wani? "Jalilah mubarak ne fa? Murmushi tayi tadan kwanta ajikinshi "adawo lafia" Wayanshi ya dauka ya kira cool AJ "Abdul pls ka shirya gone za muje bauchi wurin family din mubarak "Wa zeyi driving? Dariya jalal yayi "amma ai zaka tausayamin ko? Mubarak din fa? Ka manta dashi fushi ma yake dani dan na gaya mishi gaskiya Dariya cool AJ yayi " kuma ahakan za muyi tafia? Ka barshi kawai Idan ya gaji zai daina "Idan kun gaji zakace air na'ima nasan fushin yana damunka" dariya sukayi ga baki dayansu jalal ya gaya mishi sammako za suyi Kallonshi jalilah tayi "ya jalal fadanku da mubarak Allah dariya yake bani " jalilah ni kaina mubarak din dariya yake bani kawai nayi mishi hakan ne dan ya sanja wani halin Murmushi tayi "bari naje na hada maka kayan ko? Kai ya gyada yana murmushi tq tashi ta shige ciki................. [25/12, 16:10] Hassan Atk: 🤴🤴JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMUNA ALHASSAN_ 211-215 Part din ummi ya nufa ya shaida musu zasuyi tafi tayi musu fata na gari ya nufi part din mai martaba acen ya sami cool AJ yaje sanar dasu mai martaba Wuri ya nema ya zauna "jalal toh me kuka shirya kai musu? "Abba ai bamusan halin da suke ciki ba bale musan me suke buqata" Murmushi mami tayi "Abdul zan baka saqo cikin garin Idan kunje" Kallonta jalal yayi "meyasa ni bazaki bani ba? Harara ta aiko mishi "bazan baka ba din" Murmushi mai martaba yayi ganin kallon da jalal yayi mata "Mami meye saqon dan bana tunanin zamu shigo da safe wucewa za muyi" "Acikin FGC azare nakeso kaje quarters dinsu duk wanda ka tambaya gidan hajiya Fatima 'yar azare zai nuna maka idan kaje duk abinda kaga ya dace sai ka bata" murmushi yayi sukayi sallama suka fice Tsaye suke parking space na gidan mubarak jalal ya kalleshi "kirashi ya fito muje" Kiranshi yayi ya daga suka gaisa "muna parking space muna jiranka" bazani ba kuje kawai" ya katse wayan Dariya cool AJ yayi "cool jalal kuna fada da mubarak ne? "Yace bazashi bane? Kai ya gyada yana dariya "Muje ciki" suka shiga Zaune yake kan kujera yana wasa da aisam "Mallam tashi ka shirya muje" Jawahir ce ta fito suka gaisa "Bazaka tashi ba? Ko kallonsu beyi ba Kusa dashi jawahir taje "abban khaleel yi haquri kuje mana kaga fa kai kadai suke jira" "Angel suje kawai bazani ba" "Kaga ka daina bata mana lokaci ka tashi ka shirya mu tafi" Cike da tsiwa yake mishi magana "nace bazani ba kuje ko dolene sai naje" ya tashi ya nufi upstair din Kallo jalal ya bishi dashi cool AJ kam dariya ya shigayi yana girgiza kai "Cool jalal ka lallabashi muje dan Allah kasan fa so yake kawai ka lallabashi ka yarda kaine bakada gaskiya" "Abdul kasan me yayi min ne? Koma menene yanzu kaga yanada bata mana lokaci ne" Upstair din ya nufa ya shiga dakinshi ya sameshi kwance, kallo daya yayima jalal ya kawar da kanshi yaje kusa dashi ya zauna "Ka tashi ka shirya muje" tsaki yayi ya tashi zai fita jalal ya janyoshi "wai mubarak me kakeyi haka? Meye amfanin zuwanmu ba tare da kai ba? Saboda nayi magana akan abinda yake damunka shine ya kawo wannan fushin? "Kaga kai kaje ka nemo izinin tafi toh ga address din sai kaje ni bazani ba" Sosai jalal ya dau zafi dashi kawai ya juya ya fice ba wanda ya kalla daga cikinsu ya fice "Tsaki cool AJ yayi ya nufi mubarak din daqyar ya lallabashi ya shirya jawahir ta hada mishi kayanshi kawai ta fice zuwa dakinta Acen ya sameta yaga sai faman fushi takeyi dashi "angel me kuma nayi? "Dan Allah me yasa kakeyin haka? Kaida bros jalal har sai wani yaji kanku sai kayita faman fushi dashi kuma kazo daga baya abin ya riqa damunka" Murmushi yayi "angel kinga jalal ya nuna shi yake sona ni bana sonshi shiyasa nake fushi dashi" Dariya abin ya bata "kai da bros jalal na kasa gane kanku walkahi" Murmushi yayi ya mata peck "kije ki dibamin su khaleel pls" kai ta gyada mishi tayi mishi rakiya Motan jalal ce wacce take irin ta mai martaba tana dauke da tambarin masarautar Fatan alkhairi jawahir tayi musu suka shiga ciki Cool AJ da mubarak ne a gaba jalal yana baya Suka dauki hanya sai cool AJ ne yake dan kawo fira hamma jalal baya kulasu sai faman gudu cool AJ yake "Cool jalal na gaji fa" ya nemi wuri yayi parking Fitowa jalal yayi ya karbi key din da sauri mubarak ya fito ya koma baya sosai cool AJ ya shiga dariya,,, kallo kawai jalal ya bishi dashi ya zaga ya shiga wurin da mubarak din ya fita "Cool jalal meya kawo muku wannan fadan? Sam jalal be kulasu ba yaja kawai sukaci gaba da tafia sosai jalal yake gudu fiye da cool AJ dan yasan mubarak bayason hakan "Malam ka tafi a hankali yara hudu nakeda ban shirya barinsu a matsayin marayu ba" Dariya cool AJ yake yana qoqarin daga wayan mai martaba "Eh abba mun kusa gaskiya saboda cool jalal ne yake driving yanzu" Harara jalal yayi mishi sukayi sallama da mai martaba Tsawon lokaci jalal ya shiga cikin garin azare ya shiga neman bayanin gidansu alhaji Mustapha azare besha wahala ba ya gane gidan yaje yayi parking ya nemi yaro ya tura ayi mishi sallama da wani daga cikin gidan Kallonshi yake sak mubarak saidai shi ba yaro bane suka gaisa "daga zaria muke mu 'ya'yan Maryam ne matar marigayi alhaji Mustapha azare" cike da tashin hankali yake kallonshi "kaine dana mubarak? Kai ya girgiza mishi "hamma Kaine Mustapha azare? Aa yayana ne ya dade da rasuwa ina mubarak din yake? Magana yayima cool AJ suka fito sosai mutumen ya shiga zubar da hawaye "mubarak ina Maryam ta yafemin na cutar da ita na cinye dukiyarka gashi yau duniya tayi mishi zafi ga ciyon shuga ya kamani na sayar da wannan gidan gobe ma zamu tashi ni kadai na rage hajiya ta rasu matata ta gujeni saini da yara kawai mubarak ku yafemin" Kallonshi kawai sukeyi ahankali jalal ya sauke ajiyan zuciya "abba ka daina wannan kukan bayada wani amfani zai iya tada ciyonka dan nasan bazaka rasa hawan jini ba" Dolene nayi kuka ba abinda Yaya Mustapha bayamin amma kaga bayan ranshi na cuci zuriarshi "ka daina cewa haka abba mu shiga ciki sai muyi magana Kallon yaran yake ga baki daya ba wanda bayada kama da mubarak din da ka gansu kasan sunajin yunwa "Abba wannan waye? Murmushi yayi "mustapha wannan yayanka ne" kallon mubarak yayi "yaya ka bamu hamsin mu siyo gari da sikari kaga maryam sai faman kuka take har tayi bacci "kawu Mustapha abba yace mu riqa kiranta da mummy fa kai bakaji ko? Toh batada kunya ne shiyasa nima ai bata girmama sunana" Murmushi jalal yayi ya juya ya fice su cool AJ suka nemi wuri suka zauna Restaurant ya nema cikin farin ya saya musu abinci akayi mishi take away ya biya kudin ya kai musu "Amm kaje ka kira mummy sai taci abinci ko? Yaya kyaleta batada kunya ta riga tayi bacci" Yaya mustapha bata fada da Maryam kaima ka daina "Abba dazu fa dukana tayi ta gudu dan kawai nasha farin da adda bilkisu ta bata Murmushi jalal yayi aranshi yace "wannan halinsu daya da mubarak" "Abba muje waje za muyi magana dakai" ba musu yabi jalal suka fice "Muje wurin wanda ka sayarwa gidan" ba musu ya shiga mota sukaje Sam jalal besha wahala wurin amincewarshi da zai bar mishi gidan shi yakeso ya saya saboda family house dinsu ne Kai tsaye jalal ya biya kudin suka shiga masjid sukayi sallah jalal ya koma dashi gidan Harara mubarak ya aika mishi sam be kulashi ba "Abba za muje Mu nemi wurin da zamu sauka saidai gobe zamu dawo" Godiya yayi musu tare da yi musu rakiya jalal yaja suka fice............. [25/12, 17:18] Hassan Atk: 🤴🤴 JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 216-220 Hotel jalal ya kama musu suka sauka cool AJ ya shiga nashi dakin yabar kayanshi haka mubarak ya tafi ya barshi da kaya ya dauki nashi ya fice kawai Bude dakinshi mubarak yayi ya juyo yana kallonshi "bani key zan dauki kayana" Key din ya bashi ya fice Waya yake da jalilah mubarak ya shigo ya nemi wuri ya zauna har ya kammala waya "malam yunwa nakeji" tashi yayi ya dauki key din ya fice kallonshi mubarak yayi yana murmushi be jimaba ya dawo suka shigo tare da cool AJ suka nemi wuri suka zauna Cin abincin suke jalal yana zaune yana kallonsu har suka kammala "cool jalal bazakaci abinci ba? Kai ya gyada mishi ba tare da ya kalleshi Tashi cool AJ yayi "ni zan kwanta bacci nakeji" ya fice kallon shi mubarak yayi ya tashi ya koma kusa dashi ya zauna "ina kukaje dazu? Sam jalal be kulashi ba "bakaji me nace bane? Kallon mubarak yayi "ka tambayeshi kaji mana "ai na ganshi na tambayeka" "Bazaka yimin magana ba? Mubarak me kakeso na gaya maka? Abinda na tamyeka" "Mun maidawa wanda ya sayi gidan kudinshi ne" meyasa kayi haka? Saboda yana family house ne bakyau a sayar dashi" Murmushi yayi "meyasa bazakaci abinci ba? Banajin yunwa ne Ba gaskiya bane kawai saboda kana jin haushi nane shiyasa Kallonshi kawai jalal yayi ba tare da yayi mishi magana ba "Jalal dan Allah ka riqa fahinta na meyasa kake tunanin na boye maka matsalana amma kai kanq gaya min baka damuwan kaga hakan yana nuna kai kake da zuciya daya ni kuma ba haka bane" "Ai ba qarya na fada ba haka ne mana me kake tunanin zanji a raina kai damuwana nakane amma naka kai kadai ya shafa" jalal bafa haka bane ka gaji sosai kuma abinda naje na gaya maka kenan sai naga kawai zan takuraka ne" "Ban tabaji a raina na taba takuraka ba amma kai har kanajin hakan aranaka saboda ni banaida matsayinda zan sha wahala akanka? Dariya mubarak yayi"nifa ba haka nake nufi ba kaine kayi wannan fassarar" harara jalal ya aika mishi "Pls ka daina wannan fushin Allah ni fushin nan yana takurani" ni nake fushi dakai? Kai ya gyada mishi,, kawar da kanshi kawai yayi "kaci abinci ni zan tafi in kwanta ya tashi kawai ya fice Washe gari jalal ya tashi da matsanancin headache idanunshi kamar wanda yakejin bacci suka nufi gidansu mubarak din Suna shiga ciki Mustapha yayi dariya wacce ta qara fito da kamarshi da mubarak "Jiya ka tafi baka gayamin sunanka ba" murmushi jalal yayi yaja hannunshi suka shiga ciki suka gaida abban "Abba muje waje za muyi magana" ya tashi suka fice Kusa 2hrs su cool AJ na jiranshi basu dawo ba suka kirashi a waya ya daga "cool jalal kana inane? Cikin sanyi yake magana saboda headache dinda ke damunshi "abdul yanzu zamu dawo" Tare suka shiga da wata mata sukayi sallama da gudu sukaje wurinta "umma oyoyo" suka rungumeta Sai faman murna suke ta nemi wuri ta zauna kallo daya tayima mubarak ta ganshi "Mubarak ina yaya Maryam? Tana zaria Kai ta gyada suka gaisa dasu cool AJ "Amma abba yanzu zama haka beze yi ba kamata yayi ka nemi wani business ka fara tunda ga iyali" "Toh abdul jalal wane Sana'a zanyi yanzu? Shafa kanshi yayi saboda tsananin ciyon da yake mishi "abba ka nemi wanda zaka iya sai ka sanar dani" Kallonshi mubarak yayi da kyau "are you sick? Kawar da kanshi yayi daga kallon mubarak "Abba zamu koma ga wannan dubu dari ukune sai kaje ka siyo abinci da zasu daya da sauran abin buqata umma kiyi manage da wannan kafin muga abinda yafi dacewa kiyi dan zaman beze yiyu haka ba" godiya sukayi tare da sanya musu albarka suka tashi abba mudassir harda kuka yake suke fice Abdul ka maidamu pls "Wai meke damunka? Murmushi kawai yayi ya buds bayan ya shiga suka nufi hotel din Kwance yake ya rufe idanunshi ko wane daga cikinsu ya zuba mishi ido kamar ma ba mubarak ba da yakeji kamar ace shine yake ciyon "Cool jalal wai meke damunka ne? Ahankali ya bude idanunshi "bacci ne kawai" "Wane irin bacci,, wannan cumin da kakeyi kuma fa? Murmushi yayi ya buqaci su bashi ruwa Addua yayi a ruwa yasha ya zuba a kanshi Shuru ba wanda yayi magana daga cikinsu mubarak sai faman kallonshi duk ya wani susucewa kallonshi jalal yayi ya sakar mishi murmushi ya tashi ya nufi toilet yayi wanka ya fito ya sanja kaya "muje ko" Ido mubarak ya zare "Allah ba inda zaka garama ka kwanta ka huta" yunwa fa nakeji" harara yayi mishi ya tashi ya fice yaje ya kawo mishi abinci Kadan yaci ya kwanta ya shiga bacci sai a likacin hankalinsu ya kwanta kowa ya nufi dakinshi Sai kusan azahar ya tashi yayi wanka yaje ya sami su mubarak suka nufi masjid Zaune suke dakin jalal "abdul duk abundant za muyi yaune yafi dacewa Mu kammalashi gobe sammako za muyi" "Wannan hajiya Fatima kadai zamu nema yanzu" Ba inda zani kuma baza aje da motana ba Wai saboda me? Ta aikeni ne? Dariya cool AJ yayi ya kira mami a waya yana shaida mata yanda sukayi da jalal Wayan ya bawa jalal ya karba "jalal Aiken nawane baza ajeba? Ni banace baza aje ba nine kawai bazanje ba Motan kuma fa? Mami meyasa bezo da motanshi ba saboda saqonki "Jalal banason shirme Idan ba zaka ba ka bada Mota suje Murmushi kawai yayi ya bawa cool AJ wayan Neman gidan matar sukayi har suka qarasa Sosai tayi farin cikun ganinsu cool AJ ya kira mami ya bata sukasha fira Kudine masu yawa jalal ya ajiye mata sai faman Santa musu albrka take suka fice Dariya taji sunayi qasa qasa yayi kamar beji ba dan yasan shi akeyiwa dariya............. [25/12, 17:18] Hassan Atk: 🤴🤴JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 221-225 Cool jalal wai kai aljihunka baya gajiya ne? Sam be kulasu ba yayi gaba suka sameshi cikin mota direct family house dinsu mubarak suka nufa ya dade zaune cikin mota yana lissafi Kallonshi kawai mubarak yake "malam daina kallona" Murmushi kawai yayi Fita yayi yaje ya dauko wani jaka ya dawo kallon kudin suke ba wanda yayi mishi magana "Abdul wane business kaga ya dace abba yayi wanda at least kullum zai lissafa shima" Dariya sukayi "bros abdul kasan me? Guy din nan asalin bahaushe ne wallahi idan yayi maka wani hausan sam bazakace shine ba" "Ya hada hausan kafacen yazo ya hada dana zazzau" yanzu harda na azare ya dauka ai" Mere baki yayi "kanku akeji" Pls abdul gayamin inji mana "Nawane kudin da zaka bashi? Naga kaga ya dace? Ni inaga kamata yayi ka bashi kudin kawai ya nemi wanda yaga zai iya yafi "Idan kuma ya kashe kudin fa? Dariya jalal yasa "mubarak dan Allah me ka maida abbane? Taya zai kashe kudin zancen abdul shine daidai gaskiya Amma nawane zaka bashi? "2 million" ido mubarak ya zare "Kai wallahi kayi hauka, Allah zaka wayi gari wannan motar bakada kudin da zaka sanya mata fuel" Murmushi yayi "Allah ne zai bani ba kai ba ka gane ko? Ya bude motan kawai ya fice Gaida abban sukayi jalal ya kira maryam yana murmushi "mamina bakya zuwa school ne? Kai ta gyada mishi "meyasa? Ba school fees ne" murmushi yayi toh ki shirya gobe sai kije school kinji? Kai ta gyada tana murmushi Mustapha ne ya shigo yana kuka jalal ya kirashi "abbana meya sameka? Adda bilkisu ce ta dakeni" Cike da girmamawa ta gaidasu "adda bilkisu meyasa kika dakeshi? Yana neman magane kuma na gaya mishi ba kyau yaje islamiya firdausi da farid sun tafi amma shi sai neman magana yake a unguwa" Murmushi jalal yayi "zaka bini muje zaria? Eh zan huta da wannan maryam din" murmushi jalal yayi Amm abba gobe sammako za muyi Mu koma saboda wurin aiki" ba damuwa jalal Allah ya kareku ya albarkaci rayuwarku Murmushi sukayi ga baki dayansu "Ya jalal zan bika fa" kai ya gyada mishi yana murmushi Abba ga wannan sai ka nemi abinyi dashi wannan kuma sai a maidasu school umma wannan kenan kiyi sanaa kada ki zauna a ahaka" godiya suka shigayi jalal kam tashi yayi ya fice yabar su mubarak Ciki abban ya shiga ya fito da wani jaka ya bawa mubarak "idan kaje saika diba ka gani kai ya gayda "abba Mu zamu tafi" Da kawu mustaphan zaku tafi? Kai ya gyada Sai faman murna yake yayi sauri yayi wanka ya sanja kaya suka fice Zaune suke a dakin da jalal yake mustapha har yayi bacci mubarak ya bude jakan ya fara dibawa Kallon jalal yayi yaga hankalinshi baya kanshi yayi murmushi ya qara fito da wani pic aiko ya shiga dariya "Cool jalal pay and see something" murmushi yayi ba tare da ya kalleshi ba Pic din abbanshi ne yana yaro ya tara suma a kanshi sosai ya tsaya jikin wani mota Duka jalal yakai mishi ya goce yana dariya "bros abdul kaga wani wanka da abba yasha? Ga baki dayansu dariya suka shigayi Pics ne masu yawa harda na Auden mamin mubarak "cool amaryar nan fa ta hade" dukanshi suka shigayi yana ihu "Zasu kasheni dan kawai banida twins brother" dariya suka shiga yi "Zaka qara dariyan mami? Allah na tuba bazan qara ba" Cool jalal kaifa mugune wallahi ya fada yana qoqarin tashi Da qarfi suka maidashi ya kwanta "cool jalal kaifa magajin sarki ne" wani bata rai jalal yayi "Allah za muyi fadan da bazamu shirya ba Idan ka qara kirana da wannan sunan" ya dakeshi yaje ya kwanta Dariya suka shigayi "ai duk wanda aka hada Allah beyi ba qarshe da fushi zai qare" dukanku sai kun gaji sarkin Yana gama fada ya fita da sauri yana dariya Kai cool AJ ya girgiza yabi bayanshi Washe gari sukayi sammako suka dauki hanya zuwa garin sarki mahmud Cike da gajiya jalal ya qarasa dasu gidan mubarak "dan Allah kada nace sai gone zaka fito ka sameni anjima" Kai ya gyada suka fice Part din Ummi ya ajiye Mustapha ya fice ba tare da yaga jalilah ba Kaya ya sayawa ya saya mishi ya bawa Ummi ya fice zuwa part dinshi Tsalle jalilah tayi tayi hugging dinshi Ajiyan zuciya ya suke ya qara hugging dinta tana dariya "Ya jalal hamma kasha gajiya gaskiya" murmushi yayi mata idanunshi suna a rufe kissing din lips dinshi tayi ya bude idanunshi da sauri lokaci daya sukayi dariya ya bata suka nufi daki *9:30pm* cool AJ da mubarak suka shigo parlour'n jalal yana kwance sukayi sallama ya amsa musu daga kwancen "Cool jalal duk gajiya ne haka? Murmushi yayi ya tashi yaje sanja kaya suka nufi gidan main mubarak Kallo daya tayiwa Mustapha tasan dan uwan mubarak din ne "Jalal wannan waye? "Sunana Mustapha" murmushi jalal yayi Kallonshi mami tayi da alaman tambaya "Abba name lokacin da aka haifeni yayi mafalkin abba Mustapha shine ya sanyamin sunanshi hamma dan rashin kirki irin da Maryam bata kirana da uncle mustapha" Dariya jalal yayi dan haka yake ganinshi kamar mubarak din "Jalal da gaske yake? Kai ya gyada mata Murmushi tayi anan mubarak ya shiga gaya mata abinda jalal din yayi "Jalal meyasa ka kashe kudinka haka? Mami air ba kashewa nayi ba na basu ne saboda su zauna lafia" dariya cool AJ yayi jalal ya aika mishi da harara "Allah yayi albarka ai ko albarkacin abban mubarak zaa iya taimaka musu,,,, jalal hamma wannan anan zai zauna ko? Sosa kanshi yayi "mami na Riga na bawa ummi" jalal ni kadai fa nake zaune a gidanan Mami zan baki aisam da khaleefa Idan suka qara girma Aa banaso dan a gidan nan mubarak zai tare Murmushi yayi suka dan taba fira sukayi mata sallama suka fice kowa yayi gabanshi jalal ya maidawa Ummi uncle qarami............. 🤴🤴JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 226-230 _Some years ago_ Sallama sukayi suka shigo aisam ne a gaba su khaleel na bayanshi "Abba sanu da gida" aisam daga ina haka? Abba mubarak mukayiwa rakiya shine mukazo gaidaka" murmushi yayi "Ummina fa? Taje batason ganin mummy jalilah"murmushi yayi Khaleefa wai school ne ya maidaka haka? Abba fada sukayi da junior" fada kuma? Abba shine yakemin rashin kunya kuma abba ya gaya mishi nine babba ya daina" Kai ka fiye zafine shiyasa,,, aisam dama nasan bazaka bani gaskiya ba amma ai lina ce shaida "Tsaki khaleel yayi "wai kai kenan komi lina ce shaida" khaleel na gayama Idan ka qara yimin tsaki zamu bata dakai Mubarak ne ya shigo shida aisha qaramar 'yar juwairiya sai kuma maryam lina wacce itace qaramar 'yar jalilah sai kuma mudassir asrim na qaramin jawahir "Wai fadan ne bazai qareba? Abba mun daina "ai bazan qara fita daku ba" Abba laifin ya khaleefa ne shi yake mishi rashin kunya "Na tambayeki? Abba wai meyasa kafison ya khaleefa ne akan ya aisam? Dariya jalal yayi "Lina su mufida da mufid fa? Dariya tayi "ummin abban jalal tace a wurinta zasu zauna yau Rana daya jalilah da juwairiya suka haihu aka sanya musu mufida da mufid jalilace keda mufid Daqyar mubarak ya hada kansu ya sasu a gaba zai wuce dasu jalal har tausayin mubarak yakeji ga baki daya ya kwashe yaran ya maida wurinshi sai faman hidima dasu yake Zaune suke a gaban mai martaba ga baki daya ya tarasu yanason magana dasu "Nasan za kuyi mamakin wannan taron dana shirya toh ba komi bane inaso na shaida muku zanyi murabus ne sabida wasu dalilai Na farko lafiana na biyu kuma shekaruna sunja banaso na Gaza da mutanen da suke qarqashin mulkina dan hakan zan sauka na samu hutu nima Shuru ba wanda yayi magana "kaka toh ka bawa abba jalal mana sai ya zama sarki" cewar aisam Harara jalal ya aika mishi "Alhaji Mustapha ai abba jalal ba jinin sarauta bane" murmushi jalal yayi yana kallon cool AJ wanda bakine dauke yake da addua akan Allah yasa a bawa jalal sarautan "Haba yaya wane irin shi ba jinin sarauta bane" toh Maryam kinsan dai jalal akan dole yake zaune damu abdul jabbar ne zai gaji sarautar zazzau Dariya ce ta subucewa jalal da mubarak ganin yanda cool AJ ya hade face Murmushi mai martaba yayi "Wannan shine dalilina kuma abdul jabbar Kaine zaka gaji wannan karagar ni kuma zan dawo gida saidai abinda ya shige maka duhu acikin shanin masarautar zaka iya zuwa ka sameni "Abba da wane ilmin ne zanyi sarauta? Murmushi abban yayi ya tashi kawai ya fice Harara mamin abdul ta aikawa jalal Na angel ni zan dan fita da jalilah zatace gidan qawarta amirah "Dan Allah Idan kaga uncle qarami ka turashi ya karbo saqon" kai ya gyada mishi ya fice Ba wanda ya qarajin voice din cool AJ ya tashi kawai ya fice mubarak ya shiga dariya "Mubarak Allah zamu bata" mami na

Chapter 12 of 13