Reading MAR ADAMS BOOK 3 BY AYSHA BAGUDU Chapter 26 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

da sauri ya bar nadiya akarkashin table ."



Ganin da nadiya tayi mr ata ya zauna ta fito da sauri ta soma tafiya tana waigen bayanta yayinda maryama Ke tafiya tana magana da zuciyarta kamar yadda tasa ba , daf da nadiya zata fita daga cikin office din ita kuma maryama na qoqarin shiga office din suka ci karo da juna cikin tsarkewar murya maryama ta furta "am sorry !nadiya batai magana ba ta sake rike mayafin data rufe fuskarta dashi gam "excuse me who are you?kina aikina a AGC company ne?”ko kuma kina bukatar wani abu ne ?Shiru nadiya tayi tana qoqarin guduwa .”shi kuwa mr ATA daga inda yake zaune acikin office dinsa ya hangosu tsaye ya tsura masu idanunshi yana kallon dawa maryama take magana ?haka jikin maryama ya bata ta bud’e fuskarta matar taga ko wacece ai kuwa maryama tayi taku biyu tasa hannu zata zame mayafin da nadiya ta rufe fuskarta dashi nan take nadiya tasa hannuwanta duka ta tura maryama da iyakar karfinta maryama ta tafi luuuuu ta fad'a Kan durowar karfe nan take hannunta ya bugu da gefen karfen nan da nan sai jini ya balle "ouch ta saki qara mai sauti sannan ta matso da sauri ta rike hannun nadiya dake rike da kofar shigowa tana qoqarin zare hannunta maryam ta sake damkewa nan suka shiga kokuwa da juna ,har maryama ta samu ta mike tana qoqarin ta zame hannun nadiya ta dake damke da mayafin fuskarta inda wayar dake rike da hannun nadiya ya fadi kasa maryama tabi wayar da kallon mamaki “ai wayar da’akawo mata ne dazu da safe .”



Nadiya ta tsugunna da sauri ta dauka tana mikewa mayafin fuskarta ya zame kafin ta rufe fuskarta tunin maryama tagan fuskarta ,a matukar rikice ta furta sunanta " anifa ! tana rike hannunta dake tsiyayyar da jini wanda adaidai lokacin mr ATA ya soma qoqarin qarasowa inda suke yana kiran “stop !amman ina idanun maryama sun rufewa babu abinda take furtawa sai sunan anifa ki bani wayar nan bazan sakeki ba sai kin bani wayar nan dan bazan bari ki tafi koina ba batare da kin bani wayar nan ba.” ta qarasa mgnr adaidai lokacin da mrs ATA ya qaraso ya rike hannun maryama yana cewa “meye kikeyi haka ko kinyi hauka ne”?” Ka sakar min hannu karka bari ta gudu a matukar fusace ya zare d’ayan hannunta dake rike da nadiya ya hadasu waje daya wanda hakan ya bawa nadiya damar juyawa da sauri maryama ta juyo ta kalli bayan nadiya tana furta "sir sir sir !!! "dan magana ma yaki fitowa daga cikin bakinta tana kokarin fisxgewa daga hannunsa "ke kina hauka ne baki ga jinin a hannunki ba ?ta girgiza masa kai "tana kallon hanyar da nadiya tabi “zakiyi wasa da lafiyarki ne akan shirmen banza ?" rasa yadda zatai dashi yasa kawai ta fashe masa dan wani rikitaccen kuka mai tsananin cin rai tare da zubewa ajikinsa .hannuwansa duka yasa ya tarairayota ya rungumeta tsam ya hadeta da faffafan qirjinsa .”



cikin tsananin tashin hankali ya soma tafiya daita zuwa cikin office dinsa ya zaunar daita akan kujerar hutawarsa ,kuka sosai maryama take tana ciza harshenta da qarfi dan zuciyarta banda zafi alokacin babu abinda take mata “tana son sani me yasa ake kiranta da number anifa “.ya dauki waya ya kira bakin get inda securities suke aiki byn an dauka ya bada umarnin akawo masa hydrogen da cottonwood byn ya gama wayar yayi tsaye rungume da hannun wansa duka a qirjinsa yana dubanta ta kife kanta akan ciyoyinta tana cigaba da kuka wanda babu tantama kuka bakinciki take .”ciza lips dinsa ya dinga yi yana cigaba da kallonta shi a ganinsa gata yayi mata dan idan ya barsu da yarinyar babu tantama maryama zata sha wahala ne domin kuwa yarinyar tafita jiki da shekaru nesa ba kusa ba yana tsaye security ya qaraso bakin kofa yana neman izinin ya fito ya amsa ya juya ya koma cikin office din ya ajiye akan table dinsa sannan ya koma inda take zaune tana kuka .bai mata magana ba ya riko kugunta a hankali ta dago fuskarta shabe shabe da ruwan hawaye ,dayan hannunta da bai da ciwo ya riko zuwa kujerar dake zagaye da table dinsa ya zaunar daita ya kamo hannunta ya daura akan table .”


Ahankali ya bude kwalbar ruwan hydrogen ya zuba acikin cottonwood ya daura akan ciwo "asshhh !ta furta tana jin radadin ciwo,” sorry !ya furta ahankali cike da tausayawa yake goge mata, ajikinta ciwon yake amman ya fita jin radadin zafin "kalli yadda jini yaki zuba ki daina wasa da lafiyarki ,idan baki damu da komai ba ya kamata ki damu da lafiyarki domin shine komai arayuwarki ,ganin wannan jinin dake zuba ajikinki yayi matukar d’aga min hankali sosai amman Ke ko ajikinki why maryama ?yayi maganar kamar zaiyi kuka tare da cigaba da goge mata ciwon .
kwayar idanunta dake cike da ruwan hawaye ta tsura masa tana kallonsa tana jin wani irin sabon tashin hankali na kusantota .”ahankali ya dago tsumam mun idanunshi ya sanya kwayar idanunshi cikin nata gabanta ne ya shiga luguden bugu kamar yadda nashi ke bugawa da sauri ".


“me yasa ka tsaidani sir ?ya sauke numfashi "yace naga anifa amman gashi ban samu damar yimata tarin tambayoyin dake zuciyata ba wallahi da kasan yadda yarinyar nan take da mahimmanci a rayuwata da baka dakatardani ba "culmdown maryama !”ya furta yana cigaba da goge mata jinin ya d’an yagi bandage ya nade mata hannun "babu abinda bazan iya miki ba maryama "ya fad'a yana tsareta da tsumammun idanunshi yayinda hannunsa Ke saman bayan tafin hannunta "zaki iya magana yanzu, fad'a min meye tsakaninki daita "?tayi shiru tana jin zafi mai radadi a hannunta"shirunki ya nuna maryama kice baki da gsky ?ban san yadda zan maka bayani ba dan ba lallai ka fahimceni ba ya lumshe tsumammun idanunshi alamun tayi magana zai fahimceta .”



“ina sauraranki maryama ahankali ta motsa lip’s dinta ta soma magana muryarta da shesheka “tun daga ranar farko da anifa tazo gidanmu amatsayin friend din yaya sadam wacce sukai karatu tare sannan suke aiki tare ,tazo ne akan wasu takardun project da suka fara aiki tare dan haka tana bukatar project ko zan taimaka mata muje dakinsa mu duba banyi mata mutsu ba mukaje , na fita na dawo ina shigowa dakin naji Kmr muryar yaya sadam na fita daga cikin wayarta alokacin ,sannan kwanaki can ina zaune ina aiki da daddare aka kirani da number wayarta akace nazo aiki da wurin sannan shekaranjiya har zuwa yau din nan byn nabi didigin layin wani ya dauka yace min tsintar wayar yayi bayan wani lokaci aka kira wayar ina dauka muryar yaya sadam naji sannan daga by naji muryata babu abinda ta boye masa "yanzu ka fahimci yadda rike wannan matar yake da matukar mahimanci a gurina domin ina da tarin tambayoyin da zan mata sannan me yasa zata shigo har cikin office din da nake aiki ta dauki wayarta wallahi bazan ta'ba samun kwanciyar hankali ba muddin bangata ta amsa min tarin tambayoyina ba ta qarasa mgnr tana sake fashewa da kuka ".



“kina da matsala maryama ko dai kina imagenation ne taya zakiji muryar wanda ya mutu a waya bayan baya duniya ?"no sir ba imagenation nake ba tabbas wannan muryar dana ji muryar sadam ce ko komai ya kasance mafarki ko imagenation agurina wannan gaskiya ne," ni yanzu taya zan fita cikin wannan tashin hankali yanzu a ina zan sake ganin anifa arayuwata ?shikenan kasa na rasata .” shiru yayi na kusan mintuna talatin dan har ta fidda rai zai yi magana sannan taga ya dago kansa yana kallonta zuciyarsa cike da zallar soyayyarta yasani mutumin daya mutu bazai dawo ba imagination kawai take tunda har lokacin tana cikin gigin mutuwarsa ne numfashi ya sauke sannan cike da tausayawa ya soma motsa lip’s dinsa "maryama ki daina kukan nan zan taimakeki kiganta ,”amman me yasa tun safe nake fama dake ki fad'a min damuwarki kika ki ?”



“nasan bazaka fahimceni bane shiyasa "me yasa zakice hk ?”amman ai ni na tamvayeki damuwarki ?” Ta gyad’a masa kai ,ko zan iya tambayarki ?“ta sake gyad’a masa kanta alamun yayi tambayarsa “me yasa kika kasa manta abinda ya faru dake baya ?bazaka fahimci yadda nayi rayuwata bane amman kuma zan iya cewa zaka fahimta ,the situation i have past or the one am going tru at this moment ,my pain’s, my suffering, I don't expect any one can understand me ,and I don't want any one to understand me amman dai nasan ni din yar Adam ce mai numfashi kuma ina yawon addua sir amman nayi facing matsalolin masu tarin yawa arayuwata tun kafin a tsaida maganar aurena da yaya sadam har zuwan sanda ya barni amman kuma duk wannna sai ya zama imagenation ?ko zaka iya fad'a min duk abinda ya faru dani duk imagenation ne ?dan allah ka fad'a min ?”.shiru mr ata yayi batare da yace komai ba yana nazarin maganganunta jin yayi shiru tayi tunanin ko ta ta'ba masa rai ne yasa tace "dan allah ka yafe min akan maganganuna idan kaji babu dadi sir .”still shiru yayi batare da wani dalili ba ina ta fadar maganganu da sam basu dace na fad'a ba na gode sosai da kulawarka sir ta qarasa mgn hawaye na sake turareniya fitowa daga idanunta .”


"Is okay maryama ki goge hawayenki zan nemo miki ita , nadiya sunanta ba anifa ba,zan nemo miki a duk inda take acikin fadin duniyar nan saboda na santa "maryama tayi saurin matsowa kusa dashi har gwiwowinta na gugan nashi "ya akayi kasanta ?sosai kuwa nasata ,amman naji kace nadiya sunanta ba anifa ba “?tabbas nadiya sunanta domin ta ta'ba aiki a daya daga cikin companies dina maganar da nake miki ma yanzu haka ta bukaci aiki da kafanina na auduga “amman ni ce min tayi tare sukai aiki da yaya sadam .”Ta yuwu sunyi aiki da sadam din tare bazan san wannan ba dan ta ta’ba aiki a IA company mahaifinta mai kudi ne sosai tru din wani abokin dad dina na d’auketa aiki a byn ,bata dade tana wani aiki damu ba tace zatai tafiya zuwa qasar amercan idan ta dawo zata sake neman aiki to ina ganin dawowarta ne ta sake tura mana sako neman aiki.”
Ya qarasa maganar yana mugun tsareta da kwayar idanun shi “maryama fad'a min me yasa kike son tsohon mijinki sosai haka ?tayi shiru qirjinta na bugawa fiyye da kaida ,tell me me zakiyi da mutumin da baya raye ?



Mmn sudais[8/31, 11:25 AM] Safwan Libiya 2: 💗💗💗💗💗💗
     MAR'ADAMS
     💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

BOOK 3

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan  09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.


             Page 30


Shiru ne ya ratsa office din ,domin kuwa maryama ta kasa bashi amsar tambayarsa ,yadda ba tace masa komai ba haka shima bai sake cewa komai ba har tsawon mintuna shabiyar yana zaune yana kallonta shiru ko bata fad'a masa ya karanci tunani kala kala take acikin zuciyarta ,har ga Allah bata son yasan komai akan rayuwarta, ba dan komai ba sai dan tsare mutuncinta  amman kuma idan sanin nashi yana cikin taimakon da zai mata ta samu ganin nadiya  bata da option zatayi "maryama !ya kira sunanta da kasalalliyar muryarsa mai tsananin kashe sansar jiki da tsuma zuciyar wanda akayi dominsa"bana maimaita magana d'aya domin kuwa baya daga cikin d'abiata ,amaman akanki kullum sai na aikata haka why ?."still shiru tayi tana nazarin abinda zata fad'a masa wanda zai gamsar dashi "ki amsa min  tamabayata akwai abinda zuciyata take bukatar sani" tana can tunanin abinda zata fad'a masa kawai sai taji ya matso ya dawo daf daita sosai yasa hannunsa d'aya ya sake riko hannunta mai ciwo yana kallo  "karki ga na damu da son sani kiyi tunanin ina yin shishigi ne acikin abinda bai shafeni ba "no sanin dalilin shine kwanciyar hankalina "."



"maryama a karo na qarshe ki  fad'a min me yasa kike son tsohon mijinki sosai ?"ya qarasa maganar yana lumshe tsumammun idanunshi "hallaci ne !"ta fad'a hawaye  na zubo mata akan kuncinta, ajiyar zuciya mr ata ya sauke sannan ya bud'e idanunshi sosai akanta yana jin wutar soyayyarta na sake ruruwa acikin zuciyarsa yayinda qaunarta mai zafi ke nacin zuciyarsa, baya qaunar ganin damuwarta bare kuma zubar  hawayenta. ya kai hannunsa d'aya ya ciro hanky acikin gaban aljihunsa mai azababben qamshi ya soma  share mata hawayen dake gangaro wa akan kuncinta, qamshin turarensa mai sanyi  ya cika hancinta ta shaqa ahankali tare da lumshe ido nã second biyu sannan  ta bud'e tana kallonsa  tana jin wani irin yanayi a gabad'aya ilahirin jikinta ."kasa daina kallonsa tayi dan hk gabad'aya tsigar jikinta suka dinga mikewa tsaye ." kallonta ya sake yi a tsanake yana d'an cizan gefen lip's dinsa ahankali ahankali!!""hallaci mahaifiyarsa tayi min tun kafin nazo cikin duniyar nan ,haka shima yaya sadam yayi min hallacin ,kuma hallacin ne  yayi sanadiyyar dasa soyayyarsa mai qarfi acikin zuciyata wanda nake ji muddin ba dashi  ba bazan iya qara rayuwa da ko wani namiji  ba ."saurin runtse idanushi yayi daga tsura ma marayama idanu da yayi zuciyarsa cigaba da bugawa fiyye da kaida ."



Ahankali yayi baya kad'an da kujera da yake zaune akai yana jin wani irin tattukin bakinciki mai had'e da zazzafan kishi ,ji yayi gabad'aya ya muzanta a gabanta "ashe rashin furta mata soyayyarsa taimako kansa yayi, kuma shine abinda yafi zama alkhairi atare dashi ,shiyasa a kullum manazarta suke cewa duk mutun mai yawon surutu tabbas wata rana sai yayi nadama ,shi kuma mutun shiru shiru kullum cikin nasara yake sakamakon hangen nesan shi "na sani dukkanin rayuwar da nayi abaya rubutaccen qaddara ne ban isa na canzawa kaina ba cike da faduwar gaba ta fara bashi labarin abinda ya faru daita daga kan masu zuwa neman aurenta har zuwa sanda umma ta yanke hukuncin had'a aurenta da yaya sadam da abinda ya faru dasu akan hanyar dawowarsu daga ogun state ta qare maganr tana zubar da kwalla mai zafi tana jin zafi a qirjinta"nasan umma tana rayuwa ne kawai amamn har ta koma ga allah zuciyarta na d'auke da rad'ad'in rashin tilon d'anta wanda nice silar faruwar haka ."



mr ata ya kalleta cike da tsarewa da tausayawa "kin tabbatar a gabanki aka binnesa da ranshi  ?"wasu hawaye ne suka sake biyo kuncinta sakamakon tuno da tashin hankalin ,nan take jikinta ya kama rawa tamkar alokacin alamarin ya faru domin kuwa tashin hankali ne da bazata ta'ba mantashi arayuwarta ."
"idan zata manta komai daya faru a past dinta ban da wannan al'amari mai firgici "No !ni ba kuka nace ki min ba "ya fad'a yana dafe kanshi sannan ya sake kai hanky ya goge mata hawaye sai daya tsareta da tsumammun idanunshi sannna ta d'aga masa gira tace "yes a gabana suka haqa rami suka binnesa ta bashi amsa ."ya sauke numfashi yana dora qafarsa d'aya akan nata  batare daya san yayi haka  ba duk da qafarsa  sanye take da safa amamn sai data ji yadda ya sauke wata naunayen ajiyar zuciya wanda tasa hawaye ya gangaro daga idanunta  sannan a can qasan makoshi yace "amamnan maryama idan aka yiwa mutun haka me kike tunanin halin da mutun zai shiga?" ko a minti goma né bare an d'auki sama da kwanaki sannna kuma ke karon kanki kin kasa gane inda abun ya faru "?naunauyen ajiyar zuciya ta sauke kana ta motsa labbanta tace "babu tantama mutun bazai rayu ba ." yayi saurin  matso da kujerar da yake zaune  still tafin qafarsa na saman nata yace "okay anyi haka a gabanki but what are you still waiting "tayi shiru ta kasa cewa komai "mutumin nan baya raye maryama me yasa zaki dinga imagenation dinsa over?"



na sani nasan baya raye amman na rasa dalilin da yasa nake jin kamar yana raye "wallahi bana jin daidai arayuwata sakamakon rashinsa atare damu domin kuwa bani kad'ai nayi rashinsa ba hatta yanuwa gabad'aya sunyi kewarsa amamn basu kai ni ba"tsakninki da allah kina jin soyayyarsa ko tausayin mahaifiyrsa ne ke dawainiya da zuciyarki "?kamar yadda na fad'a maka a farko hallacci ne amamn a yanzu ina son shi har ina jin bazan iya rayuwa da wani namiji ba idan bashi ba  I really love him son shi da qaunarsa sun mamayeni ."yayi mata wani irin kallo yana  mai jin zafin mgnarta aransa amman sai ya dane tare da d'auke qafarsa akan nata ya juya tare da janyo laptop dinsa gabansa ya soma da daddana laptop din da qarfi a yadda yake operating din laptop din kasan acikin zafi zuciya yake ,yana daddanawa yana fitar da zazzafan numfashi yana jin wani azababben kishi from know where na shigarsa ."



"wato duniya juyi juyi ne yau gareka gobe ga d'an uwarka ,abinda ya baka dariya wata rana shi zai sakaka kuka ,dan girgiza kanshi yayi yana zance zuci wato shi kuma haka qarshen soyyarsa ta zama yana son maso wani ,ina ma mafarkinta ya cigaba da yi da wannan lukutar matseefar da ta samesa .wai kamar shi yau soyayya take kutimememiya dashi haka ?""karkaji komai aranka adam, sannan karka manta ita soyayya allah ne yake sakata acikin zukatan wad'an da yaso ,kuma babu wanda ya isa ya rabata ko kuma ya hana faruwar abinda allah ya had'a kai kanka da kasan haka rayuwar soyayyarka zata zo a qarshe da duk yadda zakayi ka goge shi dakayi amman dake had'in Allah ne  har ma yake jin babu abinda zai iya sawa ya juya mata baya ko kuma ya daina sonta dan  a yadda yake jin  soyayya da qaunar da yake mata babu wani abu a duniyar da zai firgitashi har yaji zai iya hakura daita  to kuma ai ita zuciyarta ta tsundu ma acikin tafkin son wani ?"zuciyarsa tayi saurin tunatar dashi "uhm ai kuwa akwai bala'i dan  kuwa ta  qarfi da qarfafa zai shigar  daita tsundum cikin kogin sonshi har ta manta ta ta'ba son wani a duniya yayinda ita kuma maryama sai goge hawaye take wasu na sake gangarowa muryarsa a tsarke yace  "kiyi hakuri banyi miki wad'an nan tambayoyin dan na 'bata miki rai ba." karka damu sir dan nima banji komai ba"ni dai ina bukatar nadiya ina son nasan wani abu dan  gabadaya a tsorace nake tana bani tsoro matuka bansan me yasa take bibiyar rayuwata ba ."



"nima abinda yaketa bani mamaki Kenan ko me yasa zata shigo har office byn ta rufe fuskarta "na samu wayarta  ina ganin akwai abinda yake tare da wayar  mai mahimanci ,ta kira taji muryata kuma tana ganin idan batayi hanzari ba  zan iya sanin wani abu akanta  idan na koma gida dan kwata kwata bana jin dan wayar kawai tazo domin zata iya samun wata wayar kuma tasan bazan tsinci komai da wayar ba tunda a kulle take idan ma nace zanyi flash din wayar dan na bude bazan ga komai ba saboda wayr zata dawo empty akwai dai abinda  ta biyo "okay zanga abinda zanyi akai dan dole na nemo nadiya."
" kana ganin zaka  iya nemo min ita ?tunda nace miki zanyi zanyi ne" taya kenan ?tana matukar bukatar aiki damu a yanzu zan tura mata sako mun d'auketa aiki ,zanyi  qoqari na had'uku sannna akwai binciken da zan yi still akanta in sha allahu .matsa war haduwarki daita zai sa kisamu kwnaciyar hankali I wil try my best ya fad'a yana cigaba da aikinsa maryama  ta mike tsaye da kyar tace "na gode sir ni zan wuce gida "."koma ki zauna na gama mu kaiki gida  ."haka ta koma ta zauna jiki a sanyaye dan gara ta jirasa din su kai gida ta sake cewa "na gode sosai."bai kulata ba illa ya cigaba da abinda yake ."



Bayan kamar minti shabiyar ya mike ya tattara wayoyinsa ya  nufi hanyar fita yana cewa  "muje ko".mikewa tayi tabi bayansa yana gaba tana biye dashi har suka sauka qasa  yaja ya tsaya tare da zura hannuwansa duka  cikin aljihun wondonsa inda masu tsaronsa suka taso  da sauri duk suka zagayesa cike da girmamawa ,a natse ya ciro hannunsa daya daga aljihunsa ya soma keyarsa sannan ya soma magana cike da kamewa "a ruwa zai kai ni agege so ku zaku iya wucewa ."iyakar abinda ya fad'a kenan dan bai son ya shiga unguwar da jami'an tsaro."
tana tsaye tana kallonsa  ya bud'e gidan baya tayi shiru tana jin mummunar faduwar gaba gabad'aya daga securities din bakin get din har na cikin ma'aikatan da masu tsaronsa babu wanda bai yi mamaki ba dan basu ta'ba ganin haka daga garesa ba har gara ma masu tsaronsa zasu iya cewa suna ganin yana yiwa mahaifiyarsa amman wata mace daban wannan ne farko ."ki bar wannan banzar tunanin naki ki  shiga"ya fad'a yana hura hanci jiki a matukar sanyaye ta shiga ta zauna ya maida kofar ya rufe mata sannan ya soma qoqarin zagayawa inda kafin ya qarasa tuni a ruwa ya bud'e masa ya shiga ya zauna yana ware qafafuwansa wanda ya zame masa jiki sannan a ruwa ya shiga mazaunin direba ya tada motar suka nufi get ."



Shiru suna  zaune a bayan motan sai driver a ruwa a mazauninshi, haka nan taji hawaye ya ziraro mata a sanda suke  hau babban titi ,  ahankali ta juyar da kanta tana kallon gefen titi tana sheshekan kuka wani dogon tsaki yaja ,tana jinsa  kamar zata juya ta kallesa  sai kuma ta fasa,ta ci gaba da barin kanta a inda yake ya motsa bakinshi kamar zaice wani abu shima sai kuma ya fasa ya ciro d'aya daga cikin wayoyinsa dake qara mara sauti yanayin yadda taji yayi maganar tasan oga amar ne, bisa dukkan alamu maganar mai mahimanci ne "karka damu dole zan nemeka cikin satin nan "eh duk acikin satin zamuje gurinsa in sha allahu to gsky dai ban gama tantacewa ba, tsarin farko zanbi ko kuwa wani tsarin ne amman dai duk abinda ake ciki zan nemeka sukai sallama kana ya dan tsaya yna kallona"wallahi kukan nan yana maseefar kona min rai ."ya fad'a yana sake jan tsaki mutun yayita kuka baya tunanin halin da mutane zasu shiga” yayi maganar acan qasan makoshinsa  ."



shiru tayi tana assessing maganarsa, ta juyo a sukwane taga ita yake kallo fuskashi  a hade tamkar wanda aka aikowa da sakon mutuwa ."ahankali  ta dauke kanta tare da tsaida hawayenta tana lissafi maganarsa  "wallahi kukan nan yana maseefa kona min rai ,mutun yayita kuka baya tunanin halin da mutane zasu shiga "bata gama tunanin makomar maganarsa ba taji  ya matso kusa daita sosai tare da daura kanshi akan kafad'anta wanda yasa ta sauke naunayen ajiyar zuciya "please maryama ki daina tunanin matacce haka ."numfashi ta sauke  kawai .
bata ankara ba taji ya kamo hannunta mara ciwo cikin nashi "ina son ki daina tunaninsa ,ko zaki min wannan alqarin ?"tun kafin tace wani abu ya cigaba "yes I know you  can do it for me "kiyi saboda ni bansan dalili ba maryama bana son ganinki cikin damuwar nan zaki daina tunaninsa " anya  kuwa zata  iya kuwa? Not thinking of yaya sadam dinta bayan a yanzu bata  iya kwana ba tare data yi tunaninsa ba  ? "Kullum sweetheart dina tana fad'a min yawon tunani

Please Login or Register in order to submit comment