Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 5
ta ke yi wa yarinyar, saboda ragowai abincin da te kawo mata. Saboda haka Humaida ki kara yin nazari, wallahi ban dace da ke ba, za ki yi zaben tumun dare, ina tsoro za ki iya fuskantar bakin hukunci a gaban Abbanki". Gabadaya ya gama raunana mata zuciya tausayinshi ta ke ji. "Ina kan bakana Mu'allim, ina son KA AURE NI, zan jure kowane irin kalubale duk hukuncin da zan fuskanta gaba zan ci galaba, please hadin kanka kawai na ke nema". ko?" Ta sake dubanshi a raunane. "Ka sake yin tunani, zan barka a nan 123 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd Ya kada kai kawai ya fito daga motar, ya tsaya yana daga mata hannu, har sai da ta bace wa ganinsa. *** *** *** Tun daga soron gidan ya hangi Umma, yana kokarin sallama ya fasa don jin abin da ta ke fada da da farko ya tsorata, a tunaninsa gamo ta yi, saboda jin da ya yi ita kadai tana magana ba tare da akwai wani ko wata a tare da ita ba. Ya maida hankalinsa sosai gare ta, ya kara lafewa a soron. Tsaye cikin sauya murya. "Kin yi kyau Umman Mu'allim, tamkar ba ke ba, kai me za a yi da talauci". Ta kuma dawo da muryarta na zahiri tana murmushi ta се. "Ai muddin Mu'allim na raye ba zan fidda rai da jin dai ba, dana shi kadai na mallaka, ga shi ya zame mini tamkar da goma. Ya dauke min komai". 124 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd Ta sake sakin murya, ta dauko wata dinkakkiyar atamfa wadda ke ajiye a kan kujera. "Ga wannan ke ma ki sa wa dana albarka" Sai kuma ta yi shiru, ta koma ta zauna ta rafka tagumi, sai ga kwalla. Ta dago kai. "Zan ga wannan rana Mu'allim ina yi maka fatan alheri, Ubangiji ya sa in mutu ina mai farin cikin ka sami sauyin rayuwa". Da sauri Mu'allim ya koma da baya gabadaya zuciyarshi ta gama narkewa, a bayan layinsu ya zauna duk ya gama shiga damuwa. Ashe talaucin nan na damun Ummansa, ashe ita ma na son rayuwa cikin jin dadi? Bai san sanda ya dauko wayarsa daga cikin aljihu ba. Layin Humaida ya shiga lalube, kamar jira ta ke ringin daya ta dauka. "Muddin ba za ki sami matsala da Abbanki ba na zabi ki zama abokiyar 125 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd rayuwata. Ina nufin mu rayu a inwa daya, ki zamo mata a gare ni, amma sharadi sai randa na sami akin yi". Yana ji ta saka karar murna. Da sauri ya cire wayar a kunne yana murmushi. Shin son humaida ya ke da gaske ko kwadayi ne? wani irin farin ciki ya dinga ji ya mike ya nufo gida. Tun daga kofar gida ya dinga jin muryar Malam Musa yana yi wa Umma tsiya. "Ai ke kin ji ba ki iya tattali ba, duk sai kin taru kin kashe kayan, irin wannan in an samo tattalawa a ke in za a yi biki ko 99 wani fitar sai a yi amfani da su". Ta dinga dariya. "Malam tunda na ke da kai ban taba yi maka kwalliya haka ba, ina son ne ka tantance da wa ka ke zaune, na hadu ne ko kuwa?" Ya kada kai. 126 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd "Yau kuruciya ta motsa, to ni ma bara na aje rawanin, ni da na ke zaunc da ke na f kowa sanin haka. Umman Mu'allim kina da kyau ko da a cikin tsumma ne ke ba kya muni, amma da ki ka ce kayan nan ina son ki dinga amfani da shi in ana wani sha'ani ne fa da kanki ki ka sanar da ni irin wulakanci da kyamar da ki ke fuskanta in kuna wani taro, ko rabar inda ki ke ba a yi, yanzu ya ki ke ji ke kanki da ki ka fita jiya cikin kyakkyawar shiga? Ce min fa ki ka yi, mutane da yawa ba su shaida ki ba". Ta ce cikin shagwabа6бiyar murya da ya sa ya dinga jin wani shauki ya dinga jin shi ma wani ne. "Ai na sani amma na fi son na yi maka kwalliya, ka gani ka yaba, ni kuima na sami lada. Yaushe rabonka da ka yi wata mu'amala da ni, amma jiya da. na yi دو kwalliya har...' Gabadaya suka dinga dariya. 127 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd Mu'allim ya yi saurin komawa da baya yana murmushi da jin kunyar abin da ya ji suna cewa. Mu'allim da Humaida sun yi matukar sakewa da juna, yana matukar sonta musamman yanzu da ya gama karantar halayyarta. Tana da son taimako, sam ba ta da kyasjhi, matsalarta kawai sangarta da rashin tarbiyya. Wannan kuma ya faru ne tun daga gidansu, ga wauta sai dai ya kudurce a ransa zai bi da ita cikin dabara ya saisaitata yadda ya ke bukata. Gabadaya ya mance matsalar mahaifinta, kodayake a kullum tana kokarin Kwarara masa gwiwa tare da tabbatar masa da fadin hargagi ya ke nan da lokaci kankani komai zai daidaita. Suna zaune a Mr. big, ice cream suke sha ta dube shi. "Yau na kusan yin kuka, na zaci ba za ka zo ba". 128 ん ni KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd "Ki yi hakuri akwai abin da ya tsare Та се, "Me ke nan?" Ya ce, "kin ga ina tashi kafin na fito sai na dibi kayan Umma da na Abba 99 sa'annan da na kawuna na wanke su "Wai waye kawun nan?" "Kawuna yana cikin gidanmu. "To shi kawun ba shi da 'ya'ya ne?" Ya kada kai, "Ba shi da kowa bai taba yin aure ba, ba shi cikin jinsin da ya kamata ya yi aure, a takaice ba shi da lafiya, ba cin haka ga shi ba shi da hankali. Kafin ya hadu da lalurar ba shi da burin da ya wuce ya ga na zamo wani. Ya yi mini irin abin da uba na gari ke wa 'ya'yansa. Ina son Kawuna fiye da kaina, zan iya yin komai domin shi, zan iya sadaukar da rayuwata don na ga farin cikinsa" Ta ajiye ice cream din hannunta.rg "Ya ya za a yi na san kawunka? Ina so na ganshi". 129 KA AURE NI!-I Bilkisu H.Muhd Ya dan yi jum, ta kafe shi da ido cikin nazarinsa. Ta sanyaya murya. "Ko ba ka so?" Ya ce, "Me zai hana?" "O. K, me zai hana ba za mu je yanzu ba?" "Ki bari in sanar a gida ko kin ga in muka je haka ban yi musu adalci ba". "Na fahince ka, in kana ganin haka ya fi shi ke nan, amma ina son ka dauke wa kanka wannan wahalar gidan, kai namiji ne irin wannan ayyukan ba su kamace ka ba, in ka amince min zan kawo wadda za ta dinga taya Ummanka aiki". "Ke ba kya taya Ummanki aiki a gida?" Ta kalle shi a yatsine. "Tunda na taso ban taso cikin wahala ba, ban san ma yadda zan sarrafa hannuna gurin yin irin wadannan ayyukan ba. Kafin na tashi daga bacci an kai mini ruwan wanka. Kafin na fito an gyaran daki an 130 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd dauko kayan da zan sa an ajiye mini a gado, da na fito za a dinga bin duk inda na taka ana tsanewa da tawul. Takalmi ma saka mini a ke yi in har mai madauri ne". Ya kallo ta cikin murmushi da son ya zolaye ta, ya nuna ta da yatsa. "To wannan kwalliyar wa ya ke miki?" "Akwai mai zuwa ta yi min". Zumbur ya ga ta mike cikin duba agogon da ke daure a tsintsiyar hannunta. Ta koma ta dafe kai, binta ya ke da kallo kamar wanda ya ga sabuwar halitta. "Lokacin baccina ya yi, kaina ya soma sara mini, na san yanzu Dad zai kira ya ji na akwanta, ni kuma ba zan yi karya ba zan gaya masa muna tare, in ya ji ba zai ji dadi ba, tunda ya shimfida min sharadi kada ka damu gaf lokacin ya ke da cika... taso mu tafi". Kokarin riko hannunsa ta ke, ya basar a inda ta saba ajiye shi ta tsaya ba tare da ya 131 KA AURE NI!-I Bilkisu H.Muhd san sun karaso ba, sharadin Dad da ta ce ya gindaya mata ya ke tunani. *** *** *** "Ke ban da abinki Hajara, ai kin san yaron nan ba zai yi zaben tumun dare ba..." Ta katse shi, "Malam don ba ka ganta ba ne, in dai wannan yarinyar ya ke fada ba zan ba shi goyon baya ba". "Ko ma ya ta ke shi ya gani ya ce yana so, in ba za ki fadi alheri ba ki yi shiru". Ya maida hankalinsa ga Mu'allim. "Ni dai abin da na ke so da kai, kada ka ce za ka tunkari aure yanzu, ka bari sai ka sami abin yi, yau ka sami abin yi gobe ka zo mini da maganar aure zan daura maka aure". Ya dubi Hajara, ta cika tamkar ta fashe. "Mu'allim ka ga Umman taka ko?" 132 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd "Abba abin da Umma ta ke zargi sam ba haka ba ne, kurum dai yarinyar 'yar masu iko ce". Da sauri ta dube shi. "Oh na fahinta, auren kwadayi ka ke son yi wanda Karshensa nadama ce". "Yo ke Hajara ban da abinki dana jarumi ne ba zubin irin wadancan ne da shi ba, babu laifi idan ya sami abin yi ta dalilinta wanda na ke yi mishi fata, amma dai ya kwanta sai an samo za a ba shi shi ne ban laminta ba. Tashi ka je, Allah ya yi maka albarka, in ka tashi sai ka kawo ta ta duba Kawun naka babu laifi". Ya mike yana shafa keya, gabadaya ji ya ke Abban nasa na kwarara masa gwiwa a akan Humaida. Ya bar su Abba na kokarin kara fahintar da Umma a kan dagewar da ta yi, da alama ta soma fahintarsa. *** *** *** 130 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd Yana zaune jiran isowarta ya ke yi, sai dai ya rasa abin da ya sa gabansa ke faduwa, sam tsintar kansa ya yi da rashin farin ciki. Zuwanta yana jin wani kunci da tsoro a can karkashin zuciyarsa, sai dai yana ganin hakan na da nasaba da yanayin da za ta ga gidansu, yana jin kamar fargabar hakan ne ya sa ya ke jin haka. To in haka ne bai kamata ya ji tsoro ba tunda ta san waye shi. Hon ta sakar masa, amma da alamun bai jì ta ba, shin tunanin me ya ke yi? Ta kashe motar kurum tana kare masa kallo, gabadaya ya sauya daga yadda ta soma saninsa. Ya yi kyau har ya gaji, sanye ya ke da riga shirt ja da bakin wando. A karo na biyu ta kara sakin wani mahaukacin hon. Da sauri ya mike ya nufi gurinta yana murmushi, ya bude mata motar ta fito. 134 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd ki". "Amincin Allah ya tabbata a gare "Kai ma haka". Suka doshi kofar gidan gabansa ya tsananta faduwa, daf da za su shiga gidan malam Musa ya fito jin karar hon din. Idanunsa suka hadu da na Humaida, murmushi bayyane a fuskarta. "Humaida ga Abbana”. Ya fada yana kallon Malam Musa. Ga Ummakinsa lokaci guda ya ga yanayinsa ya sauya, jikinsa na wani irin tsuma, ya fidda hannu da kyar yana nuna ta da yatsa. "Wace ce wannan?" "Ita... it... it... itta се". Ya fada cikin rawar murya. "Na ce ita ce wa?" Ya tambaya cikin muryar tsawa. "Wacca na gaya maka". "Kana nufin wannan се?" 135 KA AURE NH-1 Bilkisu H.Mund Ita kanta Humaisa ta gama firgita da yanayinsa, tsintar kanta ta yi da komawa bayan Mu'allim. Yana huci ya ce. "Ban taba tsanarka ba irin yau, wallahi na yi da na sanin haihuwarka, da na san za ka hadu da wannan (ya nuna ta da yatsa) da na kashe ka da hannuna kafin zuwan wannan ranar. Kaico da kai Yusufu" Ya dafe kirji yana tari, da gudu Mu'allim ya Karasa gare shi zai rike shi, ya dakatar da shi. "Kada ka taba ni!" Ya fada yana сі gaba da tari. Ya dubi Humaida ya koma ya dubi Abbansa. "Abba ka gaya min, na shiga rudu". Ya sake kallon Humaida da ido fal kwalla. "Humaida, Abbana a ina ki ka sanshi?" 136 KA AURE NI!-1 Muryarta na rawa ta ce. Bilkisu H.Muhd "Wallahi ban sanshi ba, ban taba ganinsa ba, sharri zai yi mini”. Ya dakatar da ita cikin daga murya. "Ke! Abbana ne zai yi miki sharri? Yau kin kara tabbatar mini da cewar ke mahaukaciya ce, bacin haka zan koma yi miki kallon dabba" Ta yi shiru tana dubansa tana son tuna inda ta sanshi, sai dai iya hangenta ba ta tuno ba. "Da gaske na ke yi, me ya sa ba za ka yarda da ni ba?" Juyawa Malam Musa ya yi zai shiga gida, ya yanke jiki ya fadi. Da gudu ya yi kansa yana kokarin daga shi, cikin yi wa Humaida tsawa. "Ki fita ki tafi na сe". Da gudu ta nufi inda ta yi fakin ta shiga ta ja motar da karfi a tsorace. Ya kallo motar yadda ta ke sheka gudu ya 137 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd daga hankalinsa, ya dawo da nutsuwarsa ga Abbansa ya rike shi suka shige ciki. *** *** *** Malam Musa zaune a kan darduma, Hajara na zaune a gefensa, tunda Mu'allim ya kawo karfi ba shi da burin da ya wuce ya ga ya faranta mana, na yi imanin tunda ka nuna ba ka sonsa da wannan na tabbata ya barta ke nan". Ya kada kai cikin raunanniyar murya. "Ban ji dadi ba, boyayyar da yaron nan ke yi mini ya sa na ke burin kullum in ya zo mini da abu in ba shi goyon baya a kai, zan iya amincewa da shi a kan duk abin da ya zo mini da shi, amma ban da wannan yarinyar, dole ne ya barta muddin ya amince ni ne ubansa". Hajara ta sanyaya murya. 138 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd "Abin ba zai kai ga haka ba, ka nutsar da zuciyarka, Mu'allim ba zai ba ka kunya ba, ni na sani. Amma Malam tun farko sai da na gaya maka cewar yahrinjyar karuwa ce ba ka yi bincike ba kawai ka ci gaba da kwarara masa gwiwa". Ya ce, "Wallahi yadda na ke son faranta wa yarona rai ko da karuwar ya dauko muddin yana sonta zan ba shi goyon baya, saboda yin hakan tamkar jihadi ne zai zamo ta dalilinsa ta shiryu, shi ya sa ki ka ga wancan karon ma ban ba ki goyon baya ba". "To arama ka sa ni a duhu, me ye dalilinka na son ya rabu da ita? Ko ban tambaya ba Mu'allim zai tambaye ka, in kuma bai ji kwakkwarar hujja ba, zai iya kafewa". Ya yi murmushi, "Zan gani kuwa ai ni ne da shi ba shi ne da ni ba, in har ni ne 139 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd na haife shi dole ya yi yadda na ke so, ba 39 lallai ne sai na gaya masa dalili ba”. Ya mike ya fita kofar gida, bai dade da zama ba sai ga Mu'allim, ya yi masa sannu zai shiga gida ya kira shi. Ya durkusa cikin girUmmawa. "Mu'allim zan shaida maka, ina so ka sani daga yau na tsinke duk wata alakar da ke tsakaninka da wannan yarinyar". biyu. Da sauri ya dube shi, suka yi ido "Eh haka na ke nufi”. Ya koma ya maida kai kasa yana son yin magana, sai dai fuskar Malam ya kasa barinsa saboda babu annuri ko guda daya a kan fuskar. Ya mike jiki a sanyaye. keya. "Na ga kamar da magana a bakinka". Ya dawo ya durkusa yana sosa "Kai na ke sauraro". Cikin rawar murya ya се. 140 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd "Ka ce in rabu da ita, kuma kai ne ka Kara karfafa min gwiwa a kanta... "Yanzu kuma na janye, janyewa ta har abada". Ya ce da Mu'allim kai tsaye. "Amma Abba mai ta yi maka, a ina ka santa?" Ya auna masa wani mugun kallo, cike da takaici wai yau shi ne zai kafa wa dan da ya haifa umarni ya ketare. Tabdijan! Lallai da sauran rigima. Mu tara a littafi na biyu, don jin yadda za ta kasance, tare suke da na dayan. Mai kaunarku. Bilkisu H. Muhd. (By Force) 141 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd DANDANO DAGA 'YAR BABBAN GIDA Ya kutsa kai dakin da yake jiyo kukanta, ya hango ta a takure a sakon gado lamarin ya yi matukar taba masa zuciya musamman da ya yi mata ganin a hargitse babu gyara. Kwalliyar nan tata mai jan ra'ayinsa yau kamar ba a taba yin irinta ba a jikin Sa'adah ba, tun kayan barci ne na daren jiya. Fuskar nan ta kode ta jeme, idanuwan sun yi luhu-luhu, ga ruwan hawaye da ya y kaca-kaca a fuskarta, gabadaya yanayinta ya sauya sai ya ke ganinta kamar ba Sa'adan tashi ba 'yar kwalisa mai iya daukar kwalliya da iya zuba dressing irin na daukar hankali ba. Tausayinta mai yawa ya tsirga masa, tabbas an shiga babin da zai iya salwantar da rayuwarta, ta sha fada masa. "Wallahi Mahmood gara na mutu kafin na ga ranar da za ka yi min kishiya". "To wai wa ya ja? Ita ce silar komai". Ya zauna gefenta cikin tattausan lafazi ya ke magana a gare ta. "Me ya yi zafi har irin. haka Sa'adah? Ashe ke din ba za ki daure ki zamo jaruma a cikin mata ba? Yanzu saboda Allah irin wannan da ki ke yi me sunansa? Wa zai dube ki a yau ya fahinci ke ce Sa'adahr nan ma'abociyar ado da kyalkyali? Dube ki yadda ki ka mayar da kanki dalilin wani abu 142 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd da bai taka kara ya karya ba har ki ke neman sukurkurta kanki, ki ke son ki zamo abar kallo da nuni a wajen sauran mata...?" Ya sa hannu ya ke jawo kanta da ta tura tsakankanin cinyoyinta, ya ke fada mata. "Ki sa hakuri da juriya a ranki, ki zamo jaruma sai ki ringa rayuwa shi wannan din wani lamari ne mai girma da ya zo gare ni daga Ubangiji, ba wai niyyar kaina ba ne, ko nufin muzanei a gare ki, a'a yi wa lamarin kallon shirin Allah ne. In ba Allah ba Sa'adah shirin ya zo daga gare Shi ya ni da na ke da kamar ke zan jawo wata cikin rayuwarmu? Haba! Haba! Ai wannan da gani kin san ba yina ba ne, yin Allah ne. saboda haka maza share hawayenki, ki zamo mai hamdala a gare Shi, don ba mu sani ba kila wata rahamar ce ya yi shirin yenta a gare mu, shi ya sa ya aiko da hakan a gare mu". Ya sa hannu yana share mata hawayen. Tа ture hannayensa daga jikinta, ta ke magana a gare shi da muryarta da ta dushe don azabar kuka. "Babu wani furucinka da zai yi tasiri a gare ni, domin na riga na gama fahintar lamarinka game da ni, nid in na zamo abin ki a gare ka..." Da sauri ya katse ta. "Wa ya fada miki ke kin zamo abin ki a gare ni?" 143 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd "Kai ka tabbatar min da haka tunda har za ka iya raba soyayyata zuwa ga wani 6angaren". Ya fada mata cikin lallami. "Ki dauki aurena kaddara Sa'adah, ba wai wani batu da ke fita a bakinki ba". Ta juya kafada da girgiza kai ruwan hawayen na ci gaba da kwaranya daga idanunta, ta ce. "Babu batun Kaddara a maganar kishiya, ka ci zarafina irin wannan ks zauna a gabana kana fada min wai Kaddara? Ina! Wannan sam ba kaddara ba ce, son zuciya ne kawaj da son muzanci a gare ni". Ya ce, "To idan ma ba kaddarar ba ce Sa'ada wa ya ha? Kar ki mance fa komai ya faru ke ce sanadi, da a ce kina tare da ni a kan kowane ra'ay nawa kina biyayya a gare ni, da yin rayuwa kyakkyawa irin ta sauran ma'aurata ta ya za a yi irin wannan ya faru? Amma ki yi duba ki ga mene ne na Batanci bai faru daga gare ki zuwa gare n da tallafin mabaifnki ba..." Ta katse shi da alama ranta ya kara hauhawa a Baci. "Na yi maka alkawarin gyara halayena da binka sau da kafa, da yi maka duk yadda ka ke bukata, amma kai ma ka yi min alkawarin bayar da saki aa gare ta tun kafin ta kai ga shigowa cikin gidan nan". Murjanatu Muhammd Dan-Guru 144 1 du, OKSHOP Bayan Sabon Gadar Gari, 194, 0809985IRIO Kano nMarubuciyar FI SONTA? UNACE СROPASANKAR WABAMBANCI TARAIRAYA MATSALAR KAUNA JINI-BIYU DACEWA ISAKE RASHIN RABO RAKIN KAZAEI KELAR SABO BESTAI KUSKURE ZAFIN HAWAYENA ZUMA DA MADACI KA AURE NI HARAFI PUBLISHERS 08025433394 Cover graphics: Anka-Graphics 19 An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 5 of 5