Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 6
ya fahimci abinda ta fi so kenan a yanzu. Saboda haka bai yi kasa a gwiwa ba ya kunno wa da Adamu maganar, "Tun kafin wannan cece-kucen yayi nisa ina ganin yakamata manya su shiga maganar, in da gaske kuke son juna ku fito ku fada mu san na yi. Ni zan dauki nauyin komai har in ga burinku ya cika, dama dukkanninku ai nauyinku a kaina yake. Kai tunda ka ki karatun dole ba zan zuba maka ido ba, zan baka jari bayan kayi aure, don ba zan baka yanzu ka shashantar min ba, in kuwa ka yi aure ka ga nauyin iyali ya hau kanka na san dole zaka nutsu" Kunya ta bayyana a Salma, amma Adamu babu abinda ya bayyana tasa fuskar sai yarda da amincewa, duk da cewa zuciyarsa na mika wuya tana kuma karbowa, yana so yaji mamakin shi za'a yi wa aure kuma Salma za'a 56 Maimuna Idris Sani Beli 3 NA SHIGA ALJANNA...2 aura masa, sannan yana so yaji murnar za'a aura masa Salman duk da cewa wata zuciyar tasa na jin nuna an fa cuce ta, "Ba ka ce komai ba" Alh. ya farko da shi daga tunani. Yayi firgigit ya dago kai ya kale shi, "Ai babu komai Alh. duk yadda kuka yi ina maraba, Allah bar zumunci Allah kuma ya Kara arziki" Cike da jin dadi Alh. ya amsa. "Amin, ba wani dogon lokaci zamu ja ba ma, in dai kun so hakan" Ba tare da jin wata kumya ba Adamu ya kalli Salma cikin murmushi ya се, "Ba komai mun so Alh." Cikin raha Alh. ya cе, "To rasa kunya" Adamu ma yayi dariya Alh. ya dan nutsu yana duban agogo ya ce. "Abinda ya rage min yanzu shi ne zuwa ofishin "Yan sanda in nemi ayi wa Salma iyaka da Salmanu" Duk da Adamu cikin jin haushi Salmanu yake amma sai ya ji kamar bai kyauta ba idan 57 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 aka tozarta Salmanu, cikin sanyin jiki da jin karfin gwiwa ya ce, "A'a ka bar ni da shi Alh. ni da kaina zan yi maganinsa, zai fi jin hukuncina ma akan na 'yan sandan ka san shi da taurin kai" Alh. da ya gama sakankancewa da Adamu nan da nan ya mika wuya, "In dai kana ganin zaka iya yi musu tsakani ai shikenan, ni kaina bana son shaidar zuwa ofishin 'yan sanda da mutuncina da komai, musamman a irin wanna lamarin da babu shaida, in ya so yana iya cewa karya aka yi masa mu ji kunya" A dokance Adamu ya ce, "Hakane wallahi Alh." Daga nan Alh. ya sallame su, Adamu da Salma suka rabu suna kallon-kallo har Adamu ya bar gidan. Salma ta fada daki a guje cikin murna kamar ta shide, Sa'a bata saurare ta ba sai da ta je gun Alh. ta jiyo kanun zancen sannan ta dawo ta sami Salma, "Iye! Amaryar kwanan nan" 58 Maimùna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 Salma ta kara fadawa katifa ta tana birgima da girgiza kai, ta cc, "Kai Anti!" Sa'a ta dan kai mata dukan wasa ta ce, "Me ye wani kai Anti, karya nake?" Salma ta tashi zaune tana sussunke fuska, "Na gode Anti...." Sa'a ta katse ta, "Da aka yi me? Kin fiye shirme, ki bar murna ina ganin fa da sauran rina a kaba, har yau Adamu bai gama zuwa hannu ba kina ganin fa yadda ba ya zuwa inda kike in ba ke kika nemo shi ba" A sanyaye Salma ta dago ta dubi Sa'a, "Haka ne Anti, to yanzu me ye abin yi?" Sa'a ta ciji lebe,. "Dole ne zamu koma gurin boka, Adamu yana da taurin kai da alama, Alh. zuwan farko da na yi masa na kama shi kirif! Amma kin ga shi yana neman ba mu gudu" Jikin Salma ya kara sanyi, Allah ya sani ita ba ta je gidan Boka domin ta dauwama tana zuwa a, ta je don Adamu ya yarda ya aureta, kuma don Sa'a ta ce babu wata mafita bayan 59 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 wannan, amma bata taba yi wa kanta mafarkin ta tabbata a wadanda bokaye ke biya wa bukata ba. Amma ba yadda ta iya, Adamu take so, har yanzu bata samu ba bare ma ta ga in zata iya nade hannun zani ta yi wa gidan bokan tawaye. gida A fuskarta ta nuna ta amince su koma. Sa'a ta ce, "Sai dai gobe mu je, kin ga yau Alh. yana Salma ta amsa, "Allah ya kai mu". Da har Salmanu zai wuce sabgarsa ya jira Adamu a a can, yana tuno wasikar cainan Adamu zuwa ga masoyiyarsa. wadda ke aljihunsa kawai sai ya saki hanya ya dauki hanyar gidansu Husna. Yana tsaye jiran yaron da zai aikaа kasancewa hantsi ne kusan ko wannne yaro ne makaranta. 60 Maimuna Idris Sani Beli S NA SHIGA ALJANNA...2 Yayi tsayuwa ta kusa ta minti goma, cikin alfarmar Ubangiji sai ga Husnan ta fito daga gidan zata siyo kayan dinki. Tana ganin Salmanu ta saki wata matsananciyar fara'a tamkar Adamun ta gani, cikin 6arin jiki ta shiga yi masa maraba da gaishe shi. Wani mugun tausayinsu ya shige shi, bai iya 6oyewa ba maimakon ya rama mata da nata murmushin ko dariyar sai ya buge da yake ya na cewа, "Husna manyan kasa, tun dazu nake tsaye ina jiran bullowar yaron da zan aika, sai kuma gashi Allah ma ya bullo min ke da kanki" Cikin kada kan farin ciki Husna t ace, "Ka san unguwar tamu manya irinku sun fi yawa, to bare kuma lokacin makaranta". Salmanu ya amsa, "Gaskiya na ga alama, to ya garin?" Husna ta jinjina kai ta amsa, "Komai kalau wallahi, Na yi farin cikin ganinka, amma dai da Adamu na gan ku zan fi haka farin ciki..." 61 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 Ya katse ta saboda ya ji tausayin da yake mata ya nunku, da gaske Husna tana son Adamu tana son ya zo wajenta shi kuma gashi can ya tafi gurin 'yar fashi da makamin soyayya watakila ma ba zai tuna da ita ba bare rainin hankalin da yayi mata a takarda. Salmanu ya daddage dai yayi mata karya. "Sabga c eta tare shi, kin san yana dan koyarwa a wata makarnta mai zaman kanta, jiya da shekaran jiya yayi fashi don haka yau aka ki lamince masa dole ya wuce bayan ya bani sakon amsarki, amma dai yau da dare ya ce zai bullo. Husna na bayyana kunya amma murna na yin gaba da kunyar tata. Cike da farin ciki ta ce, "Babu laifi Allah ya kai mu Salmanu ya zaro wasikar daga aljihu ya mika mata, wasikar tun daga makunshinta ta nuna da yaren da aka rubutota. Husna ta karba cikin mamaki tana godewa, amma dai bata yi nauyin baki bat a bi ba'asi tana ta faman juya gaba da bayan wasikar, 62 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 "Anya wannan tawa ce kuwa" Salmanu yayi fuska, "Taki ce mana, me kika gani?" Ta nuna masa rubutun bayan enbilop din, "Ka ga rubutun da ya sa ni zaton ba tawa ba ce Salmanu ya basar yana yarfe hannu alamar ko in kula, "Au ba kya jin wannan yaren?" Husna ta shiga nazarinsa don ta gane da gaske yake ko da wasa? Alamunsa ya nuna da gaske yake saboda haka ta kada kai, "Ban da a fim ni ko wanda ya taba jin yaren ban gani ba..." Ya tare ta da sauri, "A'a da wasa kike" Ta kada kai tana dariya, "Me yasa zan maka wasa? Wallahi da gaske nake, in kai ka taba ganin mai iya yaren sai ka bani labari" Salmanu ya sake yin fuska, babu ta yanda zaka dube shi ka zaci karya yake shirgawa, 63 Maimuna Idris Sani Beli OHN SAS A NA SHIGA ALJANNA...2 "To ai Adamu yaren da ya fi ji kenan fiye ma da turanci, shi ma yake koyarwa a makarantar" Ba karamin girgiza da jin wannan almarar Husna ta yi ba, ta ji mamaki ta gaji, kuma Adamu ya kara shiga ranta da birge ta, sai juya wasikar take tana kallo tana karawa. A karshe ta buge da kallon Salmanu cikin murmushi, "Ya ji dadinsa wallahi" Ta zarce da dariya cikin kallon wasikar, a "Amma ban da abinsa ai yakamata ya fara sanin idan ina jin yaren, ni ko bindiga za dora min ai ba zan iya kawo kalma daya a nan ba". "Kamar dai yadda kika rubuta masa yaren da kike ji" Salmanu ya fada cikin ransa, amma ya kawar da fuska yana basarwa, "Haba kar ki ba da mata don Allah, ki daure ki buda ba zaki rasa abinda zaki gane ba" Ya fara duban agogo yana alamar haramar tafiya. Husna ba don ta so ba ta kasa musawa, sai don kar ta bayar da matan kuma kar ta cigaba 64 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 da rike shi musamman da alamunsa suka nuna yana son ya kauce, dole ta rausaya kai ta ce, "To babu laifi, Na gode ka gaisar min shi" Ya yi gaba yana yana cewa, "In sha Allah" Maimakon Adamu ya dauki hanyar fadar bokancinsu, kawai sai ya gan shi a hanyar gida. Zuciyarsa ta fara rabuwa biyu ko ma fiye, neman dalilan yin abinda yayi, nadamar abinda yayi da kuma shakkun in ma shi din yayi. Wai shi ne ya karkace baki ya ce a aura masa Salma? Wai shi ne ya zabi Salma ya watsar da Salmanu kuma ya kware masa baya ya goyi bayan aka aibata shi alhalin har ga Allah ya san zuciyarsa ta fi son Salmanu akan Salma, ta fi amincewa Salmanu akan Salma? A yanzu ya fara jin lallai ma kawai Sharri aka yi wa Salmanu bai aikata abinda ya aikata ba, suna zargin Salmanu da shaye-shaye, tabbas su ne mashayan, domin yana da yakinin 65 Maimuna Idris Sani Beli 1 C NA SHIGA ALJANNA...2 wata hodar suka busa masa har ya zauna aka saki wadannan sina-sinan da shi a matsayin rayuwarsa ta zahiri, amma an ci karya an kwana da yunwa ace cikin hankalinsa ya ce aura masa Salma, don ma wani tsabar iya dialogue har da fadin da gaggawa. Duk da yana cikin matsawa zuciyarsa da kwanyarsa mayar da abinda ya faru fim, har yanzu kansa a rude yake, sai dai yana kala wa zargin hodar mayen da suka busa masa ce bata sake shi ba, sai ma ya ji kan ya rude da ciwo, ba zuciyar tasa kawai da take zogi ba. A daddafe ya isa gida idanuwansa na zagi ya bude dakinsa ya fada katifa ya runtse ido, babu abinda yake hangowa sai lokacin da Alh. ke masa tayin auren Salma shi kuma yana amsawa cikin murna da karsashi har ma yana jefawa shegiyar Salma kallon so wanda sam bata cancance shi ba, don dai kawai tayi masa fashinsa ne. Ya jima cikin mawuyacin hali sannan wani mawuyacin bacci ya silalo ya sure shi dauke da mafarkai marasa dadin ji da gani, 66 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 saboda haka da ya farka hankalinsa sai ya kara tashi. Dayake Allah yayi masa arahar kuka kawai sai ya ganshi zaune yana ta sharbar hawaye. Zuciyarsa kuma ta fara jin abinda ke faruwa da shi cuta ce ba kaddarar haka kawai ba, lallai kyautuwa ne ya je neman magani in ba haka ba yayi mutuwar tsaye. Yana nan zaune yana sharbar hawaye dajin lallai wani shaidani ne ya hau kan zuciyarsa yake sarrafa masa ita ba shi ne da kansa ba. Kawai sai ga kiran Salma ya shigo wayarsa, kamar yadda ya gama hasashen kuwa sai ya ji tilashin bashi da abu mafi soyuwa irin daga wayar, jikinsa na bari ya daga yayi mata Magana a ladabce muryasa har sarkewa ta ke, "Ranki ya dade me ya faru, ko wani 99 kiran ne' Daga can 6angaren a yangace Salma ta amsa, ne "Kai haba dai wani kiran, yanzu kana ina Ya sami kansa da jin sheka mata karya, 67 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 "Ina hanyar gidansu Salmanu in je mu kwashi 'yan kallo" Ran Salma yayi fari tas! A yangance ta sake cewa, "Kai Adamu wai dambe zaka yi da shi ne?" Ya sake amsawa cikin farin jiki, "Sai in yi abinda ya fi dambe da shi mana Salma, ke fa ya taba! Yau ni na taba jin irin wanna ta'addanci ma? Don kawai ina sonki sai abin ya tsaya masa a rai? Ai kin ga dole ma na bi ba'asi in yake sonki na ji dalili....." Salma ta katse shi cikin dariya, "Kai haba! Allah ya tsari gatari da sara shuka, ni me zan da shi?" Muryar Adamu ta nuna tsabar jin dadinta ga kalaman Salma, cike da zumudi ya ce, "Ai kin ga dole na je na fada masa hakan, in ma sonki ya dauka ba sai ya sauke ba...' Salma ta tare, "Eh haka ne kuma, amma dai kar ka yarda ka yi fada da shi, ka san dan ganye ne, zai iya Burma maka wuka na shiga uku... kawai dai ka ja masa kunne ya fita harka ta, kai ma kuma 68 Maimuna Idris Sani Beli 3 NA SHIGA ALJANNA...2 ka fita harkarsa, ba kai ba shi, in so samu ne ma ko hanyar da ya bi kar ka bi..... ni fa koо ya baka hakuri kun shirya in mun yi aure kar ka sake ka kawo min shi gidana..... Ya tare ta cikin yanayin bin umarni da nuna gamsuwa, "Ni ma yaushe zan yarda da hakurinsa na shirya da shi bare har na kawo miki shi gidanki? Ai tunda ba kya son ganin Salmanu ni kuma zan mutu wajen hana ki ganinsa' Ta yi wata "Yar shewar farin ciki a shagwabe, "Na san zaka iya Adamu, komai ka dauka kai Jarumi ne a cikinsa" Ya ji matukar dadin yabon da tayi masa, cike da fara'a ya ce mata, "Ni jaruminki ne kawai Salma ba jarumin kowa ba, zan iya sadaukar miki da rai, ba zan iya sadaukarwa da kowa ba..." Kawai sai Salma ta ji wani zazzafan hawayen tausayinsu ya ciko mata idanuwa, wai Adamu ne ke sakar mata irin wadannan zafafan kalaman soyayyar ba cikin hayyaci ba? Ta ji tausayin wannan dolen soyayya da tayi masa, 69 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 sannan ta ji tausayin kanta da bata cancanci Adamu ya so tab a sai ta gusar masa da hankali. "Na gode Adamu' Ta sami kanta da fada cikin raunin muryar da ta bayyana kukan da take. Nan kuma hankalin Adamu ya tashi, ya shiga barin jikin tambayarta, "Na bata miki rai ko? Ban san Maganata zata bata miki rai ba, don Allah ki yi hakuri ki yafe min" Da sauri Salma ta katse shi tana rarrashi, "Ni ma jarumarka ce Adamu, ba zaka bata min rai ba, hawayen farin ciki nake da jin kamar a mafarki, wai ni-kake so haka Adamu?" A dokance ya amsa, "Ki bar shakku Salma, ina sonki kuma ba יי zan fasa ba har mutuwata" Farin ciki ya fara korar hawayen da take, tana gogewa tana amsa masa, "Ni ma haka Adamu. Yanzu yaushe zaka zo?" Ya amsa, "Ko yanzu kika cë na taho" 70 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 Da sauri ta girgiza kai, "Ai ba zan so abinda zai wahalar da kai ba, yanzu ka bar gidan kuma nà ce ka dawo, ka bari da dare ka zo" Ya ce, "Allah ya kai mu, In sha Allahu da vuri zaki gan ni" Ba don ta so su bar hirar ba sai dan kudi wayarta sun kare, ta yi masa sallama suka rabu dukkansu suna nuna begen juna. Salma ta sauke waya tana farin ciki. Adamu ya sauke tasa zuciyarsa na kuntacewa, maimakon ya rafsa kuka kamar yadda ya so, kawai sai ya fasa ya hau binciken wani ruwan madubi da ba shi da amfani a wajensa sai idan zai yi gyara fuska. Ya shiga duban kansa a madubin tamkar yana tantamar in shi ne Adamu dan Hajiya. Bai iya barin abin a zuciyarsa ba sai da ya fito fili ya hau tambayar dodon madubin da muryar tausayi, "Don Allah fada min gaskiya kai ne Adamu? In ka ce min kai ne, na rantse da Ubangijin day a kage ni ka zama mugun makaryaci, Adamu ba wawa ba ne, Adamu ba 71 Maimuna Idris Sani Bali NA SHIGA ALJANNA...2 soko ba ne, Adamu ba Salma yake so ba, Adamu Salma bata isa ya so ta ba....... duk abinda ya jaza wa Adamu zama soko yanzu Allah ya isan sa bai yafe ba!' Bai tsaya a nan ba sai da ya zauna musamman ya hau turawa Salma iyayen ashar, ba ita ba hatta Alhajinsa ya sha zagi shi da Satma, sai kuma da ya gama zagin ne sannan ya fara kuka ya hau fadin, "Wallahi dama na fada, na haukace, na san na haukace dole sai an yi min Rukiyya ko kuma Girka. Wayyo Na shiga aljanna na kasa fita" Yana ta faman wannan Samabatun Salmanu da ya gaji da jira ya biyo sawu ta waya, dama ga dokin ya bashi labarin yadda su yi da Husa ya dame shi, ga kuma aiki yayi musu kaca-kaca har ma suna sa ran fara samun kostoma daga farkon sati. Ya gintse murya ya ce masa, "Wai har yanzu wannan yarinyar bata bar ka ka taho ba ne?" "Haukana ne ya tashi Salmanu" kundubar 72 Maimuna Idris Sani Beli A NA SHIGA ALJANNA..2 Adamu ya amsa cikin rarraunar murya mai son fashewa da kuka. Salmanu ya dauke wuta,cikin rashin abin cewa. "Shiyasa na so ka raka ni Salmanu, na san in kana nan komai zai iya zuwa da sauki, kila ma ba zasu sami damar busa min hodar da suka busa min haukan nawa ya tashi ba" Salmanu yayi ta maza ya samo abin cewa, "Yanzu kana ina?" "Ina gida" Adamu ya amsa. A tausashe Salmanu y ace, יי" To ka taho nan Zawaciki mu hadu" "In zan iya ko?" Adamu ya fada a raunane. Salmanu y ace, "Ai daurewa zaka yi, in ka zo din zamu tattauna dukkan abin yi, kar ka damu Adamu, in dai ina raye sai inda karfina ya kare a nemar wa zuciyarka da gangar jikinka Salama, ban taba alkawari irin wannan ba sai a kanka, ba ni da gatan dą ya fika, ba ni da wanda ya ki watsar da ni saboda yadda na sami rayuwa sai 73 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 kai don haka nake jin rayuwata tamkar an samar da ita ne domin in yi maka hidima in samar maka farin ciki.. ka zo kawai, ina jiranka nan da rabin awa" ba. Ya sauke wayar ba tare da ya jira cewarsa Adamu ya ji farin ciki da nutsuwa a maganganun Salmanu, ko bai samar masa mafitar da yake lissafi ba, tabbas yayi masa abinda ake cewa zoka ci tuwo yafi tuwon dadi. Da karamin kuzarinsa ya shirya ya dauki hanyar Zawaciki. Ba karamin girgiza Salamanu yayi da jin labarin da Adamu ya bashi ba, wanda bai rage masa komai ba tun daga kan kashedin raba sun da aka yi masa da kuma maganar aurensa da Salma da ake shirin yi nan kusa har ma da wayar da suka yi da Salma daga baya. Salmanu ya sake gaskata zaton da yayi wa Salma na cewa sihiri suka yi wa Adamu, ya fito fili kuma ya shaida masa cewa tabbas shi ya tare Salma yayi mata abinda ta fada ya kuma fadi dalilinsa na yin abinda yayi, ya kare da cewa, 74 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA. 2 "Ko a jikinka yakamata ka ji sauyi, in ba rami babu abinda zai kawo rami. Ko Husa da kake so da gaske don Allah kana yi mata barin jikin da kake wa Salma idan ka ganta?" Adamu babu bakin Magana sai kallo. Salmanu ya dora, "In mun nutsu dole mu karya asirin da suka yi maka, ni ban yarda abinda ke faruwa daga Allah ba ne" Adamu yayi kasake kamar ba zai tanka ba, amma cikin yanayin kuluwa sai ya kada kai, "Ka zauna kai ka nutsu, ni kuma zan san abin yi Salmanu ya dan yi nazarin Adamu da kyau, sannan ya nisa y аce, "Babu laifi, amma dai duk abinda zaka yi kar na ji ka a wajen Malam-Na-Allah, don na san kai duk duniyar nan ba ka da malamin da ka amincewa kamarsa" Haushi ya cika Adamu, amma dai bai tanka ba. Shirun da yà yayi ya tabbatarwa da Salmanu wajen nasa zai je in dai har.zuwan da 75 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 gaske ne, dole ya shiga tunanin hanyar da zai tankwabe shi. Da kokarin tunanin mafitar ya basar da shi, "Ka zo mu yi katangar nan ta cikin daki, yakamata mu kammala duk wani gyara kafin mu fara aiki" Bai jira cewarsa ba ya bar falon zuwa cikin tafkeken dakin ya hadu da samarin da suka gayyato taya su aiki. Adamu ba shi da zabi, dole ya watsar da tunani da damuwa ya bi Salmanu, don yana jin in bai yi wasa ba haukan nan dab yake da fara sanya shi zabura. Sai dai fa ya kudure a ransa dole ne da yamma ya halarci gurin Malam-NaAllah. Salmanu ma ya kudure a ransa, duk runtsi ba zai sake Adamu ya kubuce ya je gurin Salma kamar yadda yayi mata alkawari ba, saboda haka ya dinga kaffa-kaffa da shi bayan ya sace wayarsa ya kashe. Daga bisani ma sai yayi masa dabarar cewa shi zai raka shi wajen Malam-Na-Allah su kai masa kuka. 76 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 Haka kuwa aka yi, karfe shidda na yammacin Ranar suka kwashi jiki suka tafi Warure. Komai a gaban Salmanu aka yi, abin mamaki Adamu bai kawo maganar Salma ba sai ya kawo maganar neman kudinsa da neman dafa'i. Malam kuwa ya sake dankara masa wurudi mai zafi, ya kuma sanar da shi a yau ba gobe ba in yayi wurudin Aljanin kudin zai zo masa ya nemi bukatarsa. Salmanu da kansa ya zube wa Malam - sadaka suka fice, a nan ne ya tambayi Salmanau, "Mun yi da kai zaka kawo matsalar Salma da Husna, me yasa ka kawo zancen kudi wanda muka kamo hanyar samunsu?" Cikin yanayin tabbaci Adamu ya kada kai, "Tun da sanyin la'asar ya busa na dena jin matsalar Salma a matsala, har wacece ita da zan aura dole?. Na ga shegen da zai aura min ita Salmanu ya kada kai cikin jin dariya amma ya hadiye, ya ce masa, "To Husna fa?" 77 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 Nan ma cikn yakini Adamu ya amsa, "Ban taba cire yakinin zan auri Husna ba, ina jin kuma na fada maka dalilin" Salmanu ya kawar da kai kamar babu wata a cikinsa, "Ai shikenan, ka je ka yi wurudin neman kudi ka kira aljan, in na ga ka samu kuma ka wuce lafiya sai nima na biyo hanya ko don kar ka canja ni daga zama abokinka idan ka yi kudin" Ya kare zancensa cikin dariya. Adamu ma ya dara. Salmanu ya sake cewa, "Ka san abinda za'ayi?" Adamu ya girgiza kai. Salmanu y ace, "Don ma kar Salma ta biyo ka gida ta shammace ka ka zo mu je gidanmu mu kwana" Da sauri Adamu ya dube shi, "Wanne gidan naku?" "Wajen sana'armu nake nufi, ka ga cikin dare kai kana wurudin neman kudinka, ni kuma ina yi mana na neman tsari da 'yan sa ido, kodayake babu ma wanda ya san cewa ko 78 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 ta silar sana'ar taka zamu samu kudin da wurudin naka ya samar" Adamu ya dan yi jimami kafin ya amince, ya ce, "Ni fadan Hajiya nake tsoro" Salmanu ya shiga rarrashi, "Kar ka damu, ka san mu da dabara dole zamu san karyar da zamu kirkiro mata' Da wannan Adamu ya yarda suka koma Zawaciki. Kafin su isa magariba ta karato. Adamu ya tsaya masallaci, Salmanu kuma ya wuce gida a guje ya fara shirin zama aljanin Adamu na tsakar dare domin katange shi daga masifar da yake shirin jefa kansa. Salmanu ya tanadi fararen kaya da farin bokitin fenti mai murfi, hade da fararen rawani ya hada biyar guri daya sannan ya zauna ya nada wa bokitin fentin nan rawani tamkar wani jibgegen kan ifritu, yayi masa. Karamin masakali yadda zai hau kansa kai tsaye ya 79 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 zauna daram, ya nemo zabgegiya fara jallabiya da kuma dogon kwagiri, duk ya tura a sako ya fara jiran dare. Karfe uku na dare Adamu ya farka ya dauro alwalarsa, ya zo ya sha turarensa jiki da kuma carbi sannan ya fara aiki. Bai ja carbin nan ya kai kwaya dari ba, kamar daga sama ya ga dirar wata doguwar halitta mai rafkeken kai a gabansa, sanye da fararen kaya dogare da Sanda daya hannun kuma rike da wata shimfidediyar bulala. Tun yammar. Adamu ke gwajin yadda zai yi Magana da aljaninsa cikin kwanciyar hankali idan ya bayyana, tare da kwatanta yadda zai yi Magana da shi da kuma abinda zai nema a wajensa, ciki har da Husna, amma abin mamaki lokacin da aljanin ya afko sai da fitsari ya kubucewa Adamu, ya sunkwi da kai cikin ransa yana cewa, Na shiga aljanna na kasa fita. Yana ta barin jiki ba tare da razana ta bar Adamu iya kallon aljanin ko tanka masa ba. Aljanin ya saki tsawa cikin wata irin razananniyar murya, ya ce, 80 Maimuna Idris Sani Beli هر NA SHIGA ALJANNA...2 "Kai Bil adam, wa ya kai ka karambanin kirana?" Jikin Adamu ya kara daukar rawa, ya kara dukad da kai yana jan carbinsa yana kuma ambaton wurudinsa a fili. Aljanin ya sake daka masa tsawa, ya ce, Dan Fatalar Gyatumarka ba da kai nake Magana ba?" Yanzu Adamu ya daure ya amsa cikin harufa daidai ba tare da ya dago kansa ba, Ranka ya dade, wai so nake na kai adadin da aka ce sai na yi zaka bayyana da alheri...nag a kamar yanzu da akasin haka ka zo... a fusace kake." Adamu bai rufe baki ba aljanin nan ya daga shimfidediyar bulalar hannunsa ya zurara wa Adamu, nan take Adamu ya baje a wajen, yana shirin sumewa, Aljani ya sake daga bulalar yana yi wa Adamu tsawa, "Ba zaka fada min abinda kake bukata ba?" Adamu na neman rasa hayyaci ya ce masa, owak Ni bukatata kawai ka bace ranka ya idade 81 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 Adamu bai rufe baki ba Aljanin nan ya dinga shirgawa Adamu ba kakkautawa sai da ya tabbatar ya sume sannan ya kyale shi. A hanzarce Salmanu ya tube shigarsa yayi saurin kawar da su daga wajen sannan ya koma shimfidar da yayi wa Adamu basajar yana ciki yana bacci yayi kwanciyarsa ba tare da ya damu da halin suman da Adamu ke ciki ba ya hau shirgar baccinsa. Sai da sanyin asuba ya daki Adamu sannan ya farko cikin mawuyacin hali na ciwon jiki da razanar zaton Aljani na tsaye kansa, Ya dinga ihu yana hurwa da neman afuwa, tare da ambaton ya shiga aljanna ya kasa fita, a iyakar imaninsa wannan Kalmar zata iya kubutar da shi tunda Hajiyarsa ta sha gargadin sa cewa, Ya shiga uku, fata nagari lamiri, in ya shiga aljanna ya kasa fita ya fi masa. Salmanu na jin sa yayi mukus yana tuntsira dariya cikin mayafi. Adamu ya gaji da hurwa ya fara neman daukin Salmanu, cikin ihu da karaji, "Salmanuna Salmanuna! Ka tashi ka kawo min dauki ana zaluntata, wannan wane irin 82 Malmuna Idris Sani Bell NA SHIGA ALJANNA...2 mugun bacci kake, wane baccin asara yau kake alhalin ana hanyar kashe ni..." Jin dariyarsa na neman kubucewa ya sa shi ya bankade mayafi ya taso a gigice ya kunna fitila, "Adamu.. Adamu...haukan ne ya tashi? Mun shiga uku Adamu..." Adamu ya tattaro wasu mayun ashar ya aunawa Salmanu cikin neman dauke numfashi saboda wahala da fishi, bayan ashar din ya dora da cewa, "Kar ka kara kira mana shiga uku nan dan kaza-kazanka, kai dan iska ne Salmanu?

Chapter 3 of 6