Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
1 / 6
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels SHARRININNIF NA AMNA ABDULLAHI SHARAБА (MRS AHMED YUSUF) SHARRIN JINNI 1 NA AMINA ABDULLAHI Hakkin Mallaka (m) Amina Abdullahi Copy right (c) Amina Abdullahi GODIYA Godiyata ga Allah Madaukakin Sarki da ya nufe ni da rubutu wannan littafi mai suna SHARRIN JINNI. Tsira da aminci su kara tabbata ga Shugaban halitta kuma cikamakin Annabawa (S.A.W), Alayensa da Sahabbansa. GODIYA TA MUSAMMAN GARE KU Nafisa Abubakar Shaba Binta Bello Suwaiba Yahaya Nafisa Dahirı Maryam Abdurrazaka (Gandu) Binta Bature Surayya Auwalu Balaraban Jamilu Da sauran irinku, wadanda ban sami damar shigar da sunayenku ba. JINJINA Gare ka Jamilu Ali Indabawa, Allah ya kara zumunci amin. KUMA BAN MANTA DA KU BА Ummi Ali Indabawa Da Sadiyatu Ali Indabawa 2 ITA TARI DA KU 'YAN'UWANA Umar K.B Sharada Kabiru Bullet (Bulman) Sharada Abdullahi Muhammad Yakubu Bauchi Yaro Abbas Sharada Aminu Samarat Sharada Babanji Salisu Sanin karfi TUNASARWA Wannan littafi Sharrin Jinni, ban rubuta shi domin wani ko wata ba, na rubuta shi ne domin nishadi, Kagaggen labari ne don haka a guji zargi. Amina Abdullahi Sharada GABATARWA Sharrin Jinni, labari ne da wani gawurtaccen Aljani ya kulla soyayya don cimma burnsa, ya dinga haddasa musufu kala-kala wanda ya kasance duk wanda ya kulla alaka da cu sai ta shafe shi. Bayan kuma yana son yarinyar sosai, hakan ne yasa duk wanda ya yi gigin taba ta, da sunan duka ko yasa ta a wani bacin rai sai ya sami horo mai tsanani a gurin Aljanin, Karshe ya shiga jikinta. Kaddai in cika ku da surutu ku biyo ni ku sha labari. Amina Abdullahi Sharada 3 SHARRIN JINNI 1 Y au kauycn garin Zanzari, an kwana ana tafka ruwan sama kamar da bakin kwarya, ya kasa ta juku ni ima ta sauka gari ya yi dadi, sai gajimare ke ta wuccwa da yayyafi lif-lif, yayin da duk wani magidanci ko saurayi tsoho da yaro da mata masu karamin karfin ke ta faman fafutukar zuwa gona shuka, tuni masu hali daga cikinsu sun sa an nome musu gonakinsu wasu da motar noma wasu da garmar shanu wasu kuwa karti suka sa majiya karfi ya danganta da ra'ayin mutum. To a daidai wannan lokacin da kowa ke fafutukar yin aikin da ke gabansa, ni kuma ina can nasa Babana a gaba ina ta faman sharar hawaye don tausaya wa ganin ccwa kowa na fafutukar kauda aikin da ke gabansa, shi ko na kwance rai'ga Allah, bai ma san wanda yake gunsa ba. Ni kadai ce 'yarsa ni ce ta fari ni ce auta, duk kuwa da cewa mahaifin nawa tsoho ne tukuf mai kimanin shekara tamanin da biyar a duniya. Itama dai Innan zata yi hamsin domin daga ninta za kasan ta kwana biyu duk da cewa wahala ma ta isa ta kara musu tsufan kasancewar ba wasu mawadata ba ne, abin da za a ci ma ba dan da noma da yake ta ba wa ba da kansa yake zaune. Kar ku yi mamakin jin cewa ni ce ta tarin nice kuma auta wannan ya samo asali daga rashin haihuwar da suka samu tun farko, sai da girma ya kama sai da gima ya kama sannan Allah ya azurta su da ni. 4 "Hamdiyya ki yi shiru ki daina kukannan haka kar kanki ya yi ciwo." Na dubi Inna dake gefe daya ta yi tagumi, na ce "Inna gani nayi garin nan kowa ya tafi gona domin yin shuka, ba wanda ke zauke sai mu, ga Baba ba lafiya ga abincin ma na waccen shekarar ya kusa karewa, gashi bana ba zamu noma ba. Inna ya zamu yi.?" Itama ta sharc hawaye ta ce "Haka Allah yaso damu, sai hakuri. Ai cuta ba mutuwa ba ce, sai kwana ya kare." Na mike gami da sharc hawayc na ce, "Inna zanje in zaga gonar Baba in gani." Ta ce "In kinje me zaki yi, tunda ga mai aikin a kwance ba lafiya? Nasan dai ke ba iyawa zaki yi ba, amma jeki sai kin dawo, kya iyo mana abin wuta ma daga can, ki taho mana da gwandar daji ki dubo nunanniya kar ki debo danya." Na cc "To." Na kama hanya na tafi. Tun daga hanya nake ta faman murza ido danganin abin da ke gonar ko idona ne yake gizo wato yake zagi. Haka dai na karasa gonar zuciyata cike da mamakin abin da na gani. Gonar na gaki an yi mata (haro) wato huda kenan, kuma har an shuke iya ganina ma'aikata ast gonar su suna ta aiki abinsu, na hango wani dan makotanmu shima a tasu gonar yana cire ciyawa, na isa gare shi a banya ye na yi masa sallama, domin Baba yana cewa dani "duk in da naje in dinga sallama, sannan in gaishe su kafin in fadi aiken da aka yi mini." Ya amsa sallamar, sannan muka gaisa na ce "Sule don Allah ko ka ga wanda ya yi aiki a gonar Babana.?" Ya ce "Wallahi kamar yadda ki ka gani, nima haka na gani. Sai dai ki tambayi Malam Shehu gashi can a 5 tasa gonar ko ya sani. Ni da ina cewa ma ko ku ne ku kasa aka yi muku.?" Na ce "A'a, wallahi ba mu ba ne, Baba dake ta kansa yaushe zai sa ayi masa noma da shuka, shi da bai san ma wa ke gunsa ba." Na ce, bari inje in tambayi shi Malam Shehun ko ya sani." Ina zuwa na tambaye shi, shima ya cc bai sani ba. Abin ya yi min dam! Na yi masa sallama na tafi gida ina cike da mamakin wannan abu. Ni kadai akan hanyata ta komawa gida, ina tafe ina ta tunani, kwatsam! Naja na tsaya cikin tsananin tsoro da fargabar ganin wanda ke tsaye a gindin wata bishiyar dorawa gashi na bar mutane, ni kuma ban karaso cikin gari ba, cak! Na ja na tsaya domin in na ce zan gudu ma, ba iya tsere masa zan yi ba, sai faman tsuma nake yi saboda da in ganshi gara in ga kumurcin maciji baki, Abubakar kenan saurayin da na tsana in gani saboda tsananin tsana da izayar da yake nuna min. A hankali ya tako yazo in da na ke yayin da ya tsare ni da ido, yana kallona, sama da kasa sbaoda tsananin firgita ban san hawaye na zuba a idona ba, sai da naga yana diga a hannuna, sannan na lura da cewa kuka nake yi, ya ce cikin dacin rai. "Ke me yasa ba kya gaida mutane in kin gansu?" Ban za ci a iya nan abin zai karc ba, don haka sai na ji wani dadi ya lullube ni, na ce "Ina gaishe ka wallahi mantawa kawai dai ka ke yi....." "Shceet! Rufan baki." Na yi saurin sunkuyawa "Ina kwana.?" Ban sani ba, ni kam na shiga uku na ce a raia, take na kakalo kalmar "Abubakar ka yi hakuri in wani laifi na ke yi 6 maka, wallahi in ka gaya min ba zan sake yi maka ba." Sai naga kawai ya lumshe ido ya bude ya girgiza kai. "Sai kin gaya min dalilin da yasa ki ke jin tsorona.?" N ayi shiru na rasa abin da zan ce masa, daga can sai na hango wata kawata mai suna Haule, tana ta sauri da ke a kanta ita kadai muna nan gurin har ta karaso ta same mu, ta ce "Hamdiyya lafiya na ganki, kinyi jigum.?" Na ce "Wai saboda bana gaishe shi, shi ne yake tuhumata." Ta cc "Abubakar ka yi hakuri, kasan Hamdiyya ba mai yawan magana ba ce, ina ga shi yasa bata gaishe ka. Ke Hamdiyya ki dinga gaishe shi, duk sanda ki ka ganshi. Zo mu tafi." Ta kamo hannuna, muka wuce shi ka fuskarsa ban kalla ba, gudun ban san me zan ga ni a fuskar tasa ba. Muna cikin tafiya ne, na k ce mata "Haule wallahi na rasa abin da nake wa Abubakar, kullum ya ganni sai ya tare ni daga yau ya cc nai masa kaza, sai gobe ya ce abu kaza na yi m2a. Yau ma kina ji wai gaishe shi ne bana yi." Ta ce "Rabuwa zaki yi da shi, ki dinga gaishe shi tunda hakan dai yake so, ko kya tsira da mutuncinki tunda dai shi namiji ne ke kuwa mace ce, bai kamata ace ma kuna wata gaba a tsakaninku ba." Na ce, "To sau nawa ina gaishe shi baya amsa min?" Та се "Кe ana baki kina kin karba, ko ba zai amsa ba, sai ki gaishe shi. Menene yafi ki yi shiru ya ci 7 mutuncinki daga gaisuwar sai mc." A haka muka yi la hirarmu har muka isa gida abinmu. Iona na zaunc na ta yi wa Baba ſirfita, na shiga na yi sallama ta amsa min, sannan ta fara yi min fada. "Yanzu Hamdiyya me yasa ki kaje ki ka y zamanki, kinsan dai na ce ki komo da wuri ko? Kuma ina abin wutar da gwandar dajin?" Sai sannan na tuna da abin wuta gashi bana son in sanar da ita halin da muke ciki ni da Abubakar. Sai kawia na labarta mata a yadda na sami gonarmu. Ta yi mamaki matuka, amma sai kawai ta ce "In bar maganar domin tana zata wani ne ya yi shuka in ya girbe sai ayi kashi mu raba, (wato ya bamu kaso daya bisa uku na amfanin gonar). Yau kwana biyar da zuwana gona, ban kuma komawa ba saboda kullum sai an tabka ruwan sama. Yau ne aka samu ruwan ya yi sauki, gari ya yi sarari, saj na shirya domin in je jeji amma wannan karon ba gona zani ba, abin wuta zan yowa Inna, sannan in samo mana ya'yan itatuwa. Ni kadai na ke ta sauri domin na biya wa Haule, ko zata je. Babarta ta ce, "ta tafi tuni." Shi yasa ma nake sauri ko zan ganta, sai mu taho tare da ita. Ina cikin lafiyata, kwatsam! Sai ga tawagar 'yammatan kauyanmu sunyo abin wuta, gabana ya yi mummunan faduwa, domin nasan abin dake tsakanina da su, ba ko wani abu ne ya jawo rashin jituwarmu ba, illah halayyarmu da tasha banbam, Su basa karatu koda Islamiyyar nan ma, ni ko ina zuwa makarantar boko da Islamiyya, har ma na gama firamare zaman jiran fitowar jarabawa ta nake yi haka Haule Kawata makarantarmu daya, tare muka gama su kuwa in ban da tallace-tallace da kokaye kokayen samari babu abin da suka iya, ni ko bana talla sai dai zama a gida ko in je abin wuta ko in zauna taya Inna aiki. To wannan kamewar kan da nakc da ita, shi ya janyo min tsangwama a cikinsu, musamman irin kyaun da Allah ya bani, duk cikinsu babu kyakkyawa kamata. Ga fari da hanci ga uwa uba gashi har baya, abin da ya sa ma ba na yarda su ja ni muyi fada da su saboda ja min gashi suke yi da karti in yi ta ihu, saboda tsananin zafi. Ina ganinsu, sai na kara azama domin kar su tarar da ni, nasan ba zamu rabu kalau ba. Da saurinsu suka Karaso in da nake, suka tare ni daya daga cikinsu ta ce "Ke Hamdiyya wato shi ne don rashin mutunci kina jin muna kira ki ka share mu.?" Na ce "Lah! Wallahi ban ji ba." Tas! Na ji sąukar mari, fayar ta ce "Yau sai kin gaya min abin da ki ka je ki ka ce wa Bala mai kifi rannan." Na ce "Me naje na ce masa?" Dayar ta ce "Kin fi kowa sani munafuka, ba zuwa ki ka yi kika soki Mairo a gabansa ba, kin san dai sani sarai saurayinta ne, shi ne ki ka ce wai wani kin gansu suna kokawa da Musa mai manja ko.?" Kai da jin zancen kasan an yi ne don aci min mutunci kawai, sai kawai na ji ta sake kwada min mari, daga nan sai suka hau ni da duka. Ba zan iya ramawa ba, domin an ce 'Sarkin yawa ya fi sarkin karfi.' Suna cikin dukana, sai ga tawagar su Abubakar nan sun danno, suma suna zuwa suka raba mu, na koma gefe ina ta harar hawaye, a kaina a sunkuye duk suka watse suka bur ni ina ta faman kuka, motsi na ji a bayana, a firgice na juya don ganın mai motsin, Abubakar ne tsaye Kyam ya zubo min ido, na yi baya cikin dimauta take na zube ina gaishe shi, sai kawai na ji ya ce "Me ki ka yi nrusu.?" Cikin shesshekar kuka na ce "Babu abın da na yi musu, kawai don suna son su dake ni ne." י Ya yi shiru, sai can ya ce "Yanzu ina zaki je ?" Na ce, "Inna zairsamo wa abin wuta." "Zo ki wuce ki tafi." Cikin sauri na fice na ta rawar jiki. ina yi ina waiwayen sa, da na waiwaya mun hada ido sai in yi saurin dauke kaina, don kar ya ga ina kallonsa, shi kuwa ya zubo min ido har sai da na yi nisa, sannan ya lafi. Nayo itace mai yawan gaske, da kyar nake dauka saboda nauyi. Tun daga nesa na fara hango mutane a kofar gidanmu, sun taru ga tabarmi an shimfida, ga bokiti da ruwa ana ta alwala. Gaba daya jikina ya yi sanyi da kyar nake tura gwiwa duk da ban san me yake faruwa ba. Na karaso. Ina shiga cikin gidan, sai naji ana cewa "Uwani ba kuka za ki yi masa ba, addu'a za ki yi masa domin irin wannan jiyar an yi kankarar zumubi ansha jiya." Abin da narji wasu tsofaffin mata ke fada kenan, yayin da na shiga dan da nan naga ne abin da ya faru, wato dai Baba ya mutu kenan. Nan da nan na yi jifa da iccen, na fara kuka ina kiran "Wayyo Allah Babana ka tafi ka barni, Allah ya jikan ka da rahamarsa." 10 Inna ce zaune, can gefe kuma kanwarta ce Baba Mairo, da kanwar Baba Hajiya Tasalla, suke tattaunawa akan batun gadonmu. Hajiya Tasalla ce mai cewa " Yo ke Uwani tunda dai gida za ko koma, ai ba kya tafi mana da 'ya ba, tunda ta isa aure kawai in yaso ta dinga zuwa tana ganinki ko ke kizo." Ta cс "A'a, ba wani abu ai kuma 'yarku сс, gata nan kun fini iko da ita. To yanzu batun gona sai muje mu sami Maigari (Dagaci), mu gaya masa halin da gona take ciki, in yaso sai ya karbar mana a nemi mai saye a sayar don kar wani ya sake kwacewa. Inna ta ce "To yanzu me muke yi, mu tafi kawai muje mu safe shi, abin da za ayi ai maganinsa yi." Suka mike sai gidan Maigari game da zancen gona. Bayan sun kwashi gaisuwa, suka yi masa bayani daya bayan daya, duk yana saurarousu. Hajiya Tasalla ta cc "Kaga bawan Allahn nan babu abin da ya mallaka sai gonar nan, ya kamata ace an binciko wanda ya aikata." Maigari ya syara zama, ya dube su daya bayan daya ya ce "Y anzu shi Malam Musan kafin ya mutu bai sanar da ku abin da ake ciki ba ne?" Suka dube shi cikin rashin fahimta, suka ce "Ba mu ganc ba.?" Ya cc "Ai wannan gona da ku ke zancc, bata Malam Musa ba ce, gonar Babana ce har wannan gidan da ku ke ciki shi ya mallaka masa tun sa'adda mahaifinsa yazo garinnan. Ke Tasalla don ke macece shi yasa ina ga bai miki bayani ba, amma ai yasan komai saboda haka gidan ma barinsa zaku yi, kunsan lamari ne na da can duk shedun da aka gabatar ada sun mutu saboda haka sai ku dau hakuri, shima Malam Musa ya sani ai ya sanar da ku tun katin va mutu, don guрп rigima, domin babu shaidu." Tasalla ta ce "Yanzu shi kenan gidan tashi zamuy kenan mu bar maka ko ?" Ya ce "Ayo, ai tashi ya zama dole dama baku ba zan tura ayi kiranku in sanar daku." ta yi murmushin Karfin hali "Ai shi kenan 'Yalla6ai, zamu bar muku gidan, ba komai." Hajiya Tasalla ce ke taya Inna hada kayanta, zata tafi garinsu, ga 'yan'uwanta duk sun zo suna taya su duka ka kwashe kayanta aka barmin nawa Hajiya Tasalla ta bada min nawa kayan kaf ta daure ta ce in je in raka su Inna in yaso na dawo da yake daga garinsu zuwa garinsu Inna ba shi da nisa da Kafa ma mutum in ba mai son jiki ba ne zai iya zuwa, dama garinmu daya da Hajiya Tasalla yar Babana duk unguwa daya muke gidan da take aure babu nisa da gidanmu tana auran wani mutum mai suna Baba Sani yana sana'ar kasa kayan miya a nan maciyar unguwar. Kwanana biyu a gidan su Inna ta tarkato ni na dawo gidan Baba ba abin da nake kiranta da shi kenan. ** Hajiya Tasalla su su uku ne a gidan mijinta, matan wa da kani wato dai mazansu 'yan uwan juna ne, amma ba sa zaman lafiya kuma babbar masifaffiyar ita ce Hajiya Tasalla, duk tsoranta suke ji duk ranar da taje 12 unguwa ranar kamar Sallah a gidan amma in ta dawo ta dinga dube-duben abin da zata yi bala'i a kai, duk da bata taßa haihuwa ba ita ke juya 'ya'yan gidan, tana da tsafta sosai haka nema yasa komai nata a killace yakc, bata bari yaro yaje ya taba mata kaya kofin da take bai wa yara ruwa ma daban yake, in kuwa ta yi shara to ko ke wace ba ki isa ki shiga dakin ba sai ta baki ruwa kin wanke kafa ga shi ta rangada kunshi ya yi jawur da ke tta fara ce tas gata kyakkyawar mace doguwa mutane suna yawan gaya min muna kama da ita, shi yasa ma take sona, tun kafin in dawo hannunta duk Sallah sai taje birni ta sayo min kayan Sallah sannan ta bayar a yi min Sinkuna masu kyau, ta kawo min gami da kayan kwalliya tun kafin Baba ya fara cuta take cewa ya bar mata ni ya ce shi ba zai iya rabuwa da ni ba, sai dai in in zauna a tsakaninsu bani nan bani can shi ne ta yarda а kan hakan, a yanzu kam muna zamanmu lafiya da Baba babu abin da na nema na rasa a wajenta, don haka hankalina kwance. A zaune nake gaban Baba muna hira, ta ce Hamdiyya maganar gaskiya ba zan zauna in zuba miki ido kina gabana gododo dake babu sana'ar komai ba, ke fa marainiya ce yanzu in auranki ya tashi mai za a kai miki in ba mu nema ba gashi Yaya Musa ba rai, ita kuma Uwani ba wata sana'ar kirki ba, haka kurum in ruwanka bai isa alwala ba sia kayi taimama ka taşhi yaushe don girman kai kace 'yarka ba za ta yi tallaba, sai karatu, in auran ya tashi karatun za a jera a dakin? Ni dai jin Baba nake kawai tana ta faman masifa, sai da ta 23 gama na ce, to yanzu Baba me zamu dinga yi na savarwa? Та сс, rogo za ki dinga sarowa rafi kuna dafawa ki dinga kaiwa tasha, an ce akwai riba sosai kinga sai ki dinga tara kudinki a banki." Na ce to kuma in jarabawata ta fito fa? Ta ta fito mana, kin san dai babu maganar karatu domin ba za ki yi ba wanda ki kaа yi a baya ma ya wadatar. Tafe nake da farantin tallan rogo akaina, ya dahu ya yi fari sal ga gari sai kamshi yake bulawa, dama Baba ta haddace haduwar rogo na dure shi a wata katuwar leda na dora bisa tray ga wasu 'yan kananan faranta masu kyau tun itip na auran Baba na debo su guda biyar ya wanke su na dora bisa ledar rogon gami da wata 'yar wuka, bayan na yo wanka nayi kwalliya na sanyo kayana na saka hijabi na fito Baba cewa take Allah ya bada sa'a 'yar gidan Baba, don Allah a tsaya a yi ciniki kar a dawo da kwantai." Na ce To ina tafe ina cewa a gaskiya Baba ta fiye san kudin tsiya ni wallahi har kunyar tallan nan nake ji, abin da ban saba ba, yanzu in wadannan marasa mutuncin suka ganni shi kenan na kade, dagangan ma zasu takale ni domin su 6arar min da kayan sana'ar bare kuma uwa uba Abubakar, Allah dai yasa har in gama tallana ba zan ganshi ba. "A hayye jama'a ku zo ku yi kallon 'yar makaranta da tallan rogo, la yau me zamu gani?" Dayar wato Jimmala da ta fara magana ta ce karya ce, ta kare wai bori ya kashe boka, sauran suka ce ai dama karyar da 14 farar duk na banza ne, wannan sabon salon ba zai yiwu ba dole a dawo hanya. Duk wadannan maganganun da suka yi ban ko kalle su ba, na nemi guri na zauna nima don da nan kuwa mutane suka rufe ni da sayen rogo mai cewa in bashi na ashirin nayi mai na goma nayi, kafin maye wannan rogo ya kare, sai kudina a hannu, kun san mutane suna son su ga abu mai kyau ga kuma tsafta ga shi dai suma rogon suke sayarwa amma sai da nawa ya Kare sannan nasu ya kare, ni kuwa ma tuni na taho gida. Baba saboda murna har rawa ta yi, ta ce, to gobe sai kije ki kuma kaiwa can. Tofa, yau da gobe sai da ya kasance in bani na kawo rogo ba, ba a saycn na kowacce a gurin nan sai ya zamana har da masu daukar min su kai min gurin sayarwa, domin ba zan iya dauka ba. Manyan, kwanika irin na mai saida gurasa da nama sai an cika, min shi har uku asa almajirai su kai min, idan na zauna bana hutawa sai ya kare, saboda masu saye Takar kudi kuwa wata katuwar lalita ce aka dinka min nake daurawa, a ciki sai na cikatą da kudi tun ban saba ba har na zo na saba, na dake bana jin kunya kuma na yi suna sosai kowa sai Hamdiyya a mutunce da girmama juna buna ciye ciyc a titi bana kokąwa da samari bana kallon fada bana yawan surutai ba kuma na fushi da mutane, baka ne ya jawo min matukar farin jini a gurin mafiya yawan saonn da ke gurin, kowa yana so ya gabatar da kansa gare ni ana shayin irin amsar da zan bayar. Al'amarin da ya kara rura wutar gaba tsakanina da 'yammatan kauyanınu har 15 suka fara shawarwarin daukar mataki a kaina, ba tare da na sani ba. A tafe nake na tura ayi min gaba da kayan domin dama sai an kai an diddire sannan nake zuwa, sai nayi kicibis da Abubakar sai na dan yi dam naja na tsaya, ya karaso dab danı ya tsaya na kalle shi a tsorace na ratse zan wuce sai ya ce "Yau ba gaisuwar?" Na ce au na manta, na dawo na gaishe shi ya amsa sannan ya dube ni ya ce wai me yasa ki ke jin tsoro na ne? Na sunkuyar da kai na ce ba komai ya yi murmushi sia kin fada min za ki bar nan." Na ce, gani na yi in ka ganni ba ka yi min dariya sai ka daure fuska, shi ne nake jin tsoro kar ka dake ni." Sai ya yi dariya ya ce dama shi kenan abin da ya jawo tsoron? Na cc E, ya ce to shi kenan daga yau na daina daure miki fuska, shi kenan kema ki daina jin tsorona na ce to na daina, ya ce to yi murmushi in gani, sia na sa hannu na biyu na rufe

Chapter 1 of 6