Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 6
bani da mai taya ni aiki ni zan dauke ta, kai Hajiya Laraba wallahi kin rude a kan 'yar nan lallai to ki karbe ta man ki hada biyu, a'a gara dai in kai ta gidan Hajiya Lamin, wai wacce Hajiya Lamin ba dai ta noman sland ba kawar nan ta ki? Ta ce ita mana, E, gaskiya na goyi da bayan a kai ta can din. Abubakar ne zaune a falon Alhaji Lawan shi da Ibrahim yayin da Aihajin ya dubi Ibrahim ya yi murmushi ya ce yaro dai yaro ne, in ban da abinka 45 ga dan uwanka Abubakar Sadik ba sai ku yi zamanku ku biyu ba a can din, ya ce ni fa Alhaji ba zan je ba a nan Kano nake son yin karatuna bana son zuwa ko ina ya ce shi kenan, kai kumka fa ina ka ke son zuwa? Ya ce ni ko ina ma zan je amma na fi son zuwa can Zariya A.B.U ya ce to shi kenan sai ku fara shirye-shirye domin nan ba da jimawa ba za ku tafi, kai sai kaje B.U.K din kai kuma sai in kai ka zariyan. Suka tashi suna farin cikin abin da Alhajin ya ce musu, sai da suka fita falo Abubakar yakc cewa Ibrahim me yasa ba zaka je can zariyan ba? Ibrahim ya ce in haka ne kai me yasa ba zaka zo mu yi B.U.K din ba? Ya ce, ai kowa da irin nasa ra'ayin ya e to ka gani, nima nan nafi kaunar zuwa. Haka suka ci gaba da hira kowa na bayyana dalilansa na son zuwa in da yafi ganin ya yi masa. Yaya Abubakar wai kazo in ji Mami, ya amsa da to ya tashi ya fita ya same ta a falo tana zaune ya durkusa ya gaishe ta sannan ya ce gani Mami, ta ce to dama abin da yasa na yi kiranka shi ne kaga dai gobe in Allah ya kaimu zaka taíi makaranta, nasan duk fadan da zan yi maka Alhaji ya riga ya yi maka shi saboda haka abin da zan Kara maka shi ne ka tabbatar abin da kaje nema ka tsaya ka yi shi, kuma ka samo shi, kaga in ka tafi sai dai hutu zaka dinga zuwa gida, sai dai in ko Alhaji yaga yana da lokaci ya kai maka ziyara, don haka ka lura ga tawa 46 Isarabar ta mika masa waya Nokia mai kyamara ta ce ma dinga gaisawa ya karba cikin farin ciki ya bude ta sabuwa ce dau, akwalinta irin ta Ibrahim ce sak ya yi matukar godiya sannan ya tashi ya tafi nuna wa Ibrahim. nake ta faman Tunda muka shiga cikin gidan zarc ido ina kallon ko ina ban gaji da kallon harabar gidan ba, muka shiga ciki. A falo muka zauna yayin da matar gidna tazo da saurinta cikin fara'a tana cewa, Hajiya Laraba sannunku da zuwa, ta zauna bayan sun gaisa ne nima na gaishe ta, ta amsa min cikin fara'a. Sun jima suna hira sannan ta ce dama wannan ita ce yarinyar da nace zan kawo miki 'yar makotan kanwata Umma, ta ce to gata kuwa kyakkyawar yarinya kai wannan yayarinya da kyau take lallai na yarda Laraba ai da na dauka zugugun ki ne kawai ta ce ato ga shi dai idanki ya gani, yanzu dai gata nan zata zauna ta dinga taimaka miki da wasu ayyukan, ke dama nasan halinki ba ki da wani aibu ita ce dai ban san halinta ba, amma da gani yarinyar zata yi hakuri da hankali Hajiya Lami ta ce ai da ganinta nutsattsiya ce, sai dai yanayi na kauye sai da Hajiya Laraba ta yini da yamma ta tafi gida, ita kuma matar gidan ta nuna min dakin da zan kai kayana sannan ta ce in je in yi wanka ta sa 'yarta 47 Nusaiba ta bani kaya har kala uku domin ta fuskanci bani da wasu wadatattun kaya masu kyau sai tsumma kawai. Ta nuna min duk irin aikin da take son in yi mata cikin ladabi da biyayya na amsa mata. Kwanci tashi na zama tamkar 'yar gida a gidansu Nusaiba, itama Nusaiban ta dinga koya min wasu abubuwan da ban sani ba, misali girki irin nasu da sauran soyc-soye su hada lemo da sauransu abinci kuwa sai na bar shi, duk kalar da suka ci da ni za aci kafin mayc wannan na goge na yi fes da ni baske na ya fito sosai har na kusa sajewa da 'yar gidan ko sakan zata je sai ta ce in tsefe kaina mu yi nan da nan sai gashina ya muke har ba ya domin nafi Nusaiba gashi sosai ita kanta tana sha'awar gashina. Ina kitchen ina wanke kwanoni da safe na gama na shiga goge-goge har na kare na share kitchen din na goge sai na ji yo kira daga falo da sauri na na fita domin Mami ce take kira kamar yadda na ji Nusaiba na kiranta na je na durkusa na ce gani Mami, ta cc kin gama ne? Na ce na gama ta cc da Allah ki dorawa Ibrahim ruwan zafi ki juye masa a flask zai zo ya dauka yanzu na ce to na tafi ina tunanin wanene kuma Ibrahim ni dai tunda nazo gidan nan naji ana yawan ambata Ibrahim amma ban san shi ba, yau dai na ganshi na yi sauri na 48 tafasa masa ruwan ina durawa a flask sai na ji an ce yi a hankali kar ki kana cikin tattausar murys na dago kaina da sauri sai muka yi ido biyu da shi ya а tsaye a bakin kitchen din na ya zubo min ido sai ne yi saurin yin kasa da idona ina tunanin ko dawa ya dade a tsaye ne ban sani ba oho, na gama durawa na durkusa na mika masa yasa hannu ya karfa yna murmushi ya ce thank you yana yi min wanı tr.n kallo da na kasa fahimta har ya tafi kaina a duke yake, na ce a raina kai ina jin dai wannan yayan Nusaiba ne domin naga suna kama sosai amma fa kyakkyawa ne sosai. Ina cikin wannan tunanin sai na jiyo kara din Nusaiba tana kiran uwar Mami, Mami kizo Yaya Abubakar ya yo waya, maza kizo ta fito da sauri nima kuma falon naje na zauna ina ta gyare-gyare na naji suna gaisawa da wanda ya yi wayar Mom na tambayarsa karatunsa da kuma hira da suka dan taba da tambayar mutanen gida sai na ji tana cewa ai lbrahim yana nan ta ce, ta ce ai nasan kuna gaisawa amma baya gaya min kasan Ibrahim da zurfin ciki, wato har can yaje ko? Oho to ya ji ga Nusaiba ku gaisa, suka gaisa da Nusaiba suka dan taba hira sannan ta bai wa Mami wayar suka yi sallama. 49 ** ** Yau mai wa su Mami sharar harabar gidansu baya nan duk ganyayyakin bishiyoyin dogon yaro ya watsu a harabar gidan, ga shi kusan duk irin kananan duwatsun nan ne farare sai Mami ta yi kirana ta ce da Allah in share iya in da zna iya nace to, na fara shara sai da na yi yafi rabi sai ga Ibrahim a motar sa maigadı ya bude masa ya shigo ya ganni ina ta faman shara ya nufo in da nake ya tsaya ya ce, ina yaran da suke wannan aikin? Na ce basa nan, ya ce to waye ya ce ki yi ai bai ai bai kamata a bar ıniki duk wannan sharar ba, na ce ai ni ce nasa kaina ba sa ni aka yi ba, ya ce to ki daina ki bar musu in sun zo sayi na ce to ban ki maganarka ba amma ka yi hakuri, in karasa wannan in yaso gaba sayi, ya girgiza kai alamar a'a na ce sai na gama ya ce to ba ke kuka sa kanki ba saki aka yi amma bari in je gidan in ji wanda ya sa ki, sai na yi saurin yar da tsintsiyar na ce na bar shi ya yi murmushi ya ce, haba ko ke fa, amma yadda ki ka hadu din nan ace kina irin wannan aikin ai sai ki jigata kanki, na cе a'a ka ji ka fa wacce haduwa ce a nan? Kai dai ka sa mi wacce ta hadu amma ba a nan ba, sai dai in ko ba a zaka yi min ya ce wallahi ba wasa nake miki ba da gaske nake, na ce uhm kawai na juya na tafi na bar shi tsaye. Ina ta faman kai ruwa sama cikin toilet din Mami da yake famfo an dauke ruwa sai masu tanka 50 batikka inashk yaلSΠ water suka kawoi ruwa, shi ne nake jida ina kai wa ciki ina juycwa a manyan robobi sai da na gama da kasa su kitchen tukunna sannan na fara kai wa sama ina cikin diba sai ga Ibrahim nan ya dawo sai nagan shi zaunc a falo a lokacin zan shige da ruwa sai ya kira ni na ji ya ce, ina ki ke kai ruwa? Na ce sama ya ce daga wannan ki bar shi kar ma ki sake daukowa, wannan din ma maida shi toilet din kasa, sai na ce ai Mami ce ta ce in kai mata sama sai ya mike zumbur ya nufi saman yasa mi Mami a zaune ya cc cikin fada fada haba Mami ya ma za'a yi ku dinga sa ta daukar ruwa?" Gaskiya daga yau ku daina sa ta ai ba daukar ruwa aka dauko ta ta dinga yi ba, kin san fa daukar ruwa abu ne mai cin rai, da yake Mami mace ce mai hakurin gaske, sai ta yi murmushi ta ce Ibrahim kenan to an daina sa ta daga yau, tun daga wannan lokacin ta daina cewa in kai ruwa sama sai dai tasa wadannan samarin gidan masu yi musu wanki da guga da share-sharc. Na gama aikina da wuri ina zaune ni kadai sai ga Nusaiba nan tazo ta same ni, muka zauna da ma ta kan zo gurina mu zauna muna ta hira har ma na kan dan sami littafi a gurin, na Hausa in dinga karantawa yana dan debe min kewa, domin in ba ku manta ba, na yi makarantar primary baba Tasalla ta hana ni tafiya sakandire da yanzu ina can. 51 Ta dube nr ta ce, wai Hamdiyya me yasa ba za ki dinga bina makarantar Islamıyyar mu ba ne? Nu ce, au a ina ku ke makarantar? Ta co Nan ne fa ba nisa makotanmu na ce to zan tambayi Mami ta barni nima sai ta dinga zuwa, in za ki je ta ce ai gara kı dinga zuw a kya rage wani abin domin zaman haka ba a rabi ba baka ba shi da dadi na yi murmushi kawai ina mamaki a raina na fa girmi Nusaiba sosai amma in ta yi magana sai ka ce babba a gaskiya tana da hankali da tarbiya maganar da zata tsaro ba zan iya tsaro ta ba. Haka muka je gurin Mami ta gabatar mata da wannan magana ta ce to ai ba wani abu ku dinga zuwa taren dukkanmu muka dinga murna saboda ta barni. Tun daga wannan rana nake zuwa makarantar Islamiyya Hamdiyya na gaya miki ki dinga barin aikin nan yana fa yin yawa, na daga kai na dube shi na ce Yaya Ibrahim abin da fa aka kawo ni yi kenan, kuma kasan fa biyana ake yi duk wata, to ya zan ce aikin ya yi min yawa ai sai dai in ba aikin zan yi ba, kuma ma ni ban ga abin yawa a wannan aikin ba, domin ni bana girki daga in yi wanke-wanke sai goge-goge sai kuma sharar kitchen shi ne fa aikına kawai." "Ke gaskiya fa ba za ki sake wani aiki a gidannan ba." 52 Na cc "A'a to sai dai in so ka kc yi in tafi." Ki je ina? Na ce in je in da na fito." Ba kya son zaman nan din ne? Na ce to ka ce in daina aiki kuma shi ne ya kawo ni, ka ce in bari. "Ai aikin Ki da ne da wahala, kuma kamar tsarinki bai kamata ace kina wani aiki ba." Yaya Ibrahim in har kana son zamana a gidannan to ka daina yi min zancan in daina aiki domin shi ya kawo ni." Ya yi shiru ya zuba min ido kawai har na gama magana ta na mike zan tafi ya kira sunana na amsa na juya muka hada ido, ina sauraron abin da yake son gaya min sai na ji ya yi shiru kawai sai kallona yake yi, sai na ce Yaya, Ibrahim in na Sata maka rai ne to ka yi hakuri ni wallahi ba da wani abu na gaya maka ba, iya gaskiya ta na fada, sai ya girgiza kai ya ce ko kadan ba bata min rai ki ka yi ba ki dawo kawai ki yi zamanki mu ci gaba da hirar mu, na yi murmushi na ce gurin Nusaiba zani mu yi haddar Hadisin da aka bamu a makaranta jiya ya ce to shi ke nan. ** ** A gaskiya Mami na tsani in ga yarinyar nan tana aiki, ya kamata ace kun daina ba ta aiki sam sam. Ta ce to ai ba aikin girki take yi min ba, daga wanke-wanke sai shara, ai su din ne bana son in ga tana yi, saboda me? Bata dace da aikin ba ne 53 kawai" Oho ai haka zaka ce ka tsaya kana wasu kewaye-kewayc, kace kawai da abin da yake cikin ranka? Shi kenan sai kaje ka sami Alhaji domin shi ne da magana kasan dai ni ba zan je in yi masa wata magana ba, ya ce ni fa ba wani abu nake nufi ba, ta ce kai tafi can sakarai kawai. Ya mike yana ta dariya ya fada dakin Alhaji Lawan dake yau yana gari. A zaune ya same shi shima ya zauna ya dube shi ya aka yi ne Ibrahim? Ya ce ba komai ya karanınka da wata matsala ne? Ya ce babu wata matsala, ya ce ai jiya naje gurin Abubakar ya ce in gaishe ka da zai zo ma ni na ce kar ya soma zuwa daga fara karatun zai fara yawo a hanya? Ya ce nima zau je ne ni da Nusaiba sai week end ya ce shi kenan kaga kuwa zai yi farin ciki sosai. Ya dauki Jaridar da Alhajin yake karantawa ya fara dubawa daga can sai ya ajiye ya yi tsaki ya dubi uban Alhaji ya kira sunansa ya ce na'am ya ce nifa Alhaji yarinyar nan tausayinta nake ji, ya dube shi a hargitse domin yana zaton Nusaiba yake nufi yana matukar ji da 'ya'yansa kwaya biyu rak shi yasa ma duk abin da suka ce suna so yake yi musu komai kuwa wahalarsa, ba ya fasawa shima Ibrahim din sanin hakan ne yasa shi yin wannan maganar, Ibrahim ya ce ba ka gane ba wannan yarinyar da aka kawo aiki nan gidan, ya ce oho ai na ga zata iya 54 domin da wayanta tausayınta nake ji, ya ce ai in an ce ta daina an sallame ta iyaycnta za su kai ta wani gurin za su yi ta aikin kuma kila in da za su kai tan ba za ta sami sakewa kamar nan ba. Ya ce to me zai hana ta yi zamanta ba sai ta yi aiki ba? Tun da Allah ya hore maka sai ya zamo kamar ka taimaka mata ne ya ce ai ba ka ma ba cc ba ma taimako ne tsakani da Allah ya ce to kaga ni sai a samo wata ta ci gaba da aikin ita kuma ta yi zamanta kasa ta a makaranta tunda ta yi primary, sai ta ci gaba da sakandire kawai. Ya ce shi kenan ba wani abu kaje ka turo min Mamin naka zan yi mata bayani ya fita ya dinga murna kamar wanda aka yi wa wani daddadan albishir. Haba Yaya Ibrahim ni dai ban ji dadin wannan lamari ba wallahi, a gaskiya ni ba ka burge ni ba, haka kawai ka tilasta musu abin da ba su yi niyya ba? Ni ban ga abin tilastawa a nan ba, wallahi da ace lokacin bayi ne in nace da Alhaji ya 'yanta ba wa wak baiwa zai iya domin yana san mu baya son abin da zai 6ata mana rai ko kadan shi yasa duk abin da ki ka ga na ce ayi ma'ana ana yi mana na ce shi ke nan na gode Allah ya saka da alheri, ya ce na manta ma ashe ban gaya miki ba jiya Alhaji ya сe zai sayo miki fom din makarantar gaba da primary za ki dinga zuwa na dafa kirji Allah da gaske ka ke yi? Ya ce sai in kin soma zuwa za ki fi gaskata ni, 55 na ce kai amma na rasa kalmar godiya da zan yi maka, ya yi murmushi ba shi ne nake so in fito dake ba amma ke sai faman ga cewa ki ke yi, na ce ai abinne ni da na aiki sai in wuce makadi da rawa kuma? Ya ce don kin shige makadi da rawa ai ba ji. Tuni har na fara zuwa makaranta abina, kullum Yaya Ibrahim ne yake kai ni kuma ya dauko ni, ita kuma Nusaiba direban su ne yake kaita ya dauko ta yau da gobe har na fara saba wa da karatun komai yana tafiya min daidai ba wata matsala kuma а gurin Alhaji kamaı 'yarsa na dawo haka ma Hajiya Lami wato Mami itama ta dauke ni kamar 'yarta Nusaiba dinki ma iri daya ake yi mana ba wani bambanci tuni yaya Ibrahim ya sa aka kai ni dakin Nusaiba na bar wannan dakin shirgin mai sauro da sauran Kwari. Muna zaune da Nusaiba muna ta hirar makaranta na ce ni ko Nusaiba in an bamu hutu zan je garin mu ta ce, Allah na ce Allah kuwa, kinga da za'a bar ki sai mu tafi tare, ta ce ina ai Alhaji ya ce gidan Yayansa can kauye zani in yi hutuna a can, na ce au dama kuma kuna da kauye? Ta сe E, mana garin su Alhaji fa in da wan Alhaji yake babansu Abubakar." Na ce yauwa wai ni waye Abubar din nan ne, da na ji kina yawan ambatarsa ko kuma ku yi masu waya ko shi yayo maku a ina yake da zama ne? Ta ce ai dan wan Alhaji ne a kauye yake shi ne 56 Alhaji ya taho da shi domin ya yi karatu, kin an kauyc ba a damu da karatun ba kamar nan. Na ce haka ne kam, ta kc tunanin nawa Abubakar fin ya fado min nace a raina Allah Sarka Abubakjar ko yaya yakc ciki oho, nan take wani irin dafin SO harba a zuciyata na ji wani irin shauki so kawa nake u ganshi na mi je wuf na ce da Nusaiba ina zuwa ta ce io na mike na je na zare hotansa ba tar da ta lura da abin da nake yi ba domin ina tashi ta fara Game a wayarta, sai da na gan shi sannan na yi ajiyar zuciya hawaye ya nemi tona min asiri, sai na yi waje kawia bayan na lallaba na mayar da hoton ma'adanarsa. Na jima ina kuka sannan na sbare hawaycna, na wanke fuskata don kar a gane ne, na yi kuka na dawo ciki zuciyata da radadin kaunar Abubakar ga Gacin ran raba mu da aka yi. ** ** Kwanci tashi muna zuwa makarantar mu kullum har muka yi jarabawą na sami kyakkyawan sakamako a wannan jarabawa, ta canja aji na zo ta daya a ajinmu, murna gurina da su Ibrahim Alhaji da Mami da Nusaiba ba a magana har kyaututtuka na samu shima Alhaji sai da ya dan hada min fati bayan mun zo hutu. Muna gama fatin da kwana daya Alhaji ya ce ibrahim ya maida ni gida in hutuna a can in yaso aka koma sai ya dawo dani. 57 Haka kuwa aka yi, da Ibrahim ya dauke ni gami da kayan tsarabar tawa sai gidan Rab, wato Aunty Rabi ita kuma ta ce ya barni a nan ma ita zata kaini gida da kanta, sai da ya nace a kan sai ya kaimu ta ce ai ba dan rakiya sai dai ita in mijin ta ya dawo ta tambaye shi sai ta raka ni washe gari haka ya hakura akan tilas. Da gari ya waye, ita ta shirya ta raka ni har kauyenmu, murna a gurin Inna kamar me, da taga na goge na kara kyau sosai. Kwanan Aunty Rabi daya ta koma a kan cewa in an gama hutun na taho tun da yenzu na gane hanya. Sai da na kwana uku sannan na tafi can zan zari guri baba Tasalla itama ta yi farin cikin ganina ta ce lallai birnin ya karbe ki, kin dawo-sai ka ce wata 'yar Turawa ai wannan tafiyar tak: ita tafi maki alkairi, shima yaron nan dan gidan Dagaci na ji ana rade-radin wai kanan uban wannan mai kudin yazo ya tafi da shí gurinsa ya sa shi a makaranta. Na tabe baki kawai don kar na yi wata magana ta balbale ni da masifar tata da ta saba, nan ta kasa min tsaraba duk na kai wa mutane sai faman mamakin kyan da na yi suke yi wasu har da taba min gashi wasu ko zuwa suke ganina takanas da zance ya bazu wai nazo ga yadda na sauya, Baba ta ce in je gidan kawata Haule itama tazo hutu, na kwashi tsarabar da naje musu da ita zan kai wa Haule gidan su hanyar gidan Dagaci nc, 58 don haka sai na sayi goro mai kyau farare a boye don kar Baba ta gani na tafi dashi in na gan shi a wajc in ba shi. Na kuwa yi sa'a na same shi bisa kujera shi kađai ba kowa, na durkusa na gaishe shi ya amsa da fara'arsa amma bai gane ni ba, na mika masa goron ya sa hannu ya karba ya ce ban shaida ki ba daga ina ki ke? Na ce Baba nice fa Hamdiyya yar gidan Tasalla, my maya, ce oho sai yanzu na ganc kina ina ne shiru na raby da jin duriyarkı Na cc ai ina cikin gavi ina karatu ya ee koda naji, shıma Abubakar din ai yana сaр, па се Allah Sarki to ni zan tafi ya ce to na fa gode, yaushe za ki koma ne? Na c e sai na gama butu ya ce a nan za ki ga? Na ce a'a gidan su Inna nake da zama ya et m za ki koma gidan su Ipnau ki zo in bakinta wa tsarabar ki tafeda ita, na ce to na gode muka yi sallama wuccne גת gidan su Haulé la tasolda muk. Ina isa gidan su Haule ta taso da guda ta tare ni mukat rungume juna muna ma, Haule la ce wallabi kin yi bala'in hadawa Hamdiyya, a aua ki kẹ yanzu? Na ce uhm, ke da bari Haule bayan afiyarkin ni naga abu, muje mu gaisa da Baba, tukunna mu zauna kisha labn daab H на subasu I Bayn mun gama gaisawa da Babar Haul cet basu tsarabar murdan (aba bira sai Hauie ta muka kebc a wan deki ta kawo min madararshant mai dumi dake su. fylani ne kuma tasan inasoplati ys 39 oted n הה madarar shanu a lokacin muna tarc. Bayan na zauna na sha na nutsu na shiga bata labarin komai tun daga farko har karshe ta yi matukar mamaki ta ce to yanzu a ina ki ke a can Kanon na gaya mata in da nake a zaune, ta ce in bata a rubuce insha Allahu sai ta nemi in da nake na ce ba zan iya yi mata kwatancen gidan da nake ba, zama ba amma zan yi mata kwatancan gidan Aunty Rabi sai tasa a rakata tunda ni ba zan gane gidan ba bare in yi mata kwatance. Ta ce shi ke nan in Allah yaso sai ta je nan muka ci gaba da hira har wani lokaci, sannan muka yi sallama ta rako ni gami da tambaya ta me nake so ta kawo min in zan koma? Na ce ina son nono mai kyau, ta ce to sai lokacin da zan koma Kano zata kawo min can gidansu Inna domin kar ya lalace. Satina daya a gidan Baba sannan na koma gidan su Inna, hade da tsarabata niki-niki da Haule muka tafi ta raka ni har gidan su Inna, sannan ta yi ni ta kamo gida dake bani sa sosai daga kauyanmu zuwa kauycn su Inna, sai da na gama hutuna cif sannan na koma gidan su Aunty Rabi can Kano. Inna ce ta raka ni da kayan tsaraba ta niki-niki. Daga ci kwan zabi ya bani mai yawa domin shi mutum ne mai saukin kai bare kuma yaga an rabu babu wata hayaniya a yanzu hankalinsa a kwance. 60 Kwanana biyu a gidan Aunty Rabi sai ga Yaya Ibrahim yazo daukata, Aunty ta ce ai yazo ya fi sau goma sai in ce ba ki dawo ba, na ce lallai Ibrahim akwai himma. Ta yi dariya akwai himma kdai akwai wata a boye? Na ce haba Aunty ba komai wallahi yana dai tausayina nc kawai, ta ce ai in ta yi wari ma ji, au ke an bar dan mutane a wajc a tsaye je ki ce masa ya shigo daga ciki, a tsaye jikin motarsa yana ganina sai na ji ya saki wata ajiyar zuciya mai karfi ya karaso cikin murmushi ya ce wai Hamdiyya me yasa ki ka je ki ka yi zamanki ne a can? Na ce kasan an jima ba a ga juna ba shi yasa ina can yaran gida da 'yan uwa da abokan ariziki da aminiyata, ya yi dariya suna nan lafiya ko? Na ce duk lafiya ya ce to shiga ki fito mu tafi. Na ce au yau ba za a shiga a gaida Aunty ba? Ya yi murmushi bari dai in shiga da sauri nake yi wallahi daga zariya nakc don na mayar da Sadik kin san shima yazo hutu satinsa biyu na ce au yazo Allah bai yi zan ga Sadik din nan naka ba, ya ce wallahi kuwa, sai dai wani hutun na ce to a ina zan gan shi bayan duk hutu kauyenmu zan dinga tafiya, ya ce kai ina ai daga wannan kin daina zuwa, na yi dariya haba sai ka ce wata matar aure? To ko aure ma nake yi ai dole ne in

Chapter 4 of 6