Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 5
lakabi da ta gaban mota. Matan da za ka nuna su a cikin ko da Larabawa ne, irin matar da duk lokacin da ka ke tare da ita za ka ji kanlka ya kumbura, kanka ya fasu, za ka ji kai wani ne. To in haka ne me ya sa ba zan amshi tayinta ba? Saboda ta fi karfinka". Zuciyarsa ta ba shi amsa, ya yi saurin bude ido, wani irin sonta mai zafi ya dinga ratsa ko ina na jikinsa ya dinga murmushi sai dai a can karkashin zuciyarsa tsoro ya mamaye shi abin da ya ji kirjinsa na yi ba abu ne mai sauki ba, ya ya zai yi? Tsintar kansa ya yi da wani azababben son jin muryarta. Ya dauko wayarsa ya shiga laluben layinta. Ya kafe lambobin nata da ido yana ganin fuskarta a kan wayar ya soma kiranta, kai ya kanga ringin ya yi saurin katsewa, to in ya kira ta me zai ce da ita? Ya maida wayar ya ajiye a wannan dare bai sami isasshen bacci ba don baccin ma da 92 KA AURE NH-1 Bilkisu H.Muhd ya samo duk cike ya ke da mafarkinta barkatai. Karfe takwas da rabi yana zaune a kan darduma, lazimi ya ke yi yau kam ko yunwa bai ji, addu'a ya ke yi Allah ya kawo dalilin da zai ga Humaida. Umma ta turo kofa rike da langa a hannu, ya yi saurin mikewa ya karbe ta. Ba laifi yau ta dan sassauta fuska, ya karbi kwanon ya ajiye ya durkusa. "Umma kin tashi lafiya?" Ta ce., "Lafiya kalau Mu'allim. Ga dumame nan ka yi maleji". "Umma kada ki damu ke ki ci, ni in na fita waje zan samo". "A'a mu'allim a sa a baka ya fi a rataya, ni ma na dan ci”. "To Umma Kawu fa?" "Shi ma nasa na nan in ka gama sai ka ララ je ka kai masa "Umma na gode" 93 KA AURE NH-1 Bilkisu H.Muhd Ta dan yi murmushi, "Allah ya yi maka albarka". Ya ce, "Amin". Ta fice. Ya bude kwanon, tuwo ne na dawa, wanda bai wuce dan shekara biyu ba ba zai ishe shi ba, ya kada kai kawai ya soma ci. Karfe hudu majalissarsu ta cika kowa na kaawo matsalar gidansa, Mu'allim ya yi shiru, gabadaya hankalinsa bai gare su, shi kansa ba zai ce ga tunanin abin da ya ke ba. wyarsa ta dau ruri, ya zaro daga cikin aljihunsa, sunan Humaida ya gani ya sauke ajiyar zuciya. Wani irin sanyi ya tsarga masa, ya yi saurin matsawa a gurin, ya latsa kore. "Abokina". Muryarta ta ratsa kunnuwansa. Ya ce, "Kin wuni lafiya?" "Wallahi lafiya kalau. Ina gayyatarka plcase za ka yi mini rakiya". "Me zai hana". 94 KA AURE NI!-I Bilkisu H.Muhd "Zan iya zuwa na dauke ka?" Ya ce, "A'a, gaya mini inda zan same ki". Tana tukain motar cikin nishadi, lokaci-lokaci ya kan ji gabansa na faduwa, haka kuma ya dinga satar kallonta wannan karon ido biyu suka yi, ya yi murmushi. Kamar ta kai hannu ta shafa fuskarsa, ta dai basar. A wani kayataccen restaurant ta yi fakin, ta sanya an kawo musu kayan ciyeciye da lashe-lashe kala-kala. Sakin jilki ta yi sosai ta take cikinta yayin da shi ya dinga ci kamar an sa shi dole, gabadaya jinsa ya ke yi a takure. Ta lura da haka, duk da tana takalarsa da hira hakan bai sa ya sake ba, tunani ya ke yi tunanin mahaifiyarsa ta ya ya zai bude ciki yana kwasar irin wannan garar alhalin ga Mamansa can cikin yunwa da wahala. "Mu'allim na ga gurin nan bai yi maka ba, bari mu wuce ko?" 95 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd Sai da ta biya kudin suka bar gurin. Wannan karon hotel ta ja shi, inda ta dinga dubansa tana tilo masa kayan da za su dace da fatarsa, sai da ta diba masa saiti ashirin sannan ta yi 6angaren takalma, naan ma ta dinga diba tana zubawa a Kwando ban da su turaruka, agoguna da sauran kayan kyale-kyale tamkar ba ta san ciwon kudin ba. Sai bayan sallar magriba suka yo gida, a dan nesa da gidansu ta yi fakin, ya fito zai tafi. "Ni zan yi maka dakon". Ta fada cikin sigar zolaya. Ya ce, "Na me fa?" Ta ce, "Kayanka mana". Kawai sakin baki ya yi yana kallonta, ga wani irin nauyinta da ya dinga ji, jin komai ya ke yi tamkar a mafarki. Ta yi tattaki ta karasa gare shi. "Abokina kalle ni”. 96 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd Ya dan dago idanunsa yana murmushi. "Me ya sa za ka yi mini haka, duk aboki na gari kokarinsa ta ya ya zai faranta wa abokinsa rai, kai abokina ne, zan iya yin komai do.min farin cikinka". Zai sake yin magana ta katse shi. "Don Allah ka yi shiru, ina neman i zan karasa da kai kofar gidanku, boda kayan za su yi maka nauyi". Kada kai kawai ya yi, suka koma motar. A cikin wata dauya kacal shakuwa. mai karfi ta shiga tsakaninsu, inda gabadaya tunanin Mu'allim ya sauya, ya amince zai iya rayuwa da ita, ya yarda da son da ya ke yi mata, sai dai abin da ya fi daure masa kai, Humaida ba ta taba cewa tana sonsa ba, sai dai ta ce ya aure ta. Haka ta 6angaren abokansa irin su Abdul da Yusuf sun shisshige inda har Humaida ta kan yi musu hidima, sha'awar 97 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd yadda rayuwar abokin nasu ya sauya suke yi, kullum za ka ganshi tsaf kamar dan wani mai iko, sai dai ba ko anini a aljihunsa. Za ta yi masa komai, sai dai naira biyar bai taba hada su ba, in ka ga Mu'allim ya goge jikinsa ya murje har wata 'yar kiba ya yi, to kullum za ta zo ta dauke shi su tafi yawo ba za su dawo ba sai bayan magriba. Haka rayuwarsa ta ci gaba da gudana. *** *** *** "Ya kin an babyna, har yanzu fushi a ke da Dad?" A shagwabe ta zauna a gefensa. "Yau dai bari na faranta wa Baby, yau وو babu inda zani ki yi masa magana ya zo". Annuri ya sauka a fuskarta, ta mike da gudunta. "Dad, ba ni takaitaccen lokaci". Ta yi cikin dakinta ta dau waya tana laluben layinsa. 98 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd - Daga can 6angaren Mu'allim wayarsa na rike a hannun Yusuf yana jujjuya shi da ya ba shi. "In ni ne da wannan dokar da shi zan yi in ja jari". Mu'allim zai yi magana wayar ta soma ruri, da sauri ya mika masa a dokance ya ke mata sallama. Yana jin dariyarta, bai taßa jinta cikin irin wannan farin cikin ba. "Ya aka yi?" Ta ce, "Yau zza ka zo gidanmu, yau Dad dina na son ganinka, saboda kai musamman ya ki fita ofis". Ras gabansa ya fadi, wani irin gumi ya gama jike shi. "Ki yi hakuri, ba zan iya ba". "Me ya sa?" Ta tambaya. Ya ce, "Saboda zuwana ba. shi da fa'ida". "Manzonmu (S.A.W) ya ce, ka amsa gayyata idan an gayyace ka". Ya yi shiru yana nazarin maganarta. 99 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd "Comon, me ka ke tunani ne?" "Ki yi hakuri..." Ya katse wayar. Yusuf ya dinga tambayarsa cikin damuwa ya ke shaida masa. "Ah haba be a man mana, ya za ka kwafsa mana?" "Ba haka ba ne ina ji a jikina kamar wani abu zai iya faruwa". "Yarinyar na sonka inda akwai matsala ba za ta nemi ka je ba". "Haka ne Yusuf bari in neme ta". Ya bi sahunta wayar ta dinga ringin tamkar ba za ta dauka ba, gaf ta ke da katsewa sannan ta daga. "Hello". Babu amsa. "Humaida kina kan layi?" Ba ta yi magana ba sai shesshekar kukanta da ya dinga ji, dulk ya kidime. "Humaida ki yi mini magana, me ya sa ki kukа?" Nan ma ba ta ce komai ba. 100 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muld "Please, am sorry ni a wa da zan kasa amsa gayyatarki? Na yi haka ne kurum don na gwada ki, yanzu ki turo mini da adireshi an zo". Cikin muryar kuka ta ce. "Na ce da kai, Dad ya ki fita ne saboda kai, abu mafi muhimmanci a gurinsa shi ne ofis, amma ya ajiye saboda ya ganka..." "Ya isa haka Humaida, na ce da ke zan zo. Tunda ya sauka a .motą yanayin unguwar ya tsorata shi, babu mai karamin karfi unguwa ce na manyan kusoshi wadanda suka ci suka tada kai, lambobin gidan ya dinga bi da kallo. Gidan nasu shi ne mafi tsari da girma a duk cikin unguwar. Tuni jikinsa ya yi sanyi, lallai ya yi ganganci, ya soma shakku a kan soyayyar Humaida. Ya fi yarda da akwai wata manufa a ranta, shawara ya ke yi na ya koma ya cire 10 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd ta a rayuwarsa duk da ya san mawuyacin abu ne ya iya mancewa da ita. "Saurayi, ko kai ne bakon Humaida?" Muryar maigadi ya katse masa tunani, ya kasa magana sai kada kai da ya yi. "Bismillah shigo ciki". Duk lokacin da ya cire kafa sai gabansa ya yi wani irin bugawa. A sace ya dinga bin ko'ina na gidan da kallo ya zama tamkar wani dan kauye, a'can nesa ya hango ta sanye cikin doguwar riga ta shadda ya sha adon surfa ni. Da sauri ta nufo shi farin ciki ya kasa bokyuwa, ya dinga yake a hankali ta sakale hannunta cikin nasa tana jansa. "Humaida ke ce kuwa?" Cikin wani salo ta yi far da idanunta. "Na sauya maka ne?" Ta fada tana duban kanta. "Na lura wannan shigar bakona ya fi bukata". 102 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd Ya dan yi murmushi sai dai har lokacin gabansa bai daina bugawa ba, ita kanta ta lura da yanayinsa, ta dai basar ne kurum. Sai da suka shige faluna har guda uku inda suka kutsa kai a babban falon. Tsarin gidan kadai zai tabbatar da gidan 'yan boko ne, yana kishingide a doguwar kujera rike da jarida a hannu. Sanye ya ke da singileti sai gajeren wando, gefensa computer ce. Daga nesa ya gama kare wa Mu'allim kallo tsaf ba tare da an fahinci abin da ya ke kallo ba, lokaci guda ya kawar da kai. "Wannan karon ba zan biye wa son ranta ba".ya fada a zuciyarsa. zama. "Baby kun Karaso?" Ya dubi Mu'allim ya nuna masa gurin "Bismillah". Gabadaya Mu'allim ya gama karaya, tun daga kan irin duban rainin da ya samu, dan dosana duwawu ya yi a gefe, ga wani 103 KA AURE NI-I N!-1 Bilkisu H.Muhd gumi da ya sauko masa cikin sakanni. Tabbas ya yi amfani da wannan Karin maganar da Hausawa ke fadin, labarin zuciya a tambayi fuska. Ya sani ya ji a jikinsa arziki ba zai biyo baya ba. yanayinsa ya nuna ba mutum ne mai mutunci ba, fuskar nan babu haske. Ya mike zaune ya ajiye jaridar tare da rufe computer ya dauko kofi ya zuki lemo tsawon minti daya ya ajiye kofin. Ita kam Humaida ta kalli uban ta dubi Mu'allim, akwai shakku a tare da ita. Daf ya koma tamkar ba shi ba, Dad mai sakat mata fuska da barkwanci duk sanda suke tare, amma yanzu ga yadda ya daure fuska kamar wanda aka yo masa aiken mutuwar mahaillyarsa. Ba ta gama shan mamaki ba sai da ta ga ya sake daukar jarida da alama ya mance da su. Ta yi gyaran murya. Ya kallo ta, yanayinta ya yi matukar kular d shi, damuwa ce kwaro-kwaro ya gani kwance a fuskarta. 104 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd Shi kam Mu'allim ya kai kololuwa gurin kuluwa gabadaya haushin kansa ya ke ji, wane karamba ni ne ya kawo shi gidan, ya aka yi ta shammace shi ya biye mata? "Mu'allim sunanka ko?" Ya katse musu tunani, a hankali ya kada kai. "Humaida ta zo mini da maganarka, sai dai yadda na zace ka ba haka na ganka ba". Cikin kafe shi da ido Injiniya ya ke maganar, haka ne ya tilasta wa Mu'allim sunkuyar da kai. Ya ci gaba da magana. "Saiurayi, anya kuwa ba ka so kanka da yawa ba? Me ya sa dan Adam ke son kai kansa inda matsayina bai kai ba? shin ba ka yi la'akari da waye kai ba?" Yana yi masa wani kaskantaccen kallo ya ke maganar. "Amma duk da haka bari na yi maka wata 'yar tambaya". 103 KA AURE NII-1 Bilkisu H.Muhd Ya yi shiru tsawon mintina biyu, sannan ya dora da fadin. "Waye kai? Me ka yaka da har ka iya tarar aradu da ka? Shin a garin nan waye ubanka? Gaya mini sunansa na ji". "Dad!" Humaida ta kira shi da karfi. Ya dakatar da ita da hannu ya sake maida dubansa ga Mu'allim. "Aikin me ka ke yi, ko kuma na ce me ka ke karanta a wane mataki ka ke a karatunka? Kodayake idan na tambaye ka ka yi digiri kamar takardar sakandire na tambaya, digiri na biyu ka ke yi ko na hudu? A zafafe Mu'allim ya mike yana huci. "Ka jita mo in na tambayo sannan na dawo na ba ka amsa". Cikin muryar tashin hankali Humaida ta fuskanci Dad din nata ta ce. "Wadannan tambayoyin sun yi rashin ma'ana, sun yi yawa haka". Mu'allim ko har ya fice a falon. 106 I KA AURE NI!-I Bilkisu H.Muhd Da gudu ta rufa masa baya tana kwala masa kira, ko bi ta kanta bai yi ba bai ma san inda ya ke cilla kafafunsa ba saboda tsananin 6acin rai da tozarcin da mahaifin Humaida ya yi masa. Komawa ta yi ciki da gudu tana faman mita, Dad na kiranta amm ko kallon inda ya ke ba ta yi ba, dakia ta shige ta kulle kanta. Me ke son faruwa da rayuwarsa? Komai ya jagule masa, me ya sa zuciyarsa ke yi masa zafi? A tunaninsa daga yau zai tsinke duk wata alaka da ke tsakaninsa da Humaida, amma zuciyarsa ya kasa laminta, jinta ya ke ui tamkar ta zamo wani sashi na rayuwarsa. Ji ya ke yi tamkar ita се numfashinsa. Humaida ta cuce shi, ya ya zai yi, wannan wace irin masifa ce? Me ya sa zuciyarsa ba ta yi la'akari da abin da ya dace da ita ba? Zuwa yanzu ya kamata a ce ya sanya tsanarta a zuciyarsa, to amma yanzu ne zuciyarsa ta ke kokarin amsarta, me ya sa? 107 4 slaw KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd Ya kasa tantance hudubar su Yusuf ne geke dawainiya da shi inda ya ke shaida masa bdd kwadaita masa yadda soyayyar Humaida ai' daukaka darajarsa, Ubangiji ya kan tsaro aarzikin bawa ta ko wacce irin hanya, shigowarta rayuwarka alheri ne, yanzu ne ya kamata ka sake da itą ka gigitata da soyayyarka, na san za ka iya. Yin haka-zai sanya rayuwarka ta sauya, in wannan hanya ta kubuce maka ba ka da wata hanya, ta dalilinta za ka mallaki dukkan abubuwan da ka ke muradi, burinka zai cika na son kyautata wa iyayenka". Ya sauke ajiyar zuciya ya cije lebe cikin runtse ido da kada kai. No, ba haka ba ne. ina son Humaida, クラ ina matukar sonta. 2 A8 5 *** *** *** иS967 Yallabai, Humaida ba ta da hankali 99 za ta lahanta kanta. 108 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd Ci gaba ya yi da bugu kamar zai 6alla kyauren. Tana zaune a baking ado, kuka kawai ta ke yi. "Humaida ki bude kofa mu yi ララ magana. mutu". Cikin muryar kuka ta ce. "Dad ba zan bude ba, ku kyale ni in "Baby zan yi yadda ki ke so". Ya ce cikin muryar lallashi. "Please ki bude kin ji". "Ba za ka yi ba dad, ba ka sona da kana sona ba za ka wofintar da abin da na kawo ba". "Ki buce ki ci abinci kada ki haddasa wa kanki wani ciwon”. Har bayan sallar magriba suna faman lallashi fir ta ki budewa, tun suna jin motsinta har sun daina. Cikin tashin hankali Dad ya fita ya samo ma'aikata suka 6alle kofar. 109 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd Hango ta suka yi ta soma fita hayyacinta, a hannu ya dauke ta tamkar jaririya, ya nufo sitroom ya kwantar da ita a doguwar kujera yana jijjigata. Da kyar ta dawo hayyacinta. Mom ta hado mata shayi mai kauri cikin dabara da lallashi suka samu ta sha. Injiniya ya dube ta yana mamakin yadda ta yi zuru-zuru, ya kada kai ya ce. "Babyna na yi miki alkawari muddin zai amince zan aura miki shi, haka ya yi miki?" A hankali ta kada kai. BAYAN SATI DAYA A kwanakin nan kullum sintiri ta ke yi duk inda ta san yana zama ta ke kai shawagi, sai dai babu duriyarsa kodayake wani fannin a kan idonsa ta ke zuwa inda ya ke samun maboya ya 6oye kansa. Koyaushe kokari ya ke yi ya cire ta a rayuwarsa, duk da yana jin ba zai iya ba. 110 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd Yanzu ne ta ke tunanin kai wa gidansu ziyara, sai dai da ta tuno mahaifiyarsa ya kan sire, tunanin gargadin da ya yi mata na game da zuwa gidansu ta ke. Yanzu dole ta san hanyar da za ta bi ta gama da mahaifiyarsa. Kaya ne a zube gaban Hajara tana faman jujjuya su cike da tsoro tare da mamaki, turamen atamfa biyar, sai leshina uku kowane yadi goma-goma sai ambulan wanda shi ne ta daga tana jujjuyawa. Mu'allim ya yi sallama cikin kallon kayan. "Umma me na ke gani haka?" "Karaso ka duba, ni ma wani yaro ne ya kawo wai a bai wa Maman Mu'allim" Gabanshi ya fadi, ta ci gaba da fadin. "Amma ina tsammanin makuwa ya yi, ka ga duba wannan takardar". Ya karba ya warware, kudi ne 'yan dubu-dubu guda ashirin, sai wata farar talarda, ya warware ya soma karantawa. 111 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd 'Ina fatan za ka yi wa Dad afuwa a bisa abin da ya aikata bisa rashin fahinta. Daga karshe ga kyauta nan na yi wa ummanmu, saboda ina son ganinta cikin wadata, kada ka ce a'a'. Ya sauke ajiyar zuciya, ya saci kallon Ummansa ta wutsiyar ido gabadaya idanunta na kansa, ya yi yake. "Umma kayanki ne ban san ta dawo ba, 'yar makarantarmu ce, shekara biyu ke nan rabona da ita. Tana da yawan alkhairi, dukkan wasu matsalolina ta kan magance mini, iyayenta masu hali ne". Kai da ganin yadda ta ke maganar za ka fahinci akwai rashin gaskiya a tattare da shi. "Allah sarki wannan kaya tamkar kayan lefe, anya Mu'allim?" "Babu damuwa Umma, za ta iya ba ki fiye da haka". "To amma sai ka rike kudin ko?" 112 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd "A'a Umma, ki bar shi ai naki ne. sai ki bada a yi miki dinki”. Ta dage a kan sai ya amsa, tilas ya dibi dubu biyar. A daidaita sahu ne ya sauke Hajara daga dan nesa da gidan Yusuf ne ya fara lura da ita ko kadan bai iya shaidata ba, ya zunguro Mu'allim. "Ga shi nan kun yi bakuwa, amma daga fani kanwar Umma ce, na ga kamar ta baci". Mu'allim ya kasa dauke ido daga kanta, la66ansa ne kawai ke rawa, gabadaya Umma ta dawo kamar 'yar shekara arba'in. ta lura da kallon da suke mata, ta yi murmushi daidai lokacin da ta karaso inda su ke. "Yusuf kai ne a gidan namu?" Ya yi mamakin yadda ta canki sunansa, sai dai ga muryar nan irin ta Umma. Ya yi murmushi. "Ni ne". 113 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd Ya gaida ta, ta amsa tana kokarin shigewa ciki ya maida kallonsa ga Mu'allim. "Ya ya aka yi ta san ni?" Idanun Mu'allim syka kada kamar zai yi kuka. "Yusuf ka ga Umma tana bukatar kulawa, ga shi kai kanka ka kasa gane ta". Yusuf ya zabura, ya ce. "Kana son ka ce min Umma cе?" A hankali ya kada kai. "Allah ya yi mana tsari da talauci, shi ya sa na ce ka yi nazari a kan al'amarin Humaida, ka ga yanzu in ma kyauta ta samo daga gurin wasu wataran ba za su yi mata ba, kuma kayan za su tsufa, amma in kana da abin kanka kuwa za ka iya wadatata. Mu'allim ka tashi ka taimaki mahaifiyarka, wallahi shekarunta bai kai a ce ta yi tsufa haka ba, dubi fa yadda ta juye ta zama tsohuwa saboda wahala yanzu ka auna ka ga sauyin da ta samu yau kadai inda a ce za ta dauwama cikin wannan kulawar haka za ta 114 KA AURE NI!-I Bilkisu H.Muhd dinga dawowa sabuwa, please ka zauna ka yi tunani". Yana alwala ya ji kiran waya, ya zaro wayar daga aljihu ya duba, Humaida ce. Ya dan saci kallon Ummansa da ke tsugune ita ma alwalar ta ke yi, gabadaya idanunta na kansa. Ya faki idonta ya katse wayar. A gaggauce ya Kaarasa alwalar ya fita zai tafi masallaci, kiran Humaida ya sake shigowa ya danna karbawa ya kara a kunne. "Ka jira ni yau zan zo". Muryarta ta ratsa kunnensa. "Kada ki zo ba na nemanki, me ya sa ba za ki fita a sabgata ba?" "O.K ka jira ni in na zo zan gaya maka dalili..." ki'. "Tsaya ni ki gaya mini inda zan same Yana jiyo dariyarta, ta ce. "Zan gaya maka amma in ka haura minti goma za ka gan ni a cikin gidanku". 115 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd Tana zaune a cikin wata rantsattsiyar mota mai duhun gilas, cool music ne ke tashi, ta ji dirar a daidaita sahu ta fan kallon gun, daidai lokacin da Mu'allim ke kokarin sallamar mai sahun ta sauke ajiyar zuciya, cikin murmushi ba ta taba tsammanin akwai mutumin da zai iya burge ta har ta ji tana sha'awar dauwama da shi ba sai Mu'allim. Yana tsaye yana ta raba ido, tunaninsa bai kawo ita ce a motar ba, ya ja kawai ya tsaya cikin sanda ta bude kofar motar ta fito tana ci gaba da sanda har ta isa inda ya ke tsaye. A daidai saitin kunnensa ta daddage ta zuba uwar kara, gabadaya ya runtse ido tare da saurin juyowa. Ta tuntsire da dariya, gabadaya ya ware idanunsa a fuskarta yana jin wani irin nishadi hadi da sonta. Yarinyar na da kyau na daukar hankali, to amma me ya sa ta ke tallan kanta? Har lokacin dariya ta ke yi cikin tafa hannu, shi kuma ya gaza dauke manyan 116 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd idanunsa a kanta, a hankali ya soma nurmushi. Burge shi ta soma yi. Ta tsagaita dariyarta, ta ce/. "Ya kamata a ce kai ne ke jirana ba ni cee jiranka ba". Ta dubi agogon da ke daure a tsintsiyar hannunta, karfe biyar da kwata, "Mintina ashirin na diba a nan kafin ka iso, me ya sa?" "Saboda kiran ba mai muhimmanci ba ne". Ta yi masa wani irin duba, lokaci daya ya daure fuska. "Na ga sakonki, amma kina tunanin zan amince da ke ne saboda wata bajinta taki? Gaskiya kin kyi kuskure". "Kada ka yi tunanin ina yin haka ne don na sami hadin kanka, ko da ban sanka ba na hadu da mutum na ga ya cancanci a taimaka masa na kan taimaka, sam ba manufata ke nan ba, amma ban ce lallai sai ka yarda ba. sa'annan na ga har yanzy 117 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd zuciyarka ba ta yi sanyi a kana bin da Dad ya yi maka ba..." "Hakan ne ya sa na zo na gargade ki". Ya katse ta da fadin haka. "Gargadi? Wane iri?" "Eh, ina gargadinki da ki fita a rayuwata "Tunda na taso ban taba jini na ra'ayin abu na rasa shi ba ina ji a jikina mu'amalarmu za ta fore". "Idan na ce da ke na tsane ki ya za ki ji?" Ta yi murmushi, "Uhm zan dubi fuskarka in har na kalle ka zan ga labarin zuciyarka a fuskarka. Ta iya yiwuwa ne ka fada ta wata manufa, amma ni na san ba haka ba ne". "Me ya sa ki ke yaudarar kanki?" "Saboda na san babu namijin da zai dube ni bai yi burin na zamo mallakinsa ba". 118 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd Ta yi bala'in ba shi dariya, musamman yadda ta ke magana cikin Gadara da nuna isa, ya ce. da ni". "Sai ga shi ni babban burina ki rabu "Karya ka ke yi, wallahi karya ne". Ta katse shi kai tsaye. "Na riga na shigo rayuwarka, sai ka zamo nawa sai na mallake ka”. Ya ce, "Ko mayya ce nan gani nan bari". "Ba mayya ba ce, amma za mu kasance tare". Juyawa baya ya yi ya soma tafiya ta shiga kwala masa kira, bai saurare ta ba. ta koma ta shiga mora ra bi bayansa, sai da ta zo daf da shi ta sha gabansa ta tsaya ta fito. "Mu'allim ka gaya mini, me ye wanda ba ka so a jikina, ko halayyata me ya sa ka tsane ni? Yanzu ka rantse ka tsane ni, ka сe ba ka son ganinaa, ka ce ba ka sona, ni kulma na rantse zan fita a rayuwarka". 119 KA AURE NI!-I Bilkisu H.Muhd Gabadaya ya ji ta dauke masa wuta, ya sanyaya murya matuka. "Babu dan Adam din da na tsana. Ke ba sa'ata ba ce, ba ajina ba ce, in na ce zan yi soyayya da ke na yi wa kaina ganganci, kowa ya sani ruwa ba sa'an Kwando ba ne. Ni talaka ne ke 'yar manya ce, na sani kuruciya ce ke dibanki, in kin zaße ni a matsayin abokin rayuwa nan gaba da kanki za ki yi da na sani, don Allah na roke ki, ki kyale ni". "Wannan ne kurum hujjarka? Wannan ne ya sa ka ke son cutar da mu?" "Ba shi ne kawai ba, dabi'unki sun zamo abar kyama". Da sauri ta kalle shi. "Wace irin kyama?" "Ina tsoron halayyarku da dabi'unku, duk da na kwarai ya kan yi kokarin sama wa yaransa uwa ta gari. Ban taba ganin mutane kamar na gidanku ba. Al'adun yahudawa sun yi muku kaka gida, ban da 120 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd wannan zan yi farin ciki idan mace irinki ta zamo mallakina, matata makusanciyata". "In ka zauna da ni za ka iya sake tsarin rayuwata. Zan bi ka ta yadda ka ke so". "Humaida, ba za ki taba fahintar abin da na ke nufi ba, shiga mota mu je ki gani”. Yadda ya ce haka ta yi, suka shiga mota, wannan karon shi ne mai tukin, kurum zuba masa ido ta yi tana kallonsa cike da tunanin inda zai kai ta. Hanyar sharada ya dauka, inda ya tsayar da motar daidai kasuwar, ya zuge gilas ya kalle ta, ya ce. "Dubi can". Wani dattijo ta hanga zaune a rana yana faman dinkin takalmi, gabansa matattun takalma ne da matattun robobi. Tа dube shi cikin rashin fahinta. Ya dan jinjina kai. "Abin da na ke son fahintar da ke, wannan dattijon da ki ke gani shi ne 121 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd mahaifina, babana ne shi ne ya haife ni. Ki dube shi, dubi suturar jikinsa, dubi yadda ya ke, kalli inda ya ke zaune, ki fara nazari". Kurum binshi ta ke yi da kallo har yanzu ta gaza fahintarshi. Ya tada motar, unguwarsu ya nufa, nan ma ya yi fakin a dan nesa da gidansu. Ya numfasa. "Na san duk lokacin da ki ke bibiyata ba kya duban unguwarmu da gidan da na ke rayuwa, ni kawai ki ke duba zuciyarki na karkata ne a guna. Nan ne gidanmu, a nan na ke rayuwa ba mu mallaki komai ba sai wannan rusasshen gidan kasan. Ina son ki dube shi da kyau duk fadin unguwar nan babu lalataçcen gida kamar wannan, kowa ya dubi gidan zai nemi tsari da rayuwa a cikinsa, mai tausayi da imani shi zai duba ya ce, Allah Sarki, gida ne wanda ko almajiri in ya zzo tsallake shi ya ke ba zai yi sha'awar bara a cikinsa ba". 122 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd Ummansa ce ta leko da wata karamar yarinya a gabanta, da sauri ya zuge gilashin. "Wannan ita ce mahaifiyata, ta rako waccan yarinyar ne kin ga alamun kamar yana yi wa yarinyar magana duk da ban ji abin da ta ke cewa ba, na sani godiya

Chapter 4 of 5