Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
6 / 6
da Haule suka gaisa Ibrahim ya ce haba gaskiya mana naga mutuniyar tawa tana ta faman washe baki, ashe bakuwa ta yi kawa ce tazo ni nasan wannan fara'ar 76 ba a banza ba. Na ce kai yanzu har ka gane irin farir. cikin da nake ciki? Ya ce ai ya zame min dole, nima a taya ni farin ciki na ce na mc kuma? Ya ce Can uwana Sadik ya kusa dawowa jibi i yanzu in Allah yaso zai dawo ya gama karatunsa gaba daya, na ce ikon Allah kenan, ni dai Sadik din nan tunda nake ban taba ganinsa ba, ko a hoto ma. Ya ce e haka ne ina kuwa da hotonsa na kawo miki ki gani sai Nusaiba ta ce to karewar hoto ma abin da jibi zai dawo, ta ganshi, ido cikin ido, na ce gaskiya kam, kuma wani abin mamaki duk sa inda zai zo gidan nan sai an sami sabani ko na tafi kauye ko kuma ina gidan aunty Rabi. Sai dai in ji yazo ya koma kuma tunda yake yo waya ba ku taßa yin yakanar ku ban mu gaisa ba, daidai da rana daya. Nusaiba ta ce kin ga kuma Allah ne bai yi ba, don rannan har zance ki zo ku gaisa ta wayar da Yayana Sadik sai na tarar kina barci, sai na kyale ki na ce ai ba komai in yazo na ganshi haka muka ci gaba da hirar mu har wani lokaci sannan muka tashi. ** ** Yau ne ranar dawowar Sadik, saboda haka Alhaji yasa aka shirya masa yar karamar liyafa a nan gidan domin taya murnar kammala karatunsa na digiri, duk gida ya cika da kamshi sai gyare-gyare muke ta yi mun gara ko in na har dakin da aka 77 mallaka wa Sadik mun gyara shi, ya yi fes muka shiga kitchen muka kama soye-soye da hade Iemuka kamar su inja da yake Haule na nan duk da ita muka dinga yin aikin. Bayan mun gama komai ne, Nusaiba ta cc, to sai ajc a kure adaka, domin yau ce ranar da zamu nuna wa dan uwanmu farin cikin kammala karatunsa. Na ce, kai Nusaiba kina ji da Yayan nan naki, sai ka се Sarki sai aman karrama shi ki ke ta yi haka. Ko dai da wata a boye ne? Ta yi dariya a'a,a'a wallahi ba komai sai zumunci kin san yanzu mutane sun watsar da zumunci, sai dai dai ke yinsa, na ce haka ne kam ya kamata kam mu dinga rike zumunci domin naka naka ne, duk tsiya ko ka guje shi tilas ka koma masa. Muna birar mu muna shirya wa sai ga Ibrahim nan ya ce to ku fa yi saurin kammala komai domin Alhaji ya ce ga su nan sun kusa isova. Ai cikin sauri muka shisshiga wanka muka fara tsala kwalliya ke kya cе gasar kyau ta duniya zamu shiga, sai da muka gama shiryawa tsaf sannan muka fito muka zazzauna. Nusaiba ta dube ni ta ce kin ga kuwa yadda ki ka hadu? Na ce kai kema dai da zolaya ki ke ta ce ki tambayi Yaya Ibrahim ki ji na ce ai shi dama haka zai ce mana, cikin wannan maganar sai ga yaya Ibrahim ya shigo da camera a hannunsa, ya fara daukarmu a hotuna gaba dayanmu sannan ya ce in zo mu yi tare na ce a'a ka bar shi kawai ya nace sai mun yi ganin mami ne ya sani yarda domin kar ta ce ina wulakanta danta, sai da muka yi kusan 78 hotuna kala goma sannan ya hakura muna wannan budurin ne sai Mami ta ce in zo ta aike ni gidan wata kawarta, kafin su zo na'ce to na dauki mayafina ta bani aiken, Haule ta ce in tsaya ta sai Nusaiba muka bari. Muka tafi dan da nan muka je, muka dawo a lokacin motar Alhaji na nan hakannen ya tabbatar mana cewa sun dawo, haka kawai sai naji gabana na faduwa, na ce da Haule, gabana faduwa yake yi haka kawai, ta ce kila ambatonki aka yi, na ce wallahi kuwa, ko ambaton Ibrahim ma kawai ya sani faduwar gaba. Muka yi dariya baki daya, yayin da muka shige cikin gidan. A zaune na same su a falo, yayin da bakon namu ke fuskantar cikin falon, su kuma suna fuskantar kofar shigowa hakanne ya samu shiga ciki domin mu sami ganin bakon sosai, sakon Mami na fara idarwa kafin in zauna, shi kuwa bakon yana ta zuba musu hira naji kamar muryar wanda na sani, shekaru masu dan yawa kamar shida, don haka nake ta Allah-Allah Mami ta ganma fada min abin da zata fada min in juyo in ga ko waye, mai wannan muryar Abubakar na ji Haule ta yi kiran sunansa na yi saurin juyowa in ga wannan Abubakar Haule ta sani cak na tsaida numfashina yayin da naga wanda Haule take kira a daidai lokacin daya kira sunanta sai tayo masa nuni da in da nake tsaye ya biyo saitin hannunta da ido muka yi ido hudu cikin wani irin mamaki ya ce "Hamdiyya." bakinsa a bude.... Kash! Ma su karatu, a kara hakurin kashi na biyu dan jin yadda zata kasance, nasan za ku ce ina Aljanin nan? To yana nan tare da su duk abin da ya yi a baya 79 wasa ne a yanzu ne zai fara gwara kansu, ku dai biyo ni a cikin Sharrin Jinni kashi na biyu ku ji yadda kauna ta ke raba kauna sannan wata da daddiyar tsohuwar kauna tazo ta hada su bayan tsananin wahalar da aka sha kamar rai zai fita. Amina Abdullahi 'yar mutan Sharada. 08085389470 80 LITATTAFAN MARUBUCIYAR ZAZZAFAR KAUNA 1, 2 & 3 TALLAFIN KAUNA 1 & 2 SIRRIN JUNA 1& 2 HAKURI DA MASOYI 1 & 2 RASHIN HALACCI 1 & 2 TSAYA KALLON RUWA... 1 & 2 SHARRIN JINNI PRINTED BY: AL AMINNG PRINTING & PUBLISHING COMPAN ANDAW O CITY 0802 An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 6 of 6