Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 5
sake furta komai ba. Ya na master room dinsa da ke bangaren Ummu, Ummu ta shigo babu sallama ta tsaya ta na kada kafada to munafiki yau dubu ta cika ka maida Shema'u sai hankalinka ya kwanta, babu yadda ban yi da kai ba akan ka korata gidansu amma ka ki wai har miliyan daya ka ba da sadaki dole ne nima ka bani kai wallahi in kana son zaman lafiya har gyaran daki sai kayi min, kai ni dama nasan sai ka mai da ita sau nawa muna kwance za ka ringa kiran sunanta, kai kun yi karya daga kai har irin munafukan da suke: goya maka baya, tunda ta ke da Nazir ba ta taba ganin irin fushin da ta gani a yau a fuskarsa ba ya na dago wa ya wanke mata fuska sannan ya ce ian so ki kula ki kuma san kalaman da ya kamata kiyi amfani da su wajen fada min magana ki kiyayen ba ki sanni ba ne rainin har ya shige kaina da kannena ya kuma gangarat kan iyaycna a hir dinki yanzu da da ba daya ba ne iria so ki gane haka kin ji ko, in za ki zauna ki zauna in kuma ba za ki zauna ba babu wanda ya rike kafafunki kuma ke ba makauniya ba ce kinsan hanya, kuma ina so in sanar da ke Shema'u matata ce wacce nake so kuma 62 ita ce uwar 'ya'yana, in kina son zama da ni ki bita ku zauna lafiya, ya juya ya fice ya barta ta na cizon yatsa ta fadi lalle dole in sake shiri Shema'u wannan karon da shirinta ta dawo. Ya na zaune falon Shema'u wanda ake ta gyara shi saboda dama ta riga ta yi pakin din kayanta, Surayya ce ta ke aikin Surayya ya kirata kirawo min Anty ki ta ce yau tun dazu ta tafi can makarantar da ta ke teaching saboda suna da meeting, cikin ransa ya ji ya yi masa zafi wato ba za ta fada masa ba illah Shema ta sake hali kuma fa in bai was aba ya na da sauran aiki ya samo kiran Number dinta amma layin a kashe yake, ko da ya ke batun yanzu ya ke kiran layin ba ya ji haka, saboda haka tuni ya soma tunanin ko ta sake layi ne da wannan tunanin ya yiwa surayya magana bani number dinta ai ba ta fita da handset din ba, ina ga garin sauri ta manta shi maza dauko min ta je ta kawo masa nan ya shiga yi mata bincike, fuskar wayar ma hoton Najib ne da ya shiga inbox din ta kuwa duk wasikun Najib ne, haushi ya kama shi gaba daya ya yi delete din su har numba dinsa ya goge ya tashi ya shige master room dinsa nan ma wani abin haushi ne dan ya yi kura sosai da alama ba ma ta amfani da shi wato yarinyar nan tama goge shi ababin rayuwarta. Alhaji Jibrin da Alhaji Yusif na zaune suna zantawa kan abin da ya faru na mayar da auren da su ka yi Alhaji Yusif ya ce ni kam ban san yadda zan 63 nuna farin cikina ba kaga fa gwara da ta zauna da yaranmu zasu ringa haka a yau da mutuwar aure ta ragu dan kasan fa da haushi kaga wani yazo zance har gidanka wai kuma wajen matarka ba ma dole takaici ya sa ka ka maida ita ba, Alhaji Jibrin ya ce haka ne amma fa kasan akwai wadanda in sun saki mace an ringa ci mata mutunci ka ji ya na cika bakin kafin yaje ya dawo ko tsinkenta ba shi da bukatar gani ai kasan wargima guri yake tararwa kasan akwai macen da zata so ta zauna har ta gama idda to amma cin mutuncin da tijarar da mijin zai yi mata ne ya kansa ta tafi gidan iyayenta, wani laifin a mace ne sai kaga dama can bata samu tarbiya ba, Allah-Allah ta ke ayi sakin ta yi shewa ta yi dariya ta hada inata ina ta ta fice dama a gidansu ta na da daki tana zuwa share shi kawai zata yi ta zauna, Alhaji Yusif ya ce zaman ne yanzu wasu iyayen idanunsu ya rufe saboda kudi sai kaga uwa tasan 'yarta tana fasikanci amma saboda dan wani kaso da zata bata na abin da ta samo sai kaga ta daure mata gindi kai dai wannan zamani Allah ya ba mu wucewa lafiya. Hajiyan su Nazir kuwa tun dare kasa rintsawa tayi saboda tsabar mamaki wai Nazir ya iya sakin Shema, kai wannan yarinya 'yar albarka ce ko ni da nake uwarta aka sake ni gidanmu zan tafi amma sai gashi yarinya karuna ta iya daurewa ta zauna ba tare da ta senar da kowa ba kuma tabbas da ta sanar din a iokacin ko ya na so ko ba ya so zai maida ita amma 64 sai ga shi ta yi shiru har sai shi da kansa ya nemi ta koma kai dan da ya sami tarbiya daban ya ke. Mahaifiyar Shema itama ta jinjina abin, ta kuma sarawa 'yarta tare da yi mata addu'a da ita da ziri'arta ta kuma jinjinawa maigidanta da ya fi karfin iyalinsa da kuma shimfida musu doka da yake wanda babu mai tsallake abin da ya fada duk wannan nasara da 'yarta ta samu tatattara ne bisa iko mijin nata, iyaye mu nutsu musan irin shimfidar da zamu ringa yi wa 'ya'yanmu domin su kasance masu tarbiya a tsakanin al'umma. Anas da Kabir kusan in ce sun fi kowa murnar wannan kome dan har wata walima su ka shirya wacce isu isu ne familes su ka hadu dan taya ma'auratan murna walima ce wacce hatta iyayensu tun daga kan maza har mata sun halatta, amma wani abin takaici Ummu fita ta yi ba tare da izinin mijin ta ba ta tafi gidansu saboda ba ta da bukatar zama wajan walimar an yi wa'azi an yi ciye ciye da tande tande har da lashe-lashe, da shaye-shaye, sannan kowa ya koma in da ya fito. Ango Nazir ya na zaune a falo saboda duk in da ya yi da Shema ta saurare shi ta ki daga karshe da ya ga wanki hula ya na nema ya kai shi dare sai ya shirya musu honey moon da farko ki ta yi wai ita ba zata ba da kyar ta amince ba dan ta so ba, saboda ya ce in ba ta shirya ba zai fadawa mahaifinta, lokacin da ya sanar da Umınu kwalarsa ta ci ita sam sai dai itama ya 65 tafi da ita ko kuma ya sake ta dan ita ba za ta zauna ta zama bora ba wani kallo ya yi mata ta saki rigar tasa ta na kuka ya ce kiyi lis din abin da kike so dan ina jin in mun tafi zamu yi wata daya ko biyu dan daga nan har dubai zamu zarce saboda harkar kasuwancina. Surayya ita aka bar wa yara sai kanwar Alhajinsu da mijinta ya rasu ta dawo gidansu Hajiya ta ce ta dawo ta zauna da yaran kafin su dawo. Kasar South Afrika muka nufa garin Capetown mun sauka a wani kayataccen hotel rayuwar da muka gudanar a wannan Kasar abu ne wanda ba zai fadu ba dan na tabbatar wa da zuciyata lallai ina tsananin son Nazir kamar yadda ya nuna cewa a iya lokacin da ba ma tare ya yi missing dina, munje kasashe sun kai goma sha hudu dan ban taba tsammanin zanje su a rayuwata ba, kwannanmu uku a London muka tafi kaiwa wani abokinsa ziyara mazaunin can ne amma ba dan kasar ba ne ya na zaune a wata unguwa mai suna Bourne street mun isa gidan sai dai matarsa muka samu ta sanar mana ya tafi asibiti gurin dan uwansa a gaskiya gidan ya dauki hankalinsa sosai, wanda ita matar nayi min hira amma hankalina ba agun ta ya ke ba. Nazir ya zungure ni to sarkin sha'awa shi ma wannan gidan ya baki sha'awa ne, ko shi za'a gina miki an fasa wancen ta yi murmushi Abbu Nur gidan nan ya yi min sosai, nan dai muka yi sallama da ita akan gobe zamu dawo in ya zo ta fada masa gobe karfe hudu ya jira mu. 66 Washe gari taxi ta ajiye mu karfe hudu daidai mun yi sa'a mun samu El-Bashari a gida sun yi matukar murnar haduwarsu domin sun dade ba su hadu ba nan fa suka yi ta hira yau zamu wuce karfe bakwai dan daga nan ma Dubai zamu daga nan sai gida a nan ya ke tambayar sa waye ba shi lafiya ya се kanina ne dan wan baba na ne ya masa mi sauki dan muna sa ran sallama gobe, Allah ya kara sauki sai kazo muje mu duba shi daga nan mu tafi dan fam mun gama shiri Nazir ba ka da kirki memakon ka sauka a gidana kayi hakuri wani lokacin in mun dawo sai mu sauka a gidanka nan mu ka shirya har matarsa dan su daga sama muka fito dan zuwa asibiti sai da ya je ya yi mana siyayyar yara sannan muka nufi asibiti, mun shiga wajan mara lafiyar kasancewar lokacin ziyara ne ya na sanye da kayan majinyata ya rame matuka kallo da ya nayi masa na dauke idona ba kowa ba ne fa ce Najiburrahaman da sauri ya sake juyowa dan ya gaskatga abin da idanunsa suka gani, duk daga ni da ya Nazir ya yi masa amma ba zai taba manta kamannin mai jan kunnunnan ba, su ka gaisa tare da tambayar jikinsa ya ce da sauki El-Bashir ya gabatar da shi wajen kaninsa ya kuma gabatar da kanin nasa gurin abokin nasa, Nazir ya ce Shema ba ki gaishe shi ba ta ce sannu ya jiki? Da kyar ya iya amsa da sauki Nazir mutum ne mai zafin kishi ko cikakken minti goma ba su yi ba su ka bar Hospital din, karfe bakwai jirginsu ya shilla Dubai. 67 Mun zauna a hotel din da yasa ba sauka kullum da yamma yakan fita da ni yawo wani lokacin ma har wajan harkokinsa ya kan fita dani kudin da Abbu Nur ya kashe min Allah ya yi yawa dashi, har furniture ya sake min na isa wanda ni Shema'u ban taba ganin irinsa ba hatta kujeru da kirin set da dukkani nau in kayan alatun da za su yi kyau da furniture din tun kafin muta ho kaya suka yi gaba. Ana i gobe zamu dawo muka yo wayar gobe a tare ma washe gari karfe biyar da rabi na yamma ta yi mana ne cikin garin Yola mun sami yara da surayya da Goggo sun tare mu amma shiru naga ta musamman, amma ko leke. Bayan ya yi mun yi wanka mun ci abinci zaga yayi 6angarenta can ya dawo ya ce wa Goggo ina Umma ta fita ta ce ai tun safe suka fita ita da Hajiyan ta ni nayi zaton ta dawo bai kara cewa komai ba ya juya, ya ce min ya tafi gida na ce ya gaishe su kafin nima in zo gaida su, bai dawo ba sai bayan goma. Muka yi sallama da shi sai gobe saboda yau dakin Ummu zai sauka, har lokacin ba ta dawo ba in da ya tafi ya bar dakinsa haka ya same shi da kansa ya zage ya gyara sannan ya yi wanka ya kwanta, sai bayan sha daya na dare Ummu ta shigo kafadarta rataye da sury dan ta tunda taga wayanta a sude tasha jinin jikinta a falo ta shimfide shi kamshin turaren Nazir ya bugu hancinta master room ta nufa da murnarta taia fadın darling saukar yaushe, shiru ya yi mata ta kai hannu zata taba shi a tunaninta bacci ya ke 68 ya yi saurin murginawa, darling meye haka ta fada cikin muryar shagwaa, cikin dakakkiyar murya ya ce ki koma in da ki ka fito ki duba agogo sha daya da kwata ki ka shigo ke ga mara kamun kai ko, na mijin arziki ba zai kai sha daya ba bai doshi iyalinsa ba cikin kukan kissa ta ce haba darling ya zaka fadi haka ya kamata ka tsaya ka ji hujjar kai wa ta iyanzu ko lafiya ko ba lafiya ba, Ummu ki fita idona in rufe kinsan tun sanda na dawo tun yaushe nake kiran lambarki, kin kashe wayarki kuma kin san cewa yau zan dawo tunda na sanar da ke na tabbata cewa tunda na tafi kema yawonki kike, to ki sani ba zan dauki raini ba, nan dai su ka yi ta taska tsiyarsu har asuba suna sa-in-sa in da ya kafa mata dokar rashin fita ya soki in taga ta fita to asibiti ne. Rayuwa gidan Nazir a yanzu komai ya sauya dan halin kowa ya fito an gane kowa yanzu duk wata fawa da Ummu take da ita babu ta dawo abin ban tausayi, duk dangin miji sun dawo daga rakiyar ta duk wani abu da tasa mu gurin miji ta rabar wa 'yan tsibbu dan darajarta ta daukaka amma a banza a yanzu ko cikin gidan-su Nazir sai abin da Shema'u ta ce domin mijin ta ne mai naira dan a yanzu ya fi mahaifinsa naira, sannan ita Shema'u ba mai bakin cikin b a duk abin da ya cancanta ba wai sai ka tambaya ba ita ta ke ba da shawarar yin komai dangi kowa santa ya ke, Ummu kuwa ta zama kamar wata mujiya gurin dangi da mutane dan da kanta ta ce ita dai ta gaji da wannan 69 aure Nazir ya sawwake mata ya ce saki ki ke so to kije ki fadawa wadanda suka hada auren sai su warware. A yau mahaifiyar Ummu ta kawo mata ziyara ne ta kawo mana labarin wani sabon boka ta ce kawai ta fidda kudi su kashe Shema'u da 'ya'yanta su huce takaici, Ummu ta ce dakata Hajiya ni yanzu ba ni da kudi ba ni da kuma hanyar samunsu abin da mu ka yi da bai kama Shema'u ko 'ya'yanta ba ko mun samu nasara sai abu ya lalace ni yanzu na gane komai ya same ka ka tsakake zuciyarka shi ya fi Shema ni na tabbatar ba na gabanta babu irin kunci da bata shiga ba same ni a yau Allah ya fitar da ita komai ya same ta ta dangana shi da Allah ai Hajiya gani ga wane ya ishi wane tsoron Allah, ko abubuwan da su ka ringa samun mu ya ishemu tunani amma ina wallahi Hajiya da ina da ikon sake uwa ni kam da na sake ki dan sam irin tafarkin da ki ka dora ni kin cutar dani ina amfani bin bokaye da 'yanbori na dawo kamar mujiya cikin dangina, ni wallahi kin cuce ni a yanzu ni na gane zan nemi gafarar abokiyar zama na da na mijina zan kuma koma ga Allah, Allah ya shiryi duk mai hali irin nawa da naki Hajiya dan ganin abin da ya same ni ya ishi duk mai irin halina ishara, jikin Hajiyarta ya yi sanyi ce to Ummu nima na yi nadama kiyafe ni, ni a tunanina ina son ki zama tauraruwa gurin mijinki shi ta ya sa na shigo hanyar bata amma nima yanzu na gane 70 zan je mu sasanta da 'yar uwata gaba daya Nazir ya tausaya musu don duk abin da suke fadi a kunnensa. Oder furniture din Shema'u ya iso dan dama irin wannan oder sai ta yi watanni uku ta ke isowa to kaya dai sun iso lafiya har an shirya su tsaf abin gwanin sha'awa nata na da ta mayar da su dakin mahaifiyarta gaba daya 'ya'yanta har dan gidan Ummu Abba su ya bude musu account duk wata akwai kudin da ya ke zuba musu ga hannun jari da ya siya musu abin nasu gwanin sha'awa. Hankalin Ummu ya kara tashi ganin cikin da Shema'u ke dauke da shi domin ita shiru babu wani labari gashi duk in da taso su shirya da 'yan uwan mijinta kowa ya watsar da ita bata da wani mutunci a idanunsu wani lokaci takan yi kuka ne da kanta domin ita ta jawa kanta da ta zauna tsakani da Allah tun farko da hakan ba ta faru ba ga shi da wanda ya isa da wanda bai isa ba kowa wani gani gani yake mata. Mahaifin Shema'u da sirikinta suna aifahari da ita domin ita ta kawo wa families dinsu sabon sauyi dan yanzu duk wata ya da ta kwana ta tashi cikin gidan su Nazir ba ta isa ta yi yaji ba ko ta kaso aurenta ta dawo domin Alhaji Yusif ya bi ra'ayin amininsa wajen sarrafa 'yayansa duk wacce ta yi yaji to kaninta ke maida ita saboda haka yaji ya kare cikin zuri'arsu. Shema'u na zaune cikin lambun gidan ta ita da kanwarta da take riko Surayya, hankalinta na kan rubutun da ta ke Surayya ta ce Anty wai yau rubutun me kike littafi zan rubuta kan labarin rayuwa dan mun yi magana da Zahra'u Baba har ta ce zata duba min idan ya 71 yi sai ta hada ni da Lis Computer daga nan sai ta hada ni da babbar harka Al-amin Bookshop babban dila, ni kuwa Anty sai naga da ya wa duk wani littafi ta Al-amin ya ke fita, tun da ki ka ga haka to mutum ne mai aminci kinga ya ci sunansa Aminu, gaba daya su ka sa dariya, sai Antina babbar marubuciya in ji Surayya, ke dai ta yani da addu'a nima zan fasa cikin marubutan zamani don in ba za tawa basirar. Kasancewar bikin Surayya ya zo kwata-kwata Shema ba ta samun zama, don a gaskiya Nazir ya yi mata komai ita kuwa ta hada ta mata kicin abin sai wanda ya gani gaba daya duniya ta yi wa Shema dadi yadda mijinta ke ji da ita haka dangin miji gashi uwa uba dole Ummu ta yi saranda dan yanda ta ke mata biyayya har abin mamaki ya ke ba ta dama hausa sun cе komai ya yi farko zai yi karfe. TAMAТ Allahumma sali ala Muhammad, wa ala ali Muhammad, kama sallaita ala Ibrahim wa ala ali Ibrahim innaka hamidul majid. Mu hadu a: --1. GWANAYE 2. 'YA'YAN HAJIYA 3. ZUBAR HAWAYE 4. DANGANTАКА Suna nan fitowa ku taya ni da addu'ar Allah ya sauke ni lafiya. Mai Launarku: ZAHRA'U BABA YAKASAI Maman Shurem) 72 LITATTAFAN MARUBUCIYAR UWAR MIJI KO KSHIYA? 1 & 2 BAN SAN HAKA KAKE BA! 1 & 2 HADIYYA 1, 2 & З TARKON SO 1, 2,3 & 4 FUREN KAN JUJI 1, 2 & 3 ZUMUNCI KO ANINCI 1, 2 & 3 HATTARA MATA 1,2&3 HUDUBAR MAZA 1, 2 & З HUZAYYA 1 & 2 GANI GA WANE... AWARWARO PRINTED BY: AL-AMIN B/PRINTING & PUBLISHING COMPANY No.; 156 S/TITIN MANDAWARI KANO CITY. 08028411703 An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 5 of 5