Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 6
bakina ina dariya, a ciki sai ya yi murnushi ya ce yanzu ina zaki je? Na ce kasuwa zani gurin sayar da rogo, ya ce to sai kin dawo na ce to, har na tafi sai ya tsayar dani na tsaya ya ce ki taho min da alakoro na ce to zan kawo maka amma sai na dawo. ** Yau ba mu da abin wutan dafa rogon gobe, don haka Baba ta ce in je in yo abin wuta maza in dawo na ce to, na dauki wata doguwar igiya na tafi domin dauro abin wuta, Dab da dajin da muke dauro abin wuta naga su Jimmala sun taru sun kai su goma suna zaune duk da 16 gabana ya fadi ban fasa karasawa ba, domin in na ce zan koma kafin inje kauyenmu sun kamo ni na yi imanin wannan zaman nasu bana lafiya ba nc, akwai abin da suke jira. Ina karasawa na yi musu sallama ba wanda ya amsa min, don haka sai na wuce su ban saurarc su ba, gaba dayansu suka tashi kamar hadin baki suka tsaya wasu a gabana wasu a bayana, na yi matukar jin tsoro amma sai na daurc na ce ku bani hanya mana in wuce suka ce dama ke muke jira yau kwananmu uku kullum sai mun zo nan nemanki, ba ki zo ba, to yau Allah ya kawo ki, sai kuma mun raunataki muga ta tallan rogo, ke ga mai kasuwa har wata takama ki ke yi kin kashe mana kasuwa ko? Na ce ni wallahi bani na kashe muku kasuwa ba, amma don Allah ku yi hakuri, in dai tallan rogo ne ni ba a son raina nake yi ba, wallahi in naje gida zan ce da Baba ta sauya min wata sanar......Ban rufe baki ba sai ji nayi sun rufe ni da duka, ta ko ina, da tsumagiyar lalle tun ina iya ihu har na kasa suka jani ta karfi suka kaini cikin dajin suka daure ni da igiyata a gindin wata bishiyar tsamiya. Wannan shi ne farkon labarin Mummunar hallitar tasa, ta saua lokaci daya, girgizar da ya yi ta koma siffar Abubakar sak, babu banbanci ya doso in da nike a daure idanuna a rufe ban san abin da yake faruwa ba, ya kwance min daurin na bude ido da kyar, na dube shi cikin tsamin jiki na ce Abubakar yaushe kazo nan? Ya c e yanzunnan na zo na same ki a daure shi ne nayi mamakin abin da ya jawo 17 haka. Ta yi murmushin karfin hali ta ce, wallahi ba wasu ne suka aikata min haka ba sai su Talatu da Jimmala, ya girgiza kai cikin tausayi ya ce'muje in raka ki gida. Baba Tasalla sai fannan fada take kamar ta ari baki, wallahi tunda haka ne, kin daina dauko rogon dagayau gara ki sake wani abun, har yausbe su dinga yi miki im wannan dukan wata rana ma ai sai sun 79ma sanadin ranki gara ki saro goro shi yafi miki sauki kawai, na ce Baba da ki ka je gidajen nasu mai suka ce, iyayen nasu? ta ce me zasu ce, kuwa cewa suka yi ayi hakuri ba za su Kara ba. Abubakar na fa gode sesai, kaga ba đon kai ba wallahi da ban san halin da zan shiga a wannan dajin ba, domin yamma ta riga ta yi ga shi ba kowa." Ya yi shiru yana mamakin wannan godiya, shi dai ya ji labarin wai yan matun unguwar sun dake ta, har ma sun daure ta a jikin bishiyar tsamiya, amma shi sam bai je dajin ba ma a wannan rana, ko dai tsananin firgita ce da azabar duka tasa ta mance wanda ya taimaka mata, ko ta kasa gane shi don haka ya ce a ransa gara kawai ya amsa mata a cewar shi ya taimake tan, ya c e ai ba komai da ya same su ma a gurin sai ya hukunta su sosai, nan suka yi sallama ta tafi saro goranta, dama a hanya suka hadu. Usaina ce tsaye daya daga cikin 'yan matan da suka yi min duka, yau ita kadai zata je ta samo abin wuta, tana tafc ita kafai yayin da shi kuma ya tsago kasa ta bayan ta cikin mummunar balittarsa mai kama da bakin goggon biri, ya yi girgiza ya juye kamannin Abubakar sak ba wani bambanci ya biyo bayanta ya 18 kirata ta juya da sauri ta tsaya ta ce au la Abubakar ina za ka je kaima icen zaka samo?" Ya ce cikin fushi, me yas aku ka daki Hamdiyya? Ta cc a'a ka ji mu. da Abubakar dinnan ni kadai na dake ta zaka wani tsare ni ka ce me yasa na dake ta? Tana gama maganarta ta ci gaba da tafiya cikin isa da rashin kunya, ya sami irin tsafgar da suka dake ni da ita, ya kama dukanta tun tana ihu tana neman taimako har ta suma, ya daure ta da igiyar hannunta a jikin dorawa ya koma kamarsa ta asali ya бace. Wani mutum ne mai saran itace ya ganta daure tana numfashi dai dai, ya kwance ta ya tafi da ita cikin kauyen, yana tambayar gidansu, har ya samu ya sami iyaycnta ya yi musu bayanin yadda ya same ta, a halin neman taimako shi ne ya taimaka mata don kar ta halaka. Iyayenta suka yi matukar godiya sannan suka shiga taimaka mata don su samo kanta ko sa ji wanda ya aikata mata wannan mugun abu. Bayan an kwana biyu ta samu sauki, shi ne take gaya wa iyayenta cewa, Abubakar ne ya dake ta wai akan sun doki Hamdiyya, haba wa, ai sai gidan dagaci, suka kai masa karar dansa Abubakar, akan abin da ya aikatawa 'yarsu, nan da nan ya kira dan dan tambayarsa dalilin da ya sa ya daki 'yar mutane, kuma ma mummunan duka irin wannan wanda ba dan da kwananta a gaba ba sai ya halakata. Da Abubakar yazo aka gaya masa laifinsa, sai ya yi mamaki wai da aka ce shi ne ya doki Usaina, ya dubi Usaina ya ce, yanzu Usaipa tsakaninki da Allah kin ganni a dajin ma? Ta cе 19 ba kai ne ka dakeni ba wai don mun daki Hamdiyya." Ya yi salati ya ce ki ji tsoron Allah Usaina, ta ce wallahi kai ka dake ni, ya rasa abin da zai ce kawai ya yi shiru yana mamakin irin sharrin da ta kulla masa. Uban ya ce, kaga kar na kara jin ka yi irin wannan ranka zai baci, ya basu hakuri matuka gami da cewa in Allah yaso ba za su kara ba. Suka tashi suka tafi, shi kuma ya yi wa dannan sa fada kamar yadda ya kamata, shı dai yasan ba shi ya dake ta ba, haka ya hakura ya amsa laifinsa. Dan da nan zance ya cika gari Abubakar ya daki Usaina akan sun daki Hamdiyya, hakanne ma yasa Hamdiyya samun Abubakar din na ce Abubakar ka da ma kyale ta ka yi ya wuce duk abin da suka yi Allah zai saka min kaga irin wannan bai da amfani a dinga zagin ka a gari ana cewa saboda ni ka daki wata ya ce ai ba komai insha Allahu daga wannan na daina. ** ** Sauri nake tayi faram-faram da farantin goro a kaina na dawo daga talla ga magariba ta kusa Baba ta ce kar in zauna. Tun daga nesa nake hanmgo duhun abin kamar mutum kamar ba mutum ba, na dai daure na ci gaba da tafiya, domin ita kadai ce hanyar da zata kaini gida. Ina zuwa gurin sai naga ba komai sai nace a raina ashe dai idanuna yake yau dara ta. Na wu ce abina kwatsam sai in nayi ta bayana an ce malama Hamdiyya gida za'aje ne nayi firgigit na juya domin ganin mai maganar, sam ban san da mutum a bayana ba, na san dai 20 ni kadai nake tafe, hakannc ya sani mamaki da sauri juyawa Abubakar nc yana tafe yana murmushi na ce Abubakar wallahi ban san da kaine ba." Ya ce ai tuni na hango ki shiyasa na ce bari in zo mu gaisa daga talla ki ke ne? Na ce e, har ma na dawo. Ya ce ina alakoro? Na ce dauki wanda ka ke so ya sa hannu farantin na bisa kaina ya dauko wani farin goro kalle babba wanda a iya sanina dai bani da irinsa a farantin domo gorukana jajaye ne duk da dunbun mamakin da na yi sai na boye na ce wannan din ya yi maka? Ya ce ya yi min wannan din ma zan bara shi biyu ki ci bari in ci bari, na ce to me aka yi kenan? Ya ce kyautar ki gudan da kika bani ni kuma 6arin da na baki shi ne kyautata da ke na yi murmushi na cinye barin nan take duk da ba cin goro nake yi ba,,ban yi mamakin cinyc 6arin da nayi ba. Ya kira sunan Hamdiyya na amsa ya ce ina son in baiyana miki wata magana amma ina tsoron irin amsar da za ki bani, na ce fadi mana ai ba komai ya ce wallahi ina matukar kaunarki sai dai ina tunanin ko kuma kina sona? Na yi murmushi na ce wallahi ina kaunarka Abubakar kar ka ji komai." Ya ce, to shi kenan na yi farin ciki da wannan kauna da ki ka nuna min ya zaro wani zobe na gold ya miko min in go saka a hanunki na kar 6a na sanya a hannuna ina mamakin irin kyau zoben na ce, ni ko ban taba ganin ka da shi ba, ya yi murmushi ai zoben aurena igiya goma sha biyu, na yi dariya dom,in a zatona wasa yake yi min ya yi murmushi to sai yaushe kenan matar?m Na ce au har na zama matar? Ya ce tun yaushe na ce to sai na ganka ya ce zan zo gobe da 21 yamma, na ce Allah ya nuna mana, ya juya ya tafi ni kuma na karasa gida. Da saurin ta fici-fici ta doro buhun nikanta aka tana ta saun ta biyo labiba kowa sai ita kadai ga yamma ta yi mata da yake yau ayi cikawa a in jin sai tana cikin tafiya sai ta ji an kwada mata mari, take dan buhun nikan ya fadi can gefe ta dafe kumatu ta ce kai kai kai Abubakar me nayı maka? Yana tsayc a gabanta ya cе Sa'ade dan ubankı me Hamdiyya ta yi muku ku ka kama ta da duka, har da dauri? Kafin ta yi magana yasa irin tsafgar da suka dake ta da ita ya fara dukanta, tana ta faman tsandara ıhu ba mai ceto sai da yaga ta galabai ta sannan ya daure ta a bishiya ya aje mata nikan ta kusa da ita ya yi girgiza ya bace, ba tarc da tasan ko waye ya dake ta ba Sa bayan magariba ubanta ya biyo sawunta yazo da dai in da take ya ji nishinta ya haska ya ganta a guje ya kwance ta yana salati ya tambaye ta wa ya yi mata wannan aika-aika ta ce Abubakar dan gidan dagacine, ai ko a wannan daran uban bai zame ko ina ba sai gidan dagacin ya sanar da shi abin da ya faru ran Dagaci ya yi mummunan baci, ya sa aka yi kiran Abubakar ya tamnaye shi dalilin da yasa shi wannan aika-aika, yana jin abin da mahaitiusa ya ce, ya yi salati ya ce wallahi Baba yau ni ina ma filin ball kuma ban baro filin ball ba sai bayan magarıba zuwa na gida kenan na yi wanka na ji alwala zan yi Sallah aka ce in zo in ji ka Daga ci yalce da uban sa'ade to kai ka ji abin da yake ya certhaba 'Yallabai da bai aikata ba, ai ba zan yi masa sharnv bà yau mike da shi? Da can ban yi masa ba sai yanzu? 22 1 Dagaci ya ce kai ka gaya min gaskiya, ba kai ne in kuma ba kai ba ne ka fada ya ce ni ina da sheduna, wadanda muka je filin ball din tare da su. Ya dubi shi Baban Sa'adan ya ce a kira su yanzu ko zaka bari sai da safe Ya ce a yi kiran su yanzu mu ji ta bakinsu kawai." Take Abubakar ya fita neman shaidu. Dan da nan ya juye kamannin Isına'il babban abokin Abubakar wanda da shi ne suka je ball din da yamma ya tsaya a kofar gidan su Abubakar din yana nan sai ga Abubakar ya fito a fusace yana ganinsa ya ce yauwa dama kai na fito nema, ya ce gani nima yanzu da zan tura a yi min sallama da kai sai na ji maganar ka a zaure gurin su ba ba," Ya ce haba ai abínne'da bakin ciki, shigo daga zauran shaida zaka yi min." Ya сe "Tо muje." Suka shiga suka zauna, bayan ya gaishe su sai Dagaci ya ce Isma'il dama tambayarka nake so in yi, ya ce to Raba Allah yasa na sani ya ce wai da gaske kunje ball yau kai da Abubakar? Ya ce yau da yaushe fa'? Abubakar ya yi saurin cewa da yamma ba muna tare a filin ball na yamma da gari ba? Ya ce labbas mun yi ball amma ba kai Abubakar ba zan goya maka baya ka dinga yi wa Baba karya ba, naga cewa ka yi ka tafi unguwar kudu gnrin Tsalha abokinmu." Baban Sa'a ya ce to ka ji gaskiya ko Allah ya taimake ka? Na gaya na shi ya yi dukan nan ya musa mana unguwar kudu nan Sa'a ta kai nika, gu yaro ya fadi gaskiya. Abubakai ya ce ekin tsananin mamaki yanzu Isma'il ni zaka yi wa kaharu ko, amma da yammar muna tare ka ce ban yi ball ba Ya damki kwalar rigarsa yana huci da kyar aka banbere shi. 23 Dagaci ya ce je ka abinka Isma'il Allah ya yi maka albarka kai kuwa yau sai ka gaya min hadinka da yarinyar nan Hamdiyya, har ka kc bugun 'ya'yan mutane domin sun dake ta daga yau ka daina in Allah yaso ba zaka maida ni mutumin banza ba sakarai kawai. Isma'il ya yi ficewarsa ya na fita ya girgiza ya koma kamanninsa na gaskiya ya yi tafiyarsa. Dagaci ya dubi Baban Sa'ade ya ce ka yi hakuri in Allah yaso daga wannan karon ya daina, ya kawo kudi masu yawa ya ce ga wannan a saya mata magani. Baban sa'ade ya karba ya yi godiya ya tafi. Dagaci ya dubi dansa Abubakar ya ce mayc hadinka da Hamdi yya? Ya ce wallahi Baba ba abin da ya hada ni da ita, abin da ko kulata bana yi sai dai ita duk in da ta ganni sai ta yi min magana, to ni kuma bana iya kin yi mata magana, domin ba kyau wulakanta mutum amma ban da haka ba wata alaka da ke tsakanina da itą. Dagaci ya ce to daga yau ka daina yi mata maganar ma in ba baka ba sai ta jefa ka a masifa, ka ji ko? Ya ce to Baba in Allah yaso ba zan kara koda kallonta ba ma." Ya ce to shi kenan tashi ka je." Abubakar, Abubakar, Abubakar, aka ji dan iska ashe kana ji ina yi maka magana ka yi banza da ni, dakata Isma'il kar ka maida ni wawa ban san abin da nake ba, daga yau wallahi kar ka kara cewa ka sanni bare har ka yi kuskuren yi min magana, bayan ka riga ka gama tozarta ni a gaban Baba jiya sannan yau zaka zo ka 24 yi min wani dadın baki? Ai ni ban san dama irin zaman da ka ke yi da ni ba sai yanzu." A da isma'il ya dauka da wasa Abubakar yake yi masa, daga bisani ya gano abin nasa da gaske ne, ya ce Abubaka r wai mc yake damunka jiya jiya mu rabu lafiya amma yau kazo min da wata fuska kodai ka shiga shayc-shayc ne, ban sani ba? Ya damki kwalarsa kai wayc dan shayc-shayen sharrin da zaka kara dora min kenan? To wallahi mu zuba wanda bai fasa ba baya kaunar uwarsa ba abin da Isma'il yake ja sai Innalillahi, domin abin ya wuce hankali, ya ce to na ji cika ni ka yi hakuri yasa mu ya banbari wuyan rigarsa da kyar, ya kama gabansa yana mamakin abin da ya faru a yau din nan tsakaninsa da babban abokinsa Abubakar. Haba Abubakar me na yi maka zaka ce kar na kara kula ka? wa ba ka ji yadda nake mutuwar kaunarka ba, in wani abu na yi maka ai sai ka fada min in yaso in kiyaye gaba, ni ba abin da ki ka yi min kuma haka ake yi ni ban ce ina sonki ba sai kawai ki ce min wani kina sona ke ko kunya ma ba kya ji a matsayinki na mace mai mutunci ai sai ki bari in ma ina son naki in fara furta miki, ta ce au ni ce ma na fara cewa ina sonka ba kai ke fara cewa kana sona ba? Yacca gidan uban wa? Abin ya bata mamaki ta ce ai har da zagi baga zoben ka da ka bani ba ka ce min na aue ne? Ya kalli zoben ya ce wai ni me yasa ku ke raina min hankali ne? A yaushe na ba ki zoben? Ta ce, ka raina min hankali ka bani abu ka се wani ba ka bani ba, to amma shi kenan ta zare zoben ta cilla masa ga kayan tsiyar ka nan nima bana so kuma kar 25 ka kara kula ni ya dube ta ya cc au kayan tsiya ta ko dai ke kayan tsiyarki, ni ban baki wani zobe ba, sai ki mayar wa mai shi yana fadar haka ya juya abinsa ya bar zoben a gurin itama ta yi shigewarta cikin gida ranta a басе. Suna barin gurın ya tsago kasa ya dauke zoben yа басс. Ina ta sharar bacci na yi nisa a cikin barcina dakin da duhu domin na rage fitilar kafin na kwanta na yi juyi gami da jan dogon minshari a fisge na ji kamar na dunguri mutum na alhalin ni daya nake kwana, na yi saurı na tashi na Karo fitila ba kowa don haka na koma na kwanta jim kadan barci ya sake fauka ta juyi na biyu sai na ji ni a jikin mutum yana rungume da ni ga wani daddadan kamshin turare wanda na tabbatar turaran da Abubakar ke amfani da shi ne, na kuwa kwala ihu gami da neman- taimakon jama'a wuf na ga an yi hanyar fita daga dakin da gudu, mutane suna fitowa suka ga an tsallaka ta katanga a guje kafin a bude kofa a bishi ko sama ko kasa ba wanda ya ganshi don da nan kowa ya hallara a tsakar gida daga masu gora sai masu sanduna aka tambaye ni waye ya hauro ya shigo dakina na сe ba kowa ba ne sai Abubakar dan gidan Dagaci, domin irin Kamshin turarensa naji kuma sannan ga zoben sa da ya bani ya barshi, mutan gidan suka ce iskancin da yaron nan yake yi ya fara isa da safe zasu je su gaya wa Dagaci. In bai ſau mataki a kan dansa ba to su za su dauki doka a hannunsu ma'ana za su hukunta shi don rai nin hankali ya shigo musu gida da tsohon dare zal lalata musu yarinya? Masifa kuwa gurin Hajiya Tasalla bakinta har kumfa yake yi, saboda fada, cewa take yi 26 ل 3 t wallahi in har dagaci bai yi wani abu ba a kai to zata kai bırni gurin Hakimi domin ba za a lalata min 'ya ba, ina ji ina gani. Kashe gari da misalin karfe bakwai na safe mutan gidan mu ne maza da kuma ni da baba da mijin baban zaune a kofar gidan maigari yayin da suka baiyana masa abin da ya faru, sai Dagaci ya cika da mamakin wannan abu ya kira dan nasa domin wannan magana ce mai girma. Yana zuwa ya ganmu a zaune alamar mamaki ya baiyana karara a fuskarsa, ya sunkua ya gaishc da 'yan gidan mu amma ba wanda ya amsa masa, ya yi kasa ke dan jin kuma abin da za ace ya yi Dagaci ya karanta masa laifinsa yana ji ya mike a fusace yana cewa wai me ake so da ni ne? Haka kawai kowacce irin shara sai a dinga kwasowa ana zuba mon sai ka ce wanda ba shi da galihu? Ke yanzu Hamdiyya irin sakamakon da za kı yı min kenan? Na ce aí da ba ka aikata ba ba zan ce kai ne ba, d ya ji abin da na ce sai ya fashe da kuka, na ce in karya na ke maka ai ga zoben kama jiya jiya muka yi fada da kai na baka kayan ka shi ne ka je dashi cikin dare don kar esirinka ya lonu ka bar min shi ka gudu. Saboda tsananin bacin rai Dagaci ya zari wani katon katako ya fara maka wa Abubakar da kyar aka kwace shi, duk kansa ya fashe va umbura saboda duka, dagaci ya dinga basu hakuri va, ve haifi da ne amma ban haifi halinsa ba, nar da kuka dorkin ciki ya dubi Abubakar ya ce wallahi in ba ka gyara halinka ba sai na tsing maka ka lalace gaba dayanin ba ka da wani amfani a tare da ni saboda bakin ciki ka 27 sa magana Abubaka r ya yi suka tashi suka yi sallama da dagaci ya dinga basu hakuri akan in Allah yaso ba za a sakc ba. Su su tara ne cif suka nifi rafi domin yin wanka sunc ya rage wadanda basu sha bulalar Abubakar ba, to su goma sha daya ne dama ya daki uku wanda iyayensu sun hana su zuwa ko ina dan gudun kar a kuma ta cikon goman kuwa ni ce ni ko dama bana shiga cikinsu, dama abokiyar yawan nawa Haula c e ita kuwa tana can bimi tana karatunta tunda ta tafi bata dawo hutu ba. Suna ta faman facakar su a cikin ruwa da iface-iface sai ya faso ta bayan wata katuwar bishiyar kuka, ya tsaya sai da ya koma siffar Abubakr sannan ya isa bakin ruwan a lokacin sun gama wankansu sun fito sun sanya kaya suna shirin tafiya, sai kawai ya ya hausu da maka ihu kake ji ta ko ina sai daya ga ya yi musu lilis sannan ya juya ya bace, ya barsu anan kwance a galabaice, kamannin Isma'il ya koma ya nufi cikin garin in da mutane ke taruwa dattawan garin ya karasa da hakinsa jiki na rawa ya ce maza ku je ku kwaso yayanku a bakin rafi Abubakar ya yi musu rotse yanzu yanzun nan gaba daya aka tashi da salati duk mutanc suka bazama bakin rafin, suka sami yayansu fululu a kwankwance kamar shanya suka kwaso yayansu suka nufo gida. A zaune Abubakar yake ya hada kai da gwiwa yana tunanin abin da yake faruwa, gefe kuma Dagaci ne zaune shima zaune yana zancen zuci, daga can ya dubi 28 dan ya ce Abubakar ni dai ina gaya maka ba danni ba don Allah ka nutsu ka daina abin da ka ke yi, kaga fa wannan abin da ka ke yi ba karamin bakin jini zai jawo mana ba, wai ace duk tadan nan da nake maka babu dayan da yake shiga kunnenka? Abubakar ya ce wallahi baba duk laitin nan da ka sani babu wanda na taba yi, koda sau daya duk sharri ne na rasa me yasa ake min wannan sharrin, suna cikin hirar ne sai suka fara jiyo hayaniya mutanc an doso nan gidansu, to dama a zaune suke sai Abubakar ya ce bari in leka in gani hayaniyar me ake yi? Har ya tashi sai dagaci ya ce a'a zauna ni in je kasan me yake faruwa kafin ya rufe baki tuni jama'ar sun karaso suna ta faman zagc-zage ga sanduna da gorori rike a hannunsu wasu ma har da sanduna suna c ewa a fito mana da Abubakar yau mu sassara shi mun gaji da rashin mutuucin da yake mana, ai kuwa sai maigari (dagaci) ya fita yana lambayar abin da ya ke faruwa, wani saurayi ya cebkagmalam in zaka fito mana da shi ka fito mana daashi yau ba zamu bar kofar gidan nan ba sai mun du fansa. Dagaci ya eub kursanar dani laifin da ya yi muku mana, in bah Nanlaifin bi rayazan ba ku shi ku hukunta shi? Wani daga cikin su ya ce da Allah kar ku saurare shi kulsa wagidah wota in yaso ya fito ko ya kone dama shl'yake yaña jihsu ya ma rasa ta cewa sai can wani dattijo ya fito ya bayyana masa laifin da Abubakar ya yi dagaci ya ce tun yaushe aka yi wannan aika-aikar? Suka cc misalin hudu na yamma ya ce to wallahi tun karfe biyu muna nan tare da Abubakar ni dama nasan wannan 29 abu da akc yi da wata makarkashiya so ake yi a raba ni da dana Kwaya daya tilo, suna jin haka suka afka masa kai duka shi shi yake tura shi ya yi wannan barnar, mutane suka afka wa maigari da bugu ya shige gida da kyar wasu suka ba da shawarar a shiga a fito dashi wasu suka ce a sa wa gidan wuta, wasu kuma suka ce a kyale su sai in sun kuma ayi duk abin da aka yi niyya, wasu sun yarda wasu kuwa suka kafe sai sunyi abin da suka yi niyya, yana can bayahsu ba wanda ya lura dashi ido ya rufe ya juye kamannin dan tsoho tukuf bakinsa daga jaja da goro yana ta Kara sandarsa ya dinga ratso mutane har ya kai tsakiyarsu ya ce yana da magana aka yi shiru ana sauraransa sannan ya c e a yanzu dai ayi hakuri amuna in har ya kara nan gaba sai a yanke hukunci take wasu sun yarda da wannan shawara wasu. kuma suka ki musamınan ma wadanda aka taba nasu 'ya'yan da yaga haka sai ya ce cikin gyaggyabin tsofa aiko dan darajar tsufannan nawa kwa yarda da abin da

Chapter 2 of 6