Reading INAAYA (Riba Biyu) by queen meenali Chapter 17 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

shimfida zaninta agurin ta kwanta tana fidda numfashi daqyar jikinta na rawar sanyi.

Babu Wanda ya lura da ita sbd suma kowa ta kansa yakeyi Bata wani ba dan kowa agurin abin tausayine.

Yarta na dungule cikin jikinta itama tayi bacci.

Hadiza Batasan inda kanta yakeba sbd kusan suma tayi saida sanyin asuba da kukan yarta ya dawo da ita
Ta bude idanuwanta daqyar tana Neman tashi Amma takasa.

Daga kwancen ta sake rungume jaririyarta ta Ciro nono tasaka Mata a Baki.

Ana Gama sallar asuba duka mabarata da Yan gudun hijira dake gurin suka fara watsewa sbd baa barin Zama gurin da daddare kawai suke zuwa su kwanta da gari ya waye kowa yatafi gurin bara.

Daqyar ta iya daddafawa ta tashi tabar gurin
Tafiya kadan tayi tasamu guri ta zauna sbd bazata iyaba.

Anan gurin ta Rana ta fito ta sameta
Mutanen dake wucewa suka fara Bata sadaka sbd sun dauka Bata takeyi

Dayake tana buqatan taimakon ana bata haka ta ringa karba har Allah yasa ta hada 400 ta tashi daqyar ta siya ruwan zafi gurin me shayi ta Sha na hamsin ta siya wasu na hamsin din ta wankewa 'yarta jiki ta gogeta ta maida Mata kayanta da daudarsu da komai.

Har yamma tana garari a hanya Dan haka tasake komawa gidansu salisu
Hajiyarsa Bata tausayawa mataba tayi Mata korar wulaqanci harda munanan kalamai akan 'yarta Dan haka ta sake komawa Inda ta kwana jiya anan ta Kuma kwanciya.

Washe gari ma haka ta sake zuwa gidansu salisu a karon karshe hajiyarsa tayi Mata mummunan gargadin sake zuwa tareda tabbatar Mata da har abada bazasu karbi shegiyar data haifaba amatsayin 'yar salisu.

Ranar tayi kukan data jima batasamu tayiba sbd maganganun hajiyar dakuma ciwo Mai tsanani daya sakota gaba da 'yarta.

A ranar ko bacci Bata samu tayiba a zaune ta kwana tana kallon yarta wadda da alama sanyi ne yayi mummunan shigarta tana numfashi daqyar.

Gabaki daya duniyar tayi mata zafi,
Qunci da nauyi takeji a zuciyarta Mai tsananin gaske..

Washe gari da safe data samu qarfin jikinta ta tallaba takai jaririyarta wani qaramin asibiti datagani a hanya.

Karon farko ana dubata akace Mata 'yar batada lfy sosai,
Zuciyarta Bata bugawa yanda yakamata hakama sanyi na Neman shigarta.

Gado aka Bata Amma sbd batada ko kudi suka korota ta fito tana bin hanya Ahankali idanuwanta na tsiyayar hawaye.

Yau Bata samu gurin kwanciyaba sbd yan hijirar dasuka qara yawa Dan haka Nesa dasu sosai tasamu ta kwanta.

Hankalinta a tashe yake da Inda ta kwanta din sbd itace a nesa qarshe sosai
Wasu irin sauro da cinnaku suka ringa cizonta tanaji Amma Bata ko iya motsawa sbd zuciyarta data Gama mutuwa.
##MAMUH#




_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

Shedar biya👇
07040727902

MTN card👇
09134848107[11/3, 7:34 PM] +234 808 746 2576: *_39_*
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
Koda garin ya waye daga ita har 'yarta  gabaki daya jikinsu kurajen cizan sauro sun bayyana ajikinsu ita hardana cinnaku dasukai Mata kaman Mai wani ciwon take fuskarta ta kumbura.

Tashi tayi ta nufi Inda suke gyara jikinsu ta gyara ta fito ta miqa hanya goye da 'yar tata.

Kwananta hudu agurin aka rarraba musu kudin sadaka a gurin akan kowa yabar gurin
tana karban nata ta tattara tsumman kayanta ta nufi asibiti takai 'yarta data fara nisa.

Kwantar dasu akai tareda sakasawa 'yar oxygen Wanda ya cinye kudin nata batareda ansamu na siyan sauran maganiba.

Daqyar takai safe cikin tashin hankali Mai tsanani da qaqa nikayi sbd jikin 'yar jaririyarta daya sake gabaki daya.

Rashin Imani da rashin tausayin asibitin haka suka sallameta sbd rashin magani da rashin kudin siyansa ta rungumo 'yarta ta fito tana hada hanya.

Yau kam komai yasake yimata tsananin da takejin mutuwa take buqata Ido rufe.

Uwarta da ubanta da salisu takeson bi Ido rufe sbd ta huta da qunci da baqin cikin duniyar datake ciki.

Kuka aranar tayisa har idanuwanta basa gani sosai sbd kumbura.

Tahau titi rungume da 'yarta wadda take tsoron dubawa ko ta mutu ko tanada sauran Rai.

Mutuwa take Kira take Kuma fata sbd Babu Inda takejin sassauci a wannan rayuwar.

Wani azababben ciwon gaba take fama dashi da ciwo ciki Mai tsanani,
Ta bangare daya qwaqwalwarta tafara kasa daukan tashin hankalin da masifar datake ciki Dan haka wunin ranar attempting kashe kanta kawai takeyi Amma tsananin qaunar datakewa yarta Yana hanata idan ta kalleta.

Tamkar mahaukaciya tafara komawa sbd taba qwaqwalwarta da abin yafara Musamman mummunan infection din daya shigeta sosai sbd rashin kulawa da gurinda ta Haihu.

Tun tana iya controlling kanta akan yanayinta dayake son juyar da qwaqwalwarta haryazo tafara tsoraran yanayinda jaririyarta da itama kusan Rai ne kawai ya rage Mata Zata shiga idan wani Abu ya sameta.

wani masallaci takai 'yar ta ajiye Zata gudu tabarta ko zaa samu Wanda zai tallafeta Amma saita kasa barinta agurin tadauketa tana hawaye tana jujjuyar dakai tabi hanya tana surautai ita kadai.

Batasan ya akaiba sai gata kwatsam takai kanta hanyar Tasha tana tafiya.

Kaduna ne?

Ina zuwa ne?

Kano ne?
Katsina ne?

A kunnuwanta kalmomin ke sauka suna sake yamutsa qwaqwalwarta...

Jikinta rawa yakeyi sosai kanta na sake juyawa sosai.

Ahankali sama sama takejin cikin nutsuwa wani yayi magana a bayanta.

Assalam alaikum,
Malama Zan wuce ko
Zaki Dan matsa.

Waiwayowa tayi da sauri a firgice  tareda kallon Mai maganar.

Saurayine matashi Wanda zatai qani dashi bamai tazaraba sosai.

Sanye yake cikin qananun Kaya Riga ash da wandon jeans black.

Cikin sauri Dan tashar masu mota ya qaraso Yana daka Mata tsawa da cewa"

Dalla matsa ki wuce daga Nan
Kinzo kintare hanya
Idan bara zakiyi ki matsa can.

Yallabai Kace gombe Abuja ne ko?

Kallonsa matashin yayi kafin ya kalli Hadiza data Matsa gefe ta rabe rungume da abinda yake sakaran 'da ne sbd yanda ta rungume zanin cikeda so da shauqi.

Hannu ya saka aljihunsa ya Ciro Dubu daya ya miqa Mata cikeda kulawa batareda yace komaiba.

Hannu ta miqa a hankali ta karba tareda kafesa da Ido tana zuba godiya Kuma takasa tafiya.

Cikin qaguwa ya kalli masu lodin motar yace"

Saura mutum nawane motar tacika hanyar kunsanfa bawani kyaune da itaba.

Yallabai Saura mutum uku motar tacika.

Muje zan biya kudin sauran gurin.

Angama ranka yallabai.

Hadiza dake rakube tanajin haka sai kawai tasamu kanta da biyo bayansa tafara kokarin Shiga motar sbd Jin zaa biya koba komai gwara tashiga duniyar tunda hakane qaddararta.

Kokarin hanata shiga motar direba yafara yana cewa"

Ke tsaya, tsaya
Ina zaki?
Wane gari Zaki?

Abuja" ta furta Kai tsaye muryarta na 'dan rawa.

Ina kudinki na mota?

Waiwayowa tayi ta kalli gefenda matashin yake zaune cikin nutsuwa Yana duba wayar hannunsa.

Ganin tana kallonsa ya fahimci batada kudin motar Dan haka yacewa drivern tahau gurin mutum daya cikin kudin mutum biyu daya biya.

Kasa kallonsa tayi bare tasake Masa godia saima sauke kanta datayi qasa tana sake rungume jaririyarta.

Hanya aka dauka aka fara tafiya Mai nisa kowa yayi tsit a motar Yana aikin gabansa masu bacci Kuma nayi.

Ahankali ahankali idanuwan Hadiza suke cikowa da hawaye tanajin wani irin masifaffen ciwon Kai da zabar ciwon ciki.

'yarta take ji,
Ita take tausayi ba kantaba,
Jin kanta na neman juyewa yasa tafara jin kaman tace a tsaya ta sauka.

Yanayin yanda take sake qanqame babynta yasashi Dan dagowa ya kalleta dakyau yaga tarin tashin hankalin dayake ciki kafin ya maida kallonsa kan babyn cikeda kulawa yace"

Ki Dan sassauta riqon
Kina matse babyn sosai Inaga.

Da sauri kaman qaramar yarinya tayi saurin sassauta riqon tareda bube jaririyar gabaki daya Dan Tasha iska.

Wani irin mamaki da firgici ne ya kamasa ganin babyn wadda alamun rashin lafiya sosai da yin nisa ya bayyana atareda da ita,

Gabaki daya babyn yunwa tagama kamata tako ina.

Dauke kansa yayi daga kallon jaririyar sbd zuciyarsa bazata iya jurewa kallontaba.

Tafiya suka cigaba dayi mai nisa da gudu..
Guri biyu aka tsaya siyan abinci Kuma ya siya Mata yabata sbd lurada akwai yunwa tareda ita.

Duk abinda ya siya Mata ya bata bataciba suna jikinta dunqule sbd bazata iya ciba ita kadai tasan tsananin halin azabar datake ciki.

Daga Nan Basu sake tsayawaba a hanya suka cigaba da zuba gudu a hanya.

Qarfe Tara da mintuna arbain da takwas suka isa birnin tarayya.

Kowa fitowa yayi daga motar yana haramar daukan kayansa ya wuce.

Daga shi sai jakarsa dake rataye a kafadarsa ya fito Yana sake saka Kiran Wanda aka aiko daukansa daga gida.

Ahankali Hadiza ta tako gefensa ta kallesa qafafuwanta na 'dan yin rawa.

Tsalle zuciyarta keyi ga abinda zuciyar tata ke ingizata ga aikatawa.

Jin takeyi zuciyarta ta kwanta data barmasa 'yarta ta gudu sbd yanada tausayi da Jin qai Dan kuwa ita batada tabbacin zatakai labari ayanda takejin azaba da radadi cikin jikinta.

Bazataso wani Abu ya sametaba 'yarta ta gararanta...

Jin mutum kusa dashi yashi juyowa da Dan sauri sbd ya Dan firgita.

Kallonta yakeyi da mamaki sosai batareda yace Mata komaiba.

Ganin kallon dayake Mata yasata kallon 'yarta cikin kokarin daidaita kanta tace"

Nagode sosai Allah yasaka maka da Alkhairi.

Amin" kawai ya iya furtawa Kai tsaye Yana cigaba da wayarsa.

Yana aje wayar drivern ya tura aljihun jeans dinsa drivern gidansu yace Saura kadan ya iso.

Jakarsa ya juyo zai dauka daga qasa gefensa idanuwansa suka sauka kan zani kan jakar tasa.

Da sauri ya waiwaya Babu kowa gefensa da bayansa.

Sake jujjuyawa yayi Yana Raba idon matar data bar Masa zanin.

Jakar ya riqe zai dauka ya watsar da zanin agurin sai zuciyarsa ta kasa Dan haka yakai hannu kawai zai janye zanin yaji alamun Abu aciki

Batareda ya taba tunanin ganin komaiba bare 'dan mutum ya bude zanin aikuwa yayi Ido biyu da babyn.

Zaro Ido yayi da sauri tareda mayarda zanin ya rufe babyn zuciyarsa na rawa.

Da sauri tafara waigawa koina Yana zazzare idon Neman Hadiza.

Daukan babyn yayi dan Dole ya rungume Yana sake jujjuyawa Neman Hadiza.

Fara tashi hankalinsa yayi dayaga dagaske yakasa ganin uwar babyn.

Kokarin komawa yakeyi gurin motar dasuka iso sai kawai ya hangota tana sauri zatabar tashar tana zazzare idon kada ya ganta.

Da sauri ya bita
tana ganinsa ta sake sauri ba Shiri ta tare Mai mashin ta haye suka bar gurin da sauri.

Tashin hankali da tsananin mamakine da firgici yasashi Neman wani mashin din ya hau Amma tuni Hadiza da me mashin dinta suka bace Masa.

Me wannan matar tayi ne?
Me take nufi?
Da gangan tana sane ta bar Masa babyn ta gudu fa.

Innalillahi wainna ilaihrrjiun..

Meyasa zatayi haka?

Dama mahaukaciyace Basu luraba?

Meyesa Zata gudu tabar Masa baby ?
Ina zai Kai babyn to?

Yawo ya ringa Yi dame mashin hankaki tashe Amma sun kasa ganin hadiza ko Mai Kama da ita.

Dukkanin qwaqwalwarsa tsayawa tayi cak shima
Ya tsaya rungume da baby ajikinsa Yana Jin jiri na Neman zubar dashi,

Ya zaiyi da wannan babyn?

Bazai iya komawa tashaba sbd baisan wazai bawa babynba,
Baimasan wazai fara tunkaraba a tasha da babyn sbd Babu ruwan kowa babuma Kuma Wanda zai karba.

Innalillahi wainna ilayhirrajiun" yafara maimaitawa dukkanin jikinsa na saki.

Mai mashin ya fadawa Inda zai kaishi

Wata qaramar police station yaje da babyn suka qi karba sukace yace babban station kawai.

Wata station din yakuma zuwa sukuma sukaqi karban 'yar suna zargin kodai yarda Yar kawai yakeson Yi.

Wata sabuwar masifar yakuma Shiga lokacinda yagama yawo da babyn Babu wata mafita ko daya.

Yanayin babyn kawai ya tabbatar masa da babyn sosai tayi nisa batada lafiya Dan haka ya tattara a nufi wani private asibiti yakaita su duba.

Suna karbanta take sukai dakin jarirai da ita.

Fada suka fara yimasa sosai ganin yanayin datake ciki.

Duk abubuwan zasuyi Mata sunyi suka sakata a kwalba sbd ma sai allah Kam idan Zata rayu.

Tashin hankali sabo yakuma Shiga lokacinda suka zayyano Masa cututtukan dasuke cin babyn.

Biyan komai yayi kafin ya samu ya wuce gida yabar babyn anan sbd akwai masu kula da babies a dakinsu.

Koda ya Isa gidansu mahaifiyarsa na ganinsa cikin tashin hankalin rashin daukan wayarsa da rashin ganinsa da driver yayi har kusan qarfe daya da rabi na daren yayi.

ABDULMAJEED..Ina ka shiga daga isowarka?
Lafiya kuwa?

Ajiyar zuciya ya sauke ahankali idanuwansa na qanqancewa da tashin hankali da damuwa yace"

Hajiya umma kaina kaman zai fashe
Zanshiga nayi sallah tukuna.

Cikeda kulawa tace"

Jeka kayi wanka da sallar ka huta da safe mayi magana.

Juyawa yayi Yana hada hanya ya nufi hanyar dakinsa Yana jin kansa na sake tsananta ciwo.

Zubewa yayi qasa tsakiyar dakin Yana dafe kansa,

Daqyar ya tashi ya qarasa isa ya tube kayansa ya shafa toilet.

Wanka yayi ko zai samu kansa ya Dan sake tareda alwala yafito.

Jallabiya da gajeran wando kawai yasake yayi sallah ya miqe a daddafa ya Isa kan gadonsa ya hau ya kwanta tareda rufe fararen idanuwansa dasuka qanqance sbd tashin hankali da damuwa.
##MAMUH#





_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

Shedar biya👇
07040727902

MTN card👇
09134848107
[11/4, 11:05 AM] +234 813 979 4675: *_40_*
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
Babban tashin hankalinsa shine a yanayinda babyn Nan take ciki bazai iya bada ita ga Yan sandaba kokuma gidan marayu sbd tana cikin mawuyacin hali,

Haka Kuma mahaifiyarsa a yanda ya santa mace ce Mai tsananin kishin 'yayanta Musamman shi ta tsani wani ya rabesa Dan haka yasan bazata taba yarda da abar babynba hannunsu harta danyi wayo tukuna akaita gidan marayun
Idanma baa ga uwar babynba kenan Dan zuciyarsa takasa yarda da uwa Zata iya jefar da 'danta ta gudu duk tsananun rayuwa kuwa..

Washe gari tun kafin kowa ya tashi daga masallaci sallar asuba ya fice zuwa asibiti da mota Yana Jin rashin nutsuwa matuqar ba zuwa yayi yasan halinda babyn ke cikiba.

Banyi baccin nutsuwaba sbd Jin yake babyn mutuwa zatayi a halinda dai yabarta.

Tunaninsa gabaki daya ya karkata akan uwarta ta gudu ne tabar 'yar sbd rashin lafiyar babyn da bazata iya daukaba wannda hakan zallar rashin imani da tausayine.

Koda ya Isa asibitin babyn ba laifi tarta fara daidaituwa sbd Madara da aka kwana ana bata duk Bayan mintuna sbd yunwace da tsananin wahala da sanyi suka Kama babyn sosai.

Fes aka shiryata cikin kayan sanyi masu tsananin taushi farare tas daya siya tun jiya a asibitin aka shiryata.

Har Inda babyn take aka Isa dashi tareda kallonsa likita yace"

Ina uwar babyn take ne?
Tayi sakaci da ganganci sosai akan wannan babyn gskia.

Wani irin sanyi yaji zuciyarsa tayi batareda ya dauke idonsa daga kan babynba dake bacci idanuwanta a rufe murya a sanyaye yace"

Batada uwa.

Dakatawa daga rubutu a file Dr yayi yana dagowa dukkaninsa ya kalli ABDULMAJEED din da mamaki yace"

Ka kuwa gane abinda na tambaya?
Mahaifiyarta nake nufi,
Wadda ta haifeta.

Wani daci yaji yakuma cika ransa ambatar sunan uwar babyn...

Yana kallonta tana kallonsa da 'yarta a hannu tahau mashin ta gudu tabarsa da 'ya jaririya Yana yawo tsakar dare nemanta.

Mezaice gameda wannan uwar?
Mezai fadawa kowa gameda uwa irin wannan aduk Inda ze Kai babyn yasan bazaa taba kaunarta ko kulawa da itaba Kamar uwarta Koda kuwa a halin talauci da qunci ne.

Numfashi ya sauke a boye tareda dagowa ya kalli likitan Kai tsaye yace"

Mahaifiyarta ta rasu.

Numfashi Dr ya sauke tareda tausayawa babyn
Saikuma ya dago ya kalli ABDULMAJEED din dakyau

Dan haihuwa Kam ya Isa ya Haihu tunda matashine Amma Kuma yanayin wayewa da hutun daya gani tattareda dashi yasan zaiyi wuya ace yayi saurin aure bare harda haihuwa
A qiyasa bazai wuce 300level hakaba zuwa 400 a karatun jami'a.

Duk tunanin dr iya lissafinsane kawai Dan haka kai tsaye yace"

But you are the Father right??

Yes" kawai yace Masa Dan bayason tambayar.

Sauran abubuwan da baayi bane jiyan aka qarasa yi qarshe dai bai baro asibitin ba sai qarfe goma Sha daya sbd babyn Kam Saida aka hada da Oxygen.

Daga asibiti report yaje yasaka na Neman uwar babyn Wanda yasan zaiyi wuya a sameta tunda tana sane ta gudu ba wai batane babyn tayiba.

Koda ya dawo gida hankalin hajiya umma yagama tashi hakama duk Inda ranta yake yagama Kai qololuwa gurin baci.

Musamman su Anty juwairiyyah dasuka Gama qara hawar da ita akan zancen ABDULMAJEED yafi daukan mutanen waje da mahimmanci akanta.

Hajiya umma wadda asalin sunanta yake AYSHATOUH mahaifiyace ga ABDULMAJEED da yayunsa Mata guda biyu.

Anty juwairiyyah itace Babba sai Anty safiyyah saikuma shi ABDULMAJEED daya kasance qarami Kuma auta.

Son da mahaifinsu da hajiya umma kewa ABDULMAJEED sosai ya zarta abinda Yan uwansa zasu iya dauka sbd bambamci ne afili.

Mahaifinsu justice Abdullahi Isah babban former justice ne a high Court dake Abuja,

Yayi retire tareda barin qasar yakoma South Africa tsawon shekaru kafin yadawo Nigeria sbd ABDULMAJEED dake shaawar karatu da rayuwarsa a Nigeria.

Dagowarsu da qanqanin lokaci akai auren juwairiyyah da wani babban barrister anan Abuja haihuwarta daya auren ya mutu tadawo gida itakuma anty safiyyah dama Bata samu mijinba aikinta kawai takeyi Dan itama aikin mahaifinsu tabi lawyer ce.

Anty juwairiyyah da Anty safiyyah tun ABDULMAJEED dasu suna qanana Allah ya sanya musu kishinsa Mai tsanani Wanda ta wani fannin yake surkuwa da baqin ciki sbd fifici da banbancin da iyayensu suke nuna musu sosai akansa Musamman hajiya umma.

Abbansu Yana iya kokarinsa gurin yimusu adalci da Basu iya tasu kulawa da kaunar Amma Kuma ko yayane baya iya boye fificin kaunar ABDULMAJEED.

Ita hajiya umma nata shine yafi tabasu sosai sbd Babu tunanin illar hakan take nuna nata fificin.

Sunkoma tamkar wasu 'yayan riqo a hannun iyayensu sbd ABDULMAJEED Wanda hakan ya Gina rashin kauna tsakaninsu da 'dan uwansu.

Bayan rasuwar abbansu Haj umma sosai ta sake qwallafa ranta akan majeed Bataji Bata ganin kowa sai shi,

Su Anty juwairiyyah dasuka fara nuna rashin Jin dadinsu a fili sai kawai ta tsana zamansu a gida kullum cikin musu fadan rashin fidda mijin aure takeyi sun fara tsufa a gida.

Wannan kalaman nata ya tsananta duk wata tsanar dasukaiwa Dan uwansu sunajin kamar shine duk wata matsakarsu da baqin cikinsu na rayuwa.

Haj umma tsananin kaunar datakewa 'danta yasa ta kasance cikin irin iyayen dake tsananin kishin 'yayansu
Kishi Mai tsanani,

Sam batason kowa ya rabi 'danta tafison kulawarsa da komai akanta ita kadai,

Shikuma Allah yayisa Mai tausayi da taimako tareda mutunta mutane Musamman marasa qarfi kusan sune mutanensa Dan yafison yayi mu'amala da wainda zasu ringa qaruwa dashi suna samun taimakonsa dan kawar da tasu matsalar.

Mahaifiyarsa kuma hakan ne yasata ta tsani duk wasu marasa karfin dake taredashi sbd ganin sunason samun kusanci dashi,

Ba abinda yake Basu bane baqin cikinta Dan idan duka zai Basu dukiya batada damuwa ita damuwarta kada kowa ya samu kusanci da 'danta Bayan ita.

A American University of Nigeria yake karatunsa badan Haj umma tasoba tabarsa yake karatu a wani garinba sai Dan hakan mahaifinsa yaso,

Burin mahaifinsane ganin yayi karatunda zai mallaki komai nasa ya Gina kansa da kansa.

Fara karatunsa da yanda yake Dan jimawa baya gida yasa su Anty juwairiyyah suka fara samun shiga gurin Haj umma har suka fara kawo sabani tsakaninta da ABDULMAJEED ta hanyar saka Mata zargi Mai girma akan yafara 'yan Mata hankinsa akansu yake Nan gaba ma mace Zata Raba tsakaninta da 'danta.

Hankalin Haj umma tashi yayi sosai sbd yanda idonta ya rufe akan kaunar da kishin danta yasa komai aka fada Mata yarda takeyi Musamman da ABDULMAJEED din yayi budurwa kullum cikin kiransa take Dan tun Kiran Sumayya din na damunsa harya daina damunsa Dole ya saba.

Soyayyar MAJEED da sumayya ta daga hankalin Haj umma sbd sosai yanzu ta tabbarda mace Zata rabata da Dan ta Dan haka ta rufe Ido tamasa kaca kaca da fada takuma hanasa kula Mata saiya kammala karatun ita Zata Nemo masa matanda zai aura.

Ganin yanda ranta ya baci sosai yasa MAJEED din takaita muamalarsa da sumayya kwata kwata baisake bi takanta.

Amma duk da hakan shikenan Haj umma taringa saka Masa Ido takasa yarda dashi.

Wannan yakawo babban gibin dayasa su Anty juwairiyyah qarasa saka zargi da rashin sukuni a tsaninin Haj umma da majeed kusan yanzu kullum cikin fitinarta da fadanta yake akan Yana hulda da 'yan Mata shiyasa yake jimawa a makaranta kafin yadawo hutu gida.

Wannan ne babban matsalar data fara kunno Kai a tsakaninsa da mahaifiyarsa wadda kwata kwata Bata yarda dashi sosai yanzu.

Su Anty juwairiyyah kuwa yanzu zancensune abin yardarta
Duk abinda suka fada mata hawa takeyi ta zauna daram tayita fada
Abbansu baya raye bare ya ganarda ita gaskiyar rashin kyautawa da tunani akan abinda takeyi.


*******Shigowarsa gidan Kai tsaye Palo yashigo lokacin daga hajiyar sai Anty juwairiyyah da rumanah 'yar anty juwairiyyah suna zaune palon anty juwairiyyah na bubbude kayanta dasuka iso daga Dubai yau na tsadaddun laces da abayas datake saidawa sosai.

Ko kallonsa hajiya bataiba lokacinda ya zauna kusada ita Yana riqo hannunta cikeda kulawa yace"

Umma...

Zare hannunta tayi tana juyowa ta kallesa fuska ba walwala tace"

Meya hadaka da asibiti kake warin asibitin?
Tun asuba fa akace ka fita¿
Ina kaje?

Ajiyar zuciya yayi cikin Hana kansa Jin rashin Jin dadin zancenta sbd takasa daina saka Masa dokar duk Ina yaje da Inda zashi saiya fada Mata bayan Shiba yaro bane da girmansa take Masa irin hakan,
Amma Kuma uwace Babu yanda zaiyi da ita bakuma zai iyajin haushintaba sbd yanda take kaunarsa haka yake tsananin kaunarta shima Dan tafiye Masa komai a rayuwarsa.

Ahankali ya bude Baki zai fada Mata abinda yake faruwa saiya dakata sbd tabbas yasan atake zatace Bata yafe yakoma gurin babynba yabarta can asibitin Susan yanda zasuyi da ita.

Ajiyar zuciya yayi tareda sakin murmushin boye damuwarsa yace"

Dubiya naje wani asibiti a kubwa.

Kasa yarda hajiyan tayi tana kallon fuskarsa dake kokarin Tona asirinsa sbd Bai iya qaryaba baikuma taba yintabama.

Miqewa yayi ya wuce dakinsa yayi wanka ya shirya yakuma sulalewa ya fice gidan batareda sun saniba.

Har dare Bai dawoba sai guraren 10 yadawo ya shige ya kwanta.

Washe garima daqyar ya iya tsayawa yasha ruwan tea kawai ya Kuma ficewa zuwa asibiti.

Kwana biyu kowa gidan ya saka Masa Ido ganin duk yabi ya rikice baya wani cikin nutsuwa gashi sai boye boye yakeyi sbd harga Allah bazai iya barin babynba shima hakama mahaifiyarsa yasan bazata taba Bari su dauki 'yar ba Dan haka hankalinsa ya tashi sosai,

Yayi yawon bincike akan gidan marayu Amma Babu Inda yaji bayanin daya kwantar Masa da hankali Dan haka yasake shiga tsaka Mai wuya.

Ta Bangare Daya ya rikice ya haukace gurin Neman uwar babyn harya gaji Babu labari,

Komai yafara tsananta lalace Masa ne bayanda anty safiyyah ta ringa bin diddiqinsa tagano asibitin dayake zuwa kullum harma da babyn dayake jinya mai amfani da sunansa ABDULMAJEEDs.

Hankali tashe cikeda firgici da mamaki takawo labarin gida Inda suka dunguma sukaje suka ganarwa idonsu Kuma suka tabbatarda babyn dai ta ABDULMAJEED dince ta hanyar bayaninda nurse Tai musu shine mahaifin babyn.

Uwar babyn suka tambaya tace musu ta rasu gun haihuwa.

Dayake suma asibitin sun dade dafara gulmarsa akan kila baasan ya haifi yarinyarba shiyasa yakasa kawo 'yan uwansa su tayasa hidimar babyn.

Gida suka koma hankali tashe suka zayyanewa hajiya komai.

Kasa yarda tayi da Abdul dinta zaiyi abinda suke fada kula Mata da aikata Zina harma da haihuwar 'yar gaban fatiha.

Sunsan zaayi hakan Dan haka suka dauketa suka kwasa zuwa asibitin
Cikin saa kuwa suna zuwa suka taddasa rungumeda babyn an jikinsa cikin tsananin kulawa.

Sallamarsu ake tunanin Yi zuwa gobe dan haka yake Jin sanyi ta wani bangaren Kuma tashin hankalin yanda zaiyi da babyn.
##MAMUH#



_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

Shedar biya👇
07040727902

MTN card👇
09134848107
[11/4, 11:05 AM] +234 813 979 4675: *_41_*
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
Ahankali Haj umma ta qaraso tana kallon babyn hannunsa a Rikice tace"

MAJEED babyn waye wannan?

Da sauri ya dago Yana kallonta dasu anty juwairiyyah.

Miqawa nurse babyn yayi yana kallon hajiyan yace"

Umma muje gida Zan Miki bayani.

Kasa motsawa tayi sbd fargaba da tsoro tace"

Majeed bazan koma gidaba wlh saikamun bayanin Inda kasamo wannan babyn.

Mezan gani majeed?
Mezan ji?
Ta tabbata kenan fasiki ka Zama har kayi nisa haka¿

Innalillahi wainnan ilaihrrjiun" zuciyarsa dake rawa tafara karantowa.

Cikin dacin kalaman mahaifiyar tasa ya dago ya kalleta Jin sunan fasiqi data kirasa dashi.

Zuciyarsa na daci ya bude Baki zaiyi magana anty juwairiyyah ta taresa da munanan kalamai tareda kiransa da sunayen mazinatai kala kala.

Kasa dago kansa yayi cikin tsananin tashin hankali da baqin ciki ya dakatar da Anty juwairiyyah da cewa"

Anty juwairiyyah me kika fada?
Sunayen mazinata fasikai kike kirana,
Idanma nine mahaifin babyn akwai yanda zakuyi ne da qaddarar Allah?...

Ba zato sukaji qarar saukan Marin da hajiya tayi sakar Masa tana kallonsa ciki tsananin bacin Rai da baqin ciki tace"

Wallahi wannan 'yar bazamu taba karbantaba idanma Kaine ubanta,
Idan Kuma wani gurin kasamota kayi gaggawar maida ita..

Kai koma Kaine ka haifeta bazaka karbetaba wuce muje gida.

Jajir idanuwansa sukayi sbd baqin ciki da damuwa,

Su Anty safiyyah kuwa ta Inda suke shiga bayanan suke fitaba take hankalin hajiya yaqarasa tashi hawan jinin datake fama dashi yayi sama take
Ba Shiri suka Jata zuwa gida har ABDULMAJEED din Wanda jikinsa yayi dukkanin sanyi.

Isarsu gida Bai qarar da komaiba sai sabon tashin hankali Dan kuwa bayanai ne daga Yan sanda sukazo anga Hadiza Kuma ta tabbatar musu da 'ya 'yarsace.

Kasa yarda da zancensu yayi saida aka kawo Hadiza wadda gabaki dayanta batada bambamci

Please Login or Register in order to submit comment