Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
8 / 8
aure. Cikin yan mintuna suka bibiyeta da congratulation, Amrah ce ta fara kiranta a waya cike da farin ciki take magana.  Congratulation ™awata kece akwai wani shagalin nan gaba. Dariya Bhatool ta yi sanan ta ce.  Bai fi wata Waya ba fa.    Ke dan Allah, muna cikin Alheri.    Tsamo-tsamo ma. Bhatool ta faWa tana dariya, daga nan sula shiga hira da sauran ™awayen na su har zuwa 12 na dare sanan su ka yi sallama.   A anagaren Dad kam ya kasa zaune ya kasa tsaye kalmar  Akwai Matsala. Da justice ya faWa masa kaWai ta ka Wa masa hanjin cikin sa. Waya ya Wauka ya ™ara kiran justice Audu amma bai Waga ba, sai dai ™arar warn da ya ji  ya sa shi tabbatar da cewa Audun ya ™araso, ta shi ya yi ya yare shi acan su ka yi wancan part Win. Bayan sun zauna Dad ya ce.  Audu mene matsalal?. Kallon Dad Justice Audu ya yi sanan ya ce.  Yunusa kasan me?.    FaWi mana.  Yarinyar nan yar gidan Habiba ce.  Wacece Habiba kuma?.  Habiba dai da ka sani, Habiba ta ka. Justice Audu ya faWa yana kallon yanayin Dad.  Ni fa bangane ba Habiba wacce. Ta shi ya yi ya matso kusa da Dad sanan ya ce.  Habiba wacce kasani guda Waya, matar da ka so kamar ranka, matar da ka so kamar ka yi hauka.    Innullahi wa inna illahir raji un! Justice kama nufin Habiba ce ta haifi yarinyar da Usman ke neman aurenta?.    Tabbas ita ce, ita ta haife ta har da wasu ma guda biyu. Mikewa Dad ya yi ya fara tuna lokutan baya da suka huce, irin soyayyar da suka shimfiWa da Habiba, irin ™aunar da ya nuna ma ta, yana tunanin ko Senate a yanzu bai yiwa Bhatool irin son da ya yi wa Habiba mahaifiyar Bhatool ba. ~~~~~~Years Back. A lokacin kallo Waya zaka yi wa Dad ka ga kammanin Senate Sak a tare da shi, sai dai Senate ya fi shi jikim hutu da gayu, A lokacin Dad yana tsaka da neman kuWi a kasuwa, kasuwanci shi bai yi wani nisa ba amma a hakan ma yana samu dai-dai gwargwado. Ranar wata juma a, bayan sun dawo daga Sallar juma a shi da Abokinsa Audu su ka yanke shawarar shiga cikin unguwa neman abinda zasu ci, sakamakon gajiya da abincin cikin kasuwa.  Wani gidan da ake siyar da abinci su ka tsaya, ganin samari ™ofar gidan suna tsai-tsaye, a lokacin ne Habiba ta zo shiga gidan tare da ™awarta, tun a kallon Farko ya ji wani Abu ya ratsa shi, wani ba™on yanayi ya ziyarce shi. Audu ne ya yi magana da su domin shi kam Yunusa ya yi nisa cikin Habiba.  Yan mata dan Allah me da me ake siyarwa gidannan?. Habiba ce ta  tsaya ita kuma ™awarta ta shige ciki, domin irin matan nan ne masu jin kai.  Taliya da wake, sai kuma gurasa da miya.  Yawwa dan Allah, za ki iya amso mun taliya da waken?. Audun ya ™ara tambaya.  Kawo. KuWin ya mi™a ma ta sanan ya ce.  Mai za a siya maka?.  Koma mene ta siyo. Ido ta Wago ta kalleshi, ita ma take a lokacin ta ji wani abu ya ratsa zuciyarta, irin kallon da yake ma ta ya shige ta.  A a ka faWa me za a siyo ma ka.   Ta ba shi amsa.  Si yo gurasa to. Ba ta ce komai ba ta shige gidan. Bayan ta shige gidan ne, ya kalli Audu ya ce.  Abokina wallahi na sami matar aure. Dariya Audu ya yi sanan ya ce.  Ai tun kallon da kake ma ta na fahimci haka, Abokina kar ka yi wasa ita dama sau Waya take zuwa a rayuwa.    To ta ina xan fara?.    Ya kake Abu kamar ba ka san yadda xaka fara ba?.    Audu kasan ban ta Sa kula mace ba ko?.  Amma ai kana da  yan matan. Tsaki ya ja sanan ya ce.  Kamar ba ka san sune ke kawo kan su ba.  Yanzu dai ka fara tambayar sunanta, da gidansu, daga nan zaka san yadda zaka bi da ita.  Angama abokina. Suna tsaye ta fito ri™e da ledar, ta mi™a mu su.  Mun gode. Audu ta faWa, shikuma Yunusa ya ce.  Yan mata anan gidan kike?. Girgixa kai ta yi sanan ta ce.  A a, nan baya na ke.    Ina ne nan baya kuma?. Murmushi ta yi mai sanyi sanan ta ce.  Layin dake bayan wanan.  Ohky, nagane toh amma ai baki fadan sunanki ba,  kuma ni na faWa miki nawa.    Bala fadamun ba Allah. Ta ba shi amsa cike da shagwaSar da ta ™ara burgesa.  Anya kuwa bam fadamiki ba. Ya faWa cike da wasa.  Allah dagaske.    Toh, sunan Yunusa.    Ni kuma Habiba. Daga nan suka fara yar hirar, wacca ta jawo shakuwa sosai a tsakaninsu, tun daga wanan lokaci Yunusa ya dawo siyen Abinci a wana unguwar, hakan nan zasu tsaya su yi ta hira shida Habiba, a hankali sha™uwa ta na ginuwa tsakaninsu, soyayya mai ™arfi ta shiga tsakanin su, wacce shi Yunusa ya sa ni amma ita Habiba ba ta san ta yi nisa cikin kogin ™aunarsa ba.  A haka shekaru su ka fara tafiya, har ta kai ga Yunusa yana zuwa takanas wajen Habiba, duk da ba ta ba shi damar tsayawa ™ofar gidansu ba, domin tasan a tsarin mahaifinsu da zarar yarinya ta tsaya da saurayi a ™ofar gida to daga wanan lokacin zata fara ™irgan raguwar kwanakin da zasu rage ma fa a cikin wanan gidan, kuma dukkanin yayyunta mata da suka yi aure mahaifinsu ne ke xaSa musu miji, wasu ma ba sa sanim waye mijin sai bayan an kai su gidan mazajen su, Amma habiba ta kasance mai fatan cewa mahaifinsu ya canja tsari akan ta.  A haka aka Wauke shekaru biyu suna tare, har ta kai ga Yunusa ya yi wa Habiba maganar cewa yana son ya tura iyayensa, sai dai ba ta ba shi dama ba sai cewa ta yi ya Wan ba ta lokaci kaWan, ko da ta zo gida ta yi magana da yayarta sai cewa ta yi.  Ki gwada sa ar ki, ki ba shi dama yazo tun da sauran dai ba su ta Sa tura maneman na su ba. Haka Habiba ta Wauki shwarar Yayarta ta sanar da Yunusa cewa ya gwada tura iyayensa.  Ranar da Yunusa ya tura iyayensa, ranar mahaifin Habiba ya sanar da su cewa ya daWe da fitarwa da Habiba miji, da wanan su ka dawo gida suka sanar da Yunusa, ta shin farko Yunusa ya faWi ™asa sumamme. Hakan ma Sangaren Habiba a ranar mahaifinta ya sanar da ita cewa ya fitar ma ta da miji kuma nan da makwanni biyu za a Waura ma ta aure, ta fara lissafa kwanakin da suka rage, Habiba ta kaWo matu™a da jin wanan lamarin, ta yi kuka ta yi kuka kamar ranta zai fita, ganin ta na neman har gitsa musu gidan ya sa mahaifinta haramta ma ta fita har zuwa ranar da za a Waura aurenta, tun daga wana lokacin Habiba ta shiga damuwa, kullum kuka babu ci babu sha, cikin yan kwanaki ta rame ta fige ta fita hayyacinta. Haka Sanagaren Yunusa ma, kullum sai yazo unguwarsu Habiba, kullum nan yake yini ko zai samu ganin ko giftarwa Habiba ba ya gani, daga baya ya yanke shawarar tun karar ™awarta, sai dai ta tabbatar mai da halin da Habiba ke ciki, tun daga hukuncin sa mahaifin ta ya yanke na Waura ma ta aure cikin yan kwanaki ™alilan, da kuma hukuncin hana ta fita gaba Waya, sanan ta gaya masa halin da take ciki na ™unci da damuwa.  Daga page 20 za mu gama Free pages, in sha Allahu ranar monday xamu fara paids page, a kan kuWi Naira 500 ta wanan asusun. 8129553971 Opay sani Muhammad lawan. Gobe da safe zan sako muku last free page, shafi na Ashirin.  *HASASHEN SOYAYYA*d'ŝ =Ĝ%Ŭ>ĜyŬ _Imagination of love_     _Stroy and written_              By    Sayyid (Legend's pen) 'ŝ    *FUTURE WRITERS ASSOCIATION* *(FUWA)=Ĝ‹Ŭŝ=ĜÚÜ*     *The Fearless Writers Team*   _Marubuta masu tsage gaskiyya_ *BISMILLAHI RAHAMANIN RAHIM =ĜOŜ=ĜĞÜ* _Page 20_ Last of Free pages& .. A cikin kwanaki ™alilan Habiba ta fita a hayyacinta, ta rame ta canja gaba Waya, kuma hakan bai dakatar da mahafinta kan ™udirinsa na aurar da ita ga mutumin da ba ta san shi ba. Ranar da makwannu biyu suka cika, ranar aka Waura auren Habiba da Ahmad mutumin da ba ta san shi ba, ba ta san ko sunan sa ba sai ranar, Habiba ta gigice bayan Waurin auren, amma ganin an Waura auren ya sa ta ha™ura ta fawwalawa Allah komai, tasan hakan ya zaSa ma ta, ta koma tausayin Yunusa da halin da yake ciki, ta dai na tausayin kan ta gaba Waya.  Yunusa kam yana lisaafe da kwanakin auren Habiba, domin ranar Waurin auren har ™ofar gidansu yazo domin tabbatarwa da kan sa, ya matu™ar kaWuwa shima, ya koma tausayin Habiba da halin da zata shiga, ya bar tausayin kansa. Bayan dawowarsa gida ne ya ga babu amfanin zaman shi cikin garin Yobe, hakan yasa ya tarkata ya bar garin Yobe zuwa Kano, ya sha matukar wahala a kano kafin ya mance da tunanin Habiba, ya fuskanci sabuwar rayuwa da sabon sauyi. Habiba kam sai da ta ™ara sati guda a gidansu kafin a kai ta na ta gidan, sakamakon doguwar jinya sa ta yi, Ahmad mijinta mutum ne mai zurfin tunani da hakuri, yasan Habiba ba ta son shi shima kuma hakan, domin umarnin mahaifinsa ya bi, hakan ya sa ya yi amfani da iliminsa da tunaninsa ya dinga bin Habiba sannu a hankali yana hakuri da halayenta, har zuwa wasu shekaru da ta yarda ta karSe shi a matsayin mijinta, ta man ta da Yunusa.  Haka shima ya Wauke shekaru da son ta a ran sa, domin har san da ya haWu da matarsa ya aura bayan ya samu abin hannu ya dawo Yobe state, ko da ya dawo tunanin Habiba ya sake dawo wa sabo cikin rayuwarsa, da ™yar ya dinga ya™i da zuciyarsa a kan ta. Wanan shine labarin Mahaifin Senate da Mahaifiyar Bhatool.  Ci gaba.  To Amma Justice aina kasamu wanan tabbacin?.  A binciken da na yi a kan lamarin auren mana.  Amma Justice idan haka ne ai bai kamata na hana auren Senate da  yar wajen ta ba, ina ganin kamar Allah ne ya tsara kasancewar su tare.    Yanzu zaka iya zuba ido Wan ka ya auri  yar Habiba.  Justice kenan, mai Habiba ta yi mun a rayuwa ban da alheri, sanan shi kan shi mijin Habiban ai ba shi da laifi.  To ai mijin ma ya rasu, shekaru da dama.    Allah ya yi masa rahama, amma akan wanan dalilin bazan hana auren su ba. Daga haka Dad ya shige ciki ya bar justice. Šakin Mom ya shiga, tana zaune gefen gado tana faman tunanin halin da Wan ta zai shiga idan ya rasa auren Bhatool. Da sallama Dad ya shigo, amsawa ta yi ba tare da ta Waga ido takalleshi ba, zama ya yi gefenta sanan ya ce.  Fushi kike da ni?. Girgiza kai ta yi kawai.  Justice ya zo mun yi magana da shi, kuma ya faWamun dalilansa.    Tom yanzu me ka yanke?.  Na yanke shawarar nema masa aurenta, domin dalilin da ya ba ni ba wanda zai hana aure ba ne. Da murmushi a fuskar mom ta juyo sanan ta ce.  To ko kai fa, amma da ka Waga hankalina ka Waga na Wana.    To yanzu sai ku sauke shi ko, domin gobe sa safe ma zan tura aje gidansu yarinyar, kuma har da ni za a je.  Alhamdulillah ya rabbi.   ~~~~~Bhatool& . ˜arar da wayarta ke yi ne ya tashi daga baccin da ta koma bayan ta yi sallar asuba, hannu ta kai ta Wauke tana jan tsaki, ba tare da ta kula da mai kiran ba.  Hello. Ta faWa murya cike da magagin bacci.  Bhatool. A zabure ta mi™e jin muryar Dr Hisham.  Na am. Ta faWa a tsorace.  Bhatool aure zaki yi?.    Innullahi wa ina illahir raji un. Ta furta a zuciyarta, a fili kuma sai ™ara cewa ta yi.  Waye?.    Dr Haisam ne.  Ina kwana?.    Bhatool tambayar ki nake fa.  Ni ba auren da zan yi, bikin Suhaima fa a ke yi.    Nasan ai bikin Suhaiman ake yi, amma ke ma ai aure zaki yi ko?.   Shiru ta yi ba ta iya cewa komai ba, sai zallan mamakin yadda a ka yi yasan da maganar.  Toh Bhatool, ki je ki yi auren kin ji, zaki ga ni a idonki. Daga haka ya kashe wayar, shiru Bhatool ta yi  wanan wace irin masifa ce, waye yasan ma zan yi aure?. Ta tambaye kan ta, amma sanin babu mai ba ta amsa ya sa ta yi shiru, ™ofar Wakin aka buga sanan a ka ce.  Wai yau ba zaki fito ba?.    Gani nan Yaya. Ta faWa tana mikewa, a falo ta sami Yaya Karima da mijinta suna zaune, ™arasawa ta yi inda suke sanan ta ce.  Ina kwana?.    Lafiya kalau Bhatool, kin ta shi lafiya?.  A a Yaya da matsala Babba.    Wace irin matsala kuma, ke fa mahaukaciya ce. yaya Karima ta faWa.  Ba irin wanan matsalal ba ce, kuma ni bake nake wa magana ba, Yaya Ka na ji?.    Ina jinki Bhatool.  Akwai wani malami a makarantar mu Dr Haisam, ya ce yana sona, kuma Wan iska ne kowa ya san shi a makaranta, ranan ya yi mun baraxana na zo na faWawa Yaya Karima, yau kuma ya ™ara kirana yanzu wai aure zan yi ko?.    Ai ina ya samu labarin zaki yi aure to?.  Nima Yaya bansani ba wallahi.    Yanzu da safe nan mahaifin senate ya kira ni, bayan na je ya sanar da ni yana so zai ce ya samu su kawu yau shi da yan uwan sa, a sanya lokacin aurenku na yi tunanin ke ma bakisan maganar ba?.  Yanzu dai nasan magnar da kafaWamun. Bhatool ta faWa sabida ita gaba Waya ta tsorata da lamarin Dr.  To amma shi ina ya sa ni?. Yaya Karima ta sake tambayarta.  Wallahi bansani ba Yaya.    Ba ni lambarsa kawai. Mi™a masa wayar ta yi yaWauki lambar.  Ki ta shi ki je ki yi breakfast. Yaya Karima ta faWa ma ta.  Tom. Ta faWa tana mi™ewa zuwa dinning, gaba Waya jikin ta ya mutu.  ~~~~~~Hausari& .. Gaba Waya yan uwan Mahafinsu Bhatool ne zaune a Wakin Goggo Larai, cike har da Furai da Habi wayanda suka kawo gulmar, wacce suma ™arya suka shirgo abun su.   Ku maimaita abinds ku ka faWa. Isiyaku ya faWa, wanda shine mahaifin Habi kuma yayan wanda suke son bawa Bhatool Saddi™u, Furai ce ta fara magana.  Daman mun sami labarin cewa Bhatool tana shirin barim gari ne, ita da Yayarta da mijin yayarta, sanan Abdul za su tafi ™asar waje shi da mahaifiyarsa da yarinyar da yake son aura har da iyayenta.    Kutumar b***a u**a. Šan ladi ya mako wata ™atuwar ashariya, sanan ya Wora da cewa.  Lallai yaranan  yan iska ne, mun sun mayar da mu banzaye kenan ko me, Shi Abdul Win har ya yi kuWin da zai tafi ™asar waje da iyayen yarinyar da zai aura, mu gamu anan shashashai.    Ai yaron da manyan yan kasuwa yake mu amala dole ya yi kuWi, amma sabida ba™at zuciya irin ta uwarsa ba zata ba shi umarnin xuwa nan cikin dangin ubansa ya nemi aure ba shine ta tura shi duniya. Isiyaku ya faWa rai a Sace.   To ni yanzu so  nake mu yi musu dirar wuri, a yau Winan a Waura auren Bhatool da Saddi™u, sanan shima Abdul a Waura masa aure da Sajida yar wajen ka Šan ladi, shikenan a raba komai.    Tabbas Larai kin yi basira kin yi tunani, kuma kin cika babba. Auwala ya faWa wanda shine Wan autan su.  Yanzu yaushe zamu samesu?. Isiyaku ya faWa.  Ai yanzunan zamu je, ayi komai da a kan lokaci. Zasu san girman dangin uba.   GIRMAN DANGIN UBA=ĜŜ=ĜŜ 1 Dangin mahaifin su Bhatool zasu Waura ma ta aure yau? 2 Idan mahaifiyar senate ta san asali ala™ar dake tsakanin mahaifin senate da mahaifiyar Bhatool zata bari ayi auren? 3 Mahafin senate zai je nema masa auren Bhatool,amma dangin mahaifinta sun neman riga shi, shin wane zai auri Bhatool? 4 Aina Dr Haisam yake samun bayanai, zai iya ha™ura da rashin Bhatool? 5 Idan Senate ya samu auren Bhatool zai iya cika al™warin da ya Wauka, ita ma Bhatool za ta yi biyayya ga Senate? Mu haWu a cikin paids page na Hasashen soyayya, wanda zai fara zuwa ranar littinin idan Allah yakaimu, ba jira sunan jirgin namu.  Naira Wari biyar kuWim tikiti. 8129553971 Opay Sani Muhammad lawan Shaidar biya 08129553971 Legendspen An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 8 of 8