ka
gabana, amma abinda ya fi damuna shi ne
ganinka hankali a tashe, wai a haka ka taho tun
daga gidanku?"
Kulawarta ta sa ya dan sami karfin
gwiwar kada kai yayi murmushin yake,
"Ban ji nauyin ki gan ni a haka ba sai
wasu mutane?"
Ta kaďa kai ba don gamsuwa ba sai don
son ta yi masa gwaninta,
110 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
"Na ji, me ya faru?"
"Bai yi kasa a gwiwa ba ya amsa mata,
"Burikana ne suka tarwatse a kasa, na san
in na tsinto su ba za su yi miki kyau ba, ba zasu
dace da irin son da nake miki ba... shi ne
kawai na debo tsawo na zo neman afuwarki,
son da na yi miki ba tare da na samu ba"
Husna bata fahimci komai a maganganun
Adamu ba sai ba zata same shi ba, cikin kura
masa ido ta ce,
"Dan kara bayani ko zan fahimce ka"
Kai tsaye ya amsa,
"Na jima ina sonki baki san ina yi ba,
ranar da Allah ya hukunto kuma zaki sani sai
aka yi fashin zuciyata da makami ba tare da
imani ba, abinda ya faru da mu a ranar nan
babu shi a tsarina, kawi mafarki ne daga cikin
munanan mafarkai..."
"Wacce ranar"
Ta tare shi cikin ci da zuci.
Adamu ba ya son hada shirgin lissafinsa
da waccan ranar, ba ya son tuna ta kuma baya
son abinda zai tuna masa ita, amma tunda shi
111 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
da zuciyarsa ba sa zuwa wajen Husna da wasa,
sai kawai ya ji ya amsa mata kai tsaye,
"Ranar da kika kawo min dinkin nan na
bayyana miki abinda ke zuciyata game da ke,
zuwan Salma kuma ya sanya na rusa abinda na
fada da karfin hali ba da karfin imani ba...
wallahi bakina karya yayi min Husna ban tabа
son Salma ba, ke na taba so son da ban taba yi
wa ko wacce mace irinsa ba..."
So da tausayi da rashin madafa sun fara
gajiyar da Husna dole ta dakatar da shi, cikin
sanyin muryar da ta 6oye ciwon ranta,
"Kar ka damu da abinda ya faru ran nan,
ni tuni ya wuce a gurina"
Adamu ya mike cikin rangaji ya fara dan
kai komo a gaban Husna kasancewar soron
gidan nasu yana da yalwa.
Idon Husna na kansa bata ko dauke fuska,
kwayar idon nata na nuna jiran furucinsa take
amma a zahiri lissafin yadda zata nada
gammon daukan jidalin rasa shi take, tana son
Adamu irin Son da ba ko wane mutum ake wa
ba, kai ba ma ko wacce irin zuciya ce yi ba, sai
112 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
irin Adamun na musamman da irin tata zuciyar
ta musamman.
Adamu ya dage ya tsayar da hawayen
fuskarsa ya kuma kawo wa fuskarsa jarumta,
sannan ya daga ido ya kalli Husna. Suka dubi
kwayar idon juna tawalli! Sai duk wata shakka
ta debe musu, Adamu ya fara jin yayi Magana
cikin kwarin gwiwa da zallar gaskiya, Husna ta
fara jin sauraron Adamu cikin yakini da
gaskata shi.
"Furucin da na yi rannan a gabanki a
gaban Salma ya tabbata, bayan balaguron da na
yi na sati guda, a yau na dawo na tarar an daura
min aure da Salma, yanzu na kawo kokon bara
ta gurin ki, ki ba ni dama na tafi, amma idan na
dawo da wani karfin gwiwar don Allah ki
karbe ni a haka ki yi maneji da ni"
Ba don idanuwanta da ke kallon Adamu
tsaye gabanta ba, da kuma iskar da take shaka
mai alfarma Adamu na shaka ya fesar ba ce, jin
wannan labarin ya isa kai Husna kasa, amma ta
dake tana kallo Adamu cikin rashin hayyaci
wani malalcin hawaye na sirnano mata.
Ta ci guru da kyar ta tanka masa,
113 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
"Allah sanya alkhairi"
"Ban fada don ki yi min addu'a ba, na
fada ne don ki san abinda na tawaye ki da shi
na auren wata alhalin ke nake so, na fada ne
domin ki ji tausayina akan kaddarar da ta afko
min, na fada don in kin yarda kaddarar ce ki
karbe ni a haka ki yi maneji da ni..."
Ya fada cikin son koma wa hawayen da ya
baro.
Husna ta sake cin wani gurun ta girgiza
kai.
"Ai duk ba zasu gagara ba. Yanzu me ka fi
bukata daga gare ni?"
Ya karaso gabanta murya kasa-kasa ya
amsa mata,
"Nan da wata biyu zaki karbe ni a
matsayin miji?
Wata rahma ta tsirgowa Husna tun daga
Kolin ka har yatsan kafa, amma dai ta shanye
nunawa a fuska bare barin jiki. Cikin nutsuwa
ta gyada kai,
"Ina jiranka"
"Da gaske kike?"
A rikice Adamu ya tambaye ta.
114 Maimuna Idris Sani Beli
$
NA SHIGA ALJANNA.2
Tayi murmushin da ya fi kama da yake, ba
tare da ta tanka ba.
"Na gode"
Adamu ya dinga ambata cikin kada kai har
bai san adadi nawa ya fada ba, sannan da baya
da baya ya dinga tafiya yana godiyar har ya
fice daga soron cikin daga mata haninu.T
Sai da ya gama ficewa sannan Husna ta ji
kukabya zo mata a guje, tuni ta durkushe a
gurin ta soke kai a gwiwa tana kokari hadiye
Kararsa. Jin zuciyarta take kamar an bulbula
fetur an kyarta ashana***
E sWannanwaneinsirin.arsoswne keshan
sharafinsa a Kirjinta? Wa ya taba irinsa ya bata
labari? Jiya ta gama karatun wani littafi wai shỉ
Mafarkin Khadija, tá rantse a fili ta rantsea
zuci son Adamu da take ji cikin ranta ya ninka
wanda Khadija jarumar littafin ke wa mijinta
Sunusi. on ide sos idavad sisd it sy sbridA
Ta ci kukanta as soro ta koshi sannan ta
goge ido jiki a sabule ta ikinkimi kujera da
tambulan ta shiga gidasusd osanew isb ni"
"B2 Idono Hajarai karaf al kantadlokacin da ta
janyo ruwa ta hau wanke fuska,
115 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
"Kar dai ke ma zuwa kika yi ku ka haďu
ku ka yi ta kukan?"
A kufule Husna ta masa,
"Kuka mu ka yi amma ba ki jiyo
tumaminmu ba?"
Umma ta wuce tana ce mata,
"To uwar bakar Magana, in ma
haukacewa kuka yi ai ku ta shafa"
Husna ba ta tanka ba, don dama don ta
kashe bakin tsanyarta ta fada mata haka.
Yana fitowa masallaci ya canja riga ya fita
ba tare da ko sallama yayi wa Hajiya wadda
sarm bata yi kwanan kwanciyar hankali ba
saboda halin da ta ga Adamu ciki, jiya ko
abincinsa bai karba ya ci ba, illah dai ta san a
gidan ya kwana.
Abinda ya fi bata haushi ma shi ne, da ta
kira Alh. ta yi masa wannan korafin sai ya
nuna halin ko in kula.
"In dai wannan banzan yaron ne mai halin
canje-canje ki bar shi kawai, ni ne maganinsa"
116 Malmuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
Kalaman da ya fada mata kenan wadanda
haushi ya sanya ta shiru ba don wai ta sallama
ba.
Da safe ta yi ta zuba idon ganin shigowar
Adamu bayan dawowarsa masallaci sallar
asuba kamar yadda ya saba, sai ta ji shiru.
Haka ta zauna cikin fargaba da ci-da-zucin
kallon kofa har hantsi ya daga bata ga Adamu
ba, ta lallaba ta je dakinsa sai ta tarar a
garkame da kwado, nan fa ta fara tsoron ko ya
koma gidan jiya ne, sai sannan ma ta tuno ko
tambayarsa inda ya shiga tsawon sati ba a bata
damar ta yi ba.
Da hantsin Alh. da kansa ya kawo mata
abinci. Ya gan ta cikin rashin walwala amma
sai ya share don ya san tatsuniyar gizo bata
wuce ta koki.
"Daga nan dorayi zan wuce"
Ya kamo bakin zarenta da haka bayan ya
lura cin maganin nata yayi yawa.
Ta motsa baki da kyar t ace,
"Me zaka yo?"
Ya amsa mata
117 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
"Gidan da wadancan yara zasu zauna zan
sanya a yi wa gyara, Adamu gata yayi masa
yawa, jiya na yi masa maganar ya karbi
mukullin ya je ya dubo... kai har maganar
kudin da nace zan bashi ma bai bi ta kai ba, na
66.
rasa wane irin yaro ne Adamu...
Haushi ya hana Hajiya barinsa ya kai
karshe,
"Idan bai koma inda ya fito ba ko? Ni tun
safe ban gan shi ba"
"Zai dawo ne, ai giji lahira ce"
Alh ya fada cikin halin ko. in kula don ya
fahimci Hajiya bayan Adamu take son bi akan
maganar auren nan, shi kuma jin kansa yake
akan maganar auren nan babu wanda zai
saurara ya tankwabe shi.
Jin hakan ya sanya Hajiya jan bakinta ta
tsuke, don dama ita mace ce mai kawaici da
hadiye damuwa, in dai ta lura za a daga matahankali sai ta sakar wa mutum.
Alh. ya gama kame-kamensa ya mike
yana ce mata,
""Dorayin zan je na kula da komai, har
kayan shagon zan siyo komai in zuba masa,
118 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
Allah basshi idan ya zo in ba zai gode min ba
ya tsine min"
"To Allah tsare"
Hajiya ta fada a gajarce.
Adamu ya tarar Salmanu ya ci Make Up
ya zama rikakken boka yadda in ba su da suka
yi masa farin sani ba kuma suka san dawan
garin ba, ba za a gane shi ba.
Yayi tirgijijin a cikin rigunan shudin saki
hade da wando, an masa tafka tafkan kwalen
farin fenti da ja a goshi da kunci, haka ma
kansa ya sha askin kwalkwal an adance shi ta
tattoo din kan mutum. Salmanu ya canja kala
daga Salmanu zuwa wani shaidanin boka duk
aikin Tanimu ne.
Suna tsaye da Tanimu yana yi masa
lissafin mutanen da ya gayyato masa yau
Salmanu ya shigo,
"Ka ga akwai matar Aramman
unguwarmu, wai ta ji labarin zai dauko uwarsa
daga kauye, uwar tasa kuma muguwar
119 Malmuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
masifaffiya ce ga jarabar sa ido, shi ne wai take
so ta zo a toshe zuciyarsa a hana shi kawo
ta....
Salmanu ya tare shi cikin yamutse fuska,
"Matar Alaramma kuma Tanimu zaka
kawo mana? Mijinta malami sannan kuma na
san ba karafa garesu ba, mu fa manyan harka
mu ke so
Cikin tsananta dariya Tanimu ya tare shi,
"Kai matsalarka gajen hakuri aradun
Allah, yo malanta ba yana kan tasa kujerar ba
ne kai kana taka?"
Salmanu ya sake tare shi rai a bасе,
"An ji, ni fa ba zan yi harkar naira hamsin
ko dari ba"
"Shiyasa ai na ce ka fiye gajen hakuri, in
ka ga dama idan ta zo ka caje ta dubu talatin,
na rantse da Allah zata baka... abincin siyarwa
fa ta ke, duk eriyar nan ba kamarta, motar doya
ake sauke mata duk wata, buhun shinkafa
kuma kwana biyu yake mata. ay amise
Fuskar Salmanu ta washe,
"A zamu tafi da ita, ta zo kawai"g
Suka tuntsire da dariya suka tafa. gg
120 Malmuna Idris Sanl Bell
NA SHIGA ALJANNA...2
Tanimu ya cigaba,
"Sai Alh. Habu mataimakin sakataren
kamafanin tabarma wanda yake son wai ka
kashe masa sakataren shi ya samu ya hau kujerar"
Salmanu ya doko wata katuwar ashar,
"Wannan da zan iya Allah shi zan kashe"
Tanimu na dariya ya amsa,
"Tunda ba zaka iya ba, sai ka karbi
kudinsa ka sallame shi yayi gaba, randa
Kwanan sakataren ya kare sai Allah ya kashe
masa shi"
Salmanu ya сe,
"Wannan rike shi zamu yi, in bai wasa ba
Allah sai na talauta shi"
"Oho maka kuma"
In ji Tanimu, sannan ya cigaba,
"Sai kuma Hajiya Kumbo, ita kuma
Mijinta ne yayi mata kishiya a 6oye, bayan ta
sakankace wani boka yayi mata alkawarin daga
ita ba zai iya kallon wata mace da sunan so ko
aure ba, kwatsam sai ga mijinta yayi aure a
boye, bayan ta gano shi kuma yake son raina
mata hankali wai amaryar zata tare, ta ce zata
121 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
zo wajenka da neman taimakon, har abada kar
Amarya ta tare, ya bar ta tayi ta lilo a gidansu
in ma rabon 'yan dozin ne a tsakaninsu duk
tayi ta haihuwarsu a gida..."
Ya sauke numfashi ya dubi Salmanu,
"Ita ma wannan matar tana da Dala.
"To an gama, ta kawo kuka gidan mutuwa.
Suka sake kwashewa da dariya. Sai
lokacin Salmanu ya kula cewa Adamu fa ya
shigo da wata irin fuska wadda ta kamata a
saurare shi, musamman da ya kasance duk
hirar da suke ya ci magani ya ki sanya musu
baki alhalin da idan ana yi ya fi kowa shan
dariya,
"Kai kuma fa?"
Tanimu ya tambayi Adamu, da alama
kuma ba jiran amsarsa yake ba, don bai jira
cewarsa ba ya fice da sauri yana cewa,
"Ni fa ban karya ba, bari na zagaya wajen
mai shayin can"
"Salma ce ko?"
Tambayar da Salmanu ya yi wa Adamu
kenan.
122 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
Adamu da yake jin ya zo da kwrin gwiwa
ya yi taku gaban Salmanu ya tsaya cikni nuna
da gaske yake,
"Ban taba nutsuwa da sana'ar nan da ka
kira ni mu yi ba sai yau, na zo da imanina da
yarda ta duka, ba mai yi muku maganar aljanu
ba, ba yi muku basaja ba, ba dan koren boka
ba, komai ake so na yi zan yi, don na shirya in
zama ko mai zan zama in dai zan sami abinda
zai shigar da Husna rayuwata, nan da wata biyu
ina neman kudaden da zasu aura min ita a
matata tą biyu, an min danyen hukunci a jiya
an aura min Salma a matsayin ta daya...."
"An aura maka Salma?"
Salmanu ya tambaya cikin karaji tare da
jin wani irin mugun takaici ya naushe shi a
kahon zucі,
Adamu ya fara naushin hannu cikin alamar
fishin da yake ji yafi na Salmanu, kuma danyen
hukuncin da yake son dauka zai iya fin nasa in
da sarari zai samu. Ya сe,
"Eh. Salma suka aura min don su nuna sun
ciyar da ni na girma, ba ni na wayi gari na
ciyar da kaina ba"
123 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
Ganin nasa fishin ya kai haka ya sanya
Salmanu rage nasa, ya kawar da kai yana
kadawa,
"Ban cika ganin laifinsu kamar na Salma
ba..."
Cikin sikewa Adamu ya tare shi,
"Don me? Don in ba su aura min ita ba
zata iya aura min kanta? Kar idonka ya rufe
Salmanu don kana kin Salma bisa kiyayyar da
na yi mata a baya, amma in neman me laifi ake
ba sai an wani sha wahala ba ana samun Alh an
وو
gama.
Ya zarce da yin kwafa cikin kufula,
"КК! Аmma ba komai zan nuna masa
tawa iyawar wallahi"
"Ni kuma zan nuna wa
iyawar"
Salma tawa
In ji Salmanu da haushin Salma ya sake
kashe shi, wato har Adamu ya daina ganin
laifinta da zargin ta yi masa wani siddabarun?
In haka ne ta ina ma zai faro wa wannan
matsalar tasu tunda mai matsalar bai dauke ta
matsala ba?
124 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
Adamu sai yi wa Salmanu duban rashin
fahimta yake bisa furucinsa na nuna wa Salma
iyakarta, har dai da Salmanu ya ki kara masa
haske cikin raunin murya,
"Ka da ka manta fa yanzu Salma matata
ce
Salmanu ya bugi kafadarsa cikin nuna
halin ko in kula,
"Oh na tuna fa! Kuma ba zan sake
mantawa ba”
Adamu zai yi magan Salmanu ya tare shi,
"Mu share wannan hayaniyar Adamu mu
zo mu yi abinda ya fi kamatarmu, ba kai kadai
zaka nemi kudin da zaka auri abinda kake so
ba, har ni idan na nema zai iya zama naka,
saboda haka ka kwantar da hankalinka in dai
matsalarka a Husna ita ce kudi to zamu taru mu
yi ta nemansu ko ido rufe ne, ka cire damuwa
ka ji gwarzon aminina?"
Ya kare maganar da zolaya.
Dole ba don Adamu ya so ba ya yi dan yake, sannan ya fitar da dariya da karamin sauti.
125 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
Salmanu ya mika masa hannu suka tafa
sannan suka saki ihu.
"Kafin wancan Tanimun ya dawo daga
shan shayin ni bari na zagaya baya na yi wani
abu..."
In ji Salmanu
Adamu ya tare shi,
"Ka zagaya baya ka sha Sigari..."
"Allah ya kiyaye, ji nake na ci maka
alwashin na daina tunda kai daga kauye kake
ko warinta baka so. Kai dai ka zauna nan ya
dawo yayi maka naka Make Up din"
Dole Adamu ya dara yana bin Salmanu da
kallo cikin wani irin kaunarsa, ji yake ban das
hi da Husna ba shi da kowa a duniya wadanda
suke iya son abinda yake so, suke kuma iya
yunkurin ba shi abinda yake so.
Karfe góma sha biyu da rabi daidai
bakuwarsu ta farko ta zo, maimakon matar
Alaramma Hajiya Kumbo ce ta fara zuwa.
126 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
Salmanu na hakimce kan shimfidar buzun
da suka lullbe da fatar Maciji, ya wadatu da
wani irin kwarjini irin nasu na bokaye, sai
muzurai yake.
Adamu kuma na daga can uwar dakin
riker da tiyon da suka huda bango suka zura
daidai saman kan Salmanu amma sun yi wa
gurin basaja da adon kayan tsubbace-tsubbace.
Ba kadan ba Hajiya Kumbo ta ji shakkar
wannan Boka, sannan ta ji yakinin tabbas in
wannan bokan yayi aiki ba za a tarar da wasa
ba.
Tunda ta shigo Salmanu bai daga kai ya
kalleta ba, illa ya kurawa fararen takardun
gabansa idon.
Hajiya sai dan nishi take na bakunta da
nuna sallamawa wannan hamshakin Boka,
wanda a labarinsa da aka bata an ce ba a fara yi
masa Magana, shi yake fadar dukan abinda ya
kawo mutum sannan ya magance masa
damuwarsa.
Kamar Salmanu ya san abinda take tunani
ya dauko daya daga cikin fararen takardun nan
ya mika mata.
127 Maimuna Idris Sani Beli
Π
NA SHIGA ALJANNA...2
Tun da safen suka samu kyandir suka
rubuce sunan mijinta da na kishiyarta da rowan
kyandir din yadda ya saje da farin takardar
babu yadda za'a yi farat daya a gano rubutun.
Hajiya ta karbi takardar cikin ladabi da
6arin jiki.
Salmanu ya cilla mata kullin nikakken
gawayi wanda suka gauraya da garin dayis.
Ta hada su duka biyun tana juyawa a
hannu tana kallonsa cikin rashin fahimta.
"Ki bude wannan maganin"
Boka ya fada mata cikin murya mara
karfin sauti, sai da ma ta nutsu sosai sannan
kwanyarta ta ruwaito mata abinda ya ce.
Da sauri ta shiga warware kullin gawayin
da suka nade da takarda, ta daga kai ta dubi
Boka cikin rawar murya t ace,
"Na ware Malam"
Salmanu yayi shiru tamkar yana karbar
wani sako daga sama, sai can ya sauke gani a
kanta,
"Ki barbada garin maganin nan kan
wannan takardar ta hannunki"
Jiki na bari tuni Hajiya ta idar.
128 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
"To karkade"
Nan ma ta karkade sai ga zanen sunan
mijinta da na kishiyarta ta dinga bi da kallo
cikin dukan zuciya.
"Ba ni nan mu gani"
Boka yayi mata umarni
Ta mika masa jikinta na bari, ta kasa
magana.
Salmanu ya kura wa takardar ido sannan
ya ya mayar da kallonsa gareta,
"Wane ne Usman?"
Ya tambaye ta,
Cikin sallamawa da rawar murya ta amsa
masa,
"Mijina ne'
"Hadiza fa?"
Sai da ta bata rai sannan ta amsa,
"Ita ce kishiyar tawa'
Salmanu ya dinga gyada kai nuna al'ajabi
da mamaki.
Hajiya Kumbo duk ta bi ta tsure.
Ya sake mika mata takardar,
"Ungo juya bayan takardar ki sake
99 barbada maganin nan
129 Maimuna Idris Sani Bell
NA SHIGA ALJANNA...2
"Boka me ka gano? Na shiga uku!"
Da kyar ta karbi takardar saboda rudewa.
Salmanu y ace,
"Abin babu kyan gani, amma sake
jarrabawa mu ga sunan wanda zai fito"
Da ta sake sai ga Usman da Hadiza sun
sake fitowa, ta mika masa hannunta na
karkarwa.
Ya duba na wasu sakanni yana kada kai
sannan ya ajiye takardar gefe yana cewa,
"Lallai wadannan mutanen da gaske suke"
Ya janyo wani kasko a gefe wanda ke cike
da rushi ya bude wani kuttu ya duntso garin
magani ya yafa wa wutar, wani irin hayaki
gauraye da kauri ya tashi a dakin, shi kuma ya
runtse ido yana ta faman mus-mus da baki
tsawon wasu mintuna marasa yawa.
Can kamar daga sama sai ga Adamu ya
fara wani irin nishi a Tiyo,
Ba Hajiya Kumbo da nan take suka gama
siye imaninta ba, hatta Salmanu da ya kwana
da sanin basajar sai da salon na Adamu ya so
tsorata shi da zargin wani aljanin na gaske yayi
musu kutse a aiki, amma dai haka ya cigaba da
130 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
mazewa yana gurnanin da ke kara ruda
Kumbo.
Sai da Adamu ya gama nishinsa can kuma
yayi dif! Tsawon wani lokaci sannan ya dage
ya kwararo wani ihu mai gigitarwa wanda ya
sanya Hajiya zabura zata arce sai da Salmanu
ya dakatar da ita da hannu tare da dora yatsa a
bakinsa alamar ta yi shiru, nan ta zube jikinta
na bari.
Adamu ya zarce da Magana cikin nishin
da ya fara da shi,
"Bisa wane dalilin ka taso ni ina baccina,
me yasa ku bil adama ba ku cika tausayi ba
ne?"
Salmanu ya marairaice murya cikin ladabi
ya ce,
"Wani bahagon aiki ne ya zo gabana ranka
ya dade, dole na kira ka, ka zo ka sanya hannu
وو
ka ceci mutuncin baiwar Allah na...
Kafin ya rufe baki Adamu ya amsa da
watą irin dariya, ya се,
"Wai Kumbo da ke zaune gabanka?"
Salmanu ya dago ya kalli Kumbo wadda
razana ke sa ta jin neman sakin fitsari a wajen,
131 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
sai dai can cikin zuciyarta cike take da farin
cikin abinda ke faruwa, wannan sabon bokan
nata da manyan aljanu yake aiki wadanda suka
sanka da matsalar da ka zo da ita.
Salmanu ya ce,
"Ita ce ranka ya dade"
"To ka fada mata ta tashi ta tafi gida, da
mijinta aka hada baki aka cuce ta
Salmanu ya marairaice Murya,
"Ita da ta zo neman waraka wajen manya
irinku ai ba kwa kora ta ba Ranka ya dade"
"A taimaka min"
Ta shiga maganar cikin barin jiki.
Adamu ya се,
"Ina buhun dankalin turawan da ya kawo
miki kamun azumi?"
Hajiya Kumbo ta shiga tunani. Ta tuna
cewa duk wata mijinta buhun dankali yake
direwa kasancewar gidansu na mutane, amma
watan azumi har buhuna hudu yake direwa a
raba wa makota buhu biyu, azumin da ya
gabata satin kama azumin ya kawo dankalin.
Nan da nan ta gyada kai,
"Eh na tuna, buhu hudun nan ko?"
132 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
Adamu ya amsa cikin dariya da ihu.
fito?"
"Yauwa su! Kin san daga hannun wa suka
Ta gwalo ido tana girgiza kai,
"Ban sani ba ranka ya dade"
Adamu ya amsa,
"Daga hannun Hadiza matar mijinki suka
fito, shiyasa na ce duk abinda aka yi miki da
sanin mijinki..".
ce,
Hajiya ta saki wani irin nishin fargaba ta
"Oh ni Allah! Alh. ya ci amanata..."
Adamu ya tare ta,
"Duk asirin da zata yi miki ta hannunsa
take kawo miki shi take bawa ya kawo miki a
zuwan daga gare shi ne, amma lamfa kawai
suka yi miki dukkansu, suna nan suna niyyar
יי tarwatsa miki rayuwa...
Sai ga Hajiya na son barkewa da kuka,
"Na lura da haka wallahi, don a da Alh.
komai na gindaya ba ya musawa amma yanzu
ko jinjirin jaki haka ya gan shi akan yadda
yake jayayya da ni"
133 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
"Ai ta gama da shi,kiris take jira ta karasa
kassara ki, ko yanzu gata can na hango ta
zaune gaban wani matsafi suna shirin yo miki
aike...
Hajiya ta dora hannu aka tana ambaton
shiga uku,
Adamu ya cigaba da ruda ta,
"Rannan da kika tsefe kai an turo Duna ya
saci gashin kanki, gashi can ana kullewa a
cikin kwai za a jefa teku, in har hakan ta
kasance to ke da mujiya ba bambanci a idon
mijinki"
Hajiya ta sake rikicewa ta cigaba da kuka
haikan tana roko da hurwar a taimake ta.
Sai da Adamu ya gama tabbatar da
imaninta sannan ya ce mata,
"Zauna ki dakata a nan, na san Aljan
Cunkokuwaso za su tura ya jefa tekun, ni kuma
zan tura Migadir ya kwato ya kawo miki nan ki
gani"
Da haka Adamu yayi musu Sallama yayi
nishi ya bace.
Hajiya ta kife kai wajen tana ta faman
kuka, Salmanu kuma yayi kus yana sauraronta
134 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
a zuciyarsa yana saka yawan kudin da zai
wafta.
Damuwarta ya sanya bata kula da lokacin
da Salmanu ya dauko farin kwan kazar gidan
gonarsu ba wanda suke da irinsa ya kai hamsin,
yadda suke wa kwan shi ne, suna tsaga shi
daga kokolinsa cikin hikima da wata siririyar
aska yadda ba zai fashe yayi baraguzai ba, sai
su zazzage ruwan su cusa tarkacen da suke so,
wani su sa gashi wani allurai, wani su cusa
danyen nama wani kyanyasai, wani kuma su
hada gashin da rowan kwan, sai su mayar da
murfin su like da gam ko super glue yayi
tamkar ba a taba bude shi ba.
To Hajiya mai gashi hade da rowan kwai
aka dauko mata wanda zuwa yanzu yayi wari.
Salmanu yayi tafi da hannu dan janyo
hankalinta kasancewar ta kife kai tana ta faman
kuka shi kuma yana ta faman Magana ba ta san
yana yi ba,
"Magadir har ya kawo kwan ya wuce kina
faman kuka, ban da abinki meye na kuka bayan
kin gamu da Sarkin Aljan Shakakiriro ya shiga
aikinki da kansa?"
135 Maimuna Idris Sani Beli
NA. SHIGA ALJANNA..2
1GN Hajiaya ta hau múrzargido
Salmanu,
tana kallon
SEVI
nion Yà mika matad kwan ya mika mata wata
tasa yana céwa fasa shi mu ganiy mesig sb
Tа karba da kwatin gwiwarta eikin dokin
fasawar, don Allah Allah take ta fasa shi ta san
fasawar ce tarwatsa asirin da kishiyar tata ta yi
mata ko take shirin yi matal isx sd sbbay eles
02 Bayan ta fasaşibazita ba hatta Salmanu sai
dá ya toshe hanci saboda azabar doyi, ya dinga
tarsmyahaurkarawavdashegantakas ita ma
hancinta toshe tana bin fasasshen kwan da
kallo?sai ta ga tabbas ma gashin kanta ne, hatta
kududunen da tayidmàsa kafin ta watsa shara
iyana manbandu ware baeny ism sviish oT
risMalam kaytaimakebni mana, me ye abin
yiryanzu? Ga sharrinsu dai an dauko shi
nomeTana nuna rubab6en kwan daita fasalued
nse siʻKitashi ki je gida zaki ga aiki da cikawa,
Shakakiriro ya zuciya sosai, na san ba sai an
bashi zabi baj ba żai wa Hadiza ba kyau ba"
asyadCikini farinciki daidokita of sut itemst
sgida "Allah ya saj ni ko kaslie annamimiya ma
ils
yayi ita ta sai wa kanta"
ksnesS" qs sikioki
2136 Malmuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
"Na fada miki ba sai kin bashi zabi ba, ke
dai ki dawo nan da sati guda"
Ta shiga zuge jaka cikin jin kwarin
gwiwa.
Salmanu ya dinga satar kallonta yana
tunanin ta inda zai bullo mata in ta ba shi
abinda ba shikenan ba.
"Malam nawa zan bayar kafin alkalami"
Salmanu yayi fuska iyakar fuska,
"Ki bada dubu hamsin"
Ta dan ji dukan zuciya, amma da ta tuna
bokan tana baya wanda ko kama kafar wannan
bai ba shi kansa yana cajar sama da haka kawai
sai ta zage jaka ta ciro ta mika masa, ya tura
mata wani faifai ta ajiye a kai sannan ta tashi
tana yi masa godiya ta fice.
Sai da ta jima da fita sannan Adamu da
Tanimu suka fito maboyarsu suka shiga
hayaniya da ihun murna tamkar sa balla dakin.
Tanimu ya dubi Salmanu y ace,
"Yanzu kai Salmanu tuni ka san da
wannan sana'ar ka bar mu muna ragaita a titi?"
"Rabonmu ne ke nesa"
Salmanu ya amsa cikin farin ciki.
137 Maimuna Idris Sani Beli
NA SHIGA ALJANNA...2
Adamu kuma ya ce,
"Ni kam yanzu na nade hannun riga zan
fara sana'ar nan, ko kun tuba ni kam