Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 5
gaya miki maza. na wahalarwa? Kin taba ganin Mom cikin wahala?" "No Dad, kai na daban ne". Ya ce, "Don haka na ke son sama miki na daban irina". "Ba za a samu ba Dad! Ina jin labarai ina kalle-kalle, ina karata littattafai kullum "9 maza ne ke wahalar da ma Ya yi dariya. 30 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd "Baby ai ke yanzu kin wuce wannan matsayin, kina da komai ko wane namiji dole ya yi miki biyayya, don haka na ke so mu bi a sannu ba za ki taba fahintar mai sonki ba, don haka na ke son ki kama zuciyarki". "Dad na gaya maka ba zan taba son wani dan Adam ba bayan ku ban jin komai ba game da shi ba, na ga dai kawai mun dace da juna". Ya san Humaida da kafiyarta, ya shiga nazarin ta inda zai 6illo mata, ya sauke ajiyar zuciya. "O, tanzu kina da tabbacin sake haduwa da shi?" "Ina ji a jikina, kuma na ba shi Katina na tabbata zai kawo kansa nan ba da dadewa ba". "To shi ke nan, na ji. A wace iriyar mota ki ka ganshi?" Ta yatsine fuska, ta yi taku uķu ta tsaya. 31 KA AURE NI!-I Bilkisu H.Muhd "A sayyadarsa na aga yana tafiya". Ya sake yin shiru duk alamin 6acin rai suka bayyana a fuskarsa, ta kafe shi da ido. "Dad ya na ji ka yi shiru?" "No, ba komai yanzu mu bari har zuwa lolkacin da zai kawo kansa sai mu san me za mu yi, yanzu ki je gida da na dawo sai دو mu sake tattaunawa. "Dad na gode, ina alfahari da kаi". Ta soma tafiya da baya cikin daga masa hannu da dan mumushi a fuskarta. *** *** Katon gida ne na gani a yaba tsakanin get zuwa cikin gidan akwai tazara mai nisa, yawan bishiyoyi da furannin da ke dashe a gidan ne ya taimaka gurin rashin wadatar haske a cikin gidan ba lallai ne matsoraci ya iya shiga ciki ba saboda duhunsa. Hakan ya sa rai da rai gidan bai rabo da hasken fitilu a harabar gudan ga motoci nan birjik tamkar kamfanin kera su. Babu abu mafi daukar 32 : KA AURE NI!-I Bilkisu H.Muhd hankali a gidan irin lambunsu wanda swimming pool ya kara kawata shi, ga wasu irin glass carpet da suka yi luf-luf a kasan gidan kana taka kafa sai ka ji wani danshi mai sanyi ya ratsa kafafunka. Gefe daya gurì ne da aka tanadi kayan motsa jiki da liluna kala-kala, kana soma tafiya harabar ma'aikatan gidan za ka fara riska, su ma sashinsu tamkar giwan wani maikudin, ana yi wa gidan lakabi da green house, saboda duk abin da aka kawata gidan da shi kore ne. Daga wajen get maigadi da Adam na zaune rediyo suke sauraro, suka aji wani gigitaccen horn. Da sauri Maigadi ya mike jiki na rawa ya hangame get. Mustapha ya kwaso motarsa a guje sauran kiris ya take wa maigadi kafa, ya yi tsalle gefe duk abin da ya yi masa bai hana shi yi masa sannu da dawowa ba. Wata yarinya ce danya shakaf manne a jikinsa, ko kadan maigadi bai ishe shi 33 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd kallo ba balle ya amsa masa. Maigadi ya gyada kai jiki a sanyaye yaa maida get ya arufe ya koma gudin Adam ya zauna yana mita. "Wannan tsinannen Mustaphan in Allah ya amince ba zai gama da duniya lafiya ba sam ba shi da imani bai san darajar kowa ba, Allah ba zai barshi ba sai ya lalace". "Fata na gari". Adam ya katse shi da fadin hakan, karon mamaki ya kama Adam hakan na nufin ba ka san ciwon kanka ba”. Maigadi ya ce da shi. "Ai komai bai ambata hakan ba Ubangiji ba zai barshi ba, don ba aya zalunci ya kuma haramta shi don ina karkashinsa ba a ce ya maishe ni dabba ba". "Kai kam na' ga alama zuciyarka ta gama mutuwa, matsoraci ne kai in ni ne ke da matsayin da ka ke da shi da yanzu na kawar da wannan fasikar Adam bai cika son 34 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Mund kananan maganganu ba don haka ya mike daga gurin. Gidan Injiniya Sunusi gida ne wanda kowa ke rayuwa ba ruwan kowa da kowa babu wanda ke shiga rayuwar wani, gida ne wanda suke tutiya da boko daga uwa har uba sun kai kololuwa gurin akidar boko bacin akidar bokon sun dauko na Turai sun dora wa kan na bokon, duk abin da za ka aikata a gidan in dai harka ne na Turai to daidai ka yi wayewa ce, don haka kullum Humaida ke tutiyar ita ma tana da nata 'yancin ta ke kuma ganin za ta iya yin abin da ta so babu mai taka mata burki irin rainon da Naninta ta koyar da ita ke nan. Nani janat wadda tunda aka haifi Humaida ita ce mai rainonta, tana wata shida mahaifiyarta ta yaye ta komai nata ya koma gurin Janet. Injiniya Sunusi sam ba sa dawowa gida sai dare, da sun dawo ba su wani bi ta 35 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd kan Humaida, har gwara Mom ta kan leka har ta sha kanta tare da sumbatarta a kunci. Da safe ma in za ta fita hakan din ce ke shiga tsakaninsu Mom laccar ce babu irin dagar da injiniya Sunusi bai da ita a kan ta a je aikinta ba, saboda yana tunanin su ba wa talauci baya har abada, ta nuna masa ita ra'ayinta ne ba ta na yi ne don wani abin duniya ba, tana yi ne don rage wa kanta zaman guri daya, tana yi ne don nishadп haka ya gaji ya sa mata ido. Injiniya ya kan aikata duk abin da ya so da matarsa a gaban kowaye, misali sumba, rikr ta, ba ta abinci a baki, tarairayarta da dai sauransu. Kwanciyar aure ce kawai ba su yi a gaban jama'a, komai nasu irin na Turai ne kodayake zaiiya yiwuwa hakan in muka yi la'akari da sirin shekarun da suka yi a Turai, kuma Turan ma cikin U.S. 8280 et id Injiniya Sunusi duk da shekarunsa ba za ka taba ganinsa cikin manyan kaya ba sai 36 : KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd kanana, ita kam Momcy tsulkewa ta ke tamkar wata 'yar sha biyar, ko da za ta fita i dai ta dora after dress da dan kwalinsa, ciyo talkalmi mai tsini ga uwar kwalliya. kan mance da yawan shekarunta, ta yi bala'in daukar duniya da zafi, babu ruwansu da kowa ba su hulda da dangi, manyan masu kudi su ne abokan mu'amalarsu, su ne danginsu su ne abokansu su ne a kan komai nasu Tun dangi na bibiyarsu har suka koma sun sanya musu ido, yau inda za ka tambayi Humaida ta kawo maka sunan danginta kwaya uku ba za ta iya kawo su ba, sai abokan Dad da Momcy. Adam shi ne kadai ta sani a cikin dangin mahaifinta, sai Mustapha wanda shi kuma a dangin mahaifiyarta. In ka dauke wannan ba za hta iya kawo maka kowa ba. Adam uwarsu daya ubansu daya da Injiniya, sai dai ba shi da wani fawa a gidan, ba shi da maraba da 'yan aikin gidan duk 37 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd kuwa da dan ilimin da ya yi ya sha 'yar murya gurin yayansa a kan ya dauke shi aiki ko da a kamfaninsa ne har kawo yanzu ya kasa ba shi gamsasshen amsa, sai dai ya се ya je gurin Madam su yi maganar, haka zai je gaban Momcy ya durkusa sai ta gama jinshi sai ta ce, me ya rasa? Yana ci yana sha yana sanya sutura bayan nan me ya ke so ko yana son ne a ce ya zama kamar kyadda suka zama? "Halayyarka suna nuna bakin ciki ka 39 ke mana Haka shi ne furucinta gare shi don haka ya zuba wa sarautar Allah ido, hatta ga abincin da zai ci a gidan wanda ma'aikatan gidan suke ci ne. Dakinsu daya da mai ba wa furanni ruwa, yayin da shi Mustapha matsayinsa kullum hauhawa ya ake. Motar da Injiniya ya hau ita ya ke hawa, abincin da ya ke ci shi ake ba shi yana da matsayi mai girma. A daya daga cikin kamfanin Injiniya. fasiki ne na a zo a gani 38 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd ba shi da mutunci, ba shi da kunya duniyarsa ya ke ci da tsinke, yau in ka ganshi ya shigo da wannan karuwar gobe da wata za ka ganshi, kowa ya san da haka, babu wanda ke tsawatar masa. Humaida ce kawai maganinsa, ita din lambaya daya ce. Wannan ke nan. *** *** *** Tana kishingide a doguwar kujera rimot rike a hannunta channel ta ke sauyawa, sannu a hankali ta zo inda ta ke muradi ta aje rimot ta mike ta shiga rausayawa. Mom ta fito daga daki da glass cup rike a hannunta. Ruwan lipton ta ke kurba, kai tsaye ta nufi soket ta off dinsa. A fusace Humaida ta juyo suka yi ido biyu da Mom, ta zumburo baki. "So na ke yi ki ci abinci". Mom ta ce da ita. 39 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd "Ina cikin zulumi, babu abin da zan ci sai Dad ya dawo". "Mai Dad zai yi miki?" Mom ta tambaya cikin yanayin mamaki. Humaida ta yatsina fuska, ta ce. "In ya dawo kya ji". Abin takaici ko kadan amsar Humaida bai fusatata ba, sai ma murmushi da ta yi. "O.K baby ci gaba da gashi". Neman guri ta yi ta zauna, ta ajiye kofin hannunta ta janyo wani magazine da ke kan center table tana karantawa. "Hello my lovely baby". Wannan shi ne sallamarsa a duk lokacin da zai shigo gidan. Ta yi tattaki cikin ihun murna. "My sweet Dad". Tana rike da shi kamar ta shige cikinsa, suka zube a kan doguwar kujera da alamun gajiya a tattare da shi. Ya dan kalle ta. 40 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd "Baby amma kin ci abinci kuwa?" Ta shagwabe murya za ta yi magana, Mom ta taso cikin takun kasaita ta dan rage tsawo ta sumbaci Injiniya a kunci. "Welcome my sweety". Ya kai hannu ya shafi kuncinta, ya сe. "Amma na ga kamar baby ba tą ci abinci ba" Da sauri Humaida ia katse shi. "Ka san ba zan iya cin komai ba". Ya ce, "Me ya sa?" Ta ce, "Saboda akwai maganarmu da kai, ina tsoron sakamakona". Ya fadada fara'arsa. "Oh ni babhy ai wannan karamin abu ne baby, ba abin da za ki nema ya gagare ki ina da komai na baiwa komi ba ya wannan duniyar taki ce". Ta yi murmushin jin dadi, wannan na daya daga cikin halayyarsa, fariya. 41 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd "Ina rayuwar ne gabadaya don na zame miki gata, da zarar ya kawo kanshi zan san abin yi". *** *** *** Daf da magriba Malam Musa yana tsugune a kofar gida, alwala ya ke daurawa, Mu'allim sanye da jesi mai taınbarin Bercelona ya nufi inda mahaifinsa ke alwala. "Abba sannu da gida". Ya fada yana kokarin durkusáwa. "Yauwa mai sunan manya, ka dawo?" Mu'allim ya gyada kai. "Abba ya Kawuna?" Ya ce, "Yana nan sai dai yau jikin 99 nasa ya matsa masa Bai tsaya jin karashen maganar ba ya diba da gudu zuwa dakin, in kana son ganin tashin hankalin Mu'allim to ka itabа kawunsa, yana kaunarsa fiye da komai da kowa. 42 KA AURE NI!-I Bilkisu H.Muhd Kamar zai fashe da ihun kuka yadda ya ga Kawu daddaure kamar wani dabba. "Umma me ya sa ku ka daddaure shi haka?" Ta dube shi da fuskar tausayi, ba ta taba mamaki da irin wannan azababbiyar kauna da Mu'allim ke wa Kawun nasa ba, ta sanyaya murya. "Ba ka ganin yadda ya ji wa kansa rauni? Dole ce ta sanya muka daure shi, in ba haka muka yi ba komai zai iya faruwa, ba ka bira da Abban naka ba ne, shi kansa ya ji jiki". Duban Kawun ya ke daga sama har kasa, idanunsa taf kwalla. "Amma Umma Kawu ya yi dauda da yawa". "Kawunka yana da lafiya kai ma ka sani دو Ya kada kai, Kawun nasa ya kafe shi da ido, Mu'allim cikin muryar rarrashi ya ce. 43 KA AURE NI-1 Bilkisu H.Muhd "Kawu ka yi hakuri na sauya maka wannan kayan ko da ban yi maka wanka ba". Ya kai hannu yana shafar fuskar Kawun nasa. "Ka yi mini magana yau ko da kalma daya ce zan yi farin ciki, ina son ka bude bakinka wanda bai gajiya da furta alkhairi a gare ni, tunda bakinka ya kulle na rasa farin ciki, na rasa abokin shawara, baccina ya yi karnci, zuciyata ta yi rauni". Ummansa da ke tsaye gabadaya ta gama karaya, kokarin rushewa ta ke da kuka. Da sauri ta bar gurin cikin dabara da rarrashi yana shafarsa ya samu ya sauya masa kayan, ya ba shi ragowar fumamen tuwon da Ummansa ta ajiye masa, ya gwammace shi ya hakura. Ya dora masa da ruwa, sannan ya samu ya koma dakinsa. Yana kwance a kan tabarma cike da tunani, ya tsananta tunaninsa a kan yadda zai iya fidda iyayensa daga cikin kangin, talauci. 44 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd Babu abin da ya fi bakanta masa rai da sanya shi jin kunya sai in ya dubi kansa gabjeje da shi a ce. iyayensa wadanda karfinsu ya gama karewa su ke nema su ba shi, mahaifiyarsa ta yi surfe, ta yi wankau ba ta tsinana wa kanta komai ba sai dai ta tattara kudin ta siya masa sutura, sai dai yana daga dakinsa yana jin nishinta na ciwon jiki. Ya kan yi kuka kamar ransa zai fita, gari na wayewa za ta mike ta dora a inda ta tsaya, haka Abbansa zai wuni rana, iska, ruwa duk du kare a kansa sannan ya samo ya yo awò gwangwani daya, biyu ya kawo a dafa. Yana tsaye a kan Umma sai ya ga an take masa kwano... Kiran Abbansa ya katse masa tunani, ya amsa tare da yunkurawa da kyra: Tsaye ya ganshi a dokin kofa. Malam Musa ya kafe dan nasa da ido yana kallon yadda kirjinsa ya jike jagab da 45 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd kwalla ga idanun nan a rine tamkar ya wanke fuska da ruwan barkono. "Mai sunan manya me ya yi zafi haka, me ke faruwa ne? kada ka mance duk halin da za ka shiga, innalillahi wa'inna ilaihi raji'un ya kamata ka fada, shi ne maganin dukkan tsanani, wataran sai labari, me ye cikin rayuwar? Na san tunaninka duk da ban shiga zuciyarka ba kawunka, da mu ko? Тo ka yi hakuri talauci ba abin kunya ba ne, ina kuma godiya ga Allah da ba ka dauko mini magana ba, kai ma ka gode wa Allah da ban zamo mai cin bashi ba, duk talaucin da na ke fama da shi hakan bai sa na bata wayona ba shekaru da yawa kawo yanzu, tun tasowarka babu wanda ya taba yin sallama da ni da zummar na biya shi bashin da na ci wannan ma kadai wata baiwa ce, don haka ka yi hakuri". Ya fada yana murmushi. "Ka kula da Kawunka zan je kauye ba zan wuce kwana uku ba, ka ji ko". 46 KA AURE NI!-1 Ya jinjina kai. Har kofar gida ya raka shi. Bilkisu H.Muhd Washegari ya shiga kujiba-kujibar tsaftace dakin Kawu, ya dibo kayan da ya cire masa jiya ya nufi tsakar gida da su. Umma na shara ya matsa gindin rariya ya soma wanke su, Ummansa ta kwashe shara za ta nufi soro ta zuba a mazubin shara, kai tsaye Humaida ta fado gidan, har tana bangaje Ummansa.. Da sauri Umman ta dube ta baki bude, sanye ta ke da wasu damammun kaya, kallo daya za ka yi mata ka kira ta da karuwa, don irinsu ne suka fi irin wannan shigar. "Subhanallahi, baiwar Allah ya haka?" Mu'allim ya dago kai da sauri don son ganin abin da ya ruda Umman tasa. Ido biyu da Humaida ya yi. Jin komai ya ke yi tamkar a mafarki, gabansa ya shiga wani irin harbawa, ga wani irin tsoro da ya lulluße shi da alamun mamaki karera sanye a fuskarsa. 47 KA AURE NI-1 Bilkisu H.Muhd Ya mike sosai cikin tamke fuska, bakinsa na rawa. "Wa... ya... nuna miki gidan nan, me kuma ki ke bukata a gare ni?" Karara kalamansa sun tabbatarwa Ummansa da ma can ya santa, akwai alaka a tsakaninsu. Humaida ta karasa inda ya ke tana yi masa wani duba. Shagala ta yi da kallonsa. Kyawunsa ya shahara fiye da ganim da ta yi masa farkon haduwarsu. Ta maida kallonta ga gidan a karo na biyu ta sake malida kallonta gare shi, kallon mai lumshe idanu ta ke masa, al'amarin tamkar a shirin wasan kwaikwayo Umma ta ke gani, ta saki baki cike da al'ajabi, shi kam Mu'allim kunyar irin kallon da ta ke masa a gaban Ummansa ya ke ji, satar kallon Umman ya yi, yadda kya ga bacin rai karara a fuskarta ne ya kara ruda shi, ya yi bala'in kaurara murya. "Me ya kawo ki gidanmu?" 48 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd "Zance na zo". Ta fada kai tsaye, "Kо ba ka yi farin ciki da hakan ba?" "I say shut up, na ce me ki ke nema, me zan yi miki ko kina bina bashi ne?" Ya karasa maganar cikin daga murya. Ummansa kam tuni ta shiga sallallami cikin tafa hannaye. "A ina ka samo wannan karuwar?" Ta fada tana kallon Humaida da kayan jikinta ko bi ta kanta ba ta yi ba balle kalamanta su daga mata hankali, maimakon haka ma sai cewa ta yi. "Ya maganarmu, Dad na son ku yi magana da shi?" Bai son ta baro masa aiki, ya fahinci ba cikakken hankali ne da ita ba, don haka da sauri ya katse ta. "Ni ki je ni zan zo". Yana magana yana satar kallon Ummansa wacce ke faman watso masa harare. 49 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd "Kafarka kafata, na sha wahala na bata lokaci sa'annan na iya gano wannan gidan "Au ba za ka raka karuwar taka ba?" Umma ta ce da shi. "Ke tsohuwa ya fa ishe ki haka!!!" Da sauri ya katse ta cikin daka wata gigitacciyar tsawa. "Mahaifiyata ce! Ya ishe ki haka". "Don mahaifiyarka ce sai ta ce da ni karuwa?" Jikinsa har wani tsuma ya ke ya shiga tankadata. "Ki fice kada na sake ganinki a cikin gidanmu. Ni da ke ba mu dace da juna ba". Yadda ya bude murya hakan ya fi komai daga mata hankali, ga idanunsa sun juye zuwa jajaye, ba ta son abin da jama'a za su taru a kanta, ta san halin talakawa abin kallo ba kadan ya ke musu ba za ka ga sun bi shì da kallo, wani zubin ma har sau su 50 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd karo da jifa don haka ta yi saurin ficewa a gidan. Ya sauke ajiyar zuciya ya sanyaya murya. "Umma ki yi hakuri don Allah, haka ba zai sake faruwa ba". Ta dube shi kamar za ta yi kuka. "Mu'allim wannan shi ne irin tarbiyyar a muka koyar da kai? Karuwa har cikin gida da rana tsaka babu kunya? Yaushe ne ka sauya, yaushe ne ka zamo haka?" Cikin rawar murya ya ce. "Wallahi Umma ba zan ha'ince ku ba. ba zan yi miki karya ba, ki amince da ni yau shi ne ganina na biyu da ita, ban san wace cе ita ba, na fi tunanin ko tana da matsala a kwakwalwarta..." "Ba ka santa ba na aga alamar hakan". Duk sai ya kara kidimewa, wasu siraran kwalla suka silalo kuncinta, ta jinjina 51 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd kai za ta sake magana ta kasa. Da sauuri ya fada daki. "Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un". Ya dinga ambata, ya dade bai ganta cikin wannan yanayin ba. Duk da kashedin da Dad ya yi mata hakan bai hana ta dosar kamfanin ba, ko gabanta ba ta iya gani sosai, daga can nesa ta hango shi tare da wasu mutane, ga dukkan alamu rakiya ya fito. Wani mahaukacin birki ta taka, gabadaya suka tsorata sauran kiris daya daga cikin bakin ya tsunduma kwata, da taimakon riko da Injiniya Sunusi ya yi masa yaa koma ya tsaya. Ta ballo murfin mota ata fito cikin kuka ta nufe shi, hankalinsa ya yi matukar tashi, duk ya gama kidimewa. "Gaya mini baby". Ta kaasa magana, ya riko hannunta yana rarrashi, ta ce. "Dad a kan wannan maganar ne na je gidansu ya ki saurarena, ya koro ni, 52 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd mahaifiyarsa ta kira ni karuwa, ya ya zan yi?" Da sauri ya tari numfashinta da fadin. "Ya isa haka, ki je gida in na zo sai mu yi maganar, kin ga yanzu ina da baki. Ina sallamarsu zan zo gidan". Ya riko hannuntaa ya sanya ta a mota, duk bakin nasa na tsaye suna kallon ikon Allah, tabbas inda ranka ka sha kallo. Ya sassauta murya. "Zak i iya tukin? In ba za ki iya ba in sa a maida ki gidan?" Bakin nashi suka shiga kallon-kallo cikin kada kai da takaici. "Dad zan iya” "O.K in kin je ki huta ki ci abinci kada ki yi tunani yanzun nan zan dawo kin ji". Ta kada kai ya sumbaci hannunta tare da shafa mata kai ya koma ya rufe mata murfin motar ta tada mota ya shigaa daga mata hannu cikin murmushi, bai saurare su ba sai da ta bace wa ganinsa. 53 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd "Ya kamata ka koya mata abin da addini da al'ada suka koyar da mu". Wani dan gaza gani a kawar da kai ya fada. Maganar ta sosa wa Injiniya Sunusi rai, ya dubi Alhaji Auwal din wanda shi kadai ne ke iya gaya masa gaskiya duk cikin abokan huldarsa. "Kada ka yi magana ina anusar da kai saboda gaba". A fusace Injiniya ya се. "Me ka ke tsammanin gaba za ta haifar? 'Yata ita ce kadai na mallaka don na biye mata abin da ranta ke so me ye laifi? Za ta je ta yi wa wani ne?" "Okey, na fahince ka, babu abin da gaba za ta haifar". Alhaji Auwal ya mayar da martini. A fusace injiniya Sunusi ya juya rakiyar da bai yi musu ba ke nan. Tsakiyar dare bacci ya kaurace wa idanunsa, tunanin rigimar da Humaida ke son debowa ya hana shi sukuni, wannan 54 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd karon dole ya jajirce, wannan karon ba za ta sami abin da ta ke so ba. Humaida yarinya ce ba ta san komai ba in ya ce zai biye mata don gudun bacin ranta za ta gurbata jininsu, babu abin da ya fi talauci zafi, don wani fannin talauci kan yi bibiya, ba zai rasa arzikinsa saboda farin cikin wadda har yanzu ba ta san wace ce ita ba, ba ta san ciwon kanhta ba. Hajiya Zainab ta janyo bargo za ta kara lullube jilkinta, idanunta fal bacci ga mamakinta ta hangi Injiniya Sunusi zaune, da sauri ta ture bargon gefe tana hamma ata mike ta matso kusa da shi. "Yallabai lafiya?" Ta ce a sanyaye. Bai ce komai ba ta kara shige masa. "Akwai abin da zai dame ka har ya hana ka bacci? A tunanina babu abin da muka rasa, muna da komai". Ya fuskance ta sosai. 55 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd "Humaida ce, Humaida ce kadai matsalata, tana son rusa mini burina a kanta. Humaida kadai na mallaka duk tanadina a kanta ya ke, ba na taba son abin da zai ruguza mata rayuwa. Ya dakata na tsawon minti biyu. "Yallabai kai na ke sauraro". Ya numfasa, "Humaida na son jawo mini rigima". Ta dube shi cikin yatsina fuska. "Ko dai suna son janyo wa kansu rigima?" Ya ja tsaki cike da takaici. "Ki bari mana ki ji karshen zancen". Hakan ya sa ta tsuke baki. "Wani yaro ta gani kwanda ba shi da دو galihu ta dage a kan sai ya aure ta... Da sauri ta katse shi, ta fahinci inda zancen nasa ya dosa. "Okey, na fahinta shi ne ka ke tunani saboda kana son biye mata? Ni kam ban 56 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd laminta ba, ba za a yi wannan abin kunyar da ni ba, ba za ta gurbata mana jini ba". Haka ta yi ta mita ta inda ta shiga ba ta nan ta ke fita ba. Ya daka mata tsawa. "Ke kin ga dakata, na ga kina faman tada jijiyar wuya, ban gaya miki don ki bata mata ba, abin da kurum na ke so ki yi mata irin dabarunku na mata don ki nusar da ita. In kuma ta matsa zan je in ga shi yaron zan iya daukar kowane irin mataki a kansa". Gabadaya hankalinta ya tafi a kan game din da ta ke yi, Momy ta fito daga sashin Injiniya. "To babyn game, a ajiye wayar nan haka ina son zan yi magana da ke". Ta yamutsa fuska cikin sigar shagwaba. "Mom ki bari na kusa kashe bos din". "Na ce ki bari haka!" Ta fada cikin daga murya. Ta sake kankame wayar. 57 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd "Ni fa sai na karasa, tun dazun fa na ke son kashe bos din sai da na kusa za ki ce na ajiye?" huci. Takaici ya sa Mom fincike wayar tana "Game har ya fi maganata, in ce da ke ki ajiye ki ce sai kin karasa, me za ki karu da shi a cikin wayar shashashar wofi?" Ta juya baya cikin turo baki. "LHaba Momy ya za ki dinga yi mini tsawa kamar wata zaburarriya? Ni fa ina da وو' yancin da zan yi duk abin da na ke so". Mommy ta yi murmushi. "Humaida har yanzu ke yarinya ce, amma zan yi maganinki, gabadaya zan yi sanadiyyar da za ki daina rike waya a gidan nan in ga ta tsiya". Humaida ta saki wata dariyar rainin hankali. "Ashe za ki takalo rigima ke nan Mom? Ni fa ko da ki hana ni rike waya gara kin hana ni abinci, waya ta fiye mini duk 58 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd abin da na mallaka, domin lita ta haska mini abin da ke kanki ba ki hasko ba, ta sa na san abin da ke kanki ba ki sani ba". Yadda ta ga Mom ta daure fuska ya sa ta mike tana dariya. ララ "Am sorry mom". Kokarin shigewa ta ke bedroom ta yi saurin dakatar da ita. "Ina son ki sanar da ni abin da ki ka sani wanda ni ban san shi ba. Humaida kyau na tabbatar da ke mahaukaciya ce, ba ki da hankali". "Okey na ji Mom, yanzu gaya mini abu daya wanda ni ban sani ba". Duk da Mom ta ji ciwon kalaminta sai ta kanne, ta janyo hannunta. "Zauna na gaya miki. Tare suka zauna ta fuskance jta sosai, ta ce. "Kin ga abu na farko na yi aure, na biyu na san daukar ciki na kuma san zafin 59 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd haihuwa tunda ga shi na haife ki kina gaya mini magana... "Madam ke da wa ki ke faman hakilo haka?" Muryar Injiniya ta katse ta, da sauri Humaida ta mike ta tare shi suka zube a kukjera, ya dubi Mom. "Na sha gaya miki ki dinga bin ta a hankali, saboda har yanzu ba ta gama hada hankalinta ba". Ya shafo fuskar Humaida ya koma ya sa hannu cikin aljihu, katin waya ya dauko na dubu biyar, ya yi bala'in sanyaya murya. "Ki yi amfani da shi zawa gobe, ya ya ne baby ki saki fuska mana ki mance da Mom dinki, ki gaya mini in kuma akwai wata matsala". Ta shagwabe murya kamar za ta yi kuka. "Dad, kullum Mom na yi mini gorin 95 aure. Ya lakuce mata hanci. 60 KA AURE NI!-1 Bilkisu H.Muhd "Rigimatuna, na ce ki rabu da ita za mu rana Ta shiga kunkuni. "To na ji, gaya mini me ki ke son na yi a kai?" Ya tambaya yana kallon Mom wadda ta yi bala'in daure fuska. "Dad ka aura mini mutumin nan, na ji abin da Mom ke yi mini

Chapter 2 of 5