Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
6 / 6
zan żarce" Cikin shegantaka Tanimu ya ce, "Ai tuban tafi-da-gidanka zamu dinga yi, muna aikinmu muna tuba, Allah sa su ma masu zuwa wajen namu su dinga zuwa tafe da tubansu" Cikin sati daya sana'ar tasu ta shahara, Tanimu na da ido a sanin mata da 'yan siyasa kasancewarsa dan bangar siyasar da ya tuba ya fada bokanci, don haka shi ne mai kawo musu mutane, mata da Alhazai, 'yan siyasa da 'yan kasuwa, su ma a junansu duk wanda ya zo ya sha basaja, aka sace imaninsa in ya tafi sai ya fada wa amininsa wani shahararren boka ya bayyana, shi ma in yazo sai ya fada wa nasa Aminin ta haka tafiyarsu ta fara nisa. Tun bayan kwana hudu da auren Salma da Adamu aka kamala duk gyaran da za'a yi wa 138 Maimuna Idris Sahi Beli NA SHIGA ALJANNA...2 gida, aka yi jere aka kuma zuba kayan kanti aka kai wa Adamu Salma kwana goma sha daya da auren. Ranar da za'a kai ta da safen ne Alh. ya shammace shi ya biyo shi gida bayan sallar asuba, kasancewar kullum daga ya dawo sallar asuba yake shiryawa ya fice, ba za'a kara ganinsa a gidan ba sai bayan sallar isha, wataran ma har karfe goma yana kai wa. Babu ko sallama Alh. ya bankada masa labule ya bi bayansa. Suka yi cirko-cirko a tsakiyar dakin suna kallon juna, fuskar Adamu da fishi, fuskar Alh. na nuna halin ko in kula. Alh. ya sanya hannu a aljihu ya ciro mukullai ya mika wa Adamu, "Don Allah ka taimaka idan ka dawo ka zarce gidanka, yau za a kai maka matarka" Adamu ya mika hannu saroro ya amshi makullan, ba tare da ya tanka ba, ya dinga motsa baki kamar yanà so ya gode wata zuciyar na kwabarsa cewa bai kamata a cuce ka kuma ka yi wa macucin godiya ba, da haka ya biyewa zuciyar ya ki godewa, kuma ya ki 139 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 tankawa har Alh. ya gaji da jiran cewarsa ya kada kai ya juya ya fita cikin kada kai da murmushin mamaki. Adamu ma ya dauke ido daga kallon wucewarsa zuwa kallon mukullan hannunsa, wasu irin abubuwa na zagaya kansa a guje, suna raya masa cewa, ba wai rayuwarsa се kawai take shirin canjawa ba, shi kansa Adamu ake son a canja. Wai shi ne da ya sha mafarkan bacci da na ido biyu a auren mace daya kacal wato Husńa, shi ne kuma yau da auren wata macen wai ita Salma? Abin sa kuka amma ba hawaye. Bai bari wata damuwa ta ci karfinsa ba ya shirya ya fice harkokinsa. Bai sanar wa Salmanu komai game da tarewarsa a gidansa: da sabuwar amarya ba, sai da ya tashi tafiya karfe tara da rabi na dare, "Au! Kai yau fa zaka raka ni siyen baki" Ya fada wa Salmanu cikin yake da kokarin hadiye damuwa. Salmanu ma ya dabe shi cikin mamakin da yake son shanyewa, 140 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 "Wai da gaske kake mantawa ka yi ko kuma tsabar basarwa се?" Adamu ya hada da dariyar yake, "Oho! Ni ma ban san takamaimai a ciki ba" Salmanu ya kame hannu ya rungume a kirji yana bin sa da kallo, "To Allah kiyaye hanya, Allah ba da zuriya mai kyau" Adamu ya yi saurin dubarsa saroro, "Au wai ba zaka raka ni ba, haka zan tafi zikau ni kadai?" Salmanu yayi dariyar karfin hali, "Kai kadai zaka tafi mana, ka manta kai kadai Salma ke son gani, ko ka manta sharuddan da ta gindaya maka cewa kar a sake na zo mata gida?" Adamu ya dinga gyada kai alamar tunawa, وو" Haka ne na tuna' Salmanu ya ji takaicin goyon bayan da Salma ta samo a wajen Adamu, dubi dai yayi masa gatse amma bai damu ba ya mayar gaske saboda umarnin Salma ne. 141 Maimuna Idris Sani Beli 1 NA SHIGA ALJANNA...2 Amma duk da haka Salmanu bai nuna a fuska ba, sai ya cigaba da dariya yana cewa, "Idan gidan Salma ya zama nasu su biyu kila a gan ni, in dai zan iya zuwa wajen Husna ba wajenta ba" Nan da nan fuskar Adamu ta rakito walwala, amma dai bai tanka ba.. Salmanu bai damu ba ya cigaba da Magana, "Amma idan ba ka sami damar auren Husna ba, to har mu kare rayuwarmu a idon danginka da Salma zamu cigaba da nuna dama mun rabu" Adamu ya banka masa harara tamkar idonsa zai fado sannan yayi gaba yana mita, "Ka kwana biyu ba ka zage nib a dama, yau in ka yi min muguwar addu'a bà laifi, to in Allah ya ba ni Husna ka hana mana Ba tare da sallama ba ya fice daga dakin. Salmanu ya bishi da kallo cikin tausayi tare da kara kullatar Salma. "Allah ya tsine miki Salma" Ya fada a fili kuma har cikin zuciyarsa so yake Allah ya amshi addu'arsa. 142 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 Kamar kullum duk wani abu da ya danganci Salma zuciyarsa ba ta bashi muhawara bare ya tantance ya zaba, kai tsaye daga can saman zuciyar tasa wani ke bashi zabi ya aiwatar bisa dole. Yau ma ya so ya ji bijrewa da nuna wa Salma iyakarta, amma ya ji wancan karfin na son matsa masa murnar zama angon da yake tafiya ga amaryarsa, hakan kuwa ya je mata har da siyayyar kaji da kayan jika makoshi. Ya dinga nuna mata doki da zumudi tamkar dama ita kadai ce sauran burinsa a duniya ya kuma samu. "Ban san kana sona haka ba Adamu" Da kalmomin da ta dinga zolayarsa da su kenan, shi kuma yana amsawa tsakaninsa da Allah, "Yanzu kin sani Salma, ina son ki fiye da son kowa a duniya" In ya fadi haka Salma na jin wani munafikin hawaye na kurdo mata ta samu ta goge abinta, abinda take so kenan wato Adamu, ta kuma samu, in ba shi kadai ne burinta a duniya ba tana jin dai ya fi rabi. 143 Maimuna Idris Sani Beli. 1 NA SHIGA ALJANNA...2 Cikin sati biyu dukkansu rayuwarsu ta canja, Salma ta mamaye zuciyar Adamu tsab, duk wata mace a waje kallon Bahuwa yake mata, bata da kyau ko bata da kwalliya ko ma gaba daya sunan mata kawai take amsawa. Salmansa ce kadai mace, ita ce kuma kawai idan an so ba a fadi ba. Duk abinda Salma ke so shi yake so, wanda kuwa ta nuna bata so nan take yake jin tsanarsa, saboda haka ya zama tamkar da gaske sabon Adamu aka sake fil! Ba wancan mai tsanar salma ba kuma ba wancan mai son Husna a kirji ba. Salmanu kansa ya fahimci haka, amma dai ya shanye ba ya tanka masa maganar Salma, ko shi ya kawo masa ma sai ya tankwabe shi da cewa, "Yanzu Salma iyalinka ce, bai kamata mu dinga hirarta ba" Da wannan hujjar suka dauke hirar Salma a tsakaninsu, iyakaci in sun hadu su yi abinda ya hada su su watse. Sai dai manta Husna da Adamu yayi ba karamin daga wa Salmanu hankali yake ba, 144 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA..2 musamman in ya tuna labarin da Adamu ya ba shi na yadda suka yi rabuwar karsheda Husnan, da alwashin day a ci mata na aurenta nan da wata biyu tun a ranar. ps nsWannan ya sa ya cigaba da sake-saken ta inda zai bullowa wannan bahagon lamarin, har ya fara jin cewa a wanna gabarazaie yanke danye hukuncin da: Zaijnunaa wai Salma iyawarsa. B siSanaar bokanci taincigaba hdasakawo imanyan kudi, don haka Adamunbaii yingigin barinta ya zauna a shago ba, kawai sai yà neii yaro ya dora shi jira, shi kuma ya cigaba da gashi prose sangu a Citapa ( Kows is ase ваAbinda ma ya takaice shi shi ne, Salmanu ba ya sakar masa kudi yayi yadda yake so ko $dan farantawa Salma raiinemset edob sist ei BinZasuyraba kudin rumi-rumi su uku bayan Sun ware na sallamar yaran da ke lyi musu hidima da kuma na siyayyar kayan aiki, amma kawai sai Salmanu ya daka wa na Adamu ils 145 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 wawaso, ya sunna masa abinda bai taka kara ya karya ba, ya ce wai zubin adashi suke, kuma wai kantinsa ya isa ciyar da Salma dai ba wata ba. Adamu ba ya son wannan dabi'ar, amma dayake ba ya zargin Salmanu da cutar kudi sai yake shanyewa, yana da tabbacin ko ba dade ko ba jima sai ya fito masa da kudinsa. Sati daya, biyu, uku, hudu, Husna bata ga Adamu ba, tun tana basarwa musamman daidai lokacin da ta ji labarin ya tare da amaryarsa a unguwar Dorayi, ta ci kuka ta ci ciwon ranta ta maze ta koma ta cigaba da zaman jiran ya waiwaye ta tunda wata biyu ya dibar wa kansa na aurenta, har aka kusa wata daya da rabi ta fara debe tsammani, juriyarta kuma ta sare. Ta cigaba da damuwa ta cigaba da kuka kuma ta cigaba da ramewa tare da lissafin ta inda zata bullowa wannan mugun ciwo day a sarke ta. 146 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 Rannan dai da ta ji zuciyarta na neman bugawa kawai sai ta wanki kafa ta tafi gidan Kawarta Amina domin neman mafita. Ta sami Amina da makociyarta Jamila suna hira cikin farin ciki. Amina na ganin Husna ta hau salati da sallallami, "Wallahi yanzu nake zancenki Husna, ai kawi ki zo mu fasa mu ma mu shallo Adamu" Husna ta zauna kan kujera jagwaf tana bin su da kallon rashin fahimta, Amina ta shiga yi mata bayani tana nuna Jamila, "Kin tuna ranar da jamila ke tatsuniyar son mai gidanta ya sai mata mota yana cewa wai bata da hankali?" Husna na dariyar yake ta ce, "Na tuna, yanzu zai siya ne don ta yi hankalin?" Suka kwashe da dariya su duka ukun. Jamila ta mika wa Amina hannu suka tafa sannan ta dubi Husna tana kada mata mukullin mota, 147 Maimuna Idris Sani Beli 1 NA SHIGA ALJANNA...2 "Tun yaushe na yi hankali, Surajo ya ji wuya jiyan nan sai ga sabuwar mota ya samfa min" Husna ta zamo daga kujera tana zaro ido cikin mamaki, "Da gaske? To duka kika fara ne ya gane in bai sai motar ba ba zaki warke ki bar dukan ba?" Suka sake tuntsirewa da dariya. Jamila ta ce, "Wanda ya fi shi karfi na sa yayi masa mahangurbа" Har yanzu Husna na cikin dokin jin labari, ta ce, "Don Allah ku fada min ku bar wana ni" Amina ta hau yi mata bayani. "Wallahi wani sabon boka aka samu mai aiki kamar yanka wuka, saboda tsabar son mota na Jamila sai da ta dangane da wajensa, ba a yi sati biyu ba kuwa kin ga har ta yi motar" Husna ta shiga gyada kai cikin mamaki da sha'awa, 148 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 "Kai! Ku dama akwai malaman Allah da gaske a duniyar nan?" Jamila ta kada kai, "Wallahi ni ma abinda na yi ta cewa kenan Husna, kawai kasada na yi na je, amma saj ka yi ta zuwa wajen wasu asirin sai ki ga kamar an shuka dusa" "Wallahi tallahi" In ji Amina, Sannan ta dubi Husna ta zarce da cewa, "Wai gobe zata je yi wa bokan godiya, shi ne na ce me zai hana mu bi ta muma mu kai tamu bukatar? Ke ki kai Adamu, ni kuma zan kai Kamąlu a kama min shi a hannu, wannan shegen kallon bal din nasa pa dare a hana shi, don ni in akwai abinda na tsana a duniya ba zai wuce kallon bal din ba" Husna ta ji wani dum! Kamar abin bai kai zafin haka ba, duk da ta san son Adamu ba sanyi ne da shi a zuciyarta ha. "Kar ki ji wani dar Husna, duniya sai da kundumbala, ki daure ki basar ki nemi cikar burinki, Salman banza da zata hana ki samin abinda kike so?" 149 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA..2 Amina ta karfafa mata gwiwa da wannan zantukan Sai kawai ta mika wuya. "A wane kauyen bokan yake?" Ta tambaya. Jamila ce ta amsa mata "Nan nan -Zawaciki yake, hanyar Panshekaга" A sanyaye Husna ta се, "To Allah ya kai mu, zan je. Karfe nawa zamu tafi?" Amina ta dubi Jamila. "A motarki fa za mu, saboda haka ki zaba mana lokaci" Kai tsaye Jamila ta amsa, "Mu je da la'asar" دو" Allah ya kai mu" Husna ta amsa a sanyaye. Da la'asariyyar ranar yau su Adamu na sanya ran zuwan wani gagarumin dan siyasa mai son tsayawa takarar dan majalisar taraiya. 150 Maimuna Idris Sani.Beli NA SHIGA ALJANNA...2 "Ku kula da kyau fa! Yau muna bukatar takatsantsan don kar mu yi abinda kwabarmu zata yi ruwa, kudi muke so.. kun gane?" In ji Oga Salmanu lokacin da suka sami wayar cewa yammar yau ko ta gobe Honorabul zai zo. "Wane sirrin damfarar zamu gwada masa?" Adamu ya tambaya. Salmanu ya dan yi shiru alamar tunani. Karaf Tanimu ya ce, "A yi masa na alkalamin nan, na ga yana dan rudar da kwanya" Salmanu ya bigi kafadar Tanimu, "Yauwa! Ka kawe shawara mai kyau, a nemo, alkaluma a fente" Adamu ya tashi da sauri ya shige cikin zuwa taskar ajiyarsu ya bar Salmar da Tanimu, Tanimun na yi wa Boka Salmänu bayanin tarihin Honorabul, nasarorinsa, faduwarsa da kuma abokan adawarsa. Adamu ya jima sannan ya fito, "Akwai alkaluma, amma babu kusoshi". 151 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 Salmanu da Tanimu suka dafe kai saboda jimami, kasancewar ba a samun kusar kusa da su har sai sun hau Mashin sun je Sabon titi. Adamu bai shiga cikin jamamin ba, kawai sai ya sa kai ya fice yana cewa, "Bari na samo ta yanzun nan na dawo" Salmanu na kiransa bai saurare shi ba. Wannan dalilin ya hana Adamu da Husna haduwa a wajen da dukkansu ba zasu so ganin juna ba. Tanimu ya shige ciki domin zama kujerar Adamu ko da zatą kama ayi muryar aljanu. Salmanu. kuma ya zauna a kujerarsa ta babban Boka. Kasancewar sun saka dokar ba a shiga mutum biyu, Jamila ce ta fara shiga, ta yi godiyarta ta kuma bayar da dubu goma na goro ta fito. Husna ce ta biyu. Ta shiga da alamun tsoro da rashin sabo, kafarta sai rawa take jiri kuma na kwasarta, dole ta zube a kasa ba tare da ta karasa kan buzun da aka tanadawa masu ziyara ba. 152 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 Yadda take jin dukan zuciya Salmanu ya ji fiye da haka na ganin Husna a gabansa a matsayinsa na boka ita kuma a matsayinta na mai bukata a wajensa. To wacce irin bukata? Abinda ya fi damunsa da sa shi faduwar gaba kenan sai kuma fargabar kar Adamu ya dawo ya tarar da ita. Da sauri ya fara shirya ta inda zai Burma ta. Ko Salmanu bai ci wani Make up ba da wahala Husna ta gane shi a yadda ta yi kasa da kai tana jin kamar kasa ta dare ta shige. Ba sai wani ya bude baki ya fada mata ba, ita da kanta tana jin ta yi abin kunya, wato zuwa gurin boka a kan saurayi. Fahimtar hakan da Salmanu yayi ya bashi tasa nutsuwar ta shirya yadda zai shammatota. "Kin zo akan maganar saurayinki Adamu ne?" Da sauri ta dago kai ta dube shi saboda mamaki, amma kamar an cije ta, da sauri ta yi kasa da kai cike da jin nadamar kallonsa, to mutumin da ba ka kalle shi ba ma shi ya kallo abinda ke faruwa a duniyarka, ina ga ka kalle 153 Maimuna Idris Sani Beli 行 NA SHIGA ALJANNA...2 shi? Ta dai cigaba da gyada masa kai alamar 'Eh" mata, Ya dan shaki iska sannan a kasaice ya се "Ba ya ce ki jira shi nan da wata biyu ba? Ai yana can yana miki tanadi Hajiya” Husna ta ji wani yakini da karfin gwiwa ya dake ta, cikin rawar baki ta amsa, "Ai wata biyun aure yake nufi, dauke kafarsa gare ni na nuna rashin damuwarsa da ni Malam, ni kuma ji nake ba zan iya rayuwar da babu shi ba, don Allah ka taimake ni..." Ta wuce da goge kwalla. Ta yi shiru, Salmanu yayi shiru saboda rashin abin fada. Ita ta sake Magana cikin hawaye, "Ina zargin ma ni asiri ya yi min, ban san ana son mutum irin haka ba, Malam da tuni na cire shi daga sabga ta wallahi" Tausayinta ya kara damun Salmanu, ya yarda Adamu ya cuci Husna, shi ya dinga zazzafar addu'a kan soyayyarta da samunta, gashi Allah ya amsa masa shi kuma ya juya mata baya ya bar ta da wahala. 154 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 Dole dai ya kakaro abinda zai karfafa mata gwiwa lokacin da ya janyo kasko ya fara yafa turare. "Ki kwantar da hankalinki ba zai wuce watanni biyun da ya dibar miki ba, zai zo ya baki mamaki, ni na yi miki alkawarin sai kin juya Adamu a tafin hannunki, sai kuma ya ninka miki son da kike masa, amma ba wani asiri da yayi miki. Husna ta sake jin wata nutsuwa a zuciyarta, ta fara godiya ba kakkautawa. Tamkar Salmanu ya saki fitsari a wajen lokacin day a ji tsayuwar mashin din Tanimu da Adamu ya fita da shi a harabar gidan gonar, ya tabbatar kuma hanyar da zai biyo ko inda zai labe dole wadda `zai iya ganin Husna ce. Da sauri ya mike daga. zaune ya shige cikin dakin yana cewa, "Ina zuwa, bari na kawo miki wani turare da zaki zuba a cikin lallen kunshi" Bai jira amsarta ba ya shige. Ya yayimo Tanimu da ke lafe a duhu da tiyo a baki yana jiran alamar da zai saki muryar aljanu, 155 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 "Maza je ka ka tare min Adamu kar ya shigo gidan nan, bi ta baya?" Tanimu ya tsaya yana radar neman ba'asi amma sai Salmanu ya tunkuda shi sai da ya kusa kifawa, dole yana tashi bai nemi wani ba'asin ba ya fice ta kofar bayan, amma tuni Adamu ya kafe mashin cikin zafin nama ya tunkari masaukin bakin da suke jiran shiga wajen boka Salmanu. Amina da Jamila na zaune suna dako, kuma yana wuce su Husna zai tarar gaban Boka Salmanu. A nan zan dakata sai mun hadu a kashi na uku. Taku Maimuna Beli. Ga kadan daga littafina mai zuwa nan ba da jimawa ba. 156 Maimuna Idris Sani Beli. NA SHIGA ALJANNA...2 RIGAR SILIKI... "Gwajin HIV?" Mujahid ya jaddada cikin kallon likita da haushi da kuma mamaki. Likita ya kada kai yana tsura masa ido cikin tabbatarwa da nuna babu fa canji. 99 "Haka na ce Mujahid ya cakumi wuyansa kamar zai gwara kansa da bango, amma sai ya sake shi cikin huci ya shi hargagi, "Haka ka ce din addini ne, ko fadar Allah ce da ba'a gogewa? Likita ya shiga gyara wuyar rigarsa da Mujahid ya cukwikuya, fuskarsa na son nuna hakuri da shanye damuwa, ya dubi Mujahid da kyau ya ce, "Abinda ka yi bai yi maka kyau a zamowarka lauya ba, yanzu in na tafi neman hakki bisa wannan cakumar da ka yi min, me kake tsammanin zai biyo baya... a kan aikina kake cin zarafina?" Mujahid ya tare cikin hargagi, "Komai ma ya biyo bayan mana, ka tafi kotun duniya in ka so. Ban da kai dan iska ne, 157 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 matar auren zaka kawo wa maganar gwajin HIV? In zargin hakan ne me yasa ba zaka ce ni mijinta zaka gwada ba? In dai ba shirin tozarta min iyali dama ka yi ba" Likita ya dinga duban Mujahida cikin takaici, kawai sai ya watsa masa sakamakon gwajin HIV din da suka yi wa matarsa Binta. "Gashi nan, ai yanzu ma bata baci ba, in ka gama duba wannan kana iya zuwa Lab kai ma mu gwada ka" ****** Jikin Mujahid a salube ya shiga dakin da Binta ke kwance. Bai tarar da Salima ba sai Binta kawai zaune kan gado ta kwanta jikin filon da ta jingina da bango. Fuskarta nan nuna farfadowa daga cuta, idanunta sun yi zuru-zuru, sai dai fa ko kadan babu wani annuri a tare da ita wanda zai sa a zaci tana cikin tashin hankali ko kuma nadama, kallon iskar da ta saba wa Mujahid da shi ta karbe shi yau ma. Shi yau tasa fuskar babu walwalar da ya saba tarenta da ita duk irin yadda ta kai ga bori, 158 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 hasalima bata taba ganinshi cikin 6acin rai irin na yau ba tun saninta da shi, amma a hakan ta debe shi ta watsar. Ya ja kujerar gaban gadon ya zauna yana mika mata takardun da likita ya watsa masa cikin kallon fuskarta kai tsaye. A wulakance ta karbi takardar ba tare da ta duba ba ta yasar gefe, kuma cikin şhan kamshi ta dube shi da kyau ta ce, "Ni ya fara kawo wa na gani kafin ya baka" Sai ya sake dubanta cike da mamaki, ya се, "Kin kuma duba takardar kin ga rainin hankalin da take dauke da shi?" Ta sake watsar da kai gefe tana cona baki, "Na gani, ai ba rainin hankali ba ne, iyakar gaskiyar kenan" Yanzu duban mahaukaciya yake mata. Dan ta nuna masa da hankalinta ta juye ta dubi kwayar idonsa fes! Ta ce, "To wai kai meye na tashin hankali don an ce ina dauke da cutar kanjamau? Ko ka manta tuni ka ci alwashin ko yaya zan kasance kana 159. Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA.,.2 so? Ai baka zabi in na zo da kanjamau baka so ba, in kuma zaka zaba yanzu ma bata 6aci ba" Mujahid ya jima da hankalinsa tsakanin karya da gaskiya a tunani da hasashe, sai can ya mike cikin nuna yakini da kumaji ya ce, "Na tuna an yi hakan, ban zabi kanjamau ba, amma yanzu na zaba... nan gaba ma in zaki zo da abinda yafi kanjamau ke da su duk ina so... kar ki damu, ki ji sauki ki zo mu koma gida mu cigaba da jinya... in ma lahira kika tafi zan nade kafar wando na bi ki" Rigar Siliki...!!! Sadaukarwa ga Mujahid Muktar Misau. 160 Maimuna Idris Sani Be An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 6 of 6