Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 6
je gidanmu. Ya yi murmushi amma dai ba ki yi wata biyu ba? Na ce uhm zancen ka ke so, kaje ku gaisa da Aunty sai in fito mu tafi ya ce 61 to ya bi bayana har ciki ya shiga Aunty ta yi masa sannu da zuwa suka gaisa sannan na ba da kayana ya taimaka min muka yi sallama da Aunty Rabi muka rankaya. Tunda muka koma makaranta karatu muke yi gadan-gadan da mun taso kuma a gida Ibrahim ke mana lesson, yana kuwa koya mana abubuwa da dama, ta yadda zamu dinga fahimta, haka dai muka dings katu ba ji ba gani, duk lokacin hutu a gida nake yın sa wato can kauyenmu gidan su Inna. Hakika vanzu ni kaina nasan na hadu sosai don in kin gan mu ba za ki banbance mu da Nusaiba ba, domin sar k za ci nima 'yar gidan ce, gashi Mami da Ahaji suna matukar kaunata saboda akwai biyuyya ga ladabi da hakuri. Ira zaune ni kadai a falo ina karatu yau Mami sun fita ita da Nusaiba, da yake lahadi ce ranar hutu. Shi kuma Alhaji ya yi tafiya kusan kwanansa hudu baya nan sai Ibrahim wanda yake dakinsa a zaune yana nazarin wasu takardu da Alhaji ya ba shi. Can sai gashi ya fito ya same ni a falon shima ya zauna ya dube ni muka hada ido ya yi murmushi ya ce yau ina kawar taki? Na ce sun fita da Mami yanzu ta ce ma in ka fito in fada maka kar ka fita tana dawowa yanzu, tana son ganiuka. Ya ce shi kenan ke me 62 yasa ba ki bisu ba? Na ce bana son zuwa ko ina nc, ya ce rabon mu yi hira ne, ya hana ki fita domin na fuskanci Allah ya zuba miki kunya duk lokacin da nazo domin in taya ki hira sai ki dinga nuna jin kunyar Mami to yau dai bata nan, na yi murmushi ai kasan kunya wata aba ce da Allah ya halicci mutane da ita musamman ma ga mu mata, domin duk yarinyar da bata da kunya kai koma matar aurc in ma takaice maka kowacce irin mace ce aka ce bata da kunya sai kaga darajarta tana zubewa, ba ma ga mazan ba har ga matan ma, ya yi murmushi nima ina son yarinya mai kunya kamar ke, na dube shi na yi murmushi na ce, sai ka yi kokari ka samu, ya сe ai na samu, na ce ya yi kyau au ba ki tambaye ni wacece ba? Na cc ai ba sauri ake ba, zan sani ko ba yanzu ba, ba ki dai damu da sanin ba kenan, uhm Ibrahim kenan to wacece? Wallahi wata yarinya ce tana nan doguwa amma ba can ba fara sosai, tana da dogon hanci da manyan fararen ido bakinta dan karami la66anta masu matukar laushi ga wushirya nan siririya a bakin in ta yi murmushi kumatun ta yakan lotsa tana da dogon gashin kai mai santsin gaske, ga muryarta mai dadin sauraro kuma......na dakatar da shi ta hanyar daga masa hannu domin na gano da wacce yake wato da ni yake saboda duk kamannin da ya zana kamannina ne, don haka na mayar masa da martanin cewa, a ita wannan da ka 63 ke so din tana da masoyinta wanda zata aura. Sun riga sun yi alkawarin aure ba tun yanzu ba, don haka sai ka yi hakuri ka nema a gaba, ya rumtse ido cikin rashin jin dadin abin da na ce ya ce tabdijan aiko ban ga abin da zai raba ni da ke ba, na yi dariya, au yanzu ka fito fili kuma ka fada min, to ai shukar dusa ka ke yi domin an riga ka. Waye ya riga ni? baka san shi ba a garinmu yake, koma waye ba abin da ya yi min zafi dashi, sai na kafa gwamnatina, na ce amma kana da babban aiki a gabanka ya ce wannan aiki ne? Abin da na sa kaina ne fa? Na ce zan sa ido in yi kallo. Tun daga ranar da muka yi wannan magana da Ibrahim sa na shiga 6oye masa kaina bana yarda ma wani abu ya hada mu domin mun fi sati biyu ba mu ga juna ba bare ma wata magana ta kara hada mu, haka muka zauna har tsawon wannan lokaci. Rannan ina zaune a dakinmu yayin da Nusaiba ke ta fafutukar hada mana kayanmu tana jerawa a cikin wardrop dinmu, an ga mu mana guga ni kuma ina warc uniform din mu daga cikin gugar sauran kayan sai ga Yaya Ibrahim ya shigo fuskar nan tasa a daure ya ce da ni maza ki je ki gyara min dakina yanzu, ba musu na ce to, na mike na ce da Nusaiba ci gaba kafin in dawo ta ce to na bi bayansa zuciyata cike da tunanin nasan ba gyaran dakin zai sani ba, domin bai taßa sa ni ba, sai da naga alamar mamaki 64 ma a fuskar Nusaiba, domin itama tasan ba ya sa ni aiki. Ina shiga dakin naja na tsaya, domin shima tsayawar ya yi, ya juyo ya kalle ni zauna ga kuj era nan magana nake son mu yi na ce to kawai na sanmi guri na zauna ina fuskantarsa ya ce Hamdiyya ba ki san abin da yake faruwa ba ko? Na cc cikin fargaba me yake faruwa? Ya yi murmushi ba komai da wasa nake miki amma wallahi naje gidan Aunty Rabi ta ce babu wari saurayi da ki ke dashi, har ku ka yi alkawari don haka ni dai in ma jamin rai ake yi don Allah na jemu haka a daure a karfi soyayyata, na ce kaima dai da komo da hannun agogo baya ka ke wallahi, na gaya ma ina da saurayi kuma shi zan aura to a name zaka damu kanka, to ai an gaya min abin da ki ka fada ba haka ba ne. Na ce wallahi itama Aunty bata sani ba, ni fa ban yarda ba saboda haka ni dole ma a soni. Uhm shi kenan tunda ana soyayya dole ma ji ma gani. Ina tafe a harabar gidan ni kadai sai ga Ibrahim nan da saurinsa, ya karaso in ia nake ya ce tun dazu fa nake miki magana kina jina wai me na yi miki ne? Na juya na kalle shi na ce, haba Ibrahim wallahi abin da ka yi min ban ji dadin shi ba, ko kadan ya ma za'ayi kaje ka sami Aunty ka hada ni da ita haka kawai yau naje ta kama ni da fada har tana cewa zata je gida ta hada ni da Innata, bayan na gaya 65 maka gaskiyar lamari wai ana soyayya dole nc? Ya ce na gaya miki ana yi kuma koma ba a yi daga kanki za'a fara bari ma Alhaji ya dawo sai na sanar da shi kuma in ce kin amince min, ban san sa in da hawaye ya zubo min ba, na ce shi kenan da ma ba kauna ta ka ke yi ba domin da kana sona zaka so abin da nake so, shi so duk sona ana sonkai ya fi saboda haka ba zan faranta wa wani ni kuma nawa ran ya yi baki ba, a nan na bar shi saboda takaici na sami guri na kebe ina ta faman kuka saboda 6acin rai. ** ** Aunty Rabi ce zaune ni kuma ina gefenta can waje da ya kuma Ibrahim ne Aunty Rabi ta ce Hamdiyya har yanzu na fuskanci akwai kuruciya a tare dake yaron nan tsakani da Allah yake kaunarki shi ko Abubakar kila ma yanzu ya mance da ke banga dalilin da zai sa ki like masa kamar kaska ba. Ibrahim ya ce wallahi aunty irin kaunar da nake wa yarinyar nan ba zan iya misalita ta ba da zan iya hakura da Hamdiyya da tuni na hakura da ita saboda haka ni ki hada ni da wani muje in sami Innar da kuma Baba Tasalla in yi musu bayanin abin da ke faruwa tunda ke ta ki jin maganar ki kila su taji tasu dan dai ma ban san garin ba ne da tuni naje, Aunty Rabi ta ce ai hakan ma za'a yi kawai ina 66 jin haka sai na sa musu kuka domin na san in har ya je gurin su Inna za su ba shi goyan baya. Rabi ta cс ai kuwa komai kukan ki dole aje ka bari ni zan kai ka da kaina." Ya ce shi kenan Aunty zan zo mujc, ya dube ni ya ce taso mu tafi gida." Na ce cikin kuka ka yi gaba zan taho Aunty ta ce ai dole ne ku koma tare tunda tare kuka za kaje ka jira ta a mota, ba musu ta tashi ya fita Aunty ta ce ke dai kam wallahi ban san irinki ba, ban da abin ki ga yaro kyakkyawa dan manyan mutane ga kudi har kika samu ma ya ce yana sonki ai kin yi barka amma komai mai ki kishi kuma kina zaune a gidansu da fa aiki a ka kai ki ki yi ya hana ki aikin yasa ki a makaranta gashi saura shekara biyu ki gama sannan ga dadin duniya ya mallaka miki amima duk a banza ki tsaye jiran wanda bai ma damu dake ba ba a masan in da ya kc ba na ce ai duk in da yake nasan yana nan yana tunanina. Shi kenan tunda ke duk fadan da ake miki, ba kya ji ni daga yau ruwana da ke kar ki kora zuwar min gida sannan kuma sai na yi kutu kutun da aka hada auran naku muga tsiya, fuuu, na mike cikin fushi na fita bako sallama sai ita ce ma ta leka ta ce dashi sai an jima ranta a ba ce har ya tada motar ta sake leko wata ce yazo ya fita da saurinsa yaje sun dan jima suna magana sannan ta koma shi kuma ya dawo a lokacin idona akan kofar gidansu kawata Safiyya, na dinga tunanin da 67 tana nan da ta bani wasu shawarwarin akan wannan lamari amma yanzu tana makaranta har ya ja motar bai juya in da nake ba nima kuma ban ko kalle shi ba sai da muka yi nisa muna tafiya sannan ya dan juyo ya ce ina son in biya gidan wani abokina za ki raka ni? Na cc Allah ya kaimu lafiya ya cc amin. A kofar wani gida muka yi parking gidan ya hadu sosai ya fito ya bude min bangaran da nake na dauke kai ya ce, fito mana, na ce a'a ka je ka dawo ina nan, abin ma ya zama abin dariya don haka sai ya yi dariya kawai ya tafi abinsa, jim kadan sai gashi da wani hadadden saurayi amma duk da haduwar sa bai kai Ibrahim ba suka karaso ya zo in da nake ya yi min sallama nima na mayar masa sannan ya dan ran kwafa yayin da shi kuma gogan yakc can gefe daya ya zubo mana ido. Ya ce yaya bakuwar tamu ta cije daga nan ba za ta karaso ba? na dan yi murmushi tunda ka karaso ai sai mu gaisa daga nan din ma kawai ya isa. Ya ce ai ba mutuncina ba ne na yi bakuwa amma na barta a nan kinga ban yi adalci ba. Na ce ai ni nasa kaina ba sa ni aka yi ba, ai ya kamata ki zo ko don ruwa kya kurba kinga ba ki taba ganina ba in ba ki zo dan shi ba kya zo danni. Na yi murmushi na ce dan ka r ka ce na yi maka wulakanci zan je mu gaisa amma da bazan fita ba ina gama fadar haka na fita ya сe yauwa ko ke fa wallahi kin kyauta na bi bayansu 68 muka shiga har falon gidan na sami guri na aena aka kawo min lemo juice da ruwa ina nan zaune sa ga wata tsohuwa fara daga ganin matar tana da kamala ga alama ma tana da rikon addini domin ina ganinta na shaida hakan. Da fara'arta ta yi min sannu da zuwa na amsa sannan na durkusa ra gaishe ta tace min dama Ibrahim yayo min waya da zu ya ce zaku zo na cce wallahi ta ce to yaya kuma lamarin naku yake tafiya haka ne? Sai na yi dam dani domin nasan Ibrahim ne ya bayyana mata halin da muke ciki, na dai yi shiru domin na rasa amsar da zan bata gashi matar tana da kwarjini a idona, na ji kin yi shiru ba ki ce komai ba duk dai da nasan ya kamata in dan baki lokaci ki yi tunani te kafin ki fara tunanin ina so in dan ba ki wasu shawarwari tukunna, ta dubi su Ibrahim da ke zaune ta се Al'mustapha ku dan ba mu guri da Allah sukata shi ba ko musu suka fice sannan ta dube ni, ta yi murmushi mayafin da ta yi lullubi da shi ya dan zama sai naga gashin kanta ya dan leko gaba da ya babu ba ki sai fari wata furfura waunan furfura tata daga gani ta nuna yawan shekaru ce ta ce da ni 'yan mata ya ma sunanki? Na ce "Hamdiyya." Та се Hamdiyya karar ki fa aka kawo min, na yi murmushi na sunkuyar da kai kasa don kunya ta ce kafin in fara cewa komai sai na tambaye ki tukunna abin da yake faruwa tsakaninki da Ibrahim kar ki 69 boye min komai, nan takc na shiga mata gaya gaskiyar lamari da kuma wanda nake kauna sai da naga tas tana jina ba tare da ta katse ni ba, sannan ta numfasa ta ce duk abin da kika fada min na gamsu da su, domin dai ita kauna daya ce kuma in har zuciya ta riga ta afu akan abu ta fa mai zare wannan abu sai ya yi kamar me kuma ba lallai ba ne ya samu nasara akan hakan don haka sai dai abi abin a hankali shi Ibrahim yaro ne da in ya kafe a kan abu duk abin da za a yi masa ba zai bar wannan abu ba, to bare kuma abu ya kasance Kauna ce kun ga kuwa sai dai abi a hankali kin ganni din nan ni Kakarsa cc mahaifiyar uwarsa wadda ki ke gurin ta, wato Hajiya Lami to kin ga dai in san raina zan bi zan goyi da bayan jikana ne to amma da yake nasan wahalar so nasan zakin kauna yadda takc a cikin zuciya ba zan goyi da bayan jikana ba domin shima yabe yazo zai yi a kan tsohon gini, wanda tun farko ba shi ya gina ba tarar wa ya yi an yi saboda haka shawarar da zan ba ki, ki janye wannan ra'ayin na kin yi masa magana da kin kulawarki a kan soyayyarsa ki ba shi hadin kai ku dinga gudanar da soyayyarku amma fa wannan batu naki yana nan a zuciyar ki kafin nan kafin ki kare makaranta, in yaso in an gama karatun sai aje a binciki shi wancan din in yana nan kan bakansa shi kenan, in kuma ya sami wata to shi kenan sai an gon nawa ya fita, to 70 kunga komai yazo da sauki kenan, amma yanzu in ki ka ce kin daina kula shi kuma haukaccwa zai dinga yi akan ki wanda a karshe giyar so zata iya tunzura shi ya shiga cikin wani halin na daban kuma duk wadannan maganganun da ta yi na yi kasake da kunne ina sauraronta, sai da ta gama na ce mata pa yarda da abin da ta ce, na kuma dauki wannan shawara tata, da hannu biyu. Ta yi farin ciki sosai sannan ta ce in je in kira su, na fita na same su a waje suna ta hira na ce su zo tana kira gaba daya suka taso idon Ibrahim a kaina na yi saurin shigewa cikin gida na same ta suma suna shigowa suka zobe ta ce angon Hajiya ga amaryar taka nan sai ku tafi ko? Ko ba amaryar ta saba ce, na ji kunyi shiru? In dai amaryarta sa ce za ki yi murmushi, yanzu na sunkuyar da kai kasa ina murmushi na rufc fuskata da mayafina ta yi dariya ta ce to shi kenan sai ku shirya maza ku je gida kar aga kun dade. Batun farin ciki kuwa a gun Ibrahim ai ba bayani, bare da ya fuskanci hakarsa ta cimma ruwa, ai nan take ya fara baiyana farin cikinsa a fili, ya ce in zo mu tafi ni na ce to muka yi wa Hajiya sallama muka tafi a kan cewa sai an kwana biyu zamu dawo. ** ** Ina zaune ni kadai sai zancan zuci nake yi, ba abin da nake tunani sai Abubakar, ko a wanne hali יר yakc? oho, in da haka ne ai sai yayo mın aikc da wasika to ta wacce hanyar? Na tambayi kaina to ko da ya janye ne? Na fara juyayin lamarin aiko in har ya yi min haka bai kyauta min ba, ga Ibrahim mai kaunata da gaskiya ban ji ina sonshi ba ne abin da zuciyata ta aiyana min kenan, ai kawai kokari zaki yi ki cusa kaunar sa a zuciyarki in ji wani bangare daga zuciyata, to ta yaya? Wancan 6angaren ya tambaye ni. Ina cikin wannan batun zucin sai jin kamshin turarc nayi ya daki hancina, na yi saurin juyawa ashe Ibrahim ne a tsayc take ya zauna dab dani jikinsa yana gugar jikina na yi saurin matsawa na ce haba Ibrahim wannan wanne irin abu ne ni gaskiya ka daina yi min irin wannan zaman. Na zakuda ya kalle ni kawai ya ce to mai na yi miki kuma? Yanzu dan na zauna sai abin ya zama laifi? Ki tuna fa mu masoyan juna ne, wata rana muna sa ran kasancewa ma'auratan juna. Na tabe baki na ce a wai to kuma shi kenan don nan gaba zamu yi aure....na sake jan wani tsakin ba tare da na gama fadar abin da nayi niyya ba, na mike domin haka kawai sai na ji yana bani haushi, ya mike shima ya tsaya kusa dani ya kira sunana na amsa a ciki ya ce wai don Allah dan Annabi me Abubakar din nan yake miki wanda yaja hankalinki haka da yawa? Nima in dinga yi miki ko na samu nima a dan Gantarar min kaunar nan nima 72 in dan ji sanyi a raina. Na juyo a fusace na ce kaga ni dai na ce ka kyale ni na ce ka kyale ni ka ki wai ya ka ke so in yi da raina ne? Sai muka ji ana cewa kai ka Ibrahim yaya nc? Me yake fanuwa dukkanmu muka juya ashe Alhaji ne yake kallonmu ta barandar bene, kuzo nan dukkanku, take muka nufi ciki, kafin mu karasa ya dakatar dani na Ki tsayawa ya ja mayafina cewa yakc don Allah in Alhaji ya tambaye ki waki ke so ki ce ni don Allah, wallahi ni ne mai kaunarki da gaskiya, na yi masa banza na ci gaba da tafiya ta abina. A zaune muka same shi yana jirarmu, cikin sanyin jiki na durkusa na gaishe shi ya amsa cikin fara'a sannan ya tambaye ni me ya hada mu da Ibrahim? Zai yi magana yasa hannu ya dakatar da shi, da cewa ba kai na tambaya ba, a gaskiya da kunya in ce don ya ce uana sona ne don haka sai na sauya dabara na ce Alhaji cewa ya yi yana son shi ne na ce ya tsaya in yi shawara shi ne yake jin haushina, yana jin haka ya yi murmushi ya ce to kai in ban da shirme irin naka don ta ce zata yi shawara maye laifinta? Kai ba jika yi ta ce bata sonka ba ba sai ka bata lokaci ba? Ka sani ma ko ta gama shawarar ta zabe ka? Na yi murmushi a boye ya ce Alhaji karya ne wai cewa ta yi tana da....ya katse shi dancewa kai kai kai yi min shiru da Allah, tashi bani guri kar in kara jin ka tsare ta da wannan 73 in dan ji sanyi a raina. Na juyo a fusace na ce kaga ni dai na ce ka kyale ni na ce ka kyale ni ka Ri wai ya ka ke so in yi da raina ne? Sai muka ji ana cewa kai ka Ibrahim yaya nc? Me yake faıwa dukkanmu muka juya ashe Alhaji ne yake kallonmu ta barandar bene, kuzo nan dukkanku, take muka nufi ciki, kafin mu karasa ya dakatar dani na ki tsayawa ya ja mayafina cewa yakc don Allah in Alhaji ya tambaye ki waki ke so ki ce ni don Allah, wallahi ni ne mai kaunarki da gaskiya, na yi masa banza na ci gaba da tafiya ta abina. A zaune muka same shi yana jirarmu, cikin sanyin jiki na durkusa na gaishe shi ya amsa cikin fara'a sannan ya tambaye ni me ya hada mu da Ibrahim? Zai yi magana yasa hannu ya dakatar da shi, da cewa ba kai na tambaya ba, a gaskiya da kunya in ce don ya ce uana sona ne don haka sai na sauya dabara na ce Alhaji cewa ya yi yana son shi ne na ce ya tsaya in yi shawara shi ne yake jin haushina, yana jin haka ya yi murmushi ya ce to kai in ban da shirme irin naka don ta ce zata yi shawara mayc laifinta? Kai ba jika yi ta ce bata sonka ba ba sai ka bata lokaci ba? Ka sani ma ko ta gama shawarar ta zabe ka? Na yi murmushi a 6oye ya ce Alhaji karya ne wai cewa ta yi tana da......ya katse shi dancewa kai kai kai yi min shiru da Allah, tashi bani guri kar in kara jin ka tsare ta da wannan 73 magana, shi so ai ba a dole, take na ji wani dadi ya lullubc ni na mike Alhaji ya ce i tafiyarki kin ji, kai kuma dakata ina da magana da kai, na yi ficewata abina ban san me zai ce masa ba ni dai a ganina cewa zai yi ya kyale ni kawai in na nutsu ya furta min. Yau gidan Aunty Rabi na nufa ban jira Ibrahim ya kai ni ba, domin ban nuna masa za ni wani guri ba. Nusaiba ce kawai ta sa ni sai Mami. Na san kuma in har ya dawo yaga bana nan ya tambayi in da naje aka gaya masa cewa zai yi zai je ya dauke ni, da isa ta gidan kamar kullum Rabi na ganina da murnarta ta tarye ni ta ce yau kuma ina mutumin nawa? Na ce ai baya nan ta ce gaskiya man na ganki ke kadai, na zauna muna gaisawa da ita kwatsam kamar daga sama sai ga Haulc nan tazo, haba wa murna a gurina kamar me take na afka jikinta saboda murna itama sai faman murna take yi mukа zauna na kawo mata abinci da ruwa, da lemo sai da taci ta nutsu sannan muka shiga sabuwar gaisuywa da tambaye-tambayan mutanan gida, ta ce duk suna nan lafiya bata je kauye su Inna ba, Baba Tasalla ma bata san zan zo ba na ce kuma kinga ne kwatacan da na yo miki ta ce na gane mana ban ma wata sha wuya ba, tasa hannun ta dafani ke na ta baki da alheri na ce ya aka yi ta zuge jakarta ta ciwo wata wasika ta ce gashi in ji Abubakar din ki ya ce 74 SL in kawo miki, na ce ke don Allah take na karba na wara jikina na Gari na bude domin in ga abin da a ka rubuta min haba wa ga abin da ya rubuto, bayan na duba adireshinsa. Gare ki abar kaunata har kullum. Tunaninki da shi na kc kwana da shi nake tashi, Allah yasa kin rike alkawari kamar yadda nima na rike alkawari? Bayan haka wallahi Hamdiyya ban ji dadin zuwa gida da na yi ban same ki ba, ina sanar miki wannan shi ne zuwana can kauye na uku ba tare da na bi ta gidan Alhaji ba, sai ace min kina Kano kema, kina karatu, to a nan nayi matukar farin ciki sai dai na rasa hanyar da zna bi mu hadu, to shi ne na yanke shawarar rubuto miki wasika in bai wa kawarki Haule ta kawo miki. Da yake na tambaye ta ko tasan in da ki ke? Ta ce min ta sani, domin kin yi mata kwatance. A karshe nake cewa a rike min amanar kaunata hannu biyu kar a sake wani abu ya jangwale ta. Daga karshen nake cewa ki huta lafiya. Mai Kaunarki, Abubakar Isa Dagaci. Na rungume letter nan a kirjina ina ihun murna kamar an yi min gafara, Aunty ta shigo da sauri domin da suka gaisa da Haule fita ta yi ta bar mu a dakin. Ta ce mayc haka kuma? Na ce Aunty wallahi Abubakar ne ya yo min wasika, kin ganta karanta ki ji, taje wani dogon tsaki ta galla min harara ta ce ke dai wallahi ta ki ji dadin halinki ba, ga yaro dan mutunci karıar ya mutu a kan kaunarki kin like wa wani banza wanda ba abin da yake ransa sai yaudara, to wallalii ki kiyayi kanki, domin wannan ba zabin arziki ki ka yi wa kanki ba. Duk abin da Aunty ta ke fada jinta kawai nake yi, kamar busa dama na ji ta dame ni da masifa sai na ce da Haule tazo mu tafi can gidan su Ibrahim kawai, muka yi wa Aunty sallama muka tafi. A falo muka sami Mami a zaunc tana ganin mu ta tarye mu da fara'arta, bayan mun gaisa ne take tambaya ta a ina ki ka samu kawa? Na ce ai Haulatun da nake gaya miki ce, tazo gurina ta yi farin ciki da ganinta sannan ta sa na kawo mata kayan ciye-ciye, da su lemo ta ce ta fara tabawa kafin a gama abinci. Nan muka zauna muna ta hira har wani lokaci na tambaye ta yaushe zata koma ta ce min kwana biyu zata yi muna nan zaune muna hira sai ga Nusaiba ita da Ibrahim, sun shigo dama ashe Mami ce ta aike su nan na gabatar musu

Chapter 5 of 6