Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 5
gori a kanshi". "Humaida loakcinki ya zo daf kin yi karatu irin yadda na ke so, kin yi karatun da za ki san me ye rayuwa, loakci kankani na ke jira zan yi miki aure, ni ma burina ke nan ina ta nazarin irin mijin da zai dace da ke, miji dan gaske. Ina son na aura miki mijin da ba zan ji kunyar nunawa kowa shi a matsayin suruki ba". "Dad ai irinsa na samu na kuma gama magana na gaya maka ka neme shi”. "Shi ke nan zan yi yadda ki ka ce, zan neme shi, ki dan ba ni lokaci mu bi komai a ११ sannu. 61 KA AURE NI!-1 yi". Ta makale kafada. "Oh my God". Bilkisu H.Muhd "To gaya mini, gaya mini yadda zan "Ka ga ba da bata lokaci ba, ka je ka same shi ka yi masa magana gobe a daura aure, jibi kuma ka gan nki da ciki, gata na haife. Ka ga na yi maganin gorin Mom, in fa ba a yi haka ba ran kowa zai 6aci a gidan nan". Ya dinga tuntsira dariya, lamarin Humaida sai ita. "Shi ke nan, yanzu a ba ni sati guda ayyuka su sassauta mini". Ta kada kai ita kam Mom yadda fuskarta ke a daure amma zuciyar nan fari kwal ya ke, tana jin dadin yadda mijinta ke ji da 'yar tata. *** *** *** 62 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd Majalisar su Mu'allim ta yi fakin daga dan nesa da su ta fito sanye da shiga irin tasu ta manya. Yusuf ya yafito Abdul. "Kai kalli wata haja can tafe". Abdul ya dana harshe, ya ce. "Kai wannan ta gaji da haduwa, ta zo duniya a sa'a, ga kyau ga masu numfashi. Amma fa wannan hajan ta fi dacewa da ta gwamnoni, kalli fa motar da ta shigo". Hankalin Mu'allim ya kai kan Humaida, ras! Gabansa ya fadi, me kuma ya kawo ta nan? Tana kara kusanto su, wuf! Ya mike da sauri Abdul ya rike gefen rigarsa. "Haba Malam, bi a hankali mana, wannan sam ba kalarka ba ce. Ya kwace daga rikon da Abdul ya yi masa cikin sauri ya doshe ta. Ya yi bala'in daure fuska. "Duk inda na ke zama kin sani, please ki gaya mini me ki ke bukata a gare ni?" 63 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd Ta yi masa kallo mai lumshe idanu, da sauri ya dauke kai daga gare ta. "Sunanka na ke bukatar ji. "Sunana Mu'allim, don Allah ki tafi ki daina bibiyata kada ki bata mini suna, in kuma ki ka ci gaba komai zai iya faruwa". Ta kalle shi a tsakiyar ido. "Kalaman so ka ke gaya min?" Ya gama kufula. "Ke wace irin bagidajiya ce wadda ba ta san bakar magana ba?" Ta yi murmushi ta cе. "Tunda na taso a gidanmu ban san wannan kalmar ba". Ya yi shiru kawai yana kallonta, tsawon mintina biyu ya hada hannayensa guri daya, ya yi kamar yana rokonta. "Don Allah ki fita daga rayuwata". A zafafe ya bar gurin, tilas ta ja jiki zuwa cikin motarta ta hada kai da sitiyarin motar ta rasa abin da ta ke ji game da shi, tana ji a ranta za ta liya jure wa duk 64 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd bala'insa, ba ta taba ganin abin da ya burge ta kamarshi ba. Muryarsa yadda ya ke masifa, fiyarsa da duk wani motsi da gabbansa ke va yi mata, sam ba ya taba ba ta haushi. T. dinga murmushi, ta dago kai ta kai wa sitiyarin duka sannan ta tada motar. "Mu'allim ba mu fa gane ba, wane siddabarun ne da kai?" Yana ji suna ta yi masa tsiya ya fahinci bugun cikinsa suke son yi, haka suka gaji da zolayarsa. bai bari sun ji komai а bakinsa ba, daga karshe ma barin gurin ya yi. Tana tsaye a wani loko da ke daf da layinsu da alamun tashin hankali a tattare da ita. Tun daga nesa ya hango ta, ya kara sauri. Tun kafin ya tambaya ta sanar da shi. "Na shiga wanka da na fito na ga kawunka ba ya ciki". Cikin kuka ta ke maganar. A guje ya kwasa ya yi iya dubansa babu duriyarsa. Ya 65 KA AURE NI!-I Bilkisu H.Muhd zauna a kan wani dandamali komai ya kunce masa, idanun nan sun yi jajir. "Zan tafi, ka kular min da kawunka". Wannan shi ne sallamarsu da Abbansa, hankalinsa ya kara tashi, ya ji zuciyarsa na yi masa zafi. "Ina Kawu ya ke, wane hali ya ke ciki? Yanzu haka yana nan yara na tsokanarsa, yana can yara na jifarsa. Yana can yana tsince-tsince. Yana can yana jin kishi da yunwa". Kwalla suka shiga kai komo a idanunsa, rayuwarsu da Kawu lokacin da bai hadu da lalura ba ta dinga dawo masa. "Ka ga tashi ka dauki roba ga naira hamsin ka saro pure water, dan abin da ka yi יי ciniki sai mu yɔ awo Kawu ya yi caraf, "Ina son ku sani muddin ina numfashi wannan yaron ba zai yi talla ba, wannan kam ba zai dauki dako ba, sai na karatu. Daga yau na dauki wannan alkawarin, Yaya ka zamo shaida duk lokacin 66 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd da Umman Mu'allim ta dora masa talla sai na yi mata saki talatin". Malam Musa ya yi murmushi. "Me ya sa zza ka ce haka alhalin mu din ba wasu ba ne?" "Na sani Yaya, amma ni ina ji a jikina yarona zai zamo wani, bango majinginarmu zai zamo wani abu wataran. Malam Musa ya ce, "Ina fatan haka, amma ta ya ya hakan zai yiwu alhalin abin da za mu ci ma yana yi mana wahala, ta ya ya za ka ci wa Mu'allim irin wannan burin?" "Ba zan gaza ba yaya, Ubangiji zai tallafi niyyata, ni na sani burina zai cika, ina alfahari da fadin Ubangiji cewa, "Ku roke ni zan amsa muku'. Zan kara jajircewa, zan hana idona bacci cikin dare na tsaya tsayin daka ba zan gajiya ba, zan ta rokonSa a kan Ya tabbatar mini da burina". Ya janyo hannun Mu'allim ya dora daya hannun nasa a kansa. 67 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd "Allah zai zamo gatanka, ni ma zan zame maka gata daga ni har Yayana kai ne sanyin idaniyarmu. Ina matukar kaunarka, Ubangiji ya dora mini sonka, ina kaunarka fite da komai. Zan yi komai domin ka sami kyakkyawar rayuwa". Hawayen da ke cikin idanun' Malam Musa suka karasa gangarowa kan fuskarsa. Bayan wani lokaci mai tsawo Kawu ya sami Malam Musa zaune, ya debi kudi ya zube masa a gabansa, cikin zaro ido Malam Musa ke kallonsa. "Yusuf kudin me na ke gani haka?" Kawu ya ce, "Na yanke shawarar zan yi tare saboda karatun Mu'allim". Malam Musa ya mike tsaye ya shiga kai komo. "Wannan da man shi ne nufinka a kan kawai ka bauta wa danka ka ke son jefa kanka cikin halaka? Mun shiga tashin hankali da yunwa mu kan yi kwanaki ba mu dora tukunya a cikin gidan nan ba, amma 68 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd ban taba tunanin sanya kaina cikin mummunar hanya ba a hakan kullum godiya na ke wa Ubangiji don me ya sa ba za ka yi oyi da ni ba? In ka jefa rayuwaeka cikin こ ari ya zan yi? Shin kana son haddasa mini wani ciwon ne? Kada ka mance, kai ne kadai shakikina, kai ne sanyin idaniyata, kai ne uwa da uba da dangina, me ya sa za ka zabi irin wannan rayuwar?" Duk Kawu ya gama rudewa. "Yaya na rasa inda maganganunka suka dosa?" A fusace Malam Musa ya ce. "Ina nufin in dai ta wannan hanyar ka zaba don ka inganta rayuwar danka to ka barshi, ka gaggauta sanar da ni inda ka samu kudaden nan... "Yaya kafin na ce wani abu ka yi wa kanka shari'a irin wannan tarbiyyar ka ba ni? Ina alfahari da tarbiyyar da dan uwana, 'yayana, Babana ya ba ni hakan ne ke kara 65 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd ba ni karfin gwiwar inganta rayuwar Mu'allim..." Malam Musa ya dakatar da shi. "Ya isa, yi mini shiru. Kana son ka ce ramuwa za ka yi, ko biyana za ka yi gwara da ka fito ka shaida min hakan. Amma bari ka ji in ba ka sani ba, wallahi na fi bukatarka fiye da Mu'allim. Yau in na rasa shi Allah zai iya ba ni wani, kai ko in na rasaka na rasa ka ke nan ba za ka dawo ba, ba kuma za a haifa min wani dan uwan ba. A kan me ka ke neman maida rayuwarka abin farautar 'yan sanda da sojoji, a kan me? Wallahi muddin ka gurbata halayyarka ba zan yafe maka ba. Barinsa ya yi a gurin cikin sharar kwalla, bai yi yunkurin binsa ba ya san duk abin da zai gaya masa ba sauraronsa zai yi ba. Ko da safe da ya je ya gaida shi kain amsawa ya yi, wani irin kaunar yayan nasa ya dinga ratsa masa zuciya. 70 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd A wannan marran kan a sami mai irin halinsa za a tauna. Shi kam in bai so Mu'allim ba Allah sai ya kama shi ta hanyarsa kawai zai iya biyan yayan nasa, yanzu ya ke kara jin yayan na zaburar da shi, ya yi bala'in sanyaya murya. "Shin aikin gini kauce hanya ne? dako kauce hanya ne, ko turin kura kauce hanya ne? Na amince ka je ka bincika wadannan ayyukan su na ke yi har na tara wannan kudaden, dubu ashirin da takwas ne, Yaya ka amince da ni". Gabadaya jikin Malam Musa ya yi sanyi, duk sai kunya ta kama shi. "Ba ka taba yi mini karya ba, na amince. Amma wadannan ayyukan sun yi tsauri da yawa, ka yi hakuri na yi maka mummunar fahinta". "Ba komai Yaya. Amma ina da shawara". Ya ce, "Ina jinka". 71 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd "Kudin nan a ciki na dibi dubu goma saura na kawo maka, na kama rumfa a kasuwar Sharada ina son zan je na siyo kayan hatsi mu zuba a shagon mu dinga saidawa. Hakan ya fi wannan sana'ar da ka ke yi ka ga a hankali rayuwar sai ta yi mana sauki, ni kuma sai na ci gaba da tarin saboda wahalar karatun Mu'allim". Malam Musa ya dinga godiya. "Kada ka yi mini godiya, yi wa kai ne, Mu'allim shi ne zai zamo madogararmu nan gaba, zan iya yin komai domin shi”. Wani yaro ne ya katse masa tunani, "Ga kawunka can a bayan layi yara na jifa". Ai da gudu ya mike. Rumfa ya yi masa duwatsun da yara ke jifarsa suka dinga sauka a jikinsa, Cikin wata masifaffiyar murya tare da tsawa ya ke cewa. "Kada wanda ya sake jifarsa, yana da gatansa, ni ne gatansa saboda kawai yana a matsayin mahaukaci ba kwa gudun hakki, 72 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd me ya yi muku, me ya ke muku? Bai san komai ba. Yadda suka ga Mu'allim ya birkice ya suka fashe a gurin, ya koma yana kade a jiki. "Ka yi hakuri, sannu, yara ne marasa 55 tart yya, sannu". ****** - *** "Sis hantsi fa ya dubi ludayi, wai wannan Gallagazar mai aikin ba ta gama girkin ba ne?" Humaida ta dube shi ta watsar ta koma tana danne-dannen waya. Ta dan kallo tare da yatsina fuskа. "Ba ta ma dora ba, aiki na sa ta". Ya daure fuska, "Sis kina jin abin da ta ke cewa ko?" "Mustapha ya ka ke so na yi?" "Amma dai fisabilillahi sis ta ya ya za ta yi haka, karfe biyu saura a ce dan Adam bai ci abinci ba?" 73 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd Ya ja tsaki, "Mustapha na ga sai wani soki burutsu ka ke, kada ka mance da ni da kai duk zamanta muke yi". "In ji wa?" Bai san sa'adda ya yi tambayar ba. Ta ce, "In ji Dad dinta mana". Sallamar Adam ya katse su, yana faman rase-rabe. "Hajiya ko zan sami yaji?" Ta ce, "Wane irin yaji?" Ya ce, "Zan ci abinci ne". "Ba ni da yaji, kai dai kawai ka fadi abin da ke tafe da kai, ya ma za a yi ka shigo har nan tambayar yaji? Ka tambayi masu aiki mana" Mustapha ya ce, "Allah ne ya kawo mini shi, da ma dan aike na ke nema. Sis ba ni dubu biyu ya karbo mini take away". Ta bude jaka ta dibo dubu uku ta watsa mas, dubu daya ya mika wa Adam. "Karbi, please ka hanzarta dawowa". 74 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd "Ba za shi ba". Humaida ta fada kai tsaye. "Kai Adam je ka wanke mini jar motar nan zan fita". Ta karbi dubu dayansa ta ajiye, ta shige daki abinta. Bakin Mustapha ya kasa rufuwa, ya dubi Mom tamkar ba ta san abin da ke faruwa ba. Ya yi kwafa. "Amma wannan yarinyar 'yar rainin hankali ce, kina jinta ko sis?" "Uhm Mustapha ke nan, wai ya ka ke son na yi ne? sam kai ba ka fahinta, a fa gidansu fa ka ke, ka ke kuma cin arzikinta". gida". Ya mike cikin daga kafada. "Well, Adam bi umarnin 'yar masu Dalleliyar motar da ta shigo sai daukar ido ta ke, yana tsaye kawai yana kallonta kafin ta fito kofar gidansu ta nufa, inda ya ke tsaye. Ya yi bala'in daure fuska, wani takaici ne ke cinsa, tsarin suturar jikinta sam bai dace da 'yar musulmi ba. 75 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd Ta dube shi tana faman kada makulli, gabadaya ya kasa cewa komai. "Ba zan daina ziyartarka ba har sai ka amsa gayyatata ta zuwa gidanmu, kuma gobe ma sai na dawo". "Wai ke mayya ce?" "Gaya mini duk abin da ranka ke so". Ya ce, "Kina son bata mini suna, ki daina wannan shigar kina zuwar mana kofar gida". Ta shiga duba ko'ina na jikinta, sam ba ta ga abin da ya ke ma raki ba. "Ina kokarin yin yadda na ga kana ra'ayi don haka na ke takura kaina gurin sanya kayan da jinsinmu suka fi tu'amali da shi kamar haka". Tunani ya ke me zai yi wa yarinyar nan ta fita a rayuwarsa. Tunda ya ke bai ktaba samun sabani da mahaifiyarsa ba sai da ta shigo rayuwarsa, rabon da ya ga sakin fuskarta tun sa'adda ta kai masa ziyara, bai 76 스 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd san sa'adda ya kai hannu ya rike gefen rigarta ba, duk don kokarin tozartata. Da wannan shigar ba za ki taba mutunci a idanun kowa ba. Da wannan shigar ba za ki taßa ba da sha'awa ba.. Macen da aka sani da mutunci kamala da hijabi a jikinta, kuma surarta ba abar kallo ba ce ga mutanen kwararo, mace mai hankali ita ke boye surar jikinta ta 6oye adonta saboda mijinta halalinta shi kadai ya kamata ta yi wa, zai gani ya ji dadi ya yi zumudi, sannan ta burge shi ba irinki ba, wadda kin gama tallar ado a kwararo". Juyawa ya yi ya shige cikin gida ya kuma danno, kwakkwaran motsi ta gaza yi, ji ta yi gabadaya ta tsani kanta, sai dai a can karkashin zuciyarta Mu'allim kara burge ta ya ke yi, tana son mutum jajirtacce. Ta yi murmushi mai ciwo, tare da kada kaki ta soma tattaki zuwa inda ta ajiye motarta. 7 KA AURE NI!-I Bilkisu H.Muhd Ta yi nisa da unguwar su Mu'allim, Yusuf ya gano ta ya sha jinin jikinsa, ba shakka Mu'allim ta ke nema. "Dan iskan nan na son wasa da damarsa, wallahi muddin yarinyar nan ta кибuce тasa ba zai taba fita a talauci ba". Daf da zasta gota shi ta dubi inda ya ke, kallon sani ta ke masa tabbas yana daya daga cikin abokan Mu'allim in haka ne za ta yi magana da shi. Ta saki hon daidai lokacin da ta yi fakin motar. وو" Ji mana Ta ce da shi. Ya dan dakata. "Don Allah zan iya yin magana da kai?" Ta yi tattaki zuwa gabansa, jikinsa na rawa, wani irin kamshi mai sanyi ya shaka. "Na ga kamar na sanka?" Ya dinga kallonta. "Please, ko kai ne abokin Mu'allim?" Da sauri ya jinjina kai. 78 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd Та сс, "Idan ba aza ka damu ba, ina son ka taimake ni da lambar wayarsa". Ya ce, "Babu matsala". Wayarta ta mika masa, ya karba ya shiga dura mata lambobin. Ya gama ya mika mata, ta karba ta balle post dinta kudi ta debo dubu gomata mika masa, tuni hannunsa ya soma skarkarwa tamkar yas fincika. Hannunsa ya riga nata isowa gare ta, ta mika masa sai zare ido ya ke yana jin komai tamkar a mafarki. "Na gode Madam". Ta dan yi takaitaccen murmushi. "Wannan ba wani abu ba'ne Ta shige mota za ta tafi, ya ce. "Shi ke nan abin da ki ke bukata?" Ta ce., "Ina neman kusanci tsakanina da Mu'allim, in har ka yi haka zan yi maka komai" Ya yi murmushi. "Zan yi kokarin ganin tabbatar da haka" 79 KA AURE N1-1 Bilkisu H.Muhd :Ta kada kai kurum ta ja mota. *** *** Shekaru kusan talatin tasowata a haka na ke ganinku, ba kwa gaba kullum baya ku ke kara wa, yanzu lokaci ya zo da ya kamata iyayenka su fanshe dawainiyar da suka yi da kai, amma kana neman kaucewa. Mu'allim wannan hanya ce kadai za ka bi ka cimma dukkan burikanka, addu'ar da ka ke yi ne Ubangiji ya karba, please ka saurari wannan yarinyar kada ka yi mana 99 mugunta... "Ya ishe ka haka Abdul, wannan cin وو fuskar ya yi yawa". Caraf Mudansir ya cafe. "Cin fuska ko gaskiya? Ka gaya mini in ba wannan hanyar ba kana sa rai da wata hanyar? Mu'allim ban taba ganin mara gata irinka ba, duk cikin danginku ba mai rufin asiri balle ka yi zaton nan gaba za ka sami wata alfarma ta dalilinsu..." 80 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd Yusuf ya katse shi, "Ya isa! Ban gaya muku don ku ci masa fuska ba, ba a dole lin yana jin ba ya ra'ayi babu lallai ba tilas". Ya sassauta murya, "Amma Mu'allim ka je ka yi tunani". So su ke ma su ji ta bakinsa amma ya ki cewa komai sai idanunsa da suka yi jajir yunwa da bakin cikin maganganun abokansa sun saukar masa da wani azababben ciwon kai, tilas ya bar gurin. Ko da ya koma gida Ummansa ce ke faman kuka, ga wani irin kaya da ke jikinta mai kama da tsumman goge leda. Gabadaya sun yayyage. Ya dauke kai tare da yin sallama, da sauri ta goge fuska tare da kirkiro murmushin dole. "Mu'allim ka dawo?" Ya daga kai, ta sake fadin. "Ya yau ma ba a dace ba ko?" Ya sake kada kai. 81 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd "To Mu'allim kada ka kosa ka ji, Ubangiji na sane da mu, ya fi mu sanin halin da mu ke ciki, wataran zai karbi rokonmu ka ji. Ya ce, "To Umma". Ta sake cewa. "Allah ya yi maka alb arka". Ya ce, "Amin". Ya shige dakinsa ya zube a kan tabarma. “Auren jari za ka yi muddin ta fito da kudirinta ka amince, ba a kanka aka fara ba, ba kuma kwanciya za ka yi ita ta ci da kai ba, aiki za ta sama maka in ka yi haka da mu da iyayenka dulk za mu sami albarkaci". Maganganun Yusuf suka dinga dawo masa, ya sauke ajiyar zuciya. "Amma ai ban da tabbacin ba mahaukaciya ba ce, ko wace iri ce ita babu ruwanka muddin za ta fidda ka daga kangin talauci, bakun talauci”. 82 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd Ya yi saurin mikewa saboda wani irin iska da ya taso, ya leka tsakar gida yana kallon Umma na kawar da kayan tsakar gida da alama an fara yayyafi. "Ka sauke asabarin nan". Umma ta ce da shki lokaci daya ruwan ya kece mai karfin gaske. Ya mike ko ina ya koma ya kwanta, a hankali ya soma jin karar wayarsa, ya zaro wayar daga aljihu yana dubawa, bakuwar lamba ya gani, ya danna amsa kira tare da karawa a kunne. "Amincin Allah ya tabbata a gare ka". Wata zazzakar murya ta ratsa kunnensa. Ya kyi shiru yana nazarin inda ya san wannan muryar. Ta katse tunaninsa da fadin. "Sunana Humaida, na san ka mance da ni da fatan ban takura ka ba?" Ya ce, "Kin dai kusa, amma kafin nan ina son yau ki gaya mini me ki ke so". 83 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd "Ina kofar gidanku, ka fito na shaida maka". "Kofar gidanmu?" Ya fada cikin kaduwa, ya maida kai yana kallon wundo ruwan sama na kara tsugewa. "Ke kina da hankali? Wai me ke damunki ne?" "Mu'allim na san kai mutum ne mai tausayi tunda ka ga na keto wannan ruwan na zo ban da nutsuwa, ba zan fito ba kuku ya gaggauta kwacewa a kofar gudan nan, Mu'allim ina tsaye har nan da zuwa lokacin da za ka saurare ni. Tsaki ya ja ya katse wayar, ya ajiye ya mike ya shiga sintiri, ya sani zolayarsa ta ke yi. Kimanin mintina biyar ya kasa sarrafa zuciyarsa, yarinyar nan mahaukaciya ce, za ta iya aikatawa. Da sauri ya bude dakin, ba kowa a tsakar gidan, ya ji dadin hakan, ga mamakinsa ganinta ya yi jingine a jikin 84 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd mota kayanta jike sharkaf sai rawar dari ta ke, ta kankame jiki. "Lallali yarinyar nan da gaske ta ke". Wani irin tausayinta ya kama shi, bai san sanda ya fita a ruwan ba ya nufi inda ta ke, ba ta gane shi ba gabadaya ta gama karaya, ta bude motar ta shiga ta kullo. Hada kai ta yi da sitiyari komai ya kunce mata, me ya sa ba za ta hakura da shi bа? me ya sa zuciyarta ta kasa samun sukuni? Me ya sa ta ke jin in ta rabu da shi tamkar ta rabu da rayuwarta ne? Me ya sa ba ya taba ba ta haushi? Duk me ya janyo wannan? Hakan na nufi ke nan shi ne farin cikinta? Kuka ya kwace mata, ta cije lebe zuciyarta na yi mata wani irin zogi da radadi. "Oh Allah, me haka ke nufi, wannan wane irin mutum ne mai shiga rai haka?" Kwankwasa motar yaa katse ta daga tunanin da ta ke yi. Ta dan dubo gurin ta wutsiyar ido ta ganshi sarai amma ta basar. 85 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd Ya dan yi murmushi cikin tausayinta, ya sa hannu ya bude motar. Kuka ta ke yi mai hade da shessheka. Da sauri ya zauna ya sassauta murya yana kallonta. "Ki dan kauce wa kofar gidan nan”. Sai lokacin ta dan dubo shi da ido jajir, cikin muryar kuka ta ce. "Saboda kada a ganka da ni?" Ya dube ta cikin kifta ido, a hankali ya dinga jin wata kasala na shigarsa, musamman da ya shaki kamshinta, cike yа ke da mamakin yadda salon ke son sauyawa. Ya yi bala'in kaskantar da kai. "Alfarma na ke nema please, ki yi abin da na ce". Tilas ta juya akalar motar dan nesa da gidan ta yi fakin. Sai da suka kafe juna da ido zuwa wani lokaci ya saukar da ajiyar zuciya, yanayin da ya ji shi a ciki ne ya sanya shi kawar da kai, sai dai ita har yanzu idanun nan nata na kafe a kansa, ba ta taba ganin 86 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd mutum kamarsa ba, komai nasa abin burgewa ne. Ya dinga dan satar kallonta, shin wannan wacce irin yarinya ce? Gabadaya ya sake dago da kai yana murmushi. Ya numfasa. "Na sani duk batunki wasa ne, yanzu ki gaya mini me ki ke bukatar gaya mini? Ko mene ne fada mini na yi miki alkawari zan ba ki, zan yi miki”. Ta yi luuu da ido cikin wani salo na daukar hankali. “KA AURE NI!" Ya dan yi jum kamar yana tunanin wani abu ya sake maida kai kasa, ya ce. "Shi ne kawai bukatarki?" Ta ce, "Kwarai". Ya ce, "To zan aure ki". Та се, "Ка yi alkawari?" Ya ce, "Ban yi ba". Ta ce, "Saboda me?" 87 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd "Saboda ban tsara zan yi rayuwa da mahaukaciya ba!" Duk da ba ta ji dadin furucinsa ba hakan bai hana ta kare kanta ba. "Mu'allim dakata, ni ba mahaukaciya وو ba ce "O.K na ji, amma me ya sa ki ke son na aure ki?" a Ta dan yi shiru tana tunanin me za ta ce masa, sai dai abu mafi burgea halayyarta ba ta iya karya ba, ba ta karya ko da rashin kyautawa ta yi ta kan fadi tunda ta san babu mai iya daukar mataki a kan haka. "Ke na ke sauraro". "Tunda na dora ido a kanka na ji ka yi mini, ka burge ni, kana da kyau ba kasafai a יי ke samun irinku ba..." Ya yi saurin katse ta cike da takaici, ga wani dariya da ta taho masa. "Ke kuma haka Allah ya halicce ki daga kin ga mai kyau sai ki nemi ya aure ki? Gaya mini aurenki nawa, don na san 88 2 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd kyawawa kullum haihuwarsu a ke yi, wannan shi ne kalar haukan naki". Ya bude motar zai fita ta yi saurin riko hannunsa. Ras! Gabansa ya buga lokaci guda ya dinga jin wata irin kasala, ya ji shi tamkar an zare masa laka, ga wani irin yanayi da ya dinga ji da sauri ya zare hannunsa daga cikin nata ya koma ya zauna yana maida numfashi. "Ban taba rantsuwa ba, amma yau na yi saboda neman yardarka. Na yi rayuwa da jinsi iri-iri na je kasashe da yawa ban taba ganin ko jin mutumin da ya burge ni na ke son mu yi rayuwa a cikin duniya daya, unguwa daya, gida daya, daki daya kamarkaа ba. ka amince mini". Har yanzu mamakinta ya ke, bai taba jin ko ganin mace irinta ba, wannan akwai rainin hankali cikin lamuranta. Ya yi bala'in daure fuska cikin kallonta. 89 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd "Duk cikin zantukanki ban ji kalmar so ko guda daya ba, sai dai ina burge ki, ina da kyau na aure ki" "Sau tari ina jin mutane na maganar so, sai dai ban san ya ake soma shi ba, ban san me ye shi ba, asalima ban yarda da shi son ba, da na yarda da kalmar so da kai tsaye cewa zan yi ina sonka, ba zan ce KА AURE NI ba". "An kuma".. Ya ce a ransa, ya yi murmushi a hankali ya dinga jin ta soma burge hi. "Ban taba jin an yi aure babu so ba, ya za a kira wannan auren? Auren jeka na yi ka ko me?" "O.K na amince na yarda ka koya mini yadda zan so ka”. Ya kyalkyale da dariya bakidaya ban dariyarki ya sanya ina jin dadin kasancewa da ke, ba zan koya miki sona ba domin ina da abin da ya fi so muhimmanci, sai dai ki. zama kawata, aminiyata that all”. 90 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd A hankali ta kada kai, "O.K zan iya tafiya". Ta sake kada kai, har ya bude motar ya fita ba ta iya cewa komai ba, ta bi shi da ido har sai da ya bace wa ganinta, ta sauke ajiyar zuciya. A dakin Mu'allim yana kwance sai faman juyi ya ke yi, lokaci-lokaci ya kan yi murmushi, musamman in ya tuno hirarsu da Humaida. Yanayinta na burge shi, ya mike zaune ya janyo filo ya rungume ya koma ya kwanta ya lumshe idanu yana wassafo kamanninta. Tana da kyau matuka, tana daya daga cikin matan da kowane namiji ke mafarkin rayuwa da su, irin matan nan ne wadanda ba su taba gundura irin matar da in an 6ata maka a waje da ka shigo gida ka adobe su za ka ji wani sanyi da nishadi na shigarka. Irin matar da duk lokacin da ka dora ido a kansu za ka kasance mai mika godiya ga Allah da ya azurtaka da ita, irin matar da ko ita kadai 91 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd ka mallaka za ka yi alfahari, irin matar da ake wa

Chapter 3 of 5