Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
1 / 6
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels MAIMUNA IDRIS SANI BELI NA SHIGA ALJANNA... NA SHIGA ALJANNA...2 Na shiga Aljanna... 2 "Tashi-tashi ka taya ni jaje na haukace Salmanu" Cikin shasshekar kuka da nuna firgita Adamu ya dinga dukan Salmanu wanda ke kwance da alamun dogon bacci har yana jan tirka-tirkan raguna, alhalin ba baccin yake ba tsabar takaici ne ya hana shi tanka Adamu wanda ya share guri ya fara tikar kuka tun farkon dare. Tun yamma da ya zo gidan ya tarar da Adamu cikin mawuyacin hali na damuwa da ciwon rai, ko abincin dare bai iya kai shi bakinsa ba, hatta sallah cikin jam'i da bata wuce shi, a jiya sai kara'in sallar isha da magariba ya hada ya gabatar wajen karfe goma na dare. Abin haushi da yayi ta cizon Salmanu shi ne, yayi-yayi Adamu ya fada masa dalilin damuwarsa ko abinda ya birkita shi haka amma Adamu ya kekasa kasa ya ki sanar da shi. 4 Maimuna Idris Sani Beli B NA SHIGA ALJANNA...2 Damuwar ta Adamu ce ta hana shi komawa tasu unguwar kawai yayi niyyar kwana a nan, ba da niyyar rarrashin Adamun ba sai dan sanin-shanun da yayi wa Adamun, ya san da kansa in ya gama damuwarsá zai fito ya fada masa. Sai gashi kuwa ya farkar da shi da sigar da ta kusa sa cikin Salmanu farkewa da dariya, amma ya kanne, ya tashi zaune yana muttsikar ido tare da mika, "Wai da gaske kake ka haukace Adamu?" Ko ma shegantaka ce Adamu ya ki yarda da hakan, cikin hawaye da kada kai ya amsa, "Wallahi da gaske nake Salmanu na haukace, kai ba ka lura ba ne?" Salmanu ya sake murza ido yana Karewa Adamu kallo, "Kuma fa kamar haka ne, yaya aka yi ka gane ka haukace?" a Adamu ya sake kecewa da kuka, "Abinda nake hankali bai taba irinsa ba, mahaukata na san sahun farko na shiga, 5 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 kaicorı rayuwata, wallahi duk cikin burikana babu hauka Salmanu, amma ka ga Allah ya jarrabe ni da shi Salmanu ya canja kallon dabyakedwa Adamu saboda zaton da gaske ya haukace din, sai tsoro ya fara kama shi, don haka ya rasi ta cewa illa bin Adamu da kallo dokacin da ya janyo ledar pure water ya huda ya hau tsiyayewa a kofi ya miko masa, sUSA eeS sedusUngò karbi ka yimin addu'a na sha kô zarı samu kullin kirjina ya warware, ko da ban warkė daga haukana duka ba, to wai idaň ma iná warke illar da yayi min zata gogu ne Salmanu? Wai zata gogu?" smas enunSalmanu yayi tà maza ya karbi ruwan ya hau yin mus-mus da baki yańa tofawa cikin rtsoro,lamma yayi fuska bayan wani lokaci ya mika wa Adamu ruwan,led umsA eweвя "Ungo yi Bismillah ka shanye Ba ja Adamu ya karba yal shanye ya ja jiki ya kwanta yana cigaba da hawaye. Dakine züciyoyinsu iyàyicltsitleillahid su dukarg wanda bugawar kunńuwansu ilea 2 6 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 kaďai ke jiye musu, Adamu na bacin rai da sarkewar al'amura, Salmanu na tsoro da tunanin hanyar tserewa. Ya daga kai ya dubi agogo sai ya tarar hudu ta karato, in ya ce fita zai yi ya tafi gida yanzu komai yana iya faruwa da shi ko hannun miyagu ko kuma jami'an tsaro, kuma dai da kunya ya shiga gida ya tayar da Hajiya y ace mata Adamu ya haukace, in haukan karya Adamun yayi kila a mayar da kalmar haukan kansa, idan kuma yace zama zai yi a nan daga nan zuwa ko wane lokaci kila Adamu ya iya ballewa da duka. Sun shafe mintuna goma sha biyar a haka, ban da kuka babu abinda Adamu yake, idon Salmanu akan sa yana tsoron ya tashi. Can da ya ji kukan Adamun ya lafa sai ya daga kai ya dubi agogo sannan ya mayar kan Adamu, "Yau ba zaka yi sallah ba ne? na ga hudu na neman sako kai" Cikin barin jiki Adamu ya tashi zaune, 7 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 "In roki Allah me Salmanu? Husna nake roka dama ya ba ni, kuma ya bani jiya na tankwabe na karbi abinda kullum nake rokon kar ya ba ni" Tsoron Salmanu ya fara raguwa, cikin rashin fahimta ya ce, "Ban gane ba Adamu, ko duk a duniyar haukan kake Magana?" Cikin kuka da girgizar kai Adamu ya kwashe labari ya bawa salmanu. Shi kansa Salmanu sai abin ya bashi mamaki, cikin jinjina kai ya ce, "Anya? Da gaske ne zuciyarka ta fara haukan da idan an kira shi na Allah da annabi an yi karya" Adamu yayi masa duban rashin fahimta, kafin yayi Magana Salmanun ya tanka, "Ni ban san me zan kira abinda nake hasashe ba Adamu, abinda kawai na sani shi ne kana son Husna kuma ba ka son Salma, don haka abinda ka yi jiya ba zaka yi shi haka kawai ba" "Shiyasa ai na ce maka na haukace" 8 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 "Ni ma na yarda" In ji Salmanu, wani irin takaicin Salma na ninkaya a kahon zuciyarsa. Har ya bude baki zai yi Magana sai kuma ya fasa bayan wani mugun tunani ya ziyarci ransa, tabbas in Salma bata yi wasa ba sai ya sassaba mata kammani. Adamu da yake jin kamar ba shi da wani gata a yanzu ban da Salmanu a duniya kuma shi kaďai zai iya fahimtar matsalarsa sai ya tattara dukkan hankalinsa ga Salmanu y ace, "Ka ce wani abu mana da zai sa naji karfin gwiwa Salmanu" Salmanu ya riko kafadar Adamu yana jinjinawa cikin fuskar alhini, "Ka share zuwa gobe, na yi alkawarin daukar wani mummunan mataki, duk tsinannen da ya nemi jazawa zuciyarka rudu da hauka na rantse da Allah shi ma ba zan bar duniyarsa lafiya ba" Cikin tattara fata Adamu ya kurawa Salmanu ido ya ce, "Alkawari?" 9 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 Salmanu ya jinjina kai, "Na dauka, kai ma ka yi min alkawarin kwantar da hankali har zuwa lokacin da zaka ji nawa matakin" Adamu ya koma jiki a sanyye ya kwanta cikin dasasshiyar murya ya ce, "Na yi" ******** Tsawon lokacin da aka ci bikin Amina aminiyar Husna aka side, sam Husna ba ta dawalwala ko kadan, ba ma wai rashin walwala kawai ba, duk wanda ya dube ta sai ya gane. lallai wani murkusheshen abu ya taushe zuciyarta da karfin hatsi, ya fi karfinta ita da zuciyar har ya bayyana a fuska da gangar jiki. Ba a cikin kawayenta kadai ba, hatta a cikin gidansu ta rasa walwala a matsayinta na mace mai kazar-kazar da shiga mutane, yanzu ta kasalce sai son kadaici da'yan kananan hawaye. Matan babanta sun dan binciki damuwarta, ba don su san ainihin matsalarta 10 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 su maganace mata ba sai don kar ace sun ganta cikin damuwa bas u tambaya ba, wato tambayar je-ki-nayi-ki, don haka ne ma basu sami amsar komai daga gareta ba duk da kuwa daidai wannan lokacin tana jin matsalar da take ciki ta cancanci abokin tattauna ta, zuciyarta zata babbake bata san babu ko hakuri a a waki'ar son da ta fada ba, lallai kenan ta nemo wanda zai taya ta nemo ruwan da zasu kwara wa zuciyar kafin ta gama Konewa. Kwanan Amina uku gidan angonta Husna ta tattara buhunhunan matsalarta ta kai mata, bayan ta kwashe mata labari ta karkare da Magana cikin hawaye, "In dai yadda nake ji akan son gayen nan haka masoya suke ji a a zuciyarsu, to ina da tabbacin zuwa yanzu da yawan mutanen duniya bai kai haka ba" Cike da mamaki da alhini Amina ta jahilci maganarta ta karshe, t ace mata, "Ban gane ba" Husna ta shaki hanci t ace, 11 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 "Eh mana, yadda rayuwa ta gaji ba yawancin abinda kake so kake samu ba, in dai yadda nake jin so haka kowa yake ji to kuwa in bai samu abinda yake so din ba sai da ya mutu, Allah na rantse miki" Sai mamaki ya cigaba da kashe Amina, kawai ta tsurawa Husna ido ta ma rasa abinda za ta ce, sai juya ido da kafada kawai take. "Abinda yake kara sakudar zuciyata shi ne, wai duk matan da ke fadin duniya a rasa macen arzikin da zata kwace saurayi a wajena sai banzar kawarki Salma... shegiya tsinanniya..." Amina ta rufe mata baki cikin matsananciyar dariya duk da tana yi tana rage mata karfi kasancewar ta fahimci lallai Husna da gaske take take, in kuwa haka ne bai kamata ta wanko kafa ta kawo mata kukanta ba kuma ta kasa bata muhimmanci, cikin ta tausasawa ta ce mata, "Kar ki rage mata alhaki don baki da yakinin ke ya fara so ko ita, kuma shi so ai ba ruwansa da wani kyau Husna, Salma macace 12 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 mai shegen wayo, zata iya hada kafada da ke دو a wajen iya jan zaren maza... Cikin tsawa da kuka Husna ta tare, "Wallahi karya ne ban yarda ba...., na san so, akwai karfa-karfa cikin abinda suka yi min.... kuma wallahi ba zan yarda ba" Sai ta zarce da kuka. Amina ta zurfafa a tunanin yadda zata tunkari lamari, da gaske ne har cikin ranta damuwar Husna ta shalle ta, Husna ba ta saba da karya ko bata lokaci kan abinda bata ra'ayi ba, don haka kamata ita ce duk abinda ta yi ra'ayi a taya ta nema don da gaske take ba da wasa ba. sbusw Cikin bulayinta ne ma ta ji aiukawai Adamu yana son "Rawarta, bugun eikinta kawaf suka shirya shi da Salma tun dadama abokin wasanta ne. ajanyowayarta ta shigasKirám Sálma don ita ma ta bugiscikin Snata ammaseikino2 akasita tarar da wayareakasher doleita saukesh cikm sadudar da sanym sa jikiidóntavakan Hdsnaw wadda ita tun dazu ta baza mata na mujiya. 6M 13 Malmuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 "Wai wa kika kira?" Husna ta tambaya. Kai tsaye Amina ta amsa, "Salma сe... دو Husna ta banka mata harara cikin munin fuska, kirjinta na ta faman bugawa ta ce, "Amma dai da kin same ta kin zalunce ni, wai ki kira ta ki ce me?" A sanyaye Amina t ace, "A'a bugun cikinta zan yi in ji da gaske ne shi zata aura? Komai zamu yi yakamata mu fara sanin wannan gaskiyar Husna" Husna ta sawa Amina ido tana yi mata wani irin kallo wanda ya sanya Aminar shan jinin jikinta ta yi sararo ita ma tana kallon Husna da fuskar nuna rashin fahimta, Husna ta kada kai ta rausayar abin tausayi, "Abinda kawai na sani shi ne, Amina ina son Adamu, sanin gaskiya zai aureta ko zai fasa ba zai hana ni sonsa ba, don haka a bi wata hanyar wadda ba ta shafi Salma ba, don 14 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 ni ko a lahira ba na fatan ma Allah ya hada mu sabga daya". Amina ta sake yin shiru cikin mamamkin irin wannan zafin kan na Husna a yau, fada babu gaskiya. Can a tunane-tunanenta ta samo dabara, "Ina kayan ankon da kika ce ya ba ki, ba shi kayansa kika yi lokacin da suka Kuga miki rashin mutuncin shi da Salma ko tafiya da abinki kika yi?" Husna ta tabe baki, "Wallahi har zuciya ta debe ni na dire masa abinsa sai kuma na ga asarar hakan, na juya na tafi da abina" Amina ta yi shewa, "Yauwa 'yar gari, gara da kika yi hakan ai kin ga sai ya zame mana tsanin haduwa da shi" Husna ta jahilce ta da ido amma bata tanka ba. Amina ta се, "Da kina da lambarsa dama kyakkayawan sakon godiya. zamu shirya 15 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 masa don bugar cikinsa mu ji inda taki sarautar ta kwana, amma tunda babu ma sai a tuna da, ki sami takarda 'da biro masu kamshi ki kashe shi da baki, na san zaki iya Hajiyata" Husna ta 6alle da murmushin jin dan kwarin gwiwa kadan, muryarta a bude ta ce, "An gama, zan gwada" Daga nan Amina tayi dabarar da suka kashe bos din a nan saboda gabadaya lamarin wannan murdaddiyar soyayyar ta kawarta, aminyarta tsoro yake bata, bata taba tsammanin Husna a irin wannan duniyar da ake mutuwa kan son masoyi ba. Kasancewar Husna ma'aboyiyar kaifin kwakwalwa da iya tsara samari, wasikar da ta rubutawa gwarzonta ta ji suga sosai, ga ta kuma 'yar faki wadda ba yawa sai lada, rabin shafi kwata-kwata ta ci, amma ta san in dai akwai 6urbushin sonta a zuciyar Adamu ko yaya son yake kamar yadda ya fara bincina mata, to tana da yakinin sai ta shallo dukkan sonsa da kaunarsa, sannan kasancewar Amina 16 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 ta fada mata matsayin karatun Salma, wadda ta tsere mata don ita iyakacinta sakandare, sai ta yi wasikar da gwanewar turancinta wanda ba duk kai ba, don tana ja a ingilishi sosai ko a makaranta shi ta fi kawowa sama da komai, dalibai da Malamai kowa ya san ta akan haka. Da sassanyar la'asar ta so ta wanki kafa ta kai takarda, a zuwan in tayi ruwa rijiya in bata yi ba masai, ma'ana in ta hadu da Adamu ta gabatar da zantukan cikin takardar da fatar bakinta, in yaso duk ma abinda zai biyo baya ya biyo. Idan kuma bata ganshi ba sai ta sami yaro ta aika masa da ita. Amma wata mace mai karbar dinkin sunan ta da za'a yi gobe ta zo ta tsaye mata sai da ta hada mata dinkunanta wanda ta jima da kawowa yana kan layi, bata sallami matar ba sai bayan sallar magariba, ita kuma ta rantse cikin ranta wasikar da ta rubuta a zuciyar Adamu zata kwana ba a doron tata zuciyar ba, don haka ta shige bayan gida ta sallo wanka ta gabatar da sallar magariba 17 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 sannan ta hau fente-fente duk da dai kwalliyar ta fi auki a turare don rashi tsammani za'a kawo wuta bare har wanda tayi wa kwalliyar ya gani. A gida tayi karyar zuwa shagon kayan dinki ta silale unguwarsu Adamu. ********* Duk yadda Adamu yayi Salmanu ya fada masa inda za shi bayan sallar magariba Salmanu ya ki sanar da shi. Ba wani abu ya tsorata Adamu da fitar ta Salmanu ba sai ganin Salmanu yayi wata irin shiga ta 'yan daban zamani, har da soke wuka a kugu. Adamu ya rikice sosai ya hau cewa, "Salmanu 'yanci fa ba hauka ba ne, ban biye maka don fin karfin iyayena ba balle ta silarka na tabbata dan jeka-ka-gani, kar ka janyo abinda za'a yi tsammanin tunkunyar tsafinmu daya" Salmanu ko kallon Adamu bai yi ba bare ya tanka shi ya sa kai ya fice. 18 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 Hankalin Adamu sam bai kwanta ba, tsoron ko kashe matar ubansa da Salmanu yake ta kirarin yi ya tafi cikawa ya kada cikin Adamu ainun, kawai sai yayi saurin rufe dakinsa ya tafi cikin gida wajen mahaifiyarsa hira, abinda ya jima bai yi ba musamman a lokaci irin wannan, shi manufarsa, idan ma wata aika-aikar Salmanu ya je yayi ko an kama Salmanun idan aka hado da shi zai iya samun shaidar cewa ai dai-dai wanna lokacin yana cikin gidansu kusa da gyatumarsa, musamman dayake gidan nasu kafa bata daukewa da masu siyen goro, ko wani bai gan shi ba wani zai gan shi tare da mahaifiyar tasa. Salmanu na zaune a dakalin Kofar gidansu Adamu cikin shigarsa ta Basaja wadda idan ba farin sani kayi masa ba daga kallo daya ba zaka shaida shi ba. Duk da ba aikin kirki yake shirin yi ba cikin nutsuwarsa yake, lokaci-lokaci yana kallon hanya har tsawon fiye da mintuna talatin. Allah ya taimake shi wadda yake jiran 19 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 karasowarta sai ga ta ya hango daidai lokacin da aka tayar da sallar Isha a masallacin unguwar. Da sauri ya mike ya shiga soron gidan wanda yake dundum da duhu ya labe. Yanzu kirjinsa na harbawa amma ba na tsoro bane face na fargabar kar Adamu da Sallar jam'I bata wucewa ya fito zuwa sallar Isha ya bata masa shiri. Salma cike da ďoki da kumajinta ta sako kafa soron gidan tana kokawar kunna fitilar wayarta, tun yamma ta sami aiken guntuwar wasika daga Adamu mai dauke da cewa, Abin 'yar haka ne? ba ni da lafiya amma kin kasa zuwa duba ni. To ina jiran zuwanki bayan sallar Isha in ban ga fuskarki ba zan iya runtsawa ba. Ita da Anti Sa'a sun sha tsallen murnar hakkansu ya cimma ruwa, bayan sallar isha kuwa ta ci kwalabo ta dauko kafa ta taho ba tare da sanin makitcin Salmanu ta ratso ba, Adamu bai san da takardar ba kuma har zuwa yau begenta bai yi masa yawan da zai kasa 20 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 NA SHIGA ALJANNA...2 runtsawa ba, yana kasa runtsawa tabbas amma kuka yake sharba yana tuhumar ta hanyar da ta bi ta shiga zuciyarsa. Salmanu da ke labe bai bari ta kunna wayar tata ba ya fizge wayar, lokaci guda kuma yaya fizgi hannunta cikin zafin nama ya jata ya makure a bango ya toshe mata baki da hannunsa na hagu, na daman kuma ya zaro wukar da ke aljihunsa ya dora mata a wuya, yayi mata Magana cikin kaushin murya da tsoratarwa, "Bari na kashe azzaluma kafin ta kashe wanda ta yi niyya" Salma ta sha kwatanta yadda ake mutuwar tsaye, amma bata taba tsammanin haka take ba sai yanzu da ta sami kanta cikin wannan wadin a 'yan wadanann sakannin. Kirjinta sai bugwa yake fat-fat. Salmanu ya sauke hannunsa da ya toshe bakinta cikin murya kasa-kasa yace mata, "Na rantse da Allah kika yi min ihu sai na Burma miki wukar nan a ciki" 21 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 Salma ta hadiye wani mugun yawu da kyar, jikinta na bari ta ce, "Wallahi ba zan yi ihu ba..... amma me kake nufi da ni?... don Allah kar ka 6ata min ...rayuwa יל Kafin ta rufe baki Salmanu ya kwaso wata uwar ashar ya rusa mata, ya dora da cewa, "Kun ci kaza-kazanku ke da abin naki, ke har kina da abinda za'a kwata da karfi? Ko kyauta kika kawo min kanki zan kalle ki?".... Salma ta ji raguwar fargaba da wannan kalaman nasa, don abinda ta fi tsoro kenan fyade, gara ma ya gurza mata wukar da yake nuna ta da ita a wuya da ace yayi mata fyaden. "To...to...to, me nayi maka? Allah ya baka hakuri don Sayyidina Rasulullahi, na bika na bi Allah" Ba tare da Salmanu ya janye wukarsa daga wuyanta ba ya се, "Wanne tsubbun kika yi wa Adamu?" 22 Maimuna Idris Sani Beli د NA SHIGA ALJANNA...2 Hantar cikin Salma ta shiga kadawa kirrrr! Har Salmanu na jiyo Kararta, bakinta na sassarfa ta ce, "Ban gane ba wallahi" Tana rufe baki Salmanu ya tare ta, "Zaki gane in kin ji kaifin wukar, kin ga in kin je lahira sai ki fadawa Allah dalilin da na turo ki can" "Na rantse da Allah da gaske nake ban gane ba". Ta sake fada cikin kuka. Salmanu ya amsa, "Adamu ba ya sonki, kin kai shi gurin boka ya tsafe masa zuciya, shin kin san kuncin da kika jefa shi kuwa? Za'a iya cutata na share mutum amma karya ne a tabа rayuwar Adamu na kyale" Yanzu tsoron Salma ya nunka na da, tana fargabar ta inda aka ganta a gidan boka kuma aka gane Adamu ta kai, sannan a daidai wannan lokacin ta dauki muryar mai gwada ta da wuka, abokin Adamu ne Salmanu, ta san kuma da gaske zai iya girba mata wukar. 23 Maimuna Idris Sani Beli 1 NA SHIGA ALJANNA...2 Numfashinta sai kai komo yake tamkar ta shide take jin kanta, sai du'a'I take Allah ya kubutar da ita. Salmanu ya dinga jero mata kwandon ashar yana saukewa, karshe ya ci mata alwashin in dai bata je ta karya asirin da tayi wa abokinsa ba to ta tabbatar kwananta kalilan ne a duniya. Yana jin ya gama yi mata kashedin ya tunkuda ta waje yana fadin, "Bace min da gani, makira mai siffar dutsen guga, don zalinci kuma kin ga sambalelen yaro kin makale masa" Kafar Salma rawa take tamkar ana kada mata gangi, amma a haka ta suri sauri, nan da nan sai ga ta ta bace kamar walkiya. Salmanu ya fito kan dakali ya zauna yana kwasar dariya har da tuntsirawa. Ya san abinda yayi kasada ce da zumuncin da ke tsakaninsa. da gidansu Adamu, amma yana da yakinin sai yayi tasirin samowa Adamu farin ciki ko kaka ne. "Barka da dare" 24 Malmuna Idris Sani Bell NA SHIGA ALJANNA...2 Ya ji wata zazzakar murya ta farkar da shi lissafin dokin ranon da yake a tunanin makomar alakarsa da gidansu Adamu, don ba ya jin Adamu, ya san mai raba su sai mutuwa. Ya dago da sauri ya kalli doguwar yarinyar da ké tsaye a gabansa wadda duhun dare bai hana shi gane ta ba, Husnan Adamu се. mata, Da hanzari cikin rawar murya ya amsa "Barkanki dai" Cikin sakewa ta sake ce masa, "Yauwa, ya harkoki ya ayyuka?« A mamakance ya sake amsa mata, "Alhamdulillahi" Ta dan yi jim, kafin da alamun karfin hali t ace, "Don Allah Adamu nake tambaya" Ya dan yi jim shi ma, har zai mike ya ce bari a kira miki shi, me ya tuna? Oho! Sai kuma ya fasa. A sanyaye ya kada kai, "Ya dan fita da nisa kuma, kila ya kai karfe goma kafin ya shigo" 25 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 Husna ta gyara tsaiwar da a bayyane ta nuna damuwar jin Adamu ba ya kusa ne, kamar ta rushe da kuka ta rarrashi kanta. A sanyaye ta mika masa wasikar da ta sherowa Adamu tana cewa, "Kai ne abokinsa da na gan ku tare rannan?" Salmanu ya karbi wasikar yana amsawa' "Eh nine, ban gane ki ba" Husna ta dan yi hucin hadiye damuwa da son nuna komai ba komai ba ne, "Ka ba shi wannan takardar don Allah" Ta fada a takaice tare da share korafinsa na bai gane ta ba. Ya shiga juya takardar yana saka abinda zai ce mata, bai Ankara ba sai jin muryarta yayi tana yi masa sai da safe tare da cewa, "Na gode" "To sai anjima" Ya sami kansa da amsawa cikin dakusasshiyar murya yana hangenta har ta bace masa, a birkice ya sake mayar da hankali ga kallon takardar amma azancinsa na 26 Maimuna Idris Sani Beli , NA SHIGA ALJANNA...2 ga tunanin yadda soyayyar abokinsa ke zuwa a hagunce. Salmanu ya jure boye takardar da Husna ta kawo wa Adamu har tsakiyar dare, kuma akan ta ne ya zauna kwana a gidan, don da farko saboda aika-aikar da ya yi wa Salma yayi niyyar barin gidan don bai san abinda zata je gida ta fada ba, kila kuma Alh. ya shiga maganar, a zo nan a same shi a titsiye shi. Sai da ya bari dare ya raba, Adamu ya hau buzunsa yana kuka yana rokon Allah. Raka'a biyu kacal yayi ya durkushe ya daga hannaye sama cikin kuka yana cewa, "Allah ka gan ta, sallar nan 'yar faki ce ba yawa sai lada, gabo6ina sun yi rauni bisa abinda ka jarrabe ni da shi, Allah ka karkato da albarkarka da rahamarka gare ni da zuciyata da kuma Husna da ka sa mana sonta, Allah kar ka kwace mana sonta da ka ba mu, 27 Maimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 kuma kar ka jarrabe mu da son abinda tun fil יי azal ba ma so A cikin tausayi Salmanu yake amma addu'ar nan ta Adamu tayi mugun bashi dariya har ta tashe shi zaune, ya ce sốKiài dan iskan ina ne da kake son kashe ni da dariya?" sAdámu bai kula ba ya cigaba da addu arsa har sai da Salmanu ya furta cewa, Kai ma ka tuna min, dazu Husna ta kawo sako a baka" Da sauri Adamu ya shafa addu'ar ya dube shi cikin shakkun jin abinda kunnuwansa suka jiye masa, ya tsurawa Salmanu ido a birkice, sKace me! Husna?" Cike darjin alfahari Salmanu ya mike ya daukowasikar a aljihun wandonsa yana cewaid inUST İV I oMexyeha shakkun, menene Allah ba.zaids iya ba?i Husnagc etankawo maka wasika kumash daganjin syaddaa takardar ke tashinshkaimshius um sd sab statoe JABI JOBWal sa is disla i6M28TSMaimuna Idris Sani Beli NA SHIGA ALJANNA...2 kowa ya san sakon soyayya take dauke da shi" Jikin Adamu na 6ari ya rarrafo daga shimfidar sallarsaa ya zo ya riski Salmanu. Suka ware takarda dukkansu da dokin ganin abinda ta kunsa, musamman Adamu, ga shi kuma Salmanu ya kankane takardar ya hana shi wai sai ya fara karantawa. Zuciyar Adamu sai bugawa take saboda ganin yadda Salmanu yayi duru-duru yana bin takardar da kallo - cikin yatsine fuska, daga ganin abinda yake karantawa a takardar ba mai dadin ji da gani ba ne. "Wai ya na ga kana ta faman tamushe fuska kamar wanda

Chapter 1 of 6