Na
hadu da masifa tun dazu amma kana kwance
wai kana bacci?"
Salmanu ya cigaba da hadiye dariyar da ke
neman kashe shi, cikin hanzari ya karasa wajen
Adamu yana marairaice murya,
"Bacci ne mai nauyi ya dauke ni Adamu,
Barayi ne suka shigo?
"Uban barayi ne suka shigo, zo ka daga
ni
83 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
Taga-taga Salmanu ya daga Adamu ya ja
shi bango ya jinginar, har wannan lokacin idon
Adamu yana runtse yana ta faman nishi.
Salmanu ya zauna a gabansa yana dubansa
da fuskar tausayi, murya cike da jimami ya ce,
"Wai me ya faru, yaya na ga fuskarka a
kumbure? Kai duk jikinka ya yi suntum wani
gurin har da jinni, mun shiga aljanna Adamu
me ya same ka? Bude idonka mana"
Adamu ya soma neman barkewa da kuka
yana cewa,
"A'a fara duba min ya tafi?"
Salmanu ya ce,
"Ya tafi? Waye ya tafi"
Adamu yа сe,
"Aljanin da na kira, daga kai ka dube shi
gashi nan akanka da rafkeken kansa"
Salmanu ya shiga waige-waige kamar
gaske, sannan ya dawo da ganinsa ga Adamu,
"Ban ga komai ba Adamu, ko dai mafarki
kake?"
Adamu ya barke da kukan da yake son yi
tun dazu,
84 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
"Ni kadai nake ganinsa kenan, gashi nan
kuma ina ganin inuwarsa"
Salmanu ya ci laya,
"Wallahi ba komai Adamu, ka daure ka
bude idonka"
"To ka roke shi ya tafi"
Salmanu ya shiga hurwa,
"Bawan Allah kai kake ganina ba ni nake
ganinka ba, Adamu ya kira ka shi ma yana
neman alfarmar ka bace, in kudi ne ya fasa
nema ka tafi da abinka"
Ya katse maganarsa ya juyo ga Adamu ya
ce,
"Ko Adamu?"
Cikin rawar jiki Adamu ya kada kai ya ce,
"Eh wallahi, ya bar ni ma da bante"
"To ka ji ta bakinsa Bawan Allah"
In ji Salmanu yana gintse dariya. Can
kuma sai ya ce,
"Bude idonka Adamu, ina jin ya tafi, na
jiyo wani huci"
Adamu bai iya bude idon kai tsaye ba sai
da ya kankame Salmanu yana ta faman karatun
ayatul kursiyyu sannan ya bude idon yana
85 Malmuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
zazzarewa cikin bin dakin da kallo a tsorace,
sannan kamar zautacce ya hau sambatu yana
tambayar Salmanu, sy nitands2
"Yanzu ashe da gaské baka gan shi ba Salmanu?"
"Ban gan shi ba Adamu aon ак оТ
"Ta daidai nan ya faso Salmanulds2
Yana nuna wa Salmańu daidai gurin da ya
tsaya, sannan ya cigaba da sambatunsasanttаg
"Kamar saukar aradusnauji dirarsasYiff!
Dogo tokarere da shi ya kusa tarar da rufin
kwanon nan, kai ina jin ma kansa yana wajen
kwanon, ko da yake nayi arba da kansa sinke
da farin rawani...." "TumsbA О
9 Кa ce ka sha kalloA Dii TEws ahliD
Salmanu ya tare shi yana son fitar da
dariyarsaisILA neWad seniled t il вя оТ"
n Adamu ya cigaba yda numfarfashi yana
cigaba da sambatu, 00 BY IAE so
En Nasha kallo ko na sha wahala Salmanu?
Na ci bakar wuya na ci dukan aljan yau na sha
bulalarsa sai ka ce shi ne walakiri, mutůwa се
kawai ban yi ba Salmanu Kila ma na mutun ha
dawohobi BY ЕДИВИ
86 Malmuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
A wannan gabar Salmanu ya sami sararin
sakin ragamar dariyarsa iyakar karfinsa.
"To kuma jaka nawa ya baka? Na zaci ai
duk bulala daya a matsayin wasu makudan
miliyoyi take"
Adamu ya dauke wuta dif! Sai can ya nisa
ya dago sosai ya dubi Salmanu,
"Ai da kai muka je wajen Malam ko? Don
Allah ka ji sharadin aljanin nan zai dake ni a
wajensa?"
Salmanu ya kanne,
"Wallahi ban ji ba kam, amma ko baka yi
daidai ba ne?"
Adamu ya sake rafkewa,
"Wallahi iyakar iyawata na kiyaye
sharudan da ya ba ni, kuma in da na san da
duka ba zan taba karba ba"
Salmanu ya sake kannewa,
"Shiyasa ai nace kila kuskure ka yi baka
san ka yi ba"
A tunzure Adamu ya се,
"To tsakani da Allah ni dai ya zalunce ni,
Allah ya isa ban yafe ba, kuma na dauke masa.
87 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
Kafata wallahi ko karin bayani ba zan koma in
ラクラク
masa ba tunda abin nasa mugunta ne
"Amin"
Salmanu ya fada a gajarce, yayin da wani
farin ciki ke cika zuciyarsa.
Wasa-wasa sai da Adamu yayi sati yana
jinyar dukan da ya sha wajen aljanninsa ba tare
da ya leka gidansu ba, yana kwance Salmanu
na jinyarsa, yana yi masa famfon kin zuwa
gidansu ko sanar da su halin da yake ciki,
wayarsa na hannun Salmanun shi yake zuwa ya
ce Hajiya na gaishe shi wai kafarta ke ciwo
shiyasa bata zo duba shi ba kasancewar Alh.
yayi tafiya zuwa Enugu.
Ba wannan ne kadai aikin da yake da
wayar ba, yayi blocking din hanyar shigowar
ko wane kira, duk sanda ya bushi iska kuma ya
kan tafa maganganun cin mutunci da cin fuska
hadi da nuna kiyayya ya tura wa Salma a
zuwan shi ne Adamu.
88 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
Salmanu ya dauki wannan matakin ne
dalilin abubuwa uku, na farko jin haushin
yadda Alh. ya runtse ido ya ce ya raba shi da
Salmanu, shiyasa a tasa iyawar yayi niyyar
nuna musu tasu iyakar.
Sannan abu na biyu ya san tabbas idan
Adamu na gida sai an yi yadda aka yi ya ga
Salma, abinda kuma Salmanu yafi tsana kenan
yanzu a filin duniyarsa, Salma ta shiga jerin
mutanen da ya tsana, saboda haka yake iyakar
yin sa ya hana ta rayuwa da Adamu.
Sai dalili na karshe, ya sami wani
Alaramma ya sanar da shi matsalar Adamu ta
zargin da yake na an masa Sihiri, saboda haka
kullum yake bada rubutu ana kawo wa Adamu,
Salmanu na yi masa karyar ai maganin bibikon
aljanin da ya make shi ne.
Adamu bai taba shakkar abinda Salmanu
ke fada masa ba don Salmanu ya iya hila,
saboda haka hankalinsa kwance yayi zamansa
a gidan gonar nan, kuma gidan sana'ar
bokancinsu da cutarsa ta dakatarsu farawa.
A can gida hankalin Hajiyarsa ne kadai
yayi kololuwan tashi saboda rashin ganin
89 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
Adamu, amma Alh. ya rantse ya kuma wallahi
Adamu yana sane ya buya, kawai so yake ya
nuna musu iyakarsu, don haka babu inda zai je
nemansa.
Hajiya ta so ta musa, amma kasancewar
Alh. na iyakar kokarinsa akan Adamu, kuma
yawancin abinda ke hado su ma Adamun ne
bashi da gaskiya, sai kawai ta daure ta cije
domin kar ta kware wa Alh. baya, musamman
da yake yana ta kumfar bakin don shi Adamu
ya buya, sai da ya sanya shi karade dangi da
maganar aurensa da Salma sannan zai juya
baya ya zo masa da rainin wayo, ya bace kowa
in ya buga lambarsa ba zai same shi ba, sai shi
idan ya ga dama ya bude ya dinga aikawa da
Salma bakaken maganganu da'nuna kiyayya.
"Na rantse da Allah, sati daya na cika in
ma bai dawo ba sai na daura aurensa da Salma
sai dai idan ya ga dama y ace ni ba jininsa ba
ne mu raba hanya"
Wannan ne alwashin da Alh. ya dinga ci
cikin tsananta fishin da ke kara tashin hankalin
Hajiya mai son ta kare Adamu ko tayi umarnin
a yi cigiyarsa.
90 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
Amma dai dole haka ta hadiye ta cigaba
da kawaici, shi kuma Alh. ya cigaba da shirye
shiryen aurar da Adamu cikin sati dayan da ya
kudurta, kuma ya himmatu cikawa, ya kuma
cika a ranar da Adamu ya cika kwanaki bakwai
da bacewa, ba tare da an yi gangamin tara
mutane ba, hasalima su isu danginsu suka hadu
da makwabta aka daura auren.
A wannan sati dayan duk zirga-zirgar da
su Salma zasu yi gidan bokansu sun yi abinsu,
shi ya tabbatar musu aure an yi an gama, shi ya
ingiza Alh. rasa kwnciyar hankali har sai da ya
daura auren, sannan ya tabbatar musu Adamu
idan ya dawo ba shi da wani katabus na
yunkurin bijirewa.
Ranar da Adamu ya cika sati dayan, da
kansa ya ji hankalinsa yayi mugun tashi a
bukatar zuwa gida.
Tun da sanyin asuba ya gallabi Salmanu
tafiya zai yi.
Ba tare da son rai ba Salmanu ya dinga
karfafa masa gwiwa, amma cikin siyasa ya
dinga ribatarsa har ya kai azahar sannan ya bar
91 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
shi ya tafi gida bayan sun ajiye ajandar cewa
gobe da sanyin safiya zai fito aiki.
*********
Ba cikin karfin gwiwa sosai ya tunkari
gidansu kai tsaye zai shiga ba, yana dab da
shiga soro suka yi kacibis da Alh. ya fito daga
gidan shi kuma zai fita.
Adamu ya ji wata irin mummunar faduwar
gaba ta daki kolin zuciyarsa. Gaskiya ba haka
ya so ba, ba Alh. ya so fara gani ba, Hajiya ya
so fara gani yadda duk yadda ya tsara ta zata
tsaru, ashe yau Allah ya hukunto masa haduwa
da abinda ba ya so.
Kawai sai ruďewa ta sanya Adamu zubewa
kasa yana gaishe shi saboda tsabar rudewa,
musamman da ya gan shi cikin fishi.
Alh. yayi masifar cin magani, maimakon
ya amsa gaisuwar kawai sai ya yafice shi ya се
masa,
"Zo mu je"
92 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
Tsoro ya kara kashe Adamu da ya ga ba
cikin gidan Alh. ya dosa ba, hanyar gidansa ya
dosa.
Wani karfin gwiwa ya shigi Adamu da
wani tunani ya zo masa kahon zuci, don me ma
zai dami kansa da tsoron Alh. sai ka ce wani
Ubangiji?
Bakinsa na rawa ya tambayi Alh. wanda
ya riga yayi gaba,
"Alh. ina za mu?"
"In mun je sai ka gani”
Ya amsa masa ba cikin dadin murya ba.
Adamu ya kara dakewa,
"To ba zan iya shiga na gaisa da Hajiya ba
tukunna? Gara na shiga ta gan ni hankalinta ya
kwanta.."
Cikin juyawa ya kale shi fuska a tamke
Alh. ya amsa,
"In kwanakin sati da kayi ba ka gida ba ta
fadi ta mutu saboda bata ga fuskarka ba ai,
rabin awa ko awa daya da zaka yi yanzu ba zai
sa ka dawo ka tarar ta mutu ba"
Adamu na jin haka ya san Alh. ya hadiyo,
don haka sai ya ja bakinsa ya rufe, a ransa
93 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
kuma ya kudurta rashin kirkin da zai yi in an
nemi raina masa wayo.
Ya tarar da gidan da hayaniya, amma dai
suna shiga aka hau kallonsa saroro yana bin
Alh. a baya yana ta faman yake yana gaisawa
da mutane har suka shige dakin Alh.
Alh. ya shige bandaki shi kuma ya nemi
kujera ya zauna ya ci magani yana ta faman
muzurai da sake-sake har Alh. ya fito daga
bandakin ya hakimce a kujera cikin kalar nasa
nuna bacin ran,
"Ba na so in ce daga ina kake Adamu, don
kar in ji amsar rainin hankali ta janyo in tashi
in kashe ka da mari"
Adamu yayi fuska iyakar fuska,
"Ni dai namiji ne, bare a ce yawon duniya
na tafi"
Mamaki ya cika Alh. wannan fa shi ake
kira karfin hali wai barawo da sallama, daga
bisani kuma sai ransa ya baci ya kura wa ido
Adamu cikin bacin rai.
Adamu ya muskuta ya sake muskutawa
yana wani basarwa,
"Wallahi fashina aka yi"
94 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
Alh. ya jima bai tanka ba saboda tsabar
haushi ya ma rasa me zai cewa Adamu, dama
abinda ya guda kenan, ya san Adamu zai iya
zuwa masa da rainin hankalin da zai tunzura
shi, ilai kuwa. Sai faman kokawar hadiye
fishinsa yake, har ya samu ya hadiyu, ya
sassauta fuska ya dubi Adamu,
Fashi wane iri, su waye suka yi fashin
naka?"
Adamu ya sake kawar da kai yana cin
magani,
"Masu fashin mutane mana, sun ga ba zan
yi musu amfani ba suka dawo da ni"
Wannan tatsuniyar ta gajiyar da Alh. sosai,
ya ga kawai mafi a'ala ya rufe babinta ya
dauko babi na gaba.
Ya girgiza kai cikin halin ko in kula,
"Allah sarki, to Allah kiyaye gaba"
"Amin"
Adamu yayi fuska ya amsa.
Alh. ya sake gyara zama sannan ya gyara
murya,
"Na zaci lafiyarka lau ka guje mu shiyasa
har na yi maka wani karambani"
95 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
Adamu ya dube shi cikin rashin fahimta,
amma bai tanka ba.
Alh. bai damu da shirunsa ba ya cigaba da
Magana.
"Kodayake ba za'a kira shi da karambani
ba illa son in faranta maka ko kuma in cika
maka wani burinka da kake fatan
tabbatuwarsa"
Yayi shiru yana jan iska.
Yanzu Adamu ya tattara masa hankalinsa
gaba daya, cikin jin dokin jin burin da Alh. zai
ce ya cika masa, shi dai ya san a duniyar nan
ba shi da wani buri da ya wuce mallakar Husna
da kuma zama attajiri domin ya jiyar da ita
dadi, su ne manyan burikansa, duk sauran da
zasu biyo baya kanana ne mahadın rayuwa
kawai, amma me!? Kawai sai Alh. ya kunno
masa da hagun wannan buri.
"Maganar da muka yi kwanaki kai da
Salma, cikin ikon Allah na yi iyakar Kokarina
na cika muku wannan buri, da safiyar yau aka
daura muku aure"
Adamu ya ji tamkar Alh. ya wurga shi a
tekun ruwan zafi, nan take ya fara hada gumi
96 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
tamkar fankar da take juyawa ita ma zafin take
bayarwa sai dai harshensa ya sarke, duk
kokarinsa na yayi furuci sai ya kasa illa sa wa
Alh. ido yana kallo.
Alh. ma ya kura masa ido,
"Yaya lafiya na ga kana hada zufa?"
Da za a sakar wa Adamu barshe babu
abinda zai hana shi tura wa Alh. ashar, amma
an daure harshen don haka ba shi da baka sai
kunne.
Alh. ya sake kada kai yana cigaba da nuna
mamaki,
"Na san ban maka ta'addanci a Adamu,
godiya na cancanci ka yi min ba wannan kallon
ba"
Har yanzu Adamu ya kasa tankawa,
lokacin da ransa ya raya masa ya tashi ya sa wa
Alh. naushi ma sai ya ji duk lakarsa ta mutu,
tamkar ko hannunsa ba zai iya dagawa ba.
Da Alh. ya karaci nuna mamakinsa sai ya
daga waya ya kira Sa'a ya ce ta turo masa
Salma.
Kafin Salma ta zo sai da ta gama tsubbacetsubbacen da boka ya bata, ta taho da maganin
97 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
da ya sanya ta barbadawa a inda Adamu zai
taka, ta barbadada a kofar dakin sannan ta yi
fuska ta shiga kai a kasa tana sallama.
Har yanzu harshen Adamu a daure yake,
amma idon zuciyarsa bai kasa ganin mugun
kyan Salma ba, ya ji a guje wani irin shauki
yana zagaye ilahirinsa, sai dai ba bakin
tankawa. Ya dauke ido daga kanta bayan ta
zauna ya mayar da ganinsa ga Alh. wanda ya
fara koro musu nasiha. Ya yiwa Salma shaidar
hakuri, ya yi wa Adamu ta mayar da kai ga
abinda ya sanya gaba, ya ce,
"To ke Salma ina fatan ki dore da
hakurinki da na san ki da shi, kai kuma Adamu
ina fatan za mu ga jajircewarka da taurin kanka
wajen kula da iyalinka tare da yi musu adalci"
Ko nishi Adamu yayi yunkurin yayi ya
kasa, ya dai bi Salma da kallo wadda farin
cikinta ya kasa boyuwa lokacin da take kada
kanta a kasa alamar bayar da amsa cikin kunya.
Wannan shirun da kallon galala din na
Adamu ya ishi Alh. amma babu yadda ya iya
haka yayi ta yi musu nasiha kana ya sallami
Salma ya kara mayar da hankali ga Adamu,
98 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
"Karamin gidan nan nawa da na siya
kwanaki a Dorayi, anjima zan baka mukullinsa
ka je ka duba 'yan gyare-gyaren da ba zai ci
kudi da yawa ba a samu a kwaskware shi ku
tare nan da sati guda"
kyar.
ko?"
"Hmn!"
Wannan karon Adamu ya kwato nishi da
Alh. ya sake shanye haushi ya cigaba,
"Ka san gidan akwai shago a kofar gida
Gyada kai kawai Adamu yayi.
Alh. y ace,
"Na lura dan zagayen unguwar gaba daya
babu shagon sayar da kayan masarufi, saboda
haka tunanina ya fada kan cewa sai na baka jari
ka zuba kaya ka dinga saidawa, daidai talaka
dai ya ishe ku cin abinci da toshe wata
6arakar"
"To"
In ji Adamu
Alh. ya dan ja fasali yana kallonsa, yanzu
ya fara zargin anya kansa daya kuwa?
Kodayake kafin yayi masa zancen aurensa da
99 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
Salma ya zo da bakinsa da cin maganinsa har
ya dan sassaki rashin kunyarsa da rainin
hankalinsa. Kenan karamin tabin kwanyar da
ya same shi na nan take ne bayan jin an aura
masa Salma. To bakin alkalami dai ya riga ya
bushe, aure ne an riga an daura, yayi haukansa
ya warke. Don haka Alh. ya share shi ya cigaba
da yi masa bayani,
"Ta bangaren Salma kuma kar ka damu,
na bawa Sa'a 'yan wasu kudi ta y mata
siyayya, babu abinda na ke nema a bangarenka
sai halarci ta hanyar yi wa Salma adalci da rike
ta bisa amana, ka ga marainiya ce bata da kowa
sai mu wanda ko ba kai ka aure ta ba kai mai
tsayawa ne ciki-ba-hatsi ba ka kwatar mata
'yancinta idan mijin da ta aura ya danne"
Da wannan nasihar Alh. ya sallami Adamu
ya fito yana layi ya doshi gidansu. Zuciyarsa
fanko ce a tuna komai ko saka komai, amma
dai wani radadi-radadi daga can kasa yana
fuzgarta, sai dai ba ya nisa yake cin tuntube ya
nuna ba komai.
Kafin ya je gida ya dinga jin kansa yana
wata irn kara tamkar yana shirin bindiga ko
100 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
kamawa da wuta, kawai sai ya tsaya wani kanti
a unguwarsu ya sai fuyo wata mai dankaren
sanyi har leda hudu ya shiga da shi gida.
Hajiya na kakabin murnar zuwansa da
kokarin fashewa da kuka saboda ganinsa a
hargitse, shi kuma yana mika mata ruwan ya
tsuguna a gabanta cikin raunin murya yana
cewa,
"Hajiya zuba min ruwan nan a tsakar
kaina kar ya kama da wuta"
Jikin Hajiya na bari ta karbi ruwan ta
dinga fashe masa su a aka har leda hudu ba tare
da ta damu da jika falonta da take yi ba ta dago
kansa cikin fuskar alhini da jimami tana
kallonsa, sannnan cikin raunin murya ta ce,
"Adamu ina ka shiga ka bace?"
Maganar da tayi cikin rauni ta karasa
raunata tasa zuciyar, ya ja jiki da kyar ya isa
kan tabarma ya zube yana shasshekar kuka.
Hankalin Hajiya ya kai kololuwan tashi,
da sauri ta durkushe a gabansa tana tambayarsa
cikin rudewa,
"Adamu me ya same ka?"
101 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
Ya ji tausayin kansa da na Hajiyarsa
wadda ta damu da shi ya mamaye ransa, ya
saki kuka mai nuna tsanantar kunan rai,
"Hajiya Alh. yayi min auren da ba zan
taba farin ciki da shi ba har abada"
Kafar Hajiya na rawa ta silale ta nemi
gurin zama tana sauke nishi cikin sauri,
"Dama ba kai ka bashi damar ya aura
maka Salma ba? Dama baka sonta Adamu?"
Ta tambaya a rikice,
Ya amsa mata da rauninsa da kuma iyakar
gaskiyarsa,
"Nine, amma ban san abinda ya shiga
cikin kaina na fadi hakan ba, wallahi ba Salma
ce zabina ba, ban taba zabarta ba, ban taba
mafarkin aurenta ba, kuma ban taba fatan ko a
mafarkin in aureta ba"
Kan Hajiya ya so ya shiga duhu duk da a
iyakar imaninta ta san iyakar gaskiyr Adamu
kenan tunda yake furucinsa cikin kuka, sai ta
rasa da Kalmar da zata yi amfani wajen karfar
wannan kalubalen nasa. Ta cigaba da zura
masa ido galala shi kuma ya cigaba da
shasshekar kuka kafin ya zarce da cewa,
102 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
"Na kasa cewa Alh. ba zan iya rike auren
da yayi min ba, amma duk lokacin da kika
sami sarari ki sanar da shi, ni dai ya tawayi
rayuwata ya kuma cutar da ni, ba Salma nake
so ba, wadda nake so ina yi mata son da ko
wane hali aka rataye zuciyata ba za'a iya raba
ni da son ba... kuma in na sami sarari zan iya
ko ma menene da zai iya samar min da ita"
Bai jira cewar Hajiya ba ya mike yana
niyyar barin dakin.
Gabadayan kan Hajiya ya kulle, a gigice
take kwarai, amma dai maganganunsa na
karshe sun zabure ta karfin halin mikewa ta
riko rigarsa kafin ya ficė, cikin rawar murya ta
се,
mata,
"Adamu zo ka fada min, wa kake so?"
Ya dakata ba tare da ya juyo ba ya ce
"Husna nake so"
"Wacece haka?"
Ta tambaya cikin nuna rashin fahimta.
Ya kada kai idanuwansa na cigaba da
zubar da hawaye, zuciyarsa na wani irin kuna,
103 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
ya koma ya zauna yana kallon Hajiya da ta
tsaya kansa hankalinta a tashe,
"Ita ce wadda tun tuni nake maganar ina
so, akanta na ki karatun boko don in sami
kudin d azan rike ta.... Kai Hajiya ko me na
zama akanta na zama, ko kuma nake shirin
zama... ina fada miki wannan ne dan ki gane
ban fara sonta don in daina ba..."
'Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un"
Kawai Hajiya ke Ambato cikin tafa hannu
mai nuna alhini da nadama, tamkar ita ta yi wa
Adamu auren dole take ji cikin ranta, ta kasa
yafewa kanta sakacin da tayi aka aura masa
abinda ba ya so.
Ta matsa can jikin bango ta jingina da shi,
"Adamu ni ban san abinda zan ce maka
ba, hakuri zan baka ko kuma sakacinka zan
nuna maka?"
Ya sake mikewa tamkar kunama ta dalle
shi yana girgiza mata hannu,
"Kar ki ba ni komai Hajiya, ko Husna kika
ba ni a yanzu ba zaki birge ni ba, don na san
Husna zata rage darajar son da ta ba ni in ta
tarar da wadda kaddara ta aura min wato
104 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA.,.2
Salma, duk ku rike abinda zaku fada min don
ban ki karbar abinda aka ba nib a wato Salma,
amma dai ba zan kasa sanar da ku an cuce ni
ba, ba zan kasa fadar ba a yi min daidai ba...."
Ya sake ficewa daga dakin cikin fishi.
Wannan karon Hajiya bata iya riko shi ba,
duk da ta fahimci ba cikin hayyacinsa yake ba,
yakamata ta ma ta bar shi ya huce, yadda zasu
fi fahimtar juna.
Haka dai ta zauna tana ta kakabin alhini da
fargabarta har lokacin da ta yanke shawarar
daukar waya ta kira Alh. su tattatuna.
Adamu bai damu da goge hawayen
fuskarsa ba ma bare ya kintsa tafiyarsa ta 6оуе
rashin nutsuwarsa ko tashin hankalinsa.
a
A dazu ya gama kaddara kwanyarsa ta
tashi daga aiki, amma a yanzu da ya gan shi
hanyar gidansu Husna ya tabbatar ko
kwanyarsa zata manta komai ba zata taba
manta Husna da abinda ya shafe ta ba.
105 Maimuna Idris Sani Beli
1
NA SHIGA ALJANNA...2
Har ya isa kofar gidan bai san abinda ya
kawo shi gurinta ba, amma yayi imanin tunda
zuciyarsa ta kawo shi ta san abinda zata fada.
A hargitsensa ya sami yaro ya tura shi
gidan yayi masa sallama da ita.
Husna na kan kekenta da ta fito da shi
tsakar gida tana ta faman dikin, yaron ya shiga
da sallamarsa, ta toshe kunnuwanta da head
phone tana sauraron wakokin da ba su fice na
soyayya ba, zuciyarta a rube take da tunanin
Adamu har kwalla na tsattsafo mata tana goge
abarta a saye. Kuma da yake tana hadawa da
dan rausaya alamun tana jin dadin wakar da
take sauraro babu wanda ya damu da gane
cewa wuya take sha.
"Wai Husna ta zo"
Yaron ya sake maimaitawa bayan yayi
Sallama duk Husna bata ji ba, sai da Hajara at
fito daga kicin ta tambayi yaron,
"Wanene yake kiranta?"
Yaron da yake irin fadi ba a tambayeka
bane ya ce,
"Wani saurayi ne, baki mai dan kauri da
tarin gashi, kuma na ga ma kamar kuka yake?"
106 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
Kukan da aka ce yana yi ne yayi mugun
jan hankalin Hajara ta yafito Husna cikin
firgita,
"Ke shashasha, ki saurari yaron nan ya zo
da maganar a kasa kunne a saurara"
Husna ta ji haushin kiranta shashashan da
Hajara ta yi, ta debo mita zata sauke Hajara ta
tare ta,
"Yanzu haka shi ma me neman naki rashin
kunyar kika yi masa, na san yanzu sai ki zage
ni...
Sai kawai Husna ta saki baki tana kallonta
cike da kunan zuciya.
Hajara ta juya tana cewa yaron,
"Ga ta nan ka sanar da ita sakon"
Tana rufe baki yaron ya furta,
"Wai Husna ta zi in ji wani..."
Shi ma Umma ta tare shi,
"Shi wai wa? Ka sanar da ita waye"
Yaro kuwa ya gyara murya ya kwatanta
mata Adamu.
Tunda ya ambaci mai tarin gashi ta ji
numfashinta na neman daukewa, zuciyarta ta
107 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
dinga bugawa da sauri da sauri tamkar tana
ambatar mata, Adamu ne! Adamu ne!
Hajara ta zuba idon ta ga Husna ta kora
mai kiran sai ta ga nan da nan ta saki dinki tat
fau janyo ruwa tana wanke kafa, a gurguje ta
auki hijabi ta yi waje.
Kamar yadda ta zata, Adamu ta tarar
wujiga-wujiga da shi tamkar an finciko shi
daga bakin kura ba, ga shi ba, ba ga zuciyarsa
ba wadda fuskarsa ta nuna alama, sannan ita
ma kanta bata sha wahalar gane cewa kuka
yake ba.
Ai jikinta na bari tamkar ta riko hannun
Adamu ta yafito shi,
"Shigo shigo nan Adamu"
Ba ta yi gaba ya biyo ta a baya ba sai ita ta
anya shi gaba suka shiga soron. Da sauri
kuma ta shige cikin gida ta nace masa,
"Bari na kawo maka kujera"
Adamu ya kasa Magana ne saboda yadda
kuka ya kara cika kansa. Ya tabbatar barin
jikin da Husna ke yi da shi na so ne, to yaya
zata ji idan ta ji cewa an aura masa kundubа
Salma? Duk yadda yayi kokarin ya dake wa
108 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
wannan tausayin sai da ya ci karfinsa,
hawayensa suka kara araha a fuskarsa dan ma
yayi namijin kokarin hana sautin kuka fitowa.
A haka Husna ta fito ta same shi, tana
dauke da kujerar zaman dinkinta da kuma pure
water mai dan Karen sanyi hade da tambulan
din roba.
Ta kula da karuwar damuwarsa kuma
zuciyarta ta kara rauni, sai dai bata nuna hakan
ba. Ta dire masa kujerar cikin kuzari ta nace
masa,
"Zauna Adamu"
Ba musu ya zauna.
Ta huda pure water ta tsiyaye shi a
tambulan din ta mika masa,
"Ungo sha ruwan sanyi hankalinka ya dan
kwanta sai na ji me ke akwai"
Adamu ya kasa Magana, kirkin Husna ya
sanya shi jin lallai an tafka masa asarar
masoyiya, asarar da ba zai taba fanshewa ba.
Sai da ya shaye ruwan tas, bata bar shi ya
ajiye kofin a kasa ba ta mika hannu ta karba
idanunta akansa tamkar in ta rufe ido zata bude
ta ga ya bace,
109 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
"Adamu me ya faru?"
Ta tambaya cikin raunin murya bayan ta
fahimci ba shi da alamar niyyar tanka mata, da
alamar kuka ya zo yi mata ba Magana ba.
Ya daga jajayen idanuwansa ya dube ta,
"Kin karanta takarda ta?"
A nutse ta girgiza kai,
"Ba na jin yaren China"
Yayi kasa da kai cikin tunani. Ba don
shegantaka yayi mata wannan tambayar ba,
yayi mata ne domin ya kamo bakin zarenta,
don ta haka ne zai gane matsayinsa a zuciyarta.
Ta dan ja fasali tare da sauke numfashi
ce masa,
ta
"Mu bar zancen takarda tunda ga