Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 5
kula da duk lamurana 30 ba sai dai Allah, wai duk ta ji in je in ji da dogarа sanda da nake da kuma magana da hanci da nake, kuma wai in Allah ya yarda na zauna a haka kenan, na yi murmushi na ce Allah ya fiki na rike hannun 'yata mu ka fice saboda naga take-takenta. Sannu-sannu ba ta hana zuwa, sai dai a dade ba aje ba, yanzu gashi na samu cikakkiyar lafiya, yawo da sanda ya zama tarihi magana ta ta dawo ras in ba ka san nayi wannan jiyar ba in na fada ba zaka yarda ba a yanzu Nur ta na Primary one yanzu ina dauke da wani cikin wanda yanzu ya sami watanni biyar Nazir yakan kwatanta adalci domin yanzu tsakanina da Ummu babu bambanci muna cin abincin rana ni da Nazir da Nur mu ka ringa jin ihun Ummu daga ni har shi mu ka mike muka yi bangaran ta me zan faru mun same ta ta rike suraj jini ya wanke falonta lafiya muka tambaye ta wai showglass dinta ta fado masa aka ga shi har kunnansa daya ya fita inalillahi wa inna ilaihir raji'un ban taba ganin tashin hankali irin wannan ba, nan da nan aka dauke shi sai asibiti nan da nan sun yi masa taimakon gaggawa amma fa kunne an rasa shi domin sun ce bazai koma ba, sai dai ayi hakuri da shi, Nazir ya ringa yi mata fada yana cewa sau nawa zan yi miki magana akan wasan da Suraj ke yi da show dinki har cewa na yi ki mai da ita wani dakin kin ki ke duk abin da yaro zai yi bakya kwabarsa wai kar ya yi kuka, to ke ai gashi nan ya saki kuka ko banza ya nakasa ita dai babu bakin magana sai kuka ya ci gaba da cewa da 32 Nur ce taje wajan yanzu kin rufe ta da duka kice uwarta ta turo ta tayi miki bari gashi nan yanzu ai kin ga sakayya duk wanda ya ce tukunyar wani ba za ta tafasa ba to tasa ko dimi ba zata yi ba, nan dai muka barta asibiti dan an kwantar da su, kullum ni da kaina nake zuwa kai abincin dare in kuma duba su har aka sallamo shi, memakon ta bar wa Allah amma sia ta ke ganin ni nayi mata asiri saboda 'yata daya ta kuma dauki aniyar sai taga bayanta, har cikina ya shiga wata tara bata san ina dashi ba, a lokacin ita kuma ta sake samun na uku, Nazir baya nan ya na Dubai saboda haka tun safe na ji alamar haihuwa ban fada wa kowa ba na kwashi kayana sai asibiti da kaina na tuka kaina saboda a lokacin ciwon ba wai zafi yayi ba sai da ciwo ya kankama sosai sannan nayi waya gidanmu na kuma sanar da gidan su Nazir ina asibiti da ya ke sun san asibitin da muke zuwa. Ban haihu ba sai bayan karfe biyar na haifi yan biyu duka maza nan da nan har an yi wa Nazir waya an sanar masa sai washe gari muka dawo gida, sai da muka dawo gida Ummu ta ji na haihu ai kuwa ta kadu tunda ba ta ban da ciki ba sai haihuwa kuma 'yan biyu duka maza, asali bai ta shigo gurin taga yara, hankalin ta bi sake tashi ba sai da taga yanda Nazir ya ringa rawar jiki ya kashe kudi sosai ban taßa tunanin Nazir zai iya yi min abin da ya ke min yanzu ba. Ni da kaina nake cewa lallai mai hakuri ya na tare da Allah, an yi suna lafiya yara sunansu Abdullah da Abdurrahaman, 33 na ci gaba da rainon yara na mijina kuma yana nuna min so da kulawa dai dai gwargwado. Ranar da na yi arba'in na ji hargowa a farfajiyar gidanmu na saka hijab na fita na sami Police ne guda biyu wai nan ne gidan Nazir Yusif? Na ce E, nan ne su ka ce suna son magana dashi na ce baya nan yana Dubai, su ka ce to matarsa ce Ummu su ka yi hatsari suna asibiti tun jiya, ban san ba sa nan ba na ce to ita da wa ina yaran ya ce ki zo muje duk sai kiji bayanin komai na ce ina zuwa na koma falo na yi wa Hajiyar su Nazir waya ta cc ai Alhaji ya na nan ga su nan na fito na baiwa mai yi min raino yaran gaba daya na fito sai da muka yi jiran su Hajiya sannan muka nufi asibiti, kai abin babu kyan gani, sun tafi wajan yawon asirinsu a nan su ka yi hatsari a hanyar su ta dawowa daga Gombe zuwa Yola domin yaranta yayeyen shi ya rasu mahaifiyarta kuwa ta karye a hannu ita kuwa saboda razana cikin da take dauke da shi ya bare shi kuwa Suraj bai ji wani ciwo ba amma babu wanda ya ke hayyacinsa abun gwanin tausayi. Saboda bacin rai Alhaji Yusif ya ce ba za ayi wa Nazir waya ba-duk san da ya dawo ya ji rasuwar dansa lokatin da 'yansanda su ka sa da kayansu da aka samu a wajan hatsari ba komai ba ne in banda jarkokin rubutu sai garin magunguna Hajiyan Nazir ban da kunya babu abin da ta ke ji, wai kanwarta ke wa dan cikinta haka kai albasa ba ta yi halin ruwa ba da ta yi da batai yaji ba, sun kwanta asibiti amma ita 34 Umma Hajiya mahaifiyar Ummu gida aka dawo da ita dan ayi mata dorin gargajiya. Wannan karon Nazir ya dade fiye da lokacin da ya saba bayan ya dawo ya samu labari daga bakin mahaifiyarsa a gaskiya fadar bacin rai ma bata baki ne dan ransa ya baci sosai har Allah ya isa ya yiwa Ummu dan ya ce ita ta kashe masa da zaman da Ummu da Nazir suke zama ne mara dadi dan ya share ta tamkar ba ita ce ta musamman dinsa ba, dan ma ni ba irinta ba ce nasan hakkin zaman takewa shi yasa duk sanda ta ke da girki sai na yi 'yandabaruna ya tafice. Ummu duk ta kade ta fige tayi lakwas domin bahaushe ya ce in duka ya yi yawa naka kan kare to wannan abu dai haka ya ke domin Ummu abin ya mata yawa ga dai mutuwar da ga shi Suraj ya nakasa cikin da ake takama da shi ya bi rariya kai wannan abu ya yi ma ta yawa amma tasan wannan ba komai ba ne in banda sa hannu da Shema'u ke mata a cikin lamuranta, kan jama'ar musulmi muyi hattara wai duk wadannan abubuwa da suke faruwa har yanzu kunne ta bai yi laushi ba har yanzu ita dai ba ta daukar kaddara duk abin da ya sa me ta wani ya yi mata, to mata muyi hattara gani ga wane dai ya ishi wane tsoron Allah. Burin Ummu bai wuce tsohuwar ta ta warke ba su sake sabon lale muje zuwa, ko zasu yi nasara akan Shema'u, Shema'u a yanzu ta mike kafa gidan mijinta 35 dan tana yin rayuwar yanci ba wai ta mallaka ba, ita da yaranta gwanin sha'awa ita kuwa Ummu ta kalla fa kanta saboda miji ya juya mata baya dan ya nun amata bacin ransa kan irin mugun halinta, a yau ta samu Nazir zaune bakin ga do a master room dinsa ta shiga ya daka mata tsawa meye haka za ki shigo min daki babu sallama, uhm wai ni Nazir ya yiwa tsawa ta fada cikin ranta sai ka ce da sallamar nake, lallai Shema'u ta yi min illah ta fada a zuciyarta a fili kuma ta yi murmushi ta ce darling mace da dakin mijinta dan zata shiga sai ta yi sallama, ka ji jahilci, Allah dai ya raba mu dashi, haushi ya kama shi ya ce dan dakin mijinki ne mijin naki ba Musulmi ba ne, sorry darling naga kamar ranka ya 6aci in dai sallama ce bari in koma in yi ta juya samgamgam da ita amma ita ba ta yarda ba wai nan kwarkwasa ta ke, ta yi sallama ta shigo ya amsa a dakile ta samu gefensa ta zauna ta soma magana darling nazo muyi magana akan abin da ya ke neman shiga tsakaninmu domin wallahi na gaji da abin da kake min kasan dai ita mutuwa guda daya ce, sababinta da yawa Lukman ko muyi atsari ko kar muyi lokacinsa ya yi ya daka mata tsawa na ji amsar da kika kasa bani ita har yanzu ita ce ina kuka je? Wa kika tambaya? Rubutu da magunguna na menene? Ta zumbura baki baka nan ban tambayi kowa ba rubutu da magani na tsarin jiki ne sanin kanka ne Shema'u ba ta kauna ta duk hanyar da zata ga bayana so ta ke to 36 sai in zauna ta kashe ni da raina, dole ne in nemi tsari da ita. Ido kawai ya zuba mata har ta gama surutunta ya ce ke dai wallahi shedaniya ce in Shema'u ba ta nemi hirji akanki ba ai ke bakin nema ba mutanen kirki su suke neman tsarin jiki ba wai irinku marasa imani ba, maganar ta yi mata ciwo saboda haka ficeva ta yi, daga dakin ta na kunkuni. Mahaifiyar Ummu hannu ya warke saj dai ya karkace sun koma gurin mai gyara ya ce sai dai a sake karya shi sannan ya koma daidai da ta tuna azabar da ta sha sai ta ce ta hakura a bar mata shi a haka memakon wannan abu da ya fa ru ya zamar musu hanyar shiriya ina sun sake fantsama. Rayuwa jin dadin da Shema'u da mijin ta suke yi ta yi kalau dan sun sabi sasan su yi haka kawai megidan ya tashi ya bi bai kaunar ya bude ido yaga uwar 'ya'yansa kai hali dai na da ya dawo domin ba ta sami tafiyarsa Dubai ku dawowar sa kai zancen wai yau girkin ta ne ya kare domin dai da ita da babu duk daya, kai abubuwa iri-iri sukan faru amma ita Shema'u ta kasa wani yunkuri saboda sauyin yazo mata ne a bazata daga ita har yara babu shi babu su kai wannan abu na Nazir na lafiya ne kuwa, kullum dare takan hana idanunta bacci wajen gayawa Allah matsalolinta takan yi kuka saboda tausayawa yaranta ganin irin maraicin da ya kama su ba wai saboda rashin uba ba dan sau da yawa suna san ganin abbansu 37 amma sai kika da sun shiga can 6angaran Ummu ta koro su yanzu Ummu ji ta ke da kanta dan abin da take sa Nazir yi abin ya shalle ke kan matarsa har ya kai kan iyayensa domin sai ya yi watanni ba su ganshi ba sai dai in su suzo gida su ritsą, shi, wannan abu ya damu Hajiyarsa ta rasa yadda zata yi shi kuwa Alhaji ido ya zuba masa dan yasan wai arina an saci zanin mahaukadya. Kun san an ce zuciya bata da kashi, to hakan ce ta faru da Shema'u ta kasa daurewa yau har falon Ummu ta higa don tana son ganin mijinta ta yi sallama ta siga babu kowa falon kasancewa ta riga tasan kan wan master room ta yi ta yi sallama ta shiga ya na une ya yi zukudin kamar mai tunani suna hada ido Shema'u ya ci na kyamis ta kai ci ya kama Shema'u boda yanda taga yada da kyau wato shi ba shi da danwa kenan, ya juyo ya kalle ta lafiya kuwa ta mayar nsa da amsa ito ina son magana da kai jeki zan zo sia lokacin ta san cewa Ummu ta shigo Ummu ta nummata hanya zo ki fice ni bana so kina shigo min wajetomin nasan duk wani abu da zai same ni ko ya samiyyana ke ce saboda haka karki kara shigowa wajena Sema'u ta shige ba tare da tayi mata magana ba abin y kuma ba wa Ummu haushi don taso ta tanka mata amma ba ta kula ta ba da sauri ta shaki wuyan Shema'utana cewa duk san da ki ka Kara shigo min sai kinga abin da zan miki Shema'u ta juyo ta kalli Nazir ta ceanin matarka ko sai a lokacin ya mike tsaye ya ce Ummu meye haka sake ta ta sake ta tana cewa daga yau sai yau in dai ta karа shigo min zan karya kafarta ne, Shema'u ta yi murmushi ta ce kamar yadda hannu tsohuwa ya karye ta kuwa zabura ta kawo mata damka ita kuma ta zille ta yi wajanta ita kuwa sai kumfar baki ta ke ta na cewa ki tsaya mana kiga yadda zamu yi da ke dan ubanki, abin haushi Nazir sai wani bata baki ya ke dan ba ya son 6acin ranta musamman da ranta ya baci gwara na kowa ya bаcі. Gaba daya yau daga Ummu har Shema'u suna family house ne domin halartar sunan dan da Babangida ya haifa, ganin Nazir ne sunan sa na ainihi Yusif shi ne su ke kiransa da Babangida, Shema'u ta yi mamaki yadda dangin Hajiya suka sakar mata fuska hatta Hajiya kaffa-kaffa ta ke yi da ita. Gaba daya matan 'ya'yan gidan sun hadu suna cin abinci suna ta hirar fahimtar juna saboda su babu wani faccalanci a tsakaninsu, saboda Usaini mijinsu a tsaye ya ke duk wacce ta kawo abin d aya ga zai riguza musu zumunci 'yaya yanzu zai yi maganinki saboda haka da fahimtar juna a tsakaninsu, Hajiyar su Nazir ta leko ta ce idan kun gama cin abinci kizo ki same ni 6angaran Alhaji ina son magana da ke, Ummu ta yi tsagal ta ce to Hajiya ta ce ba da ke nake ba da Shema'u na ke Shema ta ce, to yayin da sauran su ka fashe da dariya su ka shiga zolayar Ummu. 39 Bayan sun kammala har ta wanke hannu ta nufi in da ake kiranta falon babu kowa in ka dauke Hajiya da ta ke zaune ta ke jiran karasowar ta, ta yi sallama ta shiga ta sami Kasan kafet ta zauna sannan ta ce Hajiya gani. Hajiya ta bi ta da kallo na tsaf sannan ta ce dama ba wani/abu ya sa na kira ki ba saboda ganin yadda kika sayya bai kamata in yi shiru ba a matsayina da mahaifiyar mijinki, Shema'u kowa ya ganki zai san kin sauya domin kin rame na kuma san cewa abokiyar zamanki te shiga hakkinki, Shema'u ki gafarce ni sai yanzu na e nadama da da na sanin hada auren Ummu da Nazir, domin ina ta kaicin ace dan uwanka na uwa daya uba daya shi ya ke neman juyar maka da hankalin dani a tunanina Hajiya Umma ko babu raina zata rike minabin da na haifa, ashe abin ba haka ya ke ba, ina so ki fito fili ki fada min me ya ke faruwa tsakaninku da mijinki da abokiyar zaman ki? Shema'u ta yi shiru ta na tunani can ta ce Hajiya babu komai kin san yanayin shayar da tagwaye kadai zai iya sani rama, tunda ba sabawa na yi ba. Hajiya ta ce na ji wannan abin da ya sa kika ga na tambaye ki shi ne, ko kin san daga ni har Alhaji mun kai wata uku ba mu sa Nazir a idanuwanmu ba, wani abin takaici ba ya barin wayarsa a bude, ko da yaushe a rufe take abin da ya sani cikin kokonto shi ne sau biyu ina aiken Surayya gidan Hajiya Umma sai ta ce taga yayanta Nazir a can, hawaye su ka zubo wa Hajiya, kin ga ya tabbata 40 ita ta janye min da kenan, ni mahaifiyarsa kenan ina ga ke matarsa nasan kina kunsar bakin cikin da ya fi nawa tun da dai mahaifinki saboda aminci irin na da ba zai saurari wannan ba, Shema'u idan ba mu dauki mataki ba mun ci amanar amincin da ya ke tsakanin Alhaji da mahaifinki, tamkar yanda na ke ji da Nazir a zuciyata haka nake sonki ki fito fili ki fada min abin da ya ke damunki, Hajiya ni abin da nake so a gare ki shi ne addu'a ki ringa yi wa Nazir addu'a sai kiga duk wani kulli nasu Allah ya rusa shi amma ni yanzu tsakanina da shi babu komai sai dan abin da ba a rasa ba, su ka yi sallama su ka rabu. A gaskiya yanzu abin na Nazir ya shige hankali, domin ya watsar da Shema'u tamkar Ummu ce kawai matarsa, ba shi da aikin da ya fi nata bai isa ya gabatar da abu da kansa ba sai abin da mahaifiyarta ta ce sun tare a jikinsa dan yanda ya ke musu facaka kan baka ce ya na da uwa da uba ba tuni Alhaji ya fita harkarsa tun Hajiya na yi masa nacin bai kamata ya ce ya cire hannunsa akansa ba har itama tazo ta ce ta fita harkarsa har da ta iyalinsa, gaba daya Nazir ya zama tamkarm waina a tanda sai yadda aka juya shi, Ummu kam an yi kudi da Nazir yadda ransu ke so sai dai ta in da aka samu kudin ta nan su ke tafiya domin dai Bokaye da 'yanbori da Malamai 'yantsibbu su suke cin kudinta, ashe gaba daya maganar da Hajiya da Shema'u su ka yi duk a kunnan Ummu su ka yi ta dan sai da tazo ta labe ta ji duk abin da su ke fada ta 41 kwashe ta fada wa uwarta ita kuma ta ce zata yi maganinsu. Shema'u ta shiga damuwa fiye da da saboda yadda Nazir ya banzatar da su a yau daga ita har yaranta a gidansu za su yau, ta shirya su su ka nufi can, saboda yau ake sa ranar bikin Yayanta Kabir. Sun je gidan da wuri saboda sunan yan zuwan farko ita da mahaifiyarta sun kule da a dakin suna ta hira ta bazawa mahaifiyarta irin halin da ta ke'ciki ta ce kiyi hakuri wata rana sai labari ina tausayawa rayuwar Ummu da mahaifiyarta saboda raba da da mahaifi sai Allah, aka raba mace da miji kinsan mahaifinki kiyi ta hakuri watarana sai labari, cikin kuka ta ce to yanzu Nana duk fa wasu bukatuna da kaina nake yi, ni kuma ba kudi ba ba aiki ba ya zan iya daukar nauyin kaina da na yarana, musulunci fa bai bar komai ba komai sai da ya bayyana shi yanzu Nana rayuwa zata yiwu a haka, Nana ta ce baya baki abinci ta ce abinci kam a kwai a store duk wata zai zuba hatta kaji da nama kwai komai a kwai shi amma rabon da kiga ficikarsa tazo hannuna zamu kai watanni biyar dai ma Allah ya sa ina da 'yan kudadena a banki kuma kinsan wancan watan na dauki kudin hayar gidana, sai kiyi wa Allah godiya tunda ya rufa miki asiri, ni kam Nana ina so in koma karatuna in kuma ci gaba da koyarwata tunda Annabi ne ya ce mu nemi ilimi ko da kuw aa birnin sin ne, ni dai ina son in koma makaranta, sun jima suna tattaunawa mahaifiyarta na bata shawara mai 42 kyau sai da mutane su ka soma zuwa su ka hakura da hirar. Kusan sha biyu zata yi na rana, Shema'u ta fito daga bangaranta dan ta fadawa mai wanki cewar ya yi sauri ta na son zata aike shi sai ta hangi Ummu ta rako Nazir mota ko ina zai fita? Oho! Dama ta na son magana dashi saboda kudin makarantar Nur jiya sun ba ta takardar dakatarwa in dai ba a biya ba ta dan tsaya ta na san Ummu ta gama abin da ta ke yi amma taga ba ta da niyya sai ta karasa, ta dan risina ta gaishe shi ya kalle ta fuskarsa dai babu yabo babu fallasa ya ce Ummu Nur ya aka yi ne, ta ce AbuNur wajan ka nazo ya ce ina jin ki ta ce kudin makarantar Nur ga shi jiya har an dakatar da ita oh ya dafe kai ya ce na sha'afa bari in baki sai kije ki biya mata, na ce to ya zura hannu a aljihu ya laluba bai dauko komai ba ya bude jakar da ke gefensa ya zaro rafar 'yan dubu dai dai ya bani ya ce gashi ki biya ragowar ayi cefane wani dadi na ji har ina ganin addu'a ta ce ta karbu na yi masa godiya mai tarin yawa, a lokacin da ta ke yi masa godiya kuwa ita Ummu ta hade fuska yayin da tausayin Shema'u ya kama Nazir har ya ke ganin wautarsa na banzatar da matarsa da ya yi ya kuma kudiri aniyar kawo gyara. Shema'u ta na zaune a falo ta gama kirga kudi dubu dari da hamsin, washe gari taje ta biya kudin Nur na makaranta ta shiga super market ta dan yi musu sayayya ita da yara ba ta koma gida ba sai da 43 taje banki ta zuba kudin ragowar da zata yi amfani da su ta bar su a jakarta sannan tayo gida. Me zai faru? Kofar wajanta ta gani an tuttula rubutu ga garin magunguna nan bakinta dauke da addu'a ta shige wajanta falon duk ta gani a hargitse wannan ya tabbatar mata Ummu ta shigo ta yi mata bincike, ta shiga gyara dakin ta ta tsinci layu sun kai biyar kafin ta gama gyarawa ta kyasta musu wuta ta kone su duk da cewar Nazir ba ya shigowa wajen ta to amma ya na kula da yara in kuma zai tafi zai basu kudi na yi mamakin wannan sauyi ko da ya ke addu'a maganin komai ce. Kamar yadda na saba in ina son ganin maigidan zan tsayar da idona ne farfajiyar gida in zai fita in yi magana da shi muna tsaye ina gaishe shi Ummu ta karaso in da kuka san wata taba6biya ta taka ni ta wuce na ce Ummu ya za ki taka ni ki wuce sai cewa ta yi an taka in kina da abin yi ki yi na ce ba ni da shi amma na barki da Allah, ji na yi ta falla min mari kafin in dawo daga gigin marin nima na rama tuni ta kama ni da kokawa tana zagina zagi na cin mutunci, Nazir ya na yi mana tsawa tare da cewa shi-fa ya gaji na ce amma dai kaga abin da ta yi min abin mamaki sai ga Nazir ya goyi da bayan Ummu har da shi a ci min mutunci zuciyata ta yi baki na kasa hakuri na ce na gaji da irin wulakancin da kake min a gabanka tazo ta yi min wulakanci ga zagi da wulakanci to ni ba zan varda ba dole ne ka bi min hakkina dan na zagi tsohon 44 banza mai dankaran kwadayi shi ne za ki damu na kada baki na ce me kanannadeddan hannu ita ki ka zaga nasan dama irin wannan addu'ar ya dace da ita domin irin tarbiyar da ta ke miki kenan babu kunya Nazir ya rufe ido wai tunda na zagi uwar Ummu zan zagi tasa nan fa ya shiga ci min mutunci itama tana yi min na juya zan bar wajan ta figo ni nan fa kokawa ta dawo sabuwa, ni dama nasan ta fi ni karfi amma dai Allah ya bani karfin zuciya da kyar ya raba mu ta fada in fada ya ce kar wacce ta kara magana a cikinmu, ni tuni naja bakina na yi shiru dan in ji hukuncin da zai yanke mana, sai cewa ya yi Shema'u na gaji da halin tsiya irin naki duk abin da ya ke faruwa ke kike janyowa saboda haka yau zan yada kwallon mangwaro in huta da kuda, Ummu sai wani karkada kafa take yi tana cewa in b an da jarraba ma mutum an nuna ba ayi da shi ai sai ya tafi gidan tsohonsa ko yau dai dubu ta cika sai a tattara a koma in da aka fito, darling fada mata ta ji Shema'u ki tattara ina ki ina ki ki bar min gida na sake ki saki daya bani da bukatar sake ganinki a gidana, abin ya zo wa Shema'u a bazata saboda haka da farko rudewa ta yi amma da ta soma jan innalillahi sai ta sami nutsuwa nan take ta ce ni ka saka Nazir? Ya ce kwarai to na ji amma bari in fada maka, zama dam in ji mara zuciya saboda ni yanzu ka zama ubana yara uku ai mun zama daya zan yi zaman 'ya'yana saboda haka ka iya zaga rabon 'ya'yana ka bani in zauna in yi musu tarbiya ta gari amma ni ba 45 zan haifi da a cikina in ba wa Ummtu ta yi rainonsa ba saboda itama ba ta da tarbiyar bare ta yi wa wani ni yanzu ko miji na samu ai kaine waliyina kai zaka daura min aure saboda haka zugu ne ba ta kare ba Ummu muna tare ina so ki rike wannan yanzu ne za muyi zama yanzu za ki san shema'u da ba ni kika sani ba saboda da igiyar aure akaina yanzu kuwa babu nauyin kowa a kaina, ta juya.ta tafi ta bar su a bushe a wajan dan ba haka Ummu ta zata ba. Falonta ta nufa ta na zuwa ciki ta shige gado ta fada ta na kuka wai ni Nazir zai saki ta shiga hada kayan ta da na yara ta na fadin ai gidan ka ba aljanna ba ce ba zan zauna ba ta gama hada ko ma maganar yayanta Kabir ta dawo mata kamar yanzu ya ke fada mata, nasha jin mahaifinmu na fadin bai haifi 'yar da zata zo masa yaji gida ta zauna ba, shi ko auranta ne ya mutu sai ya tabbatar ta gama idda gidan mijinta ji ta yi jiri na dibarta wai wane irin hali ne da mahaifinsu ta yi shiru ta na tunanin yanzu in naje ma dawo dani za ayi in na zauna burin Ummu kawai ya ishe ni waya ta dauka ta yi wa yayanta Kabir bayan sun gaisa ta ce Yaya ina son ganinka yanzu dan Allah kazo ya ce ga shi ba na gari ina Kaduna ina duba ginina, da ya ke a can ya ke aiki kuma in an yi bikinsa can za su zauna, Yaya yaushc za ka dawo? Zuwa jibi zan dawo, lafiya in kuna da damuwa ki fada min, ina son magana da kai amma sai ka dawo din, yinin ranar 46 nan ta yi zuru-zuru saboda in da ta tsinci kanta cikin damuwa. Damuwar da tasa cikin

Chapter 3 of 5