Reading MAR ADAMS BOOK 3 BY AYSHA BAGUDU Chapter 8 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

bace ."to Allah ya kyauta amman babu dadi a dinga kiran mutun ayi shiru ni yanzu ma yanke shawarar bazan sake daukar kiran layin ba koma Kiyi min blooking din layin na huta inji cewar ummah "uhm umma ki barshi kawai idan mai shi ya gaji ya daina kiranki tana rufe baki wani kiran ya sake shigowa wayar maryama  the same number daaka kirata ,da kamar bazata dauka ba sai kuma tayi tunanin ta dauka idan baa yi magana ba ta kashe wayar gabad'aya dan haka ta dauka tare da sallama sannan tace hello wai wake magana ne ?"


A zafafe yace "zakice baki gane mai magana ba ?"ni  gsky ban gane mai magana ba hassalima ban san number ba bare muryar mai magana "okay kina magana da mr ata "what !? ta fad'a tare da zaro ido waje jikinta na d'aukar rawa  daga haka bata sake cewa komai ba ta katse kiran jikinta na wani irin rawa "tabbas muryarsa ne" shikenan na rasa aikina inna lillahi wa inna ilaihi rajiun  umma ta matso kusa daita ta zauna akan hannun kujerar da take zaune  tana tambayarta "wani aikin zaki rasa ?cikin kuka ta girgiza mata kai tana saka hannu ta rufe bakinta saboda wani kukan da yake sake kufce mata.


"Ashe  maryama  akwai damuwar da zaki kasa fad'a min ?tayi shiru tana kuka kafin ahankali taji shigowar sako wayarta nan jikinta ya sake daukar rawa ta sake tabbatarwa kanta sakon dakatarwa ce "shikenan na rasa aikina ".shine kawai abinda ta dinga  maimatawa a fili cikin kankanin sakanni idanunta suka kada suka koma jazur ta dinga fidda huci " wani bala'in tausayin maryama din ya mamaye umma , "me kikayi  har aka dakatar dake aiki ?shiru maryama ba magana sai kuka "ni daman tun da kika dawo na fahimci kina tattare da damuwa amman kikace babu komai kinfi son kiyita boye  damuwa a zuciyarki tana cutar dake kina tunanin  boye damuwar shi zai miki maganin halin da kike cikine?"



cikin  murayar kuka ta shiga fad'awa umma abinda ya faru shiru umma tayi tana sauraronta har ta dasa aya umma  tace "maryama baki kyuata ba ya dace kisan yadda zaki masa magana duk da nasan kureki yayi ."wallahi umma kureni yayi sam mr ata bai da mutunci ni bansan sanda yana fad'a ina fad'a ba "amamn tunda a qarqashin ikonsa kike dole sai kinbi dokarsa sannan zaki zauna lafiya nan dai umma tayi mata fada sosai tare da kwantar mata da hankali dan bata son tana  yawan shiga damuwa da tunani saboda ba wai ta gama dawowa normal bane  da kyar ta  samu maryama tayi shiru ta share hawayenta  tace ta bata wayar ta duba taga sakon daaka turo  mata."


"A'a umma karki bude kawai ni nasan babu abinda zai saka mr ata kirana adaidai wannan lokacin ko ganin sakon madam some sai dan dakatar dani "ni umma miko min charbinki kawai na fara ja  ko
tunani  da damuwa zasu barni  ta qarasa mgnr tana sake furta kalmar "Inna lillahi wa inna ilaihir raji un, tana hadawa da salatin Annabi da istigifar "maryama ki natsu  in sha allahu ba abinda kike tunani bane Allah yana sane dake kuma zai kawo miki dauki bani wayar na duba jiki a sanyaye ta mikawa umma wayar  ta amsa ta shiga inbox dinta  umma ta fara karanta sokon a fili  "ki tabbatar da kin zo da aikin da muka baki Gobe karfe tara daidai wani irin juyowa maryama tayi ta fuskanci umma hawaye na bin kuncinta ."



Kallon kallo suka shiga yiwa juna "kingani ba duk da abinda kikayi masa amman har yanzu suna bukatarki a ma'aikatan su lumshe seyx eyes dinta tayi tana godewa allah da ba dakatar daita sukayi ba sako na farko umma ta karanta "ki dauki kiran mr ata magana ce akan desing's din daaka baki aiki shine sakon some dayafi komai daga mata hankali naunayen ajiyar zuciya ta sauke " yanzu sai ki tashi kije ki fara abinda ake bukata daga gareki "wallahi ni yanzu duk jikina a sanyayye yake akan aikin baa wa mr ata gwaninta komai kayi baka iya ba komai bai masa ba wallahi umma bansan ta ina zan fara ba ."


" haka zaki karfafa zuciyarki ki tashi kije ki fara sosai umma ta dinga karfafa mata gwiwa har  ta samu natsuwa da jin zata iya masa fiyye da abinda yake bukata daga gareta ."ahankali ta mike ta shiga dakinta taja kujera ta zauan ta fito da kayan aikinta d'auki farar takardar data fara zanen tana duba zanen da yace bai masa ba zanen yayi kyau sosai tana cikin tunanin yadda zata kawo wani sauyi akan zanen ya sake  kiranta  jiki a sanyaye ta d'aga cike da sanyi muryar tace " barka da dare sir ?you are very stupid dake da  gaisuwarki".shiru tayi hankalinta na sake tashi "ni zaki katsewa kira ?muryata nã rawa ta soma bashi hakuri ai kuwa hakan ya bawa mr ata damar zuba  mata ruwan matseefa."


Aiko  hanakalinta yay mugun mugun   tashi gabanta ya dinga  dukan tara tara cike da jin tashin hankali tace "nifa sir bana son fad'a kabi komai ahankali tunda kace tara ka bari taran gobe tayi mana idan banyi abinda kake bukata ba sai ka dauki mataki akai ".daga can inda yake zaune ya gyara zama tare da motsa bakinsa da niyyar sake mata wani sabon rashin mutunci  tunin maryama  ta kashe wayarta gabad'aya ta zuba tagumi da hannuwanta duka  tana mai runtse idanunta wayar ya cire a kunnensa yaga dip alamun ta kashe ya sake kira yaji swichoff
Tsaki yaja yasan zata rina ga rashin kunya ga tsoro wanda shine abinda yafi bukata tagani atattare daita
Ata nã zaune  yana tunanin had'uwarsu da maryama Gobe kamar ance ya d'ago kwayar idashin kawai yaga fitowar mutun daga kitchen ."


Tsumammun idanunshi ya ware akanta maryam ce da  ritsetsen cikinta da  yayi  girma sosai tana d'aga kafafuwanta da kyar yayi mugun tsura mata ido yana    kallota  nan take  yaji qirjinsa na wani irin  bugawa da qarfi  "duk da  cikin jikinta yayi girma sosai sai dai cikin bai  sa  tayi wata kiba ba sai uban fari data qara da gajarcewa yayinda hannunta ke rike da plet wanda bai san ko meye aciki ba ,ahankali ta cigaba da tafiya da kyar irin tafiyar masu ciki ta samu waje opposite dinsa ta zauna  tana danne damuwarta dan ita kad'ai tasan irin damuwar da zuciyarta take ciki akanshi ,dan ta  dauka kiyayyar da yake mata zata tsaya ne a iya kanta a she har da cikin jikinta kiyayyar  zata shafa ta sunkuyar da kanta kasa tana danne hawayen daya cika kwarnin idanunta ta soma cin d'anwake  wanda shi har lokacin bai san ko meye acikin plet din ba  sakamakon tazarar dake tsakaninsu tsumammun idanunshi kawai ya zuba mata yana kallonta da cikin jikinta ."


Mmn sudais
[8/31, 11:24 AM] Safwan Libiya 2: 💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

BOOK 3

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan  littafin  na kudi ne mai bukatar karantashi   byn na kammalashi zai  biya 1000 ta wannan  account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura  domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina  (Hausa bakwai ) a YouTube.


Page 9

Yadda mr ata ya tsurawa maryam kwayar idanunshi yana kallonta zaka d’auka zuciyarsa ta d’an saduda ne akanta ,sai dai azahirin gaskiya ba haka bane kawai tsabar mamaki ne cunkushe a zuciyarsa” wai d’ansa ko ‘yarsa ne kwance acikin matar da yake jin duk duniya bashi da abinda ya tsana sama daita tunda ta bar rayuwarsa ya d’an samu natsuwa da kwanciyar Allah a yanzu idan yace yaji dadin ganin fuskarta yayiwa Allah karya haka zalika ganin girman cikinta bai saka zuciyarsa jin komai aransa ba ko jin digon tausayinta ba sai ma jin haushi da bakinciki ganinta ne ke nunkuwa a kasan zuciyarsa yayinda zuciyarsa ke zafi da suya.” dogon tsaki yaja wanda yasa maryam tabar cin abinci da take ta d’ago kanta ta zuba masa ido dan ko bai fad’a ba tasan saboda ita yaja tsaki .”shiru tayi kawai tana faman sauke ajiyar zuciya .”fuskarshi babu walwala ya sauke kwayar idanunshi akanta alokacin da kiran gaggawa ya shigo wayarsa ya kai dubansa ga wayar ,d’aya daga cikin abokan kasuwan cinsa ne daga haka ya mike tsaye, a natse ya nufi hanyar fita waje dan gara tun wuri ya qara gaba kafin sweet heart tazo masa da batun yarinyar dan yasan dole zata masa maganarta wanda shi kuma abinda yafi tsana kenan .”


Mikewarsa ya daidai da sake jefa zuciyar maryam cikin gagarumin tashin hankali juyawa tayi tabi bayansa da ido tana kallon yadda yake d’aga qafafunsa tamkar baya son taka qasa .” kallo d’aya zaka mata ka tabbatar da cewar bata cikin natsuwa da walwala da kwanciyar hankalinta dan tunda ta sauka hankalinta da natsuwar da kwayar idanunta babu abinda suke da muradin gani tamkarsa so take taga yadda reactions dinsa zai yi idan ya ganta d’auke da cikinsa ,sai dai kash a ganin farko yayi buris daita da cikin jikinta tamkar bai gansu ba ,ita kuwa burinta ta ganshi hakazalika babynsu taji dumin jikin mahaifinta duk da tasan abu ne mai matukar wahala ya basu wannan damar .” bata san tsananin qaunar da take masa ya zarta dukkanin tunaninta ba sai data d’aura kwayar idanunta akanshi yanzu .


“ tunda taganshi taji komai ya dawo mata sabo ji tayi tamkar ada can bata ta’ba són shi ba a yanzu ne take son shi . numfashinta ya shiga sauka da sauri sauri sai ga hawaye sharr sun shiga turereniyar zubowa daga cikin kwarnin idanunta saboda rashin kulawar daya nuna mata ita da cikinsa ,gabad’aya taji gwaiwarta tayi sanyi wanda hakan ya sake tabbatar mata babu abinda zai canzasa daga ra’aayinsa ita da babynsa baza su ta’ba samun kulawa da soyayyarsa ba “me yasa bazata ciresa aranta ba tunda har qiyayyar ta kai haka ?”me yasa take son shi haka ?meye laifinta dan taso shi fiyye da komai a duniya ?”babban tashin hankalinta yanzu cikin jikinta wanda likitanta ya tabbatar mata bazata iya haifa da kanta ba ,yanzu shikenan idan ta rasa ranta wajen haifa masa baby bashi da asara babyn ce kawai zatayi rashin mahaifiya ya kamata maryama ki qarfafa zuciyarki ,ki manta dashi ki rayu ko dan abinda yake cikinki domin Ita kad’ai ce gantaki itace zata zama abokiyar adawa ga rayuwar adamcy”


ko cikakken mintuna goma mr ata bai yi da fita ba sai ga mami ta fito da sauri ta qaraso inda take zaune tana kallon kofar fita had’e da kiran sunanta “maryam lafiya ?”meke damunki?”ta fad’a tare da zama kusa daita ta riko tafin hannunta cikin nata .”hawaye kawai take zubarwa saboda tasan me zai iya faruwa idan mami taji damuwarta ita kad’ai tasan yadda take jin cikin jikinta baqaramin tokare mata qirji da mara yayi ba “kiyi min magana maryam meke damunki ?still shiru tayi ta kasa cewa komai sai sheshekan kuka take “kun had’u da adamcy ne ?”ahankali ta gyad’a mata kai alamun “eh! “wani abu yayi miki ne kike kuka ?ta girgiza mata kai alamun babu “to kukan me kikeyi haka ?”still kai ta girgiza mata bugun zuciyarta na qaruwa .”


shiru mami tayi tana rike da hannunta tana nazarinta “ki dinga tausayawa kanki maryam ,ki duba halin da kike ciki komai zai iya faruwa dake “ina tausayawa kaina mami bansan me yasa na kasa cire damuwar nan araina ba.” ta fad’a jikinta na d’aukar rawa “dan allah maryam ki ciresa gabad’aya aranki saboda muna tsananin bukatarki da abinda ke cikinki a raye “mami yaya baya sona baya son cikin da nake d’auke dashi na d’auka zai d’an sauko ko dan cikin jikina “shine ya fad’a miki haka ko kuwa hasashenki ne ya fad’a miki haka ?cike da sheshekan kuka tace “mami yanayinsa ne ya nuna min haka “ki rabu dashi ke dai kiyi fatan ki rabu da cikin lafiya “ta kalli mami ido cikin ido tace “mami ina ji ajikina mutuwa zanyi “gaban mami yayi wata irin fad’uwa tana sake damke hannunta cikin nata tace “in sha allahu mryam bazaki mutu yanzu ba kima cire wannan zance aranki nasiha da kwantar da hankali mami tayita mata tana karfafa mata gwiwa har taji zuciyarta ta d’an yi sanyi .”


Cike da natsuwa mr ata ya dawo parlour’n yana cincin magani har lokacin maryam na zaune tare da mami inda mami ta tsiyaya mata sobo a cup ta mika mata ko kallon inda suke bai yi ba kai tsaye hanyar step ya nufa har yayi taku uku ya jiyo sautin muryar mami ta doke dodon kunnensa “adamcy !”cak yaja ya tsaya batare daya juyo ba, kusan second biyar yana tsaye har sai daya sake jiyo murya mami “kana jina fa ka wani tsaya ni zanzo na sameka ko me kake nufi ?”ahankali ya juyo ya zuba hannuwansa duka cikin aljihunsa ya soma takowa zuwa inda suke batare daya kalli inda mrym take zaune tana dubansa ba “ka samu waje ka zauna .”ta nuna masa opposite din kujerar da take zaune babu mutsu ya zauna yana duban yatsun hannunsa “.


Parlour’n ya d’auki shiru baka jin motsin komai sai na tv da ac dake aiki acikinsa sai kuma saukar numfashin mrym dake fita da karfi tana kallonsa tana jin tsantsar soyayyarsa na sake hud’a zuciyarta bayan soyayyarsa da take ji har da tsananin shaawarsa kamar taje ta kwanta ajikinsa ta rungumesa tsam tsam ajikinta “adamcy baka ga maryam bane ?”uhm na ganta sweetheart !amman shine kayi uwar watsi daita ?“to me zanyi mata sweetheart ?”ni kake tmby me zaka mata ?”kai bakasan abinda zaka mata ba ?”mace na d’auke da cikinka tsawon wattani yau lafiya gobe babu amman ka ganta kayi kamar baka ganta ba ko bazaka ce mata komai ba ai ko dan cikinka dake jikinta ka …”no sweetheart ! yayi saurin katse mami cikin ‘bacin rai “ sai daya furzar da numfashi mai zafi kana ya cigaba da magana cikin zafin rai “ba cikina take dauke dashi ba sai dai cikinta “ya fad’a yana tsaida kallonsa ga maryam din “.


maganarsa ta daki kunnuwan mrym sannan ta wuce har cikin zuciyarta wanda ya sake kunno mata damuwarta da take ta qoqarin dannewa acikin zuciyarta “bance ina son na haihu daita ba shiyasa bana bukatar wani ciki daga gareta wannan cikin ba nawa bane nãta ne har abada kar wanda ya sake dangantani da cikinta “sharrrr…”sai ga wasu hawaye masu zafi sun zubo mata akan kuncinta ahankali ta fara rera kuka mai ban tausayi fuskarshi ya daure sosai “ban san ma me yasa ta kwaso jiki tazo ba “kana hauka ne ?to wallahi bari kaji baka isa ka hana mrym zuwa inda muke ba dole mrym ta shigo cikin gidan nan “well tazo wannan ba damuwata bace da zuwanta da rashinsa duk d’aya ne a wajena maganganu marasa dadi ya dinga fad’awa mrym mami dai a qarshe tayi hakuri ta danne zuciyarta tasa masa ido batare data qara cewa komai ba amman adame take sosai game da lamarin adamcy mutun Kmr sheid’an bai da yafiya kuma abu baya wucewa a wajensa .”


mrym ta sake kallonsa taga har lokacin ita yake kallo yana sake murtuke fuskasa byn ya gama ya mike ya nufi hanyar step yana cewa “sweetheart sai da safe .”
Mami tayi masa banza tana qoqarin gogewa maryam hawaye . sauka maryam tayi daga kan kujerar da take zaune zata zauna kasa kan tayis mami tayi saurin rikota”a’a maryam muje d’akina taja hannunta suka nufi d’akinta tana rarrashinta ahankali mami ta zaunar daita akan gado tana shafa bayanta tana mata sannu amman ita bata wannan take ba kukan tausayin kanta kawai take da abinda Ke cikinta mami ta janyo pillow tasa mata abayanta tana sake rarrashinta sai data ga sautin kukanta ya ragu sannan ta fice daga d’akin zuwa na ata byn fitar mami maryam tayi kuka sosai tmkr ranta zai bar gangar jikinta .”


Tana zauna shiru tana kallon saman d’akin kukan abinda ata yayi mata a yanzu ne ko kuma na tashin hankali da zata shiga anan gaba ne idan ta haihu take yi batasani ba ?tayi bitar maganganun ata tana son tayi placing dinsa a scale daidai da rashin daidai a iya fahimtarta tun suna yara tasan yana da mugun kafiya da muguwar zuciya sune ma manya flaws dinsa kuma har yanzu da girma yake zuwan masa bai rage komai ba .”tasan tunda yace bai son cikin tasan komai zaayi ko sama da kasa zasu had’e bazai qaunaci cikin ba .ita kuwa me tayiwa rayuwarta haka?“ta cutar da kanta da abinda Ke cikinta da tasan zata kasance a cikin wannan tsaka mai wuya din data hakura bata kusamcesa ba ”


Bangaren ata kuwa yana zaune a d’akinsa ya natsu acikin kogin revenge ,yadda har yana qoqarin yayi lossing kansa “bazan ta’ba karbar cikin jikinki ba wannan shine hukuncin da zan miki ta yadda a gaba idan an sake halittoki a duniya bazaki sake reaping din wani ba .”da sauri ya kalli kofar shigowa mami ce ta shigo ranta a matukar’bace ganin itace ya sauke naunayen ajiyar zuciya yana ciza gefen lips dinsa ta nunasa da babban d’an yatsanta “adamcy ka kashe ka huta gbdy tunda kafin bukatar haka “ ya d’ago idanunshi ya kalleta kawai “eh gara ka kasheni kafin naga mutuwar mrym “to ni sweetheart meye laifina ne ?duk abinda nayi akan gskyta nake yarinyar nan nace banso kin matsa na hakura na rungumeta as ending tayi raping dina har yau ina kan shan magani sanadiyyar pills din datayi min amfani dashi” bayan shi dumu dumu na kamata da tukunyar tsafi yau datayi nasara akaina me zaki ce ?mami tayi shiru tana dubansa “ tabbas ya fita gsky .”dan ita kanta taji ciwon abun bare shi to amman yane zatayi maryam dolenta ce bata da yadda zatayi daita .”?



Zazzafan numfashi ya fesar “taya zan iya yafe mata sweetheart bare naso abinda tayi ta’adanci wajen samunsa ?”wallahi sweetheart matukar na riga wannan yarinyar mutuwa bazan yafe mata ba ,gara ma kiyi mata fatan mutuwa watakilla zan iya yafe mata idan bata duniya.” jikin mami yayi mugu mugun sanyi “hankalinta yayi matukar tashi cike da tashin hankali ta cigaba da mgn “babu wanda ya wuce qaddara adamcy wannan alamarin yana cikin qaddaearku .sannan kowani dan adam mai laifi ne “haba sweetheart me yasa wasu lokutan kike kin gsky ne ?wannan qaddara ne ko tsabar iskanci ko son rai ?”qaddara ne adamcy “no no!! sweetheart iskanci ne kawai “ta matso kusa dashi ta zauna tare da kamo hannunsa cikin nashi “munji munyi laifi ka zama mai yafiya domin Allah da kanshi yana son bayinsa masu hakuri ni kuma ina son adamcy nah ya kasance acikin jerin mutane da allah yake so dan Allah ka yafe mata kodan halin da take ciki .”


numfashi ya sauke sannan yace naji zanyi tunani akai daga hk bai sake cewa komai ba ya runtse idanunshi .”na kawo maka abincin nan ne ?”anya sweetheart abincin nan zai samu shiga ? bari naje na kawo maka ko kad’an kaci bai ce mata uhm ba bare uhm har ta fice byn wasu mintuna ta dawo d’akin daya daga cikin masu aikinta na biye daita mai aikin ta ajiye tray ta qara gaba yayinda mami ta zuba masa abinci sai da mami ta matsa masa sannan ya fara ci bawani abinci kirki yaci ba ya ture plet din gefe ahankali ya maida bayansa ya jingina da kujera da yake zaune akai tare da zamowa kad’an yana duban maminsa itama mami shi take kallo “ba dai har ka koshi ba adamcy ?”ya d’age mata girasa d’aya “ko na hado maka tea ne ?dakin ya dauki shiru har tsawon minti goma batare yayi ko tari ba sai da mami ta sake yin mgn yace mata baya bukata gajiya mami tayi da zaman ta fito ta koma dakinta ta cigaba da rarrashin mrym .”



Ranar kwana marym tayi batayi bacci tana juyi da tunanin matsayar rayuwarta yayinda maganganun mr ata yake barin kunnuwanta da zuciyarta su huta “bance ina son na haihu daita ba shiyasa bana bukatar wani ciki daga gareta wannan cikin ba nawa bane nãta ne har abada kar wanda ya sake dangantani da cikinta tayi wani irin juyi da karfi wanda yayi sanadiyyar da yar cikinta ta qara tokare mata qirjinta ta runtse idanunta gam .”haka ma mami bata runtsa ba da zarar taji motsinta zata mike ta tamvayeta ko akwai abinda take bukata ko akwai inda ke mata ciwo .”washegari tun da sassafe mr ata ya fice daga gidan ya wuce office wanda sai lokacin maryam ta samu damar runtsawa . bai jima da fita ba sai ga yaran mami gbdy tare da nana hauwa’u sun taho daita gida daga hospital kai tsaye d’akinsu aka wuce daita wanda ya sha gyara sannan suka dawo parlour’n mami inda mami take sheida masu abinda adamcy ya fad’a mata akan mrym daren jiya “kalmarsa sunyi tsauri dayawa akan mrym yace “bazai yafe mata ba nasani mrym tayi kuskure amman yayi hakuri mana haka .”


“A halin yanzu zuciyata zafi take min banason na mutu na bar baya da kura na rasa yadda zanyi da adamcy hayaniyarsu da koke kokensu yasa mrym farkawa daga baccinta ta yunkura da kyar ta mike ta zauna tana murza idanunta sannan ta zura silipa ta fito nan ta iske mami tana kuka ita da yaranta wad’an da suka had’a kai suna nasu kukan daga can gefe ta hango wacce batayi tunanin ganinta ba wato nana hauwa’u dan a tunaninta gidanta zaa wuce daita , itama kuka take sosai rungume da babynta ta qaraso wajensu tana qare masu kallo d’aya bayan daya bayan ta gama jin duk tautaunawarsu sannan ta kira sunansu daya byn daya da sauri suka d’ago suka zuba mata ido.” murmushi ta sakar masu tana mai cewa “mai yasa kuke kuka ?atare suka mike suka kamota suka zaunar daita a tsakiyarsu “.


“muna kukan abinda adamcy yayi miki ne ta sunkuyar da kanta kasa tana lissafin fingers dinta “karki daga hankalinki mrym mu muna qaunarki kuma muna qaunar abinda zaki haifa mana ta sakar masu murmushin karfin hali wanda kana ganin kasan na dole ne dan tayi dan ta kwantar masu da hankali “me zaki haifa mrym mace ko nmj ?duk scan din da nayi mace yake nunawa“ masha Allah zaa haifa mana beautiful “ta tsura masu ido kawai suma duk ita suke kallo cike da kulawa “me zaa kawo miki kici ,tayi shiru tana tunani kafin ahankali tace na gode sosai yan’uwana , kunata qoqarin kuga kun fitar dani cikin damuwar da nake ciki,dole ne mrym damuwarki itace damuwarmu.”


ta sake numfasawa ta kai hannunta ta kamo hannuwansu gbdy ta d’aura akan cinyarta “duk naji tautauwarku ina neman taimakonku ,nasan nayiwa yaya laifuka masu girma tabbass na cancanci ya d’auki kowani irin mataki akaina ,na d’auki laifina “. “karki damu komai ya wuce in sha allahu zamuyi convincing din adamcy ya yafe miki “murmushi tayi tace “ko amafarki bazai yi ba mutumin da yake son ganin bayana ta yaya kuke expecting zai yafe min ?sukai shiru dan su kansu basusan ta inda zasu bullo masa ba amman zasuyi iyakar qoqarinsu ya yafe mata “ki kwantar da hankalinki zamu masa mgn kuma zai yafe miki ,da kuwa naji dadi sosai bugu da qari kuma ya maidake gidansa ku cigaba da rayuwa mrym tayi murmushi “kai da dai kun barmu haka kowa yayi rayuwarsa idan na haihu lafiya nayi aurena, shima yayi nashi ai kuwa zamu taru mu rusa

Please Login or Register in order to submit comment