Reading MAR ADAMS BOOK 3 BY AYSHA BAGUDU Chapter 29 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

“ba ita bace kuma babu wani kamar da sukai .”




Nana hauwa’u ta sauke numfashi tana dubansa a tsanake kafin ahankali tace “to yaushe ne zaka sake kawo mana mu gaisa ina son na sake ganinta ".
A fusace ya d'ago tare da galla mata wata uwar harara yace. get out tun kafin inxo in tattakaki anan wajen nak'i in kawota d'in munafukar banza kawai ni zaki kawo salon munafurci ?”yaya …”shhiiii maza ka gabanki na sake jin ki sake min maganarta wata yarinyar sai kinga yadda zanyi dake nonsense kawai
Tashi tayi ta shuri takalmanta tana qoqarin barin parlon mami ta fito tana cewa “lafiya ku dana barku lafiya me kuma ya kawo batun nonsense?”nana hauwa’u bata tsaya ba ta wuce tana k'unk'uniaiko ya qara mata da "Very stupid". Yace yana rakata da harara, dan bayason abinda zai taso da maganar maryama a gidan yanzu sai ya gama komai da kanshi zai fito da maganar mami dake tsaye tana jinsa ta ajiye plet din hannunta tare da zare glass d'in idanunta.kallonshi tayi ta b'ata rai tare da fad'in.
  "Wai adamcy sai yaushe zaka can zane?, uhm yaran nan fa basu da wani d'an uwa daya wuceka idan basuyi hira dakai ba dawa zasuyi?kullum tsakaninka dasu hantara ne ko wulakanci to banason haka kaji na fad'a maka".



  "Toh sweetheart ". yace yana rufe computer tare da sauketa k'asa,"Kuma fa maganar nana hauwa’u nakan hanya ya kamata ka kawo mana ita yarinyar kamar yadda mukayi da kai mu gaisa ko".ya jiyo muryar mami na fad'a."Kai sweetheart wai dan Allah ya zaki biyewa shirmen yarinyar nan".idan na kawota kuce mata me ?”yarinyar nan babu komai tsakaninmu ku jira mana har na fara sonta ,”
Murmushi mami tayi tace “ ba wani shirme ya kamata ka kawota mu ita mu gaisa in ganta kafin tazo a matsayin matarka".  Kan dole ya amsa mata saboda bai son yin musu da ita.system d'inshi ya d'auka ya nufi side d'inshi yana tunanin ta inda zai kawo maryama gidansu yasan ma yana mata maganar kai tsaye zata fassara shi .”




    


Mmn sudais
[8/31, 11:25 AM] Safwan Libiya 2: 💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

BOOK 3

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan  littafin  na kudi ne mai bukatar karantashi   byn na kammalashi zai  biya 1000 ta wannan  account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura  domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina  (Hausa bakwai ) a YouTube.


Page 34


Zaune hajiya rahma take a gefen katifarta hannunta rike da hotuna wanda a 'yan shekarun nan a duk sanda zata ke'bance kanta to wad'an nan hototunan sune abun kallo agareta, wani lokaci yasata zubar da hawaye ,wani lokacin kuma tayi murmushi tare da nadamar zartar da hukuncinta akanta ,tayi shiru cikin tsananin tunanin wacce ke cikin hotunan kamar yadda ta saba ,ta dade zaune tana kallon hotunan tana sake zurfafa tunaninta da nadamar abinda ta aikata kafin ahankali ta fara zance a fili "Allah sarki bilkisu baiwar Allah mai tsananin hakuri da son mutane, mai tsananin kawaici ,Allah sarki diyata duk inda akaje sai anyi jimamin rashinki bilkisu mai tsananin son yan'u wanta har da ma wad'an da ba yan’uwanta ba ,bilkisu mai tausayi da amana ,nayi rashinki diyata Allah ka juyo min da hankalinta zuwa gareni.."nan kuka mai qarfi yaci karfinta "ai ko ta soma kuka sosai tana duban hotunanta "yau tsawon shekaru nawa kenan tana fama da abu d'aya?"kusan shekaru ashirin da wani abu kenan ,lokacin da abun yana sabo sabo bai dameta ba amman sai daga baya ta fahimci kusku renta,a kullum idan ta tuna sai ta tuna maganar hajiya safiyya aminiyarta,ta kance kiyi hakuri rahma ki rungumi qaddarar diyarki wata rana komai zai wuce .haka kullum take fad'a mata ,kuma baa wata shida bata kirata ba,tai ta rarrashinta tana bata baki amman duk tasa qafa ta shure maganarta .ta tuna shekaru goma da suka wuce mijinta alhaji rafi'u giwa tun yana jin zai iya hakura da lamarin bilkisu har yazo ya kasa yazo yana nuna a zahiri bazai iya rashin bilkisu ba ,har ma yace zai je ya nemi inda take amman tace masa a'a yayi hakuri ya d'aure yayi zamansa kar yaje zata dawo da qafafuwanta domin matsawar sukaje gareta tayi nasara akansu kuma taci bulus akan kuskurenta gara a barta idan ta sha wahala da kanta zata dawo ."



alokacin sai Allah yazo ya dora ma alhaji rafi'u giwa wani irin hakuri akan bilkisu ya cigaba tsabgoginsa da harkar kasuwancinsa da muamula da sauran ya'yansa ."sai gashi ita daga baya ta kasa hakuri tayi ta zuba ido yaushe ne bilkisunta zata zo ?"yaushe ne zata dawo garesu a tun shekarun goman nan gashi har an haura shekara ashirin bilkisu shiru tun tana ganin abun kamar film har sai da'aka d'auki wannan shekarun babu ita babu labarinta tasan cewar lallai bilkisu tayi fushi mai tsanani dasu kuma babu tabbas din zata dawo domin duk inda take a yanzu ta tsaya bisa qafafuwanta  kuka take sosai," wannan ciwon na rashin bilkisu ciwo ne da kullum yake cin zuciyarta wanda take jin bazai ta'ba warkewa ba har qarshen rayuwarta ,tunda zuciyarta tayi nisa daita ta rasa wani bangaren na rayuwarta ."tana zaune tana kuka yaya mahmud ya shigo d'akin bakinsa d'auke da sallama ,ganin halin da take ciki ya bita da wani irin kallo kafin ahankali ya qaraso gareta jikinsa na d'aukar rawa ya durkusa agabanta ya kamo hannun ta cikin nashi babu abinda ya tsana kamar ganin hawayen iyayensa balle mahaifiyarsa da bai da kamarta a duniya kukanta har cikin zuciyarsa yake ji "mum kiyi hakuri ki daina kuka nan ki fad'a min damuwarki kafin tace wani abu tuni hotunan bilkisu guda uku dake rike a hannunta suka zubo."



yabi hotunan da kallon mamaki yana jin wani iri acikin zuciyarsa dama gangar jikinsa nan take jikinsa yayi mugun sanyi domin kuwa ko bata fad'a masa damuwarta ba yasan kukan rashinta take yi nan take yaji da akwai yadda za'ayi ya dawo mata da bilkisunta da zai yi amman sun rigada sun ma kansu alqawari muddin ba itace ta dawo da qafafuwanta babu wanda zai taka zuwa gareta ,ya matso sosai kusa daita yasa kanshi akan cinyarta yana jin yadda zuciyarsa take ta fasa yana jin kamar sune silar kukan mahaifiyarsu ,yana jin duk laifinsu ne da suka taru suka had'a kai akan kin auren bilkisu ina ma sun sani sun amince a tun farko sun inganta rayuwar yaron da yanzu suna cikin walwala da farinciki  ." nan take shima hawaye suka fara gudu akan kuncin soja aka rasa mai rarrashin wani acikinsu ."yaya mahmud yayi amfani da qarfin zuciya irin tasu ta sojoji ya cigaba da bata hakuri da rarrashinta "kiyi hakuri nasan bamu yi miki adalci da muka biyewa son zuciyarmu akan rayuwar bilkisu ba ,munyi nadamar abinda muka aikata agareta , kuma a yanzu a shirye muke da muje gareta, zamu dawo da yaruwarmu cikinmu mu cigaba da rayuwa ,mu had'u gabad'aya mu dinga faranta miki ."



wani sanyin dadi ne ya ziyarci zuciyar hajiya rahma dan ta dade tana mafarkin zuwan wannan ranar ta dade tana rokon allah yasa ya'yanta su fahimceta sosai yaya mahmud ya gyara kanshi akan cinyarta "ina mai sake baki hakuri ki yafe mana ko zamu samu sausauci abinda muka aikata, bai kamata mu biye miki alokacin da kika d'auki zafi akan bilkisu ba ,kamata yayi mu zamanto masu rarrashinki da baki hakuri tare da nasiha ki rungume qaddarar bilkisu amman sai muka zama mune gaba  gaba gurin  nuna isa da iko  tare da jayayya da hukuncin ubangiji ,yau gashi bilkisu ta kar'bi qaddarata ta manta damu ta cigaba da rayuwarta cikin kaskanci batare data nemi mu ba bare ta nemi taimakonmu  wanda mu abinda muka kudurta kenan aranmu tasha wahalar rayuwa ta wulakanta ta tozarta tasan amfaninmu sannan ta dawo garemu mu kuma mu samu damar nuna mata kuskurenta na za'bar wani ta barmu sai gashi tayi hakuri kuma ta  jure duk wani tsanani  ta cigaba da rayuwarta ta bar zukatan mu da tarin kewarta ."



ahankali hajiya rahma ta kai hannu tana shafa kanshi tace "kukan ya isa haka mahmud ni baku min laifin komai ba hassalima hukuncin da kuka zartar da yardata da kuma amincewata ne na yafe maku duniya da lahira ,ni dai ka nemi sauran yanuwanka kuyi magana a tsakaninku ina son ganin bilkisu kafin mutuwata, wallahi mahmud nayi nadamar abinda nayi ma bilkisu ku kawo min ita kafin mutuwata duk da nasan mijin data aura bai cancanta daita ba amman na hakura tunda qaddararta kenan ya d'ago kanshi yana kallonta kafin ya saka kafin ahankali yasa hannunshi ya rike kunnuwansa "I promise you mum in sha allahu very soon zamu kawo miki bilkisu har cikin d'akin nan ya qarasa maganar yana sakar mata murmushi itama murmu shi tayi tana jin wani dadi sanyi at the same time tana tunani aranta daman tasan addua bata faduwa kasa banza Allah mai amsa addua, ta godewa Allah da yasa mahmud ne ya fara fahimtarta domin shine yafi kowa zafin zuciya da d'aukar zafi tunda har ya sauko tasan saukowar sauran ma bazai yi wahala ba ."




Alhaji rafi'u  yayi sallama ya shigo d'akin yana
kare musu kallo, yana ganin  farin cikin a kwance a fuskar kowanensu wanda ya jima bai gani ba haka nan shima with a smile yana godewa Allah daya
bashi family d'inshi da kuma ya had'a masa kansu guri d'aya. yace. "ahhh ana mommy and son time ne haka ?" nima bari nazo ayi dani, shikenan sai ya zama daddy mommy and son time." dukansu suka kwashe masa da dariya cikin farincikin da kwanciyan hankali hajiya rahma ta kasa hakurin rike maganar
bakinta ,ta tashi taje ta rike hannun alhaji rafi'u tana murmushin jin dadi  “dadynnmu albishirinka "dake wani lokacin haka take ce masa tamkar yadda yoroba kan kira mazajen aurensu " murmushi ya sake yi sannan yace "mumynmu goro "!ta kallesa tace kuma  dole sai an bani tuk'uici" tana magana tana dariya yace momynsu "an gama amaryata ran gidana ,dadybmu mahmud  yace very soon zai dawo  mana da bilkisu cikin gidan nan very soon zamu ga bilkisu da yan jikokinmu " yadda take murna kamar karaman yarinya, shima alhji rafi'u ya biye mata sunata dariya suna magana tare da murna yaya mahmud kuwa kamar kasa ta bud'e ya nutse a cikinta haka yakeji dan haka ya yunkura ya tashi da sauri ya bar musu dakin yayinda alhji rafi'u da hajiya rahma suka cigaba da tautaunawa kuma duk akan bilkisu ."



*****


Bayan kwanaki bakwai din da mr ata yasa aka turawa nadiya sakon an dauketa aiki tazo domin interview ranar da kwanakin ya cika ya dauki maryama zuwa kamfaninsa na ATA dake cikin ikeja wani office dabam  ya kai maryama  yace ta zauna shi kuma ya shiga office dinsa ya zauna  kusan awa uku da zuwansu inda ake ta faman yiwa sabbabin ma'aikata interview amman nadiya shiru  babu ita babu alamunta nan hankalinsa ya fara tashi ya mike tsaye ya fara zariya yana  kai kawo  daga office dinsa zuwa office din da  maryama  take amman ita sam bata ma lura dashi ba  ita kanta hankalinta naga babbar kofar shigowa ne yayinda pencil ne a bakinta tana cizawa tana tunanin nadiya akaro na karshe ne yana shigowa zuwa inda take ya fixge pencil din bakinta ta waigo  a natse  ta kallesa wanda shi daman  kwayar idanunshi na kanta shiru sukayi suna kallon juna kafin ahankali ta motsa lip's dinta "so.."karki ce min wani sorry !”yayi saurin katseta ta hanyar cewa haka yana furza mata hucin numfashin bakinsa kafin ahankali yaja qaramin tsaki ya cigaba da magana"me yasa zaki dinga over thinking haka ?".



Maryama ta sauke numfashi cikin tsananin damuwa sannan ta mike tsaye ta tsaya kusa dashi "har yanzu  ina mamakin nadiya da karfin halinta ne  sannan ina mamakin abinda yasa ta bawa wani numberta ya kira akan nazo aiki da wuri anya kuwa babu cutarwa acikin lamarinta "wannan kuma ya rage naki da hankalinki da tunaninki baki ta'ba ganin mutun ba koda a hira  shi wancan mataccen bai ta'ba  baki labarinta ba amman ki bari ta shigo muku gida kuma har ki kaita d'akinsa yanzu idan ya zamo ta ajiye wani mugun abu acikin d'akin fa ?ko kuma akwai abinda ta shirya maki akan hanyar ki ta zuwa aiki  yasa tasa aka kiraki kizo aiki da wuri ?duk hakan zai yuwu, ku duk wanda yazo maku da maganar masoyi sai kuyi saurin yarda dashi  saboda gaku yan gani kashenin soyayya ."ya fad'a yana fesar da iska”.



"bare ni akan ya sadam kam idanuna sun rufe kuma ina saurin yarda da duk wanda yazo  gareni da sunansa ko maganarsa ." tsaki yaja tare da yin shiru yana kallonta yana jin wani zafi aransa, ta kalli agogon hannunta "sir did you realize one thing ?" yana jinta kuma stil tsumammum idanunshi na kanta amman yayi mata banza "wallahi idan banga nadiya ba yau bazan ta'ba samun kwanciyar hankali ba  har qarahen rayuwata duk rayuwar da zan gudanar acikin kunci zanyita "numfashi ya sauke kana ya lumshe tsumammun idanunshi yace "ina tabbatar miki sai kinsan gskyar da take boye miki dan rashin kwanciyar hankalinki zai iya shafar aikina ."na gode sosai sir !” ta fad'a adaidai lokacin da wani ma'aikaci ya shigo ya mika masa cup cike da girmamawa ya amsa ya  kai cup din coffee bakinsa ".ya fara kurba ahankali ahankali.



Maryama ta dubesa a tsanake yana shan coffee yana lumlumshe idanunshi "bansa yadda zan misata maka farincikina ayau ba ina jin kamar ka bani komai dake cikin duniyar nan  ne ,na gode na gode sosai sir "maryama waya fad'a miki ina yin duk wannna abun saboda ke ne ?ta kallesa a matukar tsorace gabanta na wani irin  fad'uwa "yes ki daina kallona haka ni duk abinda nayi ina yi ne dan company dina  ne kamar yadda na fad'a miki yanzu banason wani abu ya samu aikina idan ban yi abinda zuciyarki zata damu natsuwa ba kasuwancina zaiyi rauni sakamakon ina son na had'a miki aiki biyu a qarqashina .”ya qarasa maganar yana sake lumshe mata ido .tsaki taja a kasan ranta "wannna anyi mugun miskilin mutun  mai shegen girman kan tsiya mai  fuska biyu kawai sai ya nuna kmr ya damu da mutun sai kuma ya dawo ya bullo da wani salo  ta fad'a a kasan ranta tana hura masa hanci ".



"me ki kace ?no..no..sir nothing “ki dawo da hankalinki jikinki wannan iskancin da kike babu abinda zai haddasa miki sai madness kizo ki rasa mai aurenki ,saboda  sosai na fahimceki  kina yawon magana da kanki , wallahi muddin baki daina ba zaki haukace irin haukan  da ko ankai ki  hospital kinfi karfinsu kinga kuwa bazasu amsheki ba ." yayi maganr tamkar bashi yayi ba yana cigaba da kurban coffee yana lumshe mata  tsumammun idanusnhi ."
"me yasa zaka min irin wannan fatan sir ?ba fatan haka nake  miki ba amman idan baki daina tunanin  abinda ya faru baya ba , sannan baki daina magana da kanki ba zaki tsinci kanki cikin yanayin dana fad'a whatever you want to say ,say it out loud". ya fad'a a matukar tsawace ."



Ranta a 'bace ta juya masa baya tana magana da kanta "aikin banza kawai  ko ina ruwan mutun dani ko.."again ? taji sautin muryarsa a bayanta "no sir zanyi magana a fili fili ."ya girgiza mata kai kawai ya koma ya zauna akan kujera yana juyi yana tunanin "taya zai aureta ma da wannan  dottin tunanin damuwarta ?”ai dole ya wanke mata kwakwaluwarta fes  kafin komai."maryama  ta cigaba da tunani tana cigaba da duba kofar shigowa ko zata hango bullowar nadiya amman shiru lokaci nata tafiya har karfe uku  ta wuce  amman shiru babu ita babu alamunta ya taso daga kan kujerar da yake ya tsaya kusa daita ya tura hannuwansa cikin aljihun wondonsa batare daya ce mata komai ba "ina tunanin nadiya bazata zo  yau ba  "why do you said that ?"Ka duba lokaci ka gani sir , har karfe uku ta wuce wani mutun ne  zai zo by this time akan aikinsa ?"kina ganin abu mai sauki ne mutun ya samu aiki a ATA company yaki zuwa?ni zuciyata ta tabbatar min da zata zo kuma nasan zata zo" allah yasa maryama ta fad'a muryarta a raunane ."



cikin haka wayarta ta d'auki ringing ta duba shima ya dan mika wuyansa yana duba screen din wayar  sunan umma ya gani dan haka  ya sauke numfashi ya juya ya koma cikin office dinsa "hello umma eh har yanzu ina office tukun akwai abinda muke yi ,aa karki damu in sha allahu zan dawo gida akan lokaci Eh komai yana tafiya daidai babu wata matsala sai na dawo tana gama wayar ta juya zuwa cikin office dinsa "sir !ya bar abinda yake ya  tattara hankalinsa akanta tun kafin tace wani abu ya soma motsa lip's dinsa "is almost four :30 pm now har yanzu bata zo ba abinda zaa yi kije office din hisham ki  jirani ."tayi shiru tana tunanin wani office kenan "office din  karshe kafin muzo nan "okay sir har ta juya ta sake juyowa ta fuskancesa "kana ganin nadiya zatazo yau kuwa gashi ina ganin lokaci na Kure min banason naje gida bakwai ta wuce sir na gode sosai ni ban ta'ba tunanin zaka bata lokacinka  akaina haka ba dan naji zuciyata ta yarda cewar dan i kayi haka ba dan wani kasuwancinka ba ,a halin yanzu babu wanda nake jin ya sake samun yarda da amincewa aciki zuciyata kamarka dan allah ka bari na cigaba da jin haka acikin zuciyata saboda naji dadin kulawarka sosai dan kana da kirki matuka , na gode maka sosai Allah ya jikan iyaye aransa yace “ameen! yayinda a zahiri "uhm!" ya fad'a yana tsareta da tsumammun idanunshi yana jin tamkar ya fixgota zuwa garesa .
Maryama ta  sauke naunayen ajiyar zuciya sannan ta juya ta fita daga cikin office din zuwa wanda yace ta shiga ta jirasa ,tafiyarta dake rikitashi yabi da kallo tare da yin tagumi yana bin every step of her nan take yaji jijiyarsa ta harba ."



Mmn sudais
[8/31, 11:25 AM] Safwan Libiya 2: 💗💗💗💗💗💗
   MAR'ADAMS
   💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

BOOK 3

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi  byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.


       Page 35




Ahankali mr ata ya kai hannunsa kan jijiyarsa dake harbawa still yana sake tsurawa tafiyar maryma ido har sai daya ga alamun ta tura kofar office din hisham ta shiga sannan ya runtse tsumammun idanunshi ,gabad'aya yanayinsa ya sauya ,wani irin ajiyar zuciya mr ata ya dinga saukewa da qarfi kana ya bud'e idanunshi yana jin wani irin yanayi a sansar jikina. yayinda gabad'aya tsigar jikinsa suka mike ."ji yayi kamar ya tashi yabi bayanta ya janyota tare da sanyata ajikinsa ya rungumeta tsam ya d'an tsotsi bakinta ko ya d'an samu sausauci abinda yake ji akanta."akaro na biyu ya sake kai hannunsa yana shafa jijiyarsa da take mike sambal ,yana shafawa yana lumshe tsumammun idanunshi at the same time yana sauke numfashi "wayyo allah ina cutar da kaina over akan yarinyar nan ahalin nasan irin matsanancin qaunar da nake mata "I love you so much maryama ,sonki da qaunarki sun mamayeni ina matukar shan wahala akanki yayi maganar fili ."wani wahalallen numfashi ya sake saukewa tare da gyara zamansa yana tura gabad'aya lip's dinsa na qasa cikin bakinsa tare da rikesu da hakorinsa."
Ahankali mr ata ya soma qoqarin kawar da abinda yake ji akan maryama dan yayi imani idan bai yi haka ba komai zai iya faruwa a tsakaninsu ya janyo laptop gabansa ya soma duba sakonin da'akayita turo masa ."



   maryama kuwa tana gama shiga office din hisham tabi office din da kallon tsanake komai tsaf tsaf gwanin burgewa ga wani qamshin turare mai sanyin dadi dake tashi acikin office din ,sosai office din ya had'u sai dai bai kai wanda mr ata yake zaune ciki ba .ta sauke numfashi da qarfi kana ta qarasa gaban makeken table din ta tsaya tare da rungume hannuwanta duka a qirjinta kafin ahankali ta maida shayayyun idanunta zuwa gefen makeken tabel din inda nan kwayar idanunta suka sauka akan wani qaramin madaidaicin fream mai azababben kyau tayi taku biyu tare da kai hannunta ta d'auki fream din tana dubawa, mace da nmj ne cikin shiga ta alfarma da wani kyakkywan baby, inda gabad'aya hannuwansu ke jikin baby sun bashi kyakkywan runguma ,sunyi kyau sosai kowannensu fuskarsa d'auke da murmushi wanda babu tantama na farin ciki ne .acikin kallon kurullar da takewa hoton ne ta gano irin tsananin kamar da matar dake cikin fream din tayi da mr ata ."tayi shiru kawai tana kallonsu gabanta na fad'uwa kafin ahankali ta ajiye fream din a inda ta dauka ta cigaba da tsayuwa tare da zance zuci"ya Allah kasa nadiya tazo"dan muddin ban yi mata tarin tambayoyin dake cunkushe da zuciyata ba bazan samu salama ba ,matsawar ban ganta ba kuwa zuciyarta zata qare ne acikin wasi wasi ."



mr ata cigaba da duba sakonin mutane ,bayan kamar mintuna talatin da barin maryamah office dinsa ya gama duba sakonin mutane tare da kashe laptop din gabansa ya rufe ya yunkura zai mike tsaye domin dai shima zuwa yanzu zuciyarsa ta aminta da nadia bazata zoba ,sai dai bai kai ga qarasa mikewa ba yaji ana knowking din kofa glass din office dinsa tare da neman izinin shigowa." a natse ya kai kallonsa ga kofar sannan ya koma a hankali ya zauna Inda tsumammun idanunshi na kallon glass din kofar shigowa ,nan take ya fahimce nadiya ce kuma daman yayi wannan tunanin duk da bashi da tabbaci kasancewarsa tare da maryama ne ya hanata zuwa ,sai dai ko wani dalili ne na dabam ."cike da jin isa ya motsa lip's dinsa ahankali yana cewa "coming!tare da yin juyi akan kujerar da yake zaune ta turo kofar ahankali ta shigo tare da maida kofar ta rufe ahankali ta tsaya batare data qaraso gabansa ba ."daga inda take tsaye ta soma magana cike da matsanancin fargaba "ammm so..."am so sorry sir nayi lattin zuwa sakamakon wani dalili na samu sakonku ta hanyar e-mail daga office dinku that's why I came "coming !"ya fad'a yana hade hannuwansa duka ya dafe ha'barsa yana qare mata kallon tsab ."



Jikinta a matukar sanyaye ta qaraso taja kujerar dake fuskantarsa baya kad'an ta zauna a hankali ,a natse ya d'auki d'aya daga cikin wayoyinsa dake ajiye akan table ,fuskarsa da zuciyarsa a dake ya soma neman number maryama yana manna wayar a kunnensa,ringin d'aya ta d'aga.yayi magana a can kasan makoshi sannan yayi disconnecting din kiran ya ajiye yace "ko kinzo da takardunki?yes sir! ta fad'a tana sauke numfashi "let me see!" ta mika masa wata jaka baka wanda takardunta ke ciki ,sai daya furzar da numfashi kana ya miko zafafan yatsun hannunsa farare sol ya kar'ba ya bude a natse ya fara duba takardunta yana cewa "kin tabbatar da komai na ciki ? yes sir komai na ciki ta fad'a tana faman kyalle kyalle acikin office  din yayinda shi kuma ya cigaba da duba takardunta daya byn daya yana satar kallonta ,gabadaya ba'a natse take ba dan kallo daya mai hankali zai mata ya fahimci bata da gaskiya "sir zuwa yaushe ne zan fara aiki ?"very soon zai iya kasancewa ma next week "ya fad'a yana mika mata takardun tasa hannunta ta kar'ba

Please Login or Register in order to submit comment