Reading MAR ADAMS BOOK 3 BY AYSHA BAGUDU Chapter 2 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

haka babu wani laifi da kikayi jarabawa ce ,itama hjy ta qaraso suka sakata a tsakiyarsu gbdy suka rud'e, umma na shafa mata kai hjy na shafa mata bayanta alamun rarrashi "akan wani dalili kenan suka koreki byn sun d'aukeki aiki ?" wai kawai dan nayi rejecting din ayyukansu wannan  kawai shine dalilin da yasa suka koreni byn ban yi hakan dan bana so yin aiki dasu  bane , nima ina son aikin nan amman alokacin suba'a  tafini bukatar shi allah ka gani nayi komai saboda kai ne."


" kun gani ba !shikenan allah ya amsa adduata ba ke uwar yan kankaba yau ga abinda gwaninta ya jawo miki sarkin iya taimako cewar Aunty hasana data fito daga kitchen ".haba hasana haba Hasana !dame kike son yarinyar nan taji ?idan bazaki mata addua ba ai  bai dace Ki fad'a mata haka ba."  ta kwabe fuska koma dai menene tunda ta rasa aikin ai shikenan bukatata  ta biya .ni a gurina wannan jarabawar daga allah ne kuma yana sane da komai bari zanje ma'aikatan da kaina naga mai kamfanin inji cewar umma "a'a umma karkije ,karki wani wahalar da kanki akan zuwa wajensu kawai suje su wulakanki a banza kamar yadda suka wulakantani "a'a bazasu wulakantani ba hakuri zan basu maryama "a'a ban yarda ba kuma wallahi ko kinje bazan qara komawa wannan kamfanin ba da sunan aiki bayan sun gama wulakantani sun tozartani har fa na fara aiki umma suka koreni basu ma tsaya sun fahimceni ba wai da gangan naki aikin dasu , wallahi banason aikin nan kuma kema bazan barki kije koina ba kuma ko zan mutu babu aiki bazan qara zuwa wannan kamfanin ba duk wannan maganar tanayi ne tana kuka har da shesheka "


umma ta rungumeta sosai ajikinta tana rarrashinta "kiyi hakuri maryama in sha allahu zaki samu sausauci ki cigaba da addau lokacin wahalarki  ta kusan zuwa karshe da izinin allah Aunty Hasana ta kallesu tana turo  masu baki alamun zund'e aranta tace "kwayi kwa gama idan wannan tsinanniyar yarinyar ce mai kashin tsiya ai duk inda arziki yake sai an korota ,sosai umma da hjy suka dinga rarrashinta har hankalinta ya d'an kwanta "yanzu umma kina ganin wata rana zan fita cikin wannan wahalar ?"sosai kuwa maryama  zaki fita mana wannan ai duk matakin d'aukaka ne amman fa idan kika d'aure kika d'aina fadar duk abinda yazo bakinki duk maseefar data samu bawa baa son yana yawo fad'ar abinda bai dace ba,abinda ake so mutun ya  yawaita furtawa inna lillahi wa inna ilaihi rajiun ko lallaha illa anta subuhanaka inni kuntun minal zalim, ya hayyu ya qayyum ya zaljalalu wal ikram da sannu allah zai wanke miki zuciyarki da farinciki
."maryama ta share hawayenta ta zauna sosai a tsakiyarsu tana jin damuwarta ta yaye, ta kamo hannu umma cikin nata "wallahi umma  bakiga kamfanin ba komai a tsare kuma na dade  ina neman aiki a gurin tun alokacin da yaya sadam yaki amincewa da yin aikina  dole ce tasa na barwa subai'a wancan aikin "karki damu  nayi imani zaki samu aiki wanda yafi wanda kika rasa  Ke dai ki rike allah da adduar allah zai bi bayanmu .maryama tayi cikin jikin umma tace "Allah yasa ummah ina sonki mamana murmushi umma tayi tace "nima ina sonki maryama in sha allahu zaki ga haske arayuwarki "ummanki kawai kike so maryama nifa ?hjy ta fad'a tana dungure mata kai lumshe idanunta tayi tana dariya suma dai dariyar sukayi ."

*****

ATA na zaune  yana aikin  tura sako wayarsa ta dauki ringing ya dauki wayar ya manna a kunnesa yana lumshe ido  "yes kuna magana dashi ,okay kuna bukatar kaya new design ok just a second cewar ATA nan take ya kira sunan sectary ,sannan ya cigaba da abinda yake da sauri ta shigo  ta tsaya tana cewa "sir ! ya katse kiran byn ta shigo still ya cigaba da daddana system "mutumin dana gama waya dashi sabon  customer ne  yana bukatar kaya sabbin design dan haka Kiyi kokari ki hada Kan masu fresh design da muke dasu su bamu design masu kyau ayi abinda sabon customer zai ji dadi fatan kin fahimta "yes sir ."ko mu gwada sabbin dauka mugani ? " Eh hakan ma yayi domin muga kwarewarsu " okay sir "ta fita da sauri "maryama hussein ?!ya furta sunan a natse yana danna keyboard din system dinsa da karfi sannan ya cire hannunsa ya jingina jikinsa da kujerar da yake zaune yana jujuya jikinsa "waye mijinta a wani unguwa  take ?da gaske dai idan bai dauki shawarar ammar ba ya rasa natsuwa kenan kuma har abada dan ya tabbatar wa kanshi bazai iya rayuwa babu ita ba"waye mijinta a wani unguwa take duk yana bukatar yasani amman dole yabi komai ahankali darajan auren da take  dashi  ." amman dai zai nemi ammar din dan yana son yasan wani abu a game daita kafin yasan abun yi ."


Cikin kankani lokaci sababbin ma'aikatan suka hallarar a cikin officer dinsa kowannensu rike da takardar zane ya yunkura ya mike da kyar ya zagayo daya bayan daya ya dinga amsa yana dubawa sai dai gabadaya babu wanda yayi masa acikin zanensu . yaja qaramin tsaki ya tsaya ya rike kugunsa yana aika masu da wani mugun kallo mai tattare da abu biyu ,abu na farko damuwar da yake ciki abu na biyu kuma takaicin basu yi masa abinda yake so ba "wannan shine iya kwarewarku?shiru sukai gaba dayansu zuciyarsu cike da matsanancin tsoro kallonsa kawai yana firgita da mutun bare kuma maganarsa cikin zafin rai ko waye kai sai kaji fargaba "ban d'aukeku aiki dan biyaku batare da kun iya komai ba ,na daukeku né saboda kunce kun iya wannan shine karshen iyawarku ?ya sake jefa masu tamabyar data sake gigitasu suka ji kamar su falla da gudu amman babu hali ."wallahi duk na daukeku né saboda best design not nonsense ya fad'a a matukar tsawace  ." sannan ya maida idanunshi Kan sactry" some can you see your self ina gwajin da kikace kinyi masu ?"sir duk angwadasu  "most of the...."


"Culmdown ata ! aka fada tare da turo kofar office din ,shiru yayi yana dago tsumammun idanunshi zuwa kofar shigowa ganin sultana yasa ransa ya qara baci ,ya lumshe idanunshi yana furzar d iska mai zafi  daga bakinsa fuskan natashi babu annuri ko daya sultana ta qaraso har gabansa hannuta rike da farar takarda "nazo da abinda kowa ya kasa kalli nan kaga" ta fada tana jujjuya masa jiki tare da kai takardar gabansa "kalli irin kwarewata nasan wannan ne exactly abinda kake bukata? shiru yayi zuciyarsa na wani irin tuttukin bakinciki "Listing !this is my last warnin karki kara shigo min office batare da kinyi knowking ba  sannan idan zaki kirani kisa girmamawa call me with sir ..."yana gama fad'ar hk ya juya  da sauri zai barta tai saurin cewa " okay sir !ta fad'a tana masa fari da idanu wanda ko kadan bai girgiza zuciyar ATA  ba sai ma qara tsanarta da yayi "my design ! ta furta cikin salon jan hankali tana duban farar takardar dake rike a hannunta a kaikaice ya juyo ya fixge takarda daga hannunta ya tsurawa zanen tsumammun idanunshi dake cike da tashin hankali yana karewa zanen kallo yayinda ta cigaba da juya  masa jikinta tana murmushi tana kallonsa sai dai gabanta banda dukan uku uku babu abind yake ."



Wani irin dariya ne yaso kufce masa saboda ganin abinda take takamar ta zana awajensa shi da  jagwal gwalo bashi da wani bambamci amman ya danne  dan dariya bata kamace masa ba a halin da yake ciki sai dai  kana kallon fuskarsa zaka fahimci abun yaso bashi dariya wani irin sanyin  dadi ne ya mamaye gabadaya ilahirin jikinta ta sake gyara tsayuwa tana kallonsa tana jiran taji me zaice ."a natse taga ya shiga matsé takardar har ya matseta  gabadaya yana  mata wani irin mugun kallo sannan ya kalli inda abun zuba shara yake ya cilla takardar aciki ."
sake fuskantata yayi cikin fushi yace "wa kike da suna sultana ko me ,wannan shine sakamakon abinda kike zana yana gama fadar haka ya juya ya soma tafiya zuwa mazauninsa wani irin numfashi ta sauke da karfin gaske tana kiran sunansa "ya Adam !a matukar tsawace yace "me zanyi miki ?wato burinka ka wulakantani a bayyanar  nasi ba ?ta sauke numfashi tana furta why ?Kina san kisan ina da ikon wulakantanki ko bani da ?tayi shiru tana dubansa "to ki daina shiga tsabgata ki kama kanki akan komai nawa ki tsaya iya inda aka ajiyeki stay a way from me sultana oya leave ..."ya fad'a yana nuna mata kofa  tare da zabga mata harara cike da in ina ta kira sunansa "ya..ya Adam"i saida leave ya sake nuna mata hanyar fita ."


"Some ai na rigada na fad'a miki ki dauki kwararrun masu zane ba muna zane ba gabadayan ni banga na dauka anan ba "ya fad'a yana jan dogon tsaki  "sir kayi hakuri kowannensu yana ta qoqarin yaga ya zana abinda zai burgeka "shiiii! "ya fad'a a tsawace "common design sun kasa abinda zai fi ki sallamesu kawai gabadayansu a nemo min wasu "kayi hakuri sir amman  me zai hana a nemi maryama hussein  nasan zata maka abinda kake ...,"stop ! ya tsadata  a tsawace just stop some karki qara kuskure ina wata magana dabam kina sako wannan yarinyar ko kin fahimceni ? tai saurin gyada masa kai "bana bukatar wannan yarinyar kuma bazata sake tako kafarta zuwa cikin wannan kamfanin ba ,bama wannan kafanin ba har kowani kafani da suna aiki ita da yin aiki har qarshen rayuwarta ."



Bayan ya gama mgn ya numfashi yana kallonsu daya bayan "ku saurarani da kyau zan sake baku lokaci "yarinyar ce zaune a lap cike da natsuwa idanunta na Kan farar takarda tana zana doguwar rigar amarya da riga da wondo na ango  sosai tayi concentration gaban doguwar rigar tana da shape daga gaba yayinda bayan rigar ta sauko wanda ya hade da dogon gashin mace yana bayani yana kallon maryama cikin kwayar idanunshi cike da matsanancin qaunarta ,lumshe lumtsatsun idanunsa yayi "wannan shine tsarin zanen da nake so ku dinga bin komai daki daki tare da tsare fatan kun fahimceni ?gabadaya suka hada baki "yes sir ."oya maza maza aje ayi daya daga cikinsu ya kallesa yace  " kayi hakuri sir inshaallahu zanyi maka abinda kake so "very good ya fad'a yana tare da komawa  mazauninsa ya zauna yana jujjuyawa akan kujera sannan ya dauko cup din glass cup dake cike da ruwa ya kai bakinsa ya kurba ya ajiye ya daura hannunsa akan hannun kujera yana cigaba da jujjuyawa."


Bangaren sultuna kuwa office dinsu ta koma ta cike da tsananin tashin hankali da takaicin abinda ATA yayi mata waya ne a kunnenta tana magana da Aunty abida "kinga wulakacin da yayi min kuwa aunty agaban ma'aikatansa bayan ya gama  wulakanta zanen dana sha wahala na zana a gaban kowa wallahi bazan dauka ba Aunty bazan jura wannan wulakanci ba" nasan halinsa shegen gaske ne  zai iya aikata abinda yafi wannan ki daina damuwa abinda ya kamata kiyi  kokarin shine ki fara daukar hankalinsa ...amman Aunty .."No ki tsaya kiji abinda nace Kiyi shi zakiyi karki min mutsu dan duk ina yin wannan abun ne saboda jin dadinki ...."



Wannan  littafin  na kudi ne mai bukatar karantashi   byn na kammalashi zai  biya 1000 ta wannan  account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura  domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina  (Hausa bakwai ) a YouTube.


Page 2

Sultana na gama wayar da take idanuwanta suka sauka akan zanen da maryama tayi akan table , shiru tayi rike da wayarta tana duban zanen zanen ne mai Shege kyau da d'aukar hankali. zanen mace ce sanye da kayan weeding gwan sosai maryama ta kwantar da hankali ta zanata had'e da zana gashin kanta har gadon bayanta tamkar dai mutun sak wani irin murmushin jin dadi ya bayyana akan fuskar sultana cike da jin dadi tasa hannu ta d'auka tana cigaba da kallon zanen "wannna ai irin zanen da ya adam yake bukata ne sak "tabbas idan yaga wannan zanen zai ji dadi sosai bari na kai masa nace ni na zana "ta juya da sauri ta nufi hanyar office dinsa alokacin da Kunnensa yake manne da waya yana magana da wani abokin kasuwansa ,yayinda hannuwansa duka ke aikin dadddana keyboard gefensa sectary dinsa ce tsaye rike da wani blue file tana dubawa ."



"Yes !muna da fiyye da abinda tunaninka ya baka ,eh !sosai kuwa akwai abubuwa masu mahimanci akan sakon dana tura maka kayi qoqari ka duba" ya fad'a yana cigaba da aiki can bayan kamar minti goma ya mike tsaye rike da system dinsa ya isa inda sectary dinsa take tsaye yana nuna mata wani sako tare da yi mata qarin bayani yadda yake son kasuwancin ya tafi bai gama rufe bakinsa ba yaji ana magana daga bakin kofa "tare da knowking " ko zan iya shigowa ?.Idanuwanshi dake manne da farin glas ya tsurawa kofar shigowa tare da yin shiru na second biyar sannan maganarsa ta biyo baya "yes !ahankali ta tura kofa ta shigo tana rausaya yana ganinta yaja tsaki ya koma kan kujera ya zauna ya dungule hannunsa duka waje d'aya ya d'aura akan table yana ciza lips dinsa na kasa wani irin numfashi ya furzar mai zafi daga bakinsa ya kawar da fuskarsa adaidai lokacin data garaso qefensa ta tsaya tare da ajiye masa farar takarda a gabansa "ko akwai abinda zaka ce akan wannan zanen ?ta gefen idonsa ya soma hango had'ad'd'en zanen ,a natse ya juyo gabad'aya idanuwan shi suka sauka akan zanen " kaga irin zanen sultuna ba?na sha fad'a maka ina da kwarewa sosai akan zane amman kullum gani kake ban iya komai ba to yanzu dai me zaka ce akan wannnan zanen sir ."?


Shiru ATA yayi tare da kallon zanen yana jin wani irin mummunar fad'uwar gaba mai tsanani na shigarsa kafin a hankali ya d'an yunkura ya mike tsaye still idanuwanshi na kan zanen jikinsa a matukar sanyaye ya kai hannu ya d'auki farar takardar data ajiye a gabansa ya tsurawa design din ido sosai ,numfashi ya sauke da karfin gaske yana cewa "zanen yayi kyau kwarai da gaske sai dai sultuna ...."sai kuma yayi shiru yana dogon nazari akan zanen "ka gani ba yayi maka ba?" ai daman na sha fad'a maka idan kaga wasu zanen da nake zanawa sai kayi mamaki wannan yayi maka ba ?"
"No ...!"
ya fad'a a natse sannan ya cigaba da magana "wannan ba zanenki ba saboda ba wannan bane karo na farko dana ta'ba ganin shrmen zanenki?"sultana tai shiru yayinda jikinta ya d'an soma rawa saboda yanayin kallon da yake mata .yayi taku biyu yayi daf daita yana ciza lip's dinsa muryarsa can kasa yace " ki kace ke kika zana zanen nan ba ?" sosai kuwa sir ni da kaina na zana shi ya gyad'a kai ya koma ya zauna akan kujera yana sake kallon zanen yana jujjuya jikinsa tare da girgiza kai. can ya d'ago ya dubeta da kyau "kikace zanenki ne ?ya sake tmbyrta ta gyada masa kai alamun "eh! gabanta kuwa banda fad'uwa babu abinda yake "shikenan sultuna tunda ke kika zana ina bukatar ki sake zana min exactly irinsa yanzu "cike da tashin hankali ta kai hannu zata kar'bi zanen dake rike ahannunsa "okay kawo na tafi naje na zana ".


Ya janye farar takardar yana girgiza mata kanshi tare da lumshe mata idanuwanshi na second biyu sannan ya bud'esu fés akanta "ki zauna ga guri nan sannan ga kayan aiki nan duk anan kiyi abinda nasakaki ta tsaya cike da matsanancin tsoro da firgici tana dubansa tare da mamakinsa "wannan mutumin fa katon mugun d'an duniya ne wato dai sai yaga karshenta ?ta fad'a haka acikin ranta ."
Ganin ta kasa kwakkwaran motsi tana tsaye tamkar an dasata yasa zuciyarsa ta soma tafarfasa a matukar tsawace yace "zauna mana Kiyi aikinki ai nasan zaki iya tunda kina da tabbacin zanenki ne cike da tsoro tace "yes sir !ya girgiza kai ya zagayo gurin sectry dinsa ya cigaba da yi mata bayanin abubuwan da yake buakta tayi masa yayinda har lokacin sultana na tsaye cikin tsananin tsoro da tashin hankali "wani irin mugun kallo ya d'auketa dashi yana zabga mata harara,da mugun sauri ta samu waje ta zauna akan d'aya daga cikin kujerun dake fuskartasa ta d'auki pencil ta rike tana tunanin ta ina zata fara ?nan da nan ta qara shiga tashin hankali mai tsanani fiyye da wanda take ciki ahankali zufa ya shiga tsatsafo mata a fuska da sansar jikinta kallo d'aya zaka mata ka fahimce a matukar tsorace take ."na shiga uku nah na dibo ruwan dafa kaina “ta ina zan fara ?tayiwa kanta tamabyar hantar cikinta na wani irin kad’awa .”


Sectary dinsa ta d'auko file green ta mika masa ya kar'ba yana cewa sultana "are you done ? batare daya kalli inda take ba" muryarta da jikinta rawa suke gurin cewa "no sir ! ya gyad'a kai "yau zaki gane baki da wayo muddin bakiyi abinda nace ba ya fad’a a kasan ranshi ,wayarsa tayi ringing some ta d'auka da sauri ta mika masa ya amsa yana manna wayar a kunnensa yana cigaba da duba file din hannunsa at the same time yana magana a waya ."Sosai ya fahimci yanayin tashin hankalin da sultana ta shiga ya sauke numfashi ya ajiye wayar ya maida hankalinsa gurin sectary dinsa suka cigaba da tautaunawa har tsawon mintuna talatin sultana na zaune cikin tsananin tashin hankali batare da tayi abinda ya sata ba ."



ya sake yunkurawa ya mike tsaye rike da zanen maryama a hannunsa ya zagayo ya isa inda take zaune jin hucinsa numfashinsa daya sauka a gefen wuyanta yasa ta waigo a gigice jikinta na wani irin kyarma "ai daman nasan bake kikayi zanen nan ba , sam sam wannna ba zanenki bane ko har yanzu kina kan kece kikayi ?ya tambayeta yana ja da baya yayi taku biyu ya tsaya yana jira yaji karyar da zata sake girba masa ya samu damar cin ubanta son ransa." cike da tsoro da in ina tace" eh gaskiya ba nice nayi ba amman kayi hakuri."tayi mgnr duk a rud'e jikinta na rawa tamakr an jona mata wutar lantarki."ai daman ko baki fad'a ba nasani wannan bazai ta'ba zama zanenki ba ya fad'a yana mai sake tsurawa zanen maryama tsumammun idanunshi kafin ahankali ya soma tafiya yana cigaba da kallon zanen yana lumshe idanuwanshi har ya qaraso ya tsaya bayan sultuna nan take ta sake shiga firgici "”mai yasa kika min karya ?tayi shiru ta kasa bashi amsa gabad’aya ilahirin jikinta na sake d’aukar rawa “why did you lie to me ?yayi maganar a tsawace dan girman Allah kayi hakuri “enough !a ina kika samu wannan zanen ko kuma waye ya zana miki shi ?”
“No sir babu wanda ya zana min.”


“Where did you get this desing?” uhmm ammm daman sabuwar staff din da'aka dakatar d'azu mai suna maryama hussein ce ta zana ta barshi akan table a office dinmu."nan take gabansa ya cigaba bugawar da yake fiyye da kaida yana kallon zanen yana jin wani irin shauki a gabad'aya sansar jikinsa da jijiyoyin jikinsa wanda bai ta'ba jin irinsa akan kowace halitta ba sai akanta lumshe tsumammun idanunshi yayi sannan ya motsa lip's dinsa ahankali "daman mutane dakikai irinki ya zasu iya zane kamar haka ? Ke..! ya kirata da haka muryarsa a kausashe ta natsu sosai agabansa ya d'an rage girman idanunshi "ki daina shiga lamarina " ki tsaya amatsayin da kike dashi a wurina wanda ni ban ma d'aukesa da mahimmaci ba kin fahimci abinda nake nufi da hakan ? tai saurin gyad'a masa kai ya d'auke akanta "kenan zumunci dake tsakaninmu "ta sake gyad'a masa kai jikinta na sake d'aukar rawa dan yanayinsa gabdaya ya gama tsoratata" gud oya leave my office .."ai da mugun sauri ta juya ta nufi kofar fita ."


Komawa yayi ya zauna akan kujera qirjinsa na wani irin bugawa da karfin gaske a natse ya dinga kallon zanen ya kasa hakura da kallon zanen wani irin sonta ne Ke taso masa yana sake bin jinin jikinsa "soyayyata qaunata farinciki rayuwata kece komai nawa ya fad'a a fili tare da mikewa ya koma Kan doguwar kujera tare da zanen a hannunsa ya zauna ganin zanen yake tamkar itace a tafin hannunsa kwakkywan fuskarta yake ganin acikin kwayar idanunshi tana masa yawo can Jim kad'an ya mike tsaye yana lumshe idanuwanshi, abun mamaki ji yayi daidai saitin inda zuciyarsa ke makale a qirjinsa yana bugawa da karfi, ya kai hannunsa daidai saitin gurin yana runtse idanunshi "Tabbas yasan lallai idan bai yi wani abu akan lamarinsa da yarinyar nan ba yana daf da kamuwa da mummunar ciwon zuciya ,"amman me zai yi tunda yarinyar nan matar wani ce ?Ahankali ya dinga daga qafafunsa yana tunanin nemawa kansa mafuta "Adam !zuciyarsa ta kira sunansa da karfi "kayi qoqari ka mallaki yarinyar nan ta kowani hali kasa karfinka ka kwaceta kamar yadda ammar ya fad'a maka "kanshi ya girgiza yana cewa ai matar aure ce ,tô shikenan ka dawo daita kusa da kai ganinta kusa da kai zai d'an samar da natsuwa arayuwarka "na koreta da kaina kuma na sake dawo daita da kaina ?ya tambayi kansa "Kai ba zan iya wannan kasadar ba sosai yayi zurfi cikin tunani ya koma mazauninsa yay rewarning d'aukar safe yana kallon tun daga shigowarta har zuwa fitarsu har inda ta mari salim ya tsaya daidai inda suka tsaya acikin office dinsa yana kallo har sanda ta fito zuwa koridoor ta juyo tana kallon office dinsa fuskata kwance da ruwan hawaye ."naunayen ajiyar zuciya ya sauke da karfi lokacin daya kawo inda salim ya sake shan wani marin a hannunta "wani sanyayyen murmushi ne ya bayyana akan fuskarsa ya kai hannu yana shafa sajen fuskarsa yana cigaba da murmushi " daman nasan dole zakiyi rigima princess."


Cike da sanyin jiki ya janyo wayarsa ya kira mataimakiyarsa ringin daya ta d'auko "kizo! ya fad'a ataikaice yana hura hanci ya d'auke idanunshi akan kallon da yake qaramin tv sakamakon knowking din da akai ,umarnin shigowa ya bayar yana sake daukar zanen maryama sectary dinsa ta shigo ta qaraso ta tsaya cike da girmamawa "sir gani !
" wannan zanen maryama né ba ? "Nata ne sir lokacin da kace naje na sallameta na isketa tana zana wannan zanen ina ganin saboda tashin hankali data tsinci kanta ciki yasa ta manta dashi amamn tabbas nata né "lallai wannan yarinyar tana da baiwa tana da kwarewa akan irin ra'ayina amman kuma zuciyata ta koreta "sir ko zamu kirata ne ?ya wani d'ago da sauri ya kalleta a d'age "wai sir saboda cigaban kasuwancinka domin zata baka duk abinda kake so kuma zama daita riba biyu ne garemu ga iya zane ga sanin Kan kasuwanci ."


Shiru kawai yayi yaki kulata duk da abinda ta fada din abinda zuciyarsa da gangar jikinsa suke bukata né amman ya rasa dalilin daya kasa bata umarni."
ta kusan mintuna talatin tsaye a gabansa bai ce mata uhm ba bare umm umm ganin qafafuwanta sun fara sagewa yasa ta bud'e baki cike da tsaro tace "sir ko zan iya wucewa ."?da hannu ya bata dama .
wunin ranar cikin tsananin tunani yayisa duk inda ya motsa yana jinta ajikinsa da zuciyarsa ganinta yau ya qara wutar soyayyarta a cikin zuciyarsa .”kiran d’aya daga cikin yaransa yayi yace akawo masa sigari dan a halin damuwar da yake ciki

Please Login or Register in order to submit comment