Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 6
aką matsawa cin kashi?" Adamu ya kaşa hakuri sai da ya tambaya. A sanyaye Salmanu ya mika masa takardar yana sakin damarar da ya yi wa fuskarsa yana cewa, "A'a babu komai, karatun takardar ne ya fi karfina saboda da harshen Ingilishi ta 66. rubuta. Sai dai kai ka karanta mana 29 Maimna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 Kirjin Adamu ya barko wata shegiyar kara saboda jin wannan samu da rashi, shi ma ba iya turancin yayi ba, karatun da yayi duk bige ne, kuma tun tuni ya sha rantsuwar ba zai bata lokacinsa a boko ba saboda babu abincinsa a ciki, ban da gaisuwa da kananan kalmomin turancin yau da kullum da ake ji har a bakin wanda bai je makaranta ba ma bai san komai ba, saboda haka a kawo masa maganar ya karanta wasikar turanci ma ya zama.wani yarfa masa yaji a gyambo. Ya sauke wani irin gwauron numfashi ya ajiye takardar jiki a sanyaye ya koma ya hada kai da gwiwa. Salmanu ya cikin shiga mamaki kwarai, ci-da-zuci ya dafa kafadar Adamu y ace, "Ina fatan ba zagi ta antayo maka ba?" Adamu ya hadiye kunan ransa y ace, 2 "Ba na tsammanin zagin ne "Yaya baka tsammmanin zagi ne, baka karanta ba ne?" Salmanu ya sake tambaya a kagauce, Adamu ya daure dai ya fito da shi haske, 30 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 "Ni ma ban da gaisuwar sama ban gane komai a turancin nata ba" "Ba ta iya ba ko, amma dole sai ta yi mana fafa" Salmanu ya fada iyakar gaskiyarsa, don shi kansa bai san Adamu bai iya turanci ba, musamman dayake in yana Magana yana jefa na kare yawa. Haushin Salmanu duk ya cika Adamu fiye ma da haushin yadda ya kasa sanin menene sakon da masoyiyarsa ta aiko masa. Salmanu ya sake daukan wasikar da Adamu ya ajiye ya hau dabura karatunta a fili. Kawai sai Adamu ya ji kuka na neman kwace masa, amma ya daure ya hadiye shi ya fanshe da cewa, "Allah ka tsinewa wadanda suka kawo mana turanci suka ce mu dinga karatu da rubutu da shi, ko kowa ya yafe musu Allah ni ba zan yafe musu ba" 31 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 Salmanu ya saki takarda, dariya-dariya da kuka-kuka na damunsa, cikin hadiye su duka ya dubi Adamu ya ce, "Au ko kai ne baka iya turancin ba ne?" "Eh mana!" Adamu ya amsa a fusace. Kawai sai Salmanu ya saki dariyarsa son ransa. Ya dinga yi babu kakkautawa, tun tana kular da Adamu har shi ma dariyar ta fara kama shi ya shiga taya Salmanu har suka ci suka koshi sannan suka dawo neman mafita. kai, "Wai yanzu yaya za'ayi ne?" In ji Salmanu. Adamu ya dan ja fasali sannan ya girgiza "Ni wallahi gaba daya kaina ya kulle sai dai zuwa gobe" Salmanu ya fara gyara filonsa yana shirin kwanciya ya ce, "Allah tashe mu kalau, ko wani ne sai mu 99 nema ya karanta mana ya bayar mana da amsa A kufule Adamu ya tare shi, "Allah ya kiyaye, ai gara har in mutu ban san abinda ta rubuto ba..." 3 32 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 Shi ma Salmanu ya tare shi, "In haka ne babu wata mafita kenan" Adamu y ace, "Mu dai jira goben mu gani" ********* Hankalin Anti Sa'a yayi mugun tashi bisa labarin da Salma ta kawo mata, ta rasa inda zata bullowa lamarin ta wanke kanta idan dai har da gaske ne wani basa'iden ya gan su a gidan boka har ya fesa labarin yadda ya koma kunnensu, hukuncin da za'ayi musu shi ne kisa da wuka? "Anya ba hasashe ba ne kawai Adamu da Salmanu suka yi Salma?" Da ta gama walankeluwar hasashenta ta yi wa Salma wanna tambayar da safe. Salma har yanzu a tsorace take, don haka bata iya tankawa ba face ta dinga ringima kai kamar kadantare tana yarfe hannu, Anti Sa'a ta sake girgiza kai, "Ina shakkar hakan, amma dai zan yi kunar bakin wake in gwada wata dabara" 33 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 Salma ta dago ta dube ta cikin zare ido, baki na rawa ta ce, "Me zaki yi? A tsorace nake wannan maganar ta je kunnen Hajiya, ina da yakinin wani ne ya gan mu ya je ya fada. Ni dai na shiga uku, ban fara bin boka a sa'a ba....” Kawai sai ta zarce da shasshekar kuka. Wani mugun takaici ya tokare wa Anti Sa'a a makoshi, ta kashe Salma da harara cikin mugun kunan rai, "Ke fa wallahi wata muguwar jaka ce, in an hada abin kirki da ke sai. kin tankwabe kokari mutum..." Salma ta katse ta cikin goge hawaye, "Ni ba haka nake nufi ba Anti, kawai dai abin ne ya firgita ni kuma dole ma kin san na yi ta hasashen ta inda suka gano mu, bugu da kari ma ban sani ba maganin ya kama Adamu ko bai kama shi ba tunda har suka sami damar tattauna na yi masa asiri shi da Abokinsa, kalli lamarin da kyau Anti dole ne ya firgita irina" Anti Sa'a ta yi shiru tsawon lokaci, can sai ta mike ta tafi Dakin maigidanta tana cewa Salma, 34 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 "Bari na gwada dabarar da na ce miki zan gwada mu gani" Salma bata iya tankawa ba, illa ta bi Antin da kallo cikin shanye baki da bugawar zuciya. A mugun tsorace take, tana fargabar abinda zai bityo baya idan kwai ya fashe, akwai zallar kunya a ce wai ita ce budurwarta da ita kuma 'yar uwar Adamu a ce ta kai kanta gurin boka neman soyayyar saurayi, saurayin ma dan uwanta. Haba wannan abin kunyar har ina! Anti Sa'a ta sami Maigidanta kishingide yana hutawa, akwai alamun. hankalinsa a G kwance yake, don haka ta karawa fuskarta da furucinta nutsuwa, amma fuskarta a bace ta yi sallama, hakan ya sanya ya karkato da hankalinsa gareta fuskarsa babu yabo babu fallasa, C "Ke da wa na ga fuskarki da fishi?" Ta nemi kujerar da ke fuskantarsa ta zauna tana ajiyar zuciya, "Ba fishi ba ne 6acin rai ne Alh. wani ta'addanci Abokin Adamu ya kwaso ya kawo mana, wanda idan an bar shi ya sha gaskiya ba. a kyautawa kai ba" 35 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 Alh. ya tsura mata ido cikin kallon rashin fahimta, ya ce, "Abokin Adamu wanne, me yayi?" Kai tsaye ta amsa, "Ka san dai me ke tsakanin Adamu da Salma, yau ya kwaso soyayya ya ya kawo tnata, gobe idan sun yi fada y ace ya fasa haka su ke, dama dai shi ka san shi, kuli-kuli ne ba a gane gabansa. To kwanan nan sai ya fara maganar aure muna dai ta yi masa tsiya har ita Salman na cewa da me zaka aure ni? Ana ta wasa da raha, amma dai na fahimci shi wannan abokin nasa Salmanu ba son abin yake ba, ban dai san dalili ba,....." Alh. ya ji ya gaji da wannan dogon sharhin kafin furta laifin, kawai sai ya tare ta cikin tuna kaguwa da sikewa, "Bar wannan labaran don Allah ki fada min gudarin abinda ya faru" Nan da nan ta yi fuska ta furta, "Ai kai ka nake Alh. kawai jiya Salmanu ya fitar da maitarsa a fili, inda na aiki Salman gidan. Hajiya da dare ya makure ta a soro ya dora mata wuka a makogwaro yana tuhumarta 36 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 da cewa wai asiri tayi wa Adamu yake sonta,wai in ba hakan ba bábu yadda za'ayi Adamu ya so ta, wai in bata je ta karya asirin ba sai ya kashe ta Duk da maganar ta zo wa Alh. a ba zato kuma ta firgita shi, amma dole wani gurin ya bashi dariya, ya dan murmusa ya ce, "Yaya ba zai so ta ba, saboda ita ba mace ba ce?" Sa'a ya ji takaicin rashin daukar maganar da muhimmanci da bai yi ba, amma dai ta hadiye ta yi fuska tana dan taya shi dariyar a yake, ta cе, "To abinda na gani kenan Alh. salmanu dan iska ne kawai" Alh. yayi shiru cikin tunanuwa barkatai, shakkunsa shi ne, ya san Adamu da kyau, bai cika boye so ko ki ba, sun yi maganar Salma da shi ya nuna babu soyayya tsakaninsu, sannan duk labarin soyayyar Salma da Adamun da ake karade dangi da ita daga bakin Sa'a dai take fitowa kamar dai yadda ta zayyano yanzu, sai Alh. ya ji kansa ya kulle ya ma rasa abinda 37 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 ya kamata ya yi nazari a kai ko kuma ya maganta, sai ya ci gaba cikin shiru. Cikin bugun kirji Sa'a ta dube shi ta ce, "Alh. ka yi shiru" Ya dan yi murmushin yake, "Abin ne ya daure min kai, ribar me Salmanu zai ci in ya raba Salma da Adamu, kuma me zai rasa idan sun auri juna?" Sa'a ta kawar da kai tana dan bata fuska, "Oho masa! Ni ba abinda ya dame ni kenan ba, ni abinda ya dame ni shi ne ta'addancin da lamarin ya zo das hi, Alh. dole ka dau mataki gaskiya" In Sa'a ta yi irin wannan bata ran Alh. ya sani bata bukatar musu, abinda take bukata kawai shi ne a aiwatar da abinda ta nufa. Вa wai in bai aiwatar din tube masa jiki zata yi ta zane ba, a'a kawai shi ne yake jin ba daidai ba ne ya ki bin umarnin nata ko aiwatar da abinda take so, don haka kawai sai ya kada kai cikin sanyin jiki, "Ai dama zan dau mataki, raba su ma zan yi gaba daya 38 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 "Yauwa yanzu na ji Magana Alh. shegen yaro kawai ya gagari iyayensa sun sallama shi mu zai shigo namu dangin mai doka da oda ya fata mana tarbiyya" Ta fada cikin jin dadi da karsashi saboda yakininta na sanin mijinta, tabbas zai dau matakin kamar yadda ya sanar. Suka yi shiru tsawon lokaci su duka kowa da sakar zuciyarsa. Alh. ba a son ransa zai shiga lamarin Adamu ba, domin tun lokacin da ya nuna masa iyakarsa akan karatunsa yayi niyyar fita harkarsa har sai duniya ta jima shi ya nemo shi da kansa, to amma Iyalinsa ta shiga lamarin, shi kuma ba ya iya ja da abinda ta zo da shi, kenan a dole zai bi. Ita kuma Sa'a tana can duniyar shirya yadda zata bullowa da Alh. dabarar yadda zai tunkari Adamu da batun auren Salma, ta saka wannan ta kwance ta kulla wannan, har dai a karshe ta zabi fadin abinda ya zo bakinta. Cikin dakewa ta daga kai ta dube shi, "Ni ina ganin me zai hana ka tuntube shi, in suna son juna kawai ayi abin nan mu huta, sai ka sami 'yan wasu kudi masu kauri ka bashi 39 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA.. 2 ya ja jari tunda ya ki karatun ai bzi kamata a bar shi ya lalace a banza ba, yana faman bin 'ya'yan iska irinsu Salmanu" Game da maganar bayar da jari ya ga gaskiyarta, don shi kansa ya lura Adamu ya kama turbar lalacewar tunda ba shi da abokin da ya wuce Salmanu, kullum kuma sai an gan su sun sha wanka sun fice tare, to amma batun a yi masa maganar auren Salma shi bai ga dabara ba don yayi masa maganar kuma bai ga wani hasken son salma a fuskar Adamu ba, sai dai ba yà son gwale Sa'a, don haka ya dan gyara zama ya cе, "Haka ne, ni ma na lura ya dauko turbar lalacewar, dole hannunka ba zai rube ka yanke ka yar ba, zan yi wani abu akan sana'ar tasa, maganar Salman ma zan kira shi mu yi maganar. Ni abin ne yake ban shakka, ranar da na yi masa maganar ba ki ga bakar maganar da ya zabga min ba, kin dai san shi" Ta yi fuska ta tare shi, "Alh. in kana shakka ka hada su tare ga shi ga Salman, ai maganin karya hallara" Cikin fuskar jimami ya girgiza kai, 40 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 "Ni ba nufina kenan ba, ba na son shiga shirgin da zan zama karamin mutum, shi Adamu ba ya jin komai in yayi karanta, ba zai ji kunyar in na hada su gabana ya keta idon Salman y ace ba ya sonta ba, ai kin ga in an yi hakan ba a kyauta ba" Ya kare da zura mata ido. Ta tamke fuska ta shiga kallon gefe, ba tare da ta tanka masa ba. Dole ya saki nasa ra'ayin ya bi nata ta hanyar kada kai cikin sanyin jiki ya ce, "Amma shikenan yadda kika fada din haka za'a yi, ki sanya Salman ta kira min shi a waya" ******** Salmanu ba yadda bai yi da Adamu kan su je su sami wani ya karanta musu wasikar Husna ba amma fur Adamu ya ki, a cewarsa cin amanar kauna ne wannan ya kai wa wani ya gane masa sirrin mata, ya kara da cewa, "Kai ko surar zagi Husna ta sauke min a wasikar nan cin amana ne na kai wa wani ya 41 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 karanta min, ni a wajena daidai ne da na bashi damar ya kare mata kallo ita Kanta..." Salmanu ya tare cikin mamaki, "Zagi fa ka ce? In nine duniya zan nunawa don in na rama kar san zalinci na yi" Kai tsaye Adamu ya amsa, "Kai da idan ta zage ka zaka dena sonta kenan, ni zaginta gareni ba zai rage komai a son da nake mata ba shiyasa in na tona sirrinta nake jin So ba zai yafe min ba" Cikin dariyar keta Salmanu y ace, "Shikenan ina jiran ganin ta yadda zaka kwaci kanka, ka san me ke cikin wasikar har ka sami damar bada amsa" "Don amsa zan bayar da amsa, ka zuba ido ka sha kallo malam, cutar da aka min daya ce, kawai ban san me ta rubuto min ba, ko zagin ne hakika in a son in sani" In ji Adamu. Salmanu ya ce, "An ji an cuce ka baka san abinda aka rubuta ba, ni kuma ina nan ina jiran ganin yadda zaka amsa alhalin ba ka san abinda aka rubuta ba" 66 42 Maimuna Idris Sani Beli fita. NA SHIGA ALJANNA...2 Adamu bai tanka ba, kawai ya mike ya Salmanu ya bishi da mita, "Malam kar ka dade, yau yakama ta muje da wuri mu kammala shirya gurin nan, na fada maka mun baza neman kostomomi daga jibi Kila zamu fara zama" Adamu dai bai tanka ba ya fice abinsa ya bar Salmanu na dariyar shegantaka. Sawon mintuna goma sai ga shi ya dawo rike da Biro da doguwar takarda. Ya nemi guri ya zauna Salmanu na bin sa da Ido, "Wato kintatar amsa zaka yi ka bata kenan?" Adamu yayi fuska ya zura hannu a aljihu ya dauko tiger balm sabo a takardarsa, yana cewa, "Ka tsaya ka yi kallo kawai, yadda ta sa ni a duhu wallahi sai na sa ta ba tare da ta canki yarenta ne ban gane ba" Har yanzu Salmanu bai fahimci inda Adamu ya dosa ba, yayi sakare yana kallonsa yana farke takarda taigan, ya kasa hakuri sai da ya ce masa, 43 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 "Wai man zafin zaka shafa a takardar maimakon ita da ta feso turare?" Adamu ya ki tankawa face ya cigaba da aikin gabansa, wato zaro takardar bayanin da ke kunshe cikin taiga wadda ke dauke da rubutun yaren China ya gwafe ya fara kwafewa a doguwar takardar da ya shigo da ita. Sai yanzu Salmanu ya ankare, ya saki ihu yana kai wa Adamu bugu, ya ce, "Shegen kasa! Wato yaren China kai kuma zaka yi mata idan ita ta yi maka turanci ko?" Adamu ya saki dariyar keta ya се, "Ashe ka gane, idan ita gama-garin yare take ji wato turanci to ni ina jin wanda kila a fadin Najeriya ba mu kai mu dari ba?" "A hasahenka kenan" Salmanu ya fada cikin tsananta dariya, shegantakar ta Adamu ta yi mugun birge shi, salin alin ya kubuta daga tozartar bai iya turanci ba, kuma ita ma Husna ya sat a a kwanar bat a iya cainanci ba, yana da tabbacin gaba ba zata yi gigin sake rubuto wa Adamun 44 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 takarda da turancin ba don kar a bata amsa da yaren da bata iya ba. Adamu ya kwafe takarda tsab yayi mata kyakkyawan ninki ya nade a enbilof hankalinsa a kwance, in dai wannan tararradin amsa wasikar ne ya gama da shi, sai dai ya jira wata, wadda yake da tabbacin da yaren da zai iya zata iso. Sun karya kumallo suna ta tattauna zancen cikin dariya, a fakaice Salmanu na yi wa Adamu hudubar kwantar, da hankalinsa ya manta da wasu mata ya kama sabgar gabansa, ya ce masa, "Ka manta da su, ka nemi kudi, wallahi in ka same su mace sai ka ture....." Cikin kada kai Adamu ya tare shi, "Husna nake so ba mace ba Salmanu" Salmanu ya ce, "Na sani, ita ma din cikin sauki zata zo in dai kana da dan karansinka a aljihu. Abinda nake so ka gane shi ne, sana'armu tana son nutsuwa da kirkirar basaja da dabaru, in kuwa ka cunkusawa. kwanyarka mata don Allah 45 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 yaushe zaka sami nutsuwar aiki bare tuna abin kirki? "Ba don Adamu ya gamsu ba said an gajarta zancen ya kada kai, "Babu laifi zan kwatanta, musamman dayake daga yau ma zaman kashe wando ya Kare" "Yauwa ashe ka gane" Salmanu ya fada da farin ciki. Suna shirin fita sai ga wayar Salma, da Adamu yaga sunanta sai da ya ji gabansa yayi mummunan faduwa. Cikin wani irin barin jiki ya daga wayar muryarsa na rawa y ace, "Ran Gimbiya ya dade" Salma ta ji kamar an tsoma ta a ruwan sukari, ta saki wata ajiyar zuciya, fargabarta da tsoronta suka gushe, a ranta ta raya, cib! Ashe har yanzu maganin na aiki! Amma a fili sai ta tausasa murya ta се; "Wacce ni ni mai ido ba dan ciki?" Da sauri Adamu ya katse ta, 46 Maimuna Idris Sani Beli 3 NA SHIGA ALJANNA...2 "Da gaske wallahi, ai ni kin fiyc min duk matan duniya? Dadi ya sake kashe Salma, ta sauke katuwar ajiyar zuciya ta ce, "Kamar gaske" "Me zan yi ki yarda da ni? Ya tamabaye ta cikin raunin murya. Ta dan ja fasali sannnan ta amsa, "Mu bar maganar, yanzu dai kiran ba nawa ba ne, Alh. ne ya ce na kira ka, wai ko me kake yanzu ka katse shi ka zo" Adamu ya dan yi dum! Ransa bai so wannan titsiyen ba, sai dai ba shi da zabi tunda ta bangaren Salma kiran ya biyo, ba don haka ba wallahi mazewa zai yi. Duk da haka said a ya dan tirje. "Kash! Anya ba zan share kiran nan ba sai na dawo? Ina da wani uzuri wallahi" Kamar Salma zata biye masa saboda rashin son bacin ransa, sai kuma ta ji yakamata ta motsa kwanjinta akan sa, cikin basarwa.t ace, "Haka dai zaka daure ka zo, in ka zo ma ai ma samu mu gaisa". 47 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 Nan da nan ya amsa, "To babu laifi zan zo yanzu tunda ke ma kina son ganina" Ta sha mur ta sake cewa, "Yauwa kar ka dade" "In Allah ya so ba zan jima ba" Ya sauke wayar tare da sauke ido akan Salmanu, "Salma ce ta ce Alh. na kira na yanzun nan, ka zo mu je sai mu wuce daga can" Ran Salmanu yayi mugun baci, ya dorawa Adamu Ido tsawon lokaci sannan ya girgiza kai, "Ka na rawar kafar tafiya ka je. ne don Alh. ne yayi kiran ko kuma don Salma ce ta zo da sakon kiran?" Abin tausayi sai Adamu ya yarfe hannu a sanyaye ya ce, "Ni ma ban sani ba Salmanu" Wani haushin ya sake cika Salmanu, amma dai bai tanka ba sai yayi zuguri yana kallon Adamu. 、 Adamu ya figi mukullin dakin yana yafitarsa, 48 Maimuna Idris Sani Beli "Zo mu NA SHIGA ALJANNA...2 je mu da sauri mu gama da shi mu wuce don Allah, ko wacce tsiyar ma zai min oho masa" Salmanu da yake tsakiyar shaka ya fashe, "Ni fa ba zani ba, kawai ka je in kuka gama ka same ni a can" Jikin Adamu yayi sanyi, ya dan yi saroro yana kallonsa, sannnan ya ce, "Ko gidansu Husnan ba zaka raka ni kai takardar nan ba?" Salmanu yayi fuska, "Kai da zaka gidansu Salma me zaka je yi gidansu Husna?" Adamu ya debo murmushin yake ya sauke, "Ka manta ni mijin mata biyu ne? ai kayan nama ba ya kasha kura" "Sai ka je ai kai daya, don ni kyanwar lami ne ko 49ay bana ci bare naman" Bai jira cewarsa 49ay a kada kai yayi tafiyarsa. Adamu ya girgiza kai yana murmushi ya janyo kofar dakinsa ya garkama mata mukulli 49 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA.2 sannan ya shige cikin gida domin yi wa gyatumarsa sallama. *********** Salma na sauke waya ta saki ihu ta bazama dakin Antin Sa'a tana bat a labarin yadda aka yi. Anti Sa'a bata yi mamakin abinda ta ji ba domin ita tayi wa aikin bokanta farin sani, ta jima da imanin ko ba dade ko ba jima sai Adamu ya kamu a tarko Salma kirif! Ta nuna jin dadinta ainun Sannan ta cewa Salma, "Kin san Allah? Da mun sani ma ba mu shigo da Alh. cikin maganar nan ba, ke kanki kin isa raba raba Adamu da Salmanu, Na rantse miki da Allah idan kika ce kar ya sake kula shi sai ya hanu" Salma ta cika da jin mamakin jin abinda Antinta ta ce, cikin sakin baki ta ce mata, "Da gaske Anti?" Sa'a t ace, "Har fa rantse miki na yi" Salma ta rausaya kai, 50 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 "Ai al'ajabi ne yake neman kashe ni, yanzu duk fandarar Adamu zan iya dankwafewa?" Sa'a ta jinjina kan jin dadi hirar, ta ce, "In kina shakka ki gwada daga kan maganar Salmanun nan, kar ki bar shi da maganar Alh. da zai iya watsarwa idan ya tashi daga gabansa, ki shiga maganar zaki ga abinda zai faru" Salma ta kasa Magana sai jínjina, kai kawai, lamarin ya girmi tunaninta, in a da can wani ya sanar mata Adamu zai iya zama haka a hannunta-zata musa masa ko da kuwa tsafe shi za'a yi ba wai karamin alhaki boka ba. Babu fargaba ko kadan a tare da Adamu ya shiga falon Yayansa domin dai shi ya san bai yi komai ba bare ace akan sa aka kira shi a balbale shi da fada, amma ga mamakinsa Salma na shigowa dakin ita ma ta zauna sai ya ji gaba daya kwanjinsa ya zube, ya dinga jin rashin katabus hade da faduwar gaba 51 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 musammman da ya saci kallon Salma ya gán ta tana kuka, sai ransa ya ji a duniyar nan bai taba cin karo da wani abu mai ciwo irin zubar hawayenta ba, amma dai haka ya daure ya sunkwi da kai gaban yayansa wanda ya dauko jawabin da ya fi zubar, hawayen Salma buga masa zuciya, "Da kai Salmanu ya hada kai ya kawo mana ta'addanci gida? Kana sane da ya tare Salma jiya ya aza mata wuka a makogwaro yana mata kashedin ta fita hanyarka" Adamu ya ji kansa yayi masa wani mugun nauyi, da kyar ya cire kai ya dubi Alh. sannan ya mayar da ganinsa ga Salma wadda ke ta. faman matsar hawayen karya. Da sauri ya girgiza kai ya ce, "Salmanun? Wallahi ban san da maganar ba Alh." "To yanzu ai ka sani" Alh. ya fada cikin daure fuska. Adamu bai damu da cin maganin Alh. ba shi ta masoyiyarsa Salma yake, wadda yake jin kamar ya shiga zuciyarta ya sanyaya mata rai ya hana ta kukan da take, ko kuma ya nuna 52 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 mata lallai ba da hadin kansa aka cutar da ita ba kuma ba za a taba hada kai da shi a cuce ta ba bare har da hukuncin dora mata wuka a wuya, shi mai dora mata wukar a wuya ma ya gani ba sai inda karfinsa ya kare ba ko kuma ayi mutuwar kasko. Cikin mugun sanyin jiki ya mayar da kai ga Alh. ya се, "Wallahi Alh. ba ni da masaniya, to wai laifin me tayi masa da har zai tare ta da wuka kamar wani shirin fim?" "In kana shakkar karya ta yi masa ai ga ka יי nan sai ka tambaye ta... A ladabce Adamu ya tare shi, "Ni ba haka nake nufi ba Alh. tsabaragin beken Salmanu na gani da haukansa wai zai zuga shi tare mace da wuka, macen ma wai Salma wadda ya san dangantakata da ita" "Kila sholishon nasa na sabo ya sheka" Alh. ya fara sakkowa saboda imanin da yayi babu hannun Adamu a abinda Salmanu yayi tunda yake wannan fitittikewar, sai ya hau bashi labarin abinda ke akwai kamar yadda Sa'a ta sanar das hi, ya karkare da cewa, 53 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 "Ni mamakina shi ne, menene ribar Salmanu in ya raba ka da Salma? in kuma ka aure ta me zai rasa?" Adamu ya rausaya ka, ya rasa abin cewa, a can cikin kansa ya ji wata shegiyar gada ta barke, ya rasa me ya tashe ta, amma dai haushin Salmanu ma ya kunno, don ya ji mugun ciwo abinda yayi, ji yake kamar ma abotarsu ta zo karshe daga yau din nan. Yana can duniyar tunani da lissafi ba ya tare da dogon sharhin da Alh. ya kunno wanda yake nufin lallai ya fita hanyar Salmanu ba mutumin kirki ba ne, kuma dama hausawa sun ce zama da madaukin kanwa yana kwo farin kai, lallai ko yanzu bashi da irin tarbiyyar Salmanu idan suka cigaba da tafiya nan gaba za a wayi gari babu abinda ya bari na batattun halayen Salmanun. Alh. ya karkare da cewa, "To ka fita hanyarsa, kar na sake ganinka da shi, in ba haka ba ranka zai yi mummunan басі" Adamu bai ji komai ba a kokarin raba shi da amininsa da ake, shi ma haushinsa ya ji 54 Malmuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 sosai don bai ga dalilin wannan danyen hukuncin da Salmanun yayi ba. Hankalinsa ba sosai yake tare da Alh. ba yana can ga Salma da tayi kicin-kicin cikin hawaye, A dan raunane ya ce mata, "Wai da yaushe ne hakan ta faru?" Sai da tayi ta faman goge hawaye sannan ta amsa, "Jiya da dare ne ya kira ni a waya ya ce min kai ne baka da lafiya wai na zo da sauri" A rikice Adamu ya cе, "Kin gani ko? Ke ma da laifinki, ko nine babu lafiya me ya kai ki fita da dare? Lallai Salmanu ya isa makiri" Babu wanda ya tanka tsakanin Alh. da Salma. Salma goge hawaye take amma tsakiyar zuciyarta bata taba samun kanta da farin ciki irin na ranar yau ba. Alh. kuma kallonsu kawai yake cikin nazari, sai yanzu ya gaskata maganar soyayyarsu da ya sha ji a bakin Sa'a. cikin ransa sai yaji gaba daya haushin Adamu da yake ji ya gushe, ya ji ma kawai ya yafe masa bata masa ran da yayi a kan maganar karatu. 55 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 Cikin ransa yayi ta bitar Allah ne kadai ya san abinda ya boye game da lamarin, aurensu zai masa dadi don shi dai yana alfahari da auren zumunci, ya gwada ya ji dadinsa, abu na biyu kuma shi ne, auren nasu zai farantawa Sa'a rai, don

Chapter 2 of 6