Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
6 / 7
da Anti Sa'a fuskokinsu na aika sakon karaya. "A'a me ka ci? Kai da tun safe kake sume?" In ji Alh. Adamu ya tattara hankalinsa ga Alh. maimakon kallon Salma wadda ta nace da mika masa farantin abinci duk da ya ce ba zai ci ba. "Ba na jin ci ne Alh. maltina da madarar da na sha sun gamsar da ni, bakina babu dadi" Karaf Anti Sa'a ta shiga maganar, Maimuna Idris Sani Beli 134 Na Shiga Aljanna...1 "Ai ba daka ta bakin naka zaka yi ba Adamu, ko loma biyar ne yakamata ka karrbi hatsi ka watsa a cikinka, ga rowan zafi ma idan shayi zaka sha" Adamu yayi fuska, "Tun da kin matsu kawai sai ki yi min dura" "Wacce ni? Wannan sai dai Salma, ita zata yi maka durar" Salmanu ya tuntsire da dariyar da ta kara hasala Adamu. Idon Alh ne ya sanya bai kashe Salma da harara ba sai kawai ya shaye ya kawar da kai. Salmanu ya mika hannu ya karbe abincin hannun Salma yana cewa, "Kin ga ni ko Maltinar ban sha ba, manta da shi ki ba ni na ci" Dole Salma ta sakar masa abincin ta ja baya a muzance zuciyarta cike da kaďe-kade, tsakaninta da Allah ko hanyar son abokin Adamu ba ta dauka ba, idan ya ci abincin shi kadai sihirin sonta ya kama shi fa? Anti Sa'a ta lura da wannan tashin hankalin na fuskar Salma don haka ta dinga rarrashinta da ido tana nuna mata kwantar da hankali. Maimuna Idris Sani Beli 135 Na Shiga Aljanna...1 Dai-dai wannan lokacin aka yi kiran Alh. a waya ya sa kai ya bar dakin domin ya amsa, da sauri Anti Sa'a ta yi wa Salma inkiyar ta saki fuskarta ta matsa kusa da Adamu. Ba karamin karfin hali Salma ta yi ba na bin umarnin Anti Sa'a, musamman da ta dubi Salmanu ta ga ya aika da rabin abincin kuma har yanzu yana kan ci. Anti Sa'a ta fara yaudaro Adamu da cewa, "Ni fa na zaci kun shirya da 'yar tawa har na ji ka sai mata anko, amma yanzu takanas mun zo duba ka kana ta faman wani shassharewa, wai ko kallon fuskarta ba zaka yi ba bare ka ci abincin da ta kawo maka?" Adamu yayi fuska ya tsurawa Anti Sa'an ido maimakon Salma da suke son ya kalla, "Menene sabo a fuskar tata da ake son na kalla? Ga abokina nan ya fanshe ni ya kalla, ba shikenan ba" Duk su biyun suka ji kamar ya rusa musu guduma a kahon zuci, na Salma dai yafi bayyana saboda dama a tsorace take da cewa ta zubawa Adamu tsafaffen maganin bokan da ba ya karya, abokinsa ya ci abincin. Maimuna Idris Sani Beli 136 Na Shiga Aljanna...1 Sun kara rikicewa lokacin da Salamánu ya debo murmushi ya ce, "Ga shi yau Salma ta yi kyauwun da bata taba yi ba, kuma ta yi girkin da ban taba cin mai dadi irinsa ba" "To ai sai ka yi mata abinda suke son ni na yi mata כי Adamu ya kara yin fuska ya fada. Sawu a likkafa Salma ta sa kai ta fice daga dakin, inda Salmanu da ma Adamun suka bi keyarta da kallo. "Babu dadi cin fuska" Anti Sa'a ta fada cikin takaici, ta kara da cewa, "Duk tsiya mai sonka ya fi mai kinka" "Me ya kawo wannan maganar?" In ji Adamu rai a bace, Anti Sa'a ta ce, "Abinda ka yi ne ban ji dadi ba, Salma fa ba neman kai muke da ita ba, kuma ba wani laifi ba ne dan ta nuna sonka a matsayinka na dan gida wanda ba wani abu ya mallaka ba bare ace ba son Allah da annabi take maka ba, ka je ka tuna wannan". Maimuna Idris Sani Beli. 137 Na Shiga Aljanna...1 Tsaki kawai Adamu yayi ya kawar da kai. Hakan ya sanya Salmanu yin shiru alhalin da yayi niyyar saka baki. "Ina ankon nata" Ta tambaya. Da sauri Salmanu ya kalli Adamu yana dokin jin Karyar da zai zabga. Kai tsaye Adamun ya amsa, "Wa yake ta wani anko? An sace shi a nan inda hadarin ya faru. Ai maganinta kenan ma da na ce ta zo ta karfa ta ce min sai ni zan kawo mata, Allah kara" Murmushi kawai anti Sa'a ta yi ta basar da zancen suka kamo wani, har lokacin ziyara ya kusa karewa sannan ta yi masa sallama ta tafi. A waje ta ci karo da Salma zaune a baranda cikin damuwa. Ta ce mata, "Yi maza ki kara goga hodar ki je ki yi masa sallama kar ki damu" Cikin sanyin jiki Salma ta goga ta shiga dakin, tana rike d karfen gadon Adamu t ace, "To yaya Adamu zamu wuce, Allah kara lafiya" Maimuna Idris Sani Beli 138 Na Shiga Aljanna...1 Ya dago ya dube ta fuskarsa babu yabo babu fallasa ya dago ya dube ta, ita kuma ta sakar masa wani murmushi, sai ya ji wani dum! Tun daga idonsa har cikin ransa, amma dai bai bayar da maza saboda canjin da yaji ba, cikin nutsuwa ya amsa mata, "To sauka lafiya, na gode" Ta dan yi dum! Da zaton bai kalle ta da kyau ba, musamman da yake ya kawar da kai. Amma babu yadda ta iya haka ta juya tana ficewa. Salmanu ya bi ta da kira, "Ki zo ki tafi da wannan abincin da yaki ci kin ga yau za'a sallame mu" Salma ko ta juyo bare ta nuna alamun ta ji abinda yake cewa. Adamu ya saba tsayuwar dare, amma yau bai yi niyyar tsayawar ba dan har yanzu jikinsa ba kwari, sai dai kuma baccin ya gagari idonsa da ma zuciyarsa gaba daya, wadda ta kuntkce iyakar kuntacewa, haka kawai ransa ya dinga mugun baci cikin daren nan ba tare da dalili ba, Maimuna Idris Sani Beli 139 Na Shiga Aljanna...1 ya kuma rasa wa yake jin haushi ko kuma abinda ke bata masa rai. Haka kuma Salma da Husna suka dinga tsere cikin zuciyarsa suna nuna masa kansu. Ya san cewa shi ma'abocin tunani ne, amma na Husna zalla! Salma ba ta taba samun ko a bonus ya zauna musamman ya tunana ta ba, tunaninsa a lokutansa na rana na yadda zai mallaki Husna ne da mafarkin yadda zasu shifida rayuwarsu, tunaninsa da lokutansa na dare na mika dukkan imani ne ga ubangiji da rokonsa ya mallaka masa ita yana mai cike da fatan Ubangiji ba zai juyar da rokonsa ba saboda haka yake yi cikin dadin rai na jiran lokaci. Amma yau komi ya canja, shi da zuciyarsa neman sa karfi suke su bar Allah, ba don su sami Husna ba sai dan su sami Salma ba tare kuma da sun dena son Husna ba, abin da bayar da mamaki! Fiye da rabin dare haka yayi ta juyi. kan katifarsa rayukansa babu dadi suna kuma ta damfara masa kala-kalar mamaki. Bai tashi yayi sallar ba bare ya fadawa Allah, bai ma yi sha"awar hakan ba saboda kasala da rashin dadin Maimuna Idris Sani Beli 140 Na Shiga Aljanna...1 zuciya, kai da ma rashin tabbas din in ya tashi me zai cewa Allah? Shi da ya shafe watanni yana neman Husna a wajensa yau kuma sai ya durkusa neman abinda baya so wato Salma? Ita wadda yake so ya kai ta ina, kuma Salman ma yaya zaı zai yi da ita? Duniyar ta taru tayi masa zafi har karshen dare, musamman da ya Ankara duk yadda ya so ya nesanta ransa da kKawancen Salma hakan yaki samuwa, kara haka muhalli take mai shegen zurfi a cikin zuciyarsa. Sai ga shi zaune da kuka shaбe-shabe da hawaye har da sauti, yana yi yana ambaton, "Na shiga uku!" Ya ci kukansaya koshi,, amma Salmanu da ke kishinire kan Kafet yana sharar bacci bai gan yana yi ba. Kasancewar ba'a sallamo su kan kari ba neya sanya shi kwana a nan, abinda ya cewa su Hajiya kenan, amma gaskiyar ita ce, sammakon aikinsu suke son dokawa, a cewar Salmanu, ko babu kudi yakamata su fara aikin da ba kudin yake bukata ba. Maimuna Idris Sani Beli 141 Na Shiga Aljanna...1 Musamman Adamu ya tashi zaune yana zungurinsa cikin kuka. A firgice Salmanu ya farka ya tashi zaune, "Adamu jikin ne?" Adamu ya sake carkewa da kuka, "Zuciyata 'yar ta'adda ce Salmanu, ta kwaso ta'addanci ta kawo wa raina, sun hana ni bacci da Alama ma har karshen rayuwata suke bukatar kar na runtsa" Salmanu duk da bai gama fahimtar Adamu ba fuskarsa ta nuna iyakar damuwa, ya ce, "Wai me ya faru?" "Wai Salma mu ke so" Ya amsa cikin shassheka. Salmanu ya sake tare gira nuna alamun rashin fahimta, "Kai da wa?" "Ni da banzar zuciyata mana" Kamar Salmanu zai tuntsire da dariya, amma har ga Allah ya ji tausayin Adamu musamman yadda ya ga yana kuka da hawayensa, a sanin da yayi masa jarumi ne daidai misali, kadayake shi halittar so na saurin sanya shi kuka, haka wancan Maimuna Idris Sani Beli 142 Na Shiga Aljanna...1 neman auren da ya taba rakitowa karfi da yaji ya mayar da shi wani Baure. Ya jima yana kallonsa cikin nazari sannan ya tanka, "Da mamaki gaskiya, to me ya janyo hakan?" "Oho! Nima na sani! Zagi nake so in rusa amma na rasa wanda zan zaga, ni ko zuciyata da haka kawai muka rakito son abinda bai cancanta ba? Allah ya tsine wa Salma wallahi, ni ban san abinda zan so a ita ba" Ga dariya ga kuma son yin nazari suka taru suka murkushe Salmanu, sai ya hada su duk biyun yana ji das u, Cikin tsananin dariya ya ce da Adamu, "Jiya Salma ta sako kwalli? In ta saka sai mu yi tsammanin Kifil ta sako maka" "Allah ya isa ban yafe ba wallahi" Saļamanu ya sake tuntsurewa da dariya yayin da Adamu ya sake sakin shasshekar kukan da ya tsayar da Salmanu dariyar da yake, "Wai baka yi bacci ba? Na san ka da sallar dare yau me ya hana ka? Ai da ka kai wa Allah karar Salma yayi mana maganinta" Ya kara da tuntsirewa da dariya. Maimuna Idris Sani Beli 143 Na Shiga Aljanna...1 Adamu ya tsayar da hawaye yana duban Salmanu, "Ka bar mayar da lamarin nan wasa Salmanu, wallahi da gaske nake zuciyata ta ci amanarmu" Sai abin ya fara bawa Salmanu mamaki, yayi suguri tare da laluben tashar da zai kamo, amma ya rasa har lokacin da ya ga Adamu ya mike daga kan katifarsa ya fara kaiwa da kawowa a tsakiyar dakin, Salmanu ya daga kai ya bi shi a kallo yana sauraronsa a nutse, "Lallai akwai wani abu da ke shirin faruwa da mu ni da rayuwata, abu mafi daure kai shi ne, ta inda makomar Husna zata bullo a rayuwar tawa, abu mafi muni shi ne kaddarar rayuwata ta zamanto babu Husna cikin rayuwar, duk da ina cike da yakinin da wahala Husna bata zamto mata gare ni ba...." "Me ya kai ka cin wannan alwashin don Allah" Salmanu ya tare shi cikin mamaki da al'ajabi tare da zaton kamar ba cikin hayyacinsa yake ba" Adamu ya amsa cikin murmushin yake, Maîmuna Idris Sani Beli 144 Na Shiga Aljanna...1 "Akwai kyakkyawar alaka tsakanina da Ubangjina Salmanu, in dai na yi masa irin rokon da na yi akan Husna yana ba ni abinda na roka, shiyasa nake cike da fatan kutsen da Salma ta yi cikin zuciyata ba zai hana ni zama mijin Husna ba" Har yanzu Salmanu cikin mamaki yake, sai ma ya rasa abinda zai ce. Adamu ma ya kulle hira daga haka, ta hanyar ficewaya dauro alwala ya tayar da sallah. Yayin da Salmanu ya koma ya kishingida. Duk sammakon ficewar da suka doka sai da Salma ta riske su da farfesun dubiya ga Adamu. A bakin kofa suka yi kacibis da Adamu bayan Salmanu ya fice waje, duk suka dubi juna da wani bakon kallo wanda ba su saba shi tsakaninsu ba, a cikin wasu sakanni kalilan, Salma ta riga shi tankawa, "Sai ina da sassafen nan?" a Ya so ya tara gira ya kuma daure murya amma sai ya ji kasa. Ya jima bai tanka ba cikin Maimuna Idris Sani Beli 145 Na Shiga Aljanna...1 kallonta a sassauce sannan ya nisa cikin sanyin murya yа се, "Ke ma me ya fito da ke da wannan sassafen?" Ta fara kokarin shiga dakin da yake son rufewa kamar zata ture shi, da sauri ya bata hanya sannan ya bita cikin dakin yana sauraron amsar da take ba shi, "Dan abin sashe baki na kawo maka a matsayinka na maras lafiya" "Uhm" kawai ya iya tanka mata da 'ita. Ta zauna kan kujera shi ma ya nemi dandaryar kafet ya zauna suna fukantar juna, "Ya jikin?" Ta tambaya tana dubansa kai tsaye. Shi ya kawar da nasa idon ya amsa, "Alhamdulillahi" Ta cigaba da kallonsa tana son kore mamakin sauyawarsa don ita ta san dalilin sauyawar, "Kuma daga fitowarka jiyan nan daga asibiti Yaya Adamu sai ka kwashi jiki ka fice yanzu da sanyin safiya ba zaka bari ka warware ba? In Maimuna Idris Sani Beli 146 Na Shiga Aljanna...1 baka damu da lafiyarka ba fa akwai irinmu da muka damu da ita" Yayi kokarin fada mata mai dací ya ji harshensa ya kulle, mai dadi yake son furtawa zuciyarsa kuma tana kyashi, don haka ya kyale aka yi biyu babu. "Yau wai ya na gan ka duk a sanyaye?" Ta tambayae shi cikin dariyar da biyu. Ya dago kai ya dube ta kawai, amma bai tanka ba. Haka ta yi ta 'yan sambatunta yana bin tad a ido hart a sauke kular farfesunta ta samo filet ta zuba masa ta kai masa har gabansa, "To dan taba wannan tunda sauri kake in ka dawo ka Karasa sauran" Ya dubi agogo sannan ya mike yana cewa, "To bari na kira Salmanu ya taya ni" Ta yi kokarin shan gabansa, "A haba dai ka ci mana ba sai ka zuba masa wani ba tunda farfesun da yawa?" Fuskarsa ta dan nuna damuwa duk da yana yi mata fada kar ta batawa Salma, ya kewaye ta ya nufi kofa yana cewa, Maimuna Idris Sani Beli 147 Na Shiga Aljanna...1 "Ai ba za'a yi wasa tare ci bamban ba, bari dai na kira shi" Ta bi shi suka bar dakin tare tana cewa "Shikenan, ni ma zan koma Allah ya kara lafiya" Ya amsa cikin fara'ar da Salma ba ta taba gani a wajensa ba. A kofar gida suka tarar da Salmanu zaune kan dakali, suka gaisa da Salma ta wuce, shi kuma Adamu ya shi cikin gida suka fara kwasar garar farfesu. Wai sai da suka ci suka side sannan Salmanu ya ce cikin zolaya, "Mu fa samari a irin wannan kwadayin namu ake neme mu,'ka san mata da barbade-barbade" Da takaici ya kulle Adamu sai ya rasa da abinda zai fanshe ie kai wa Salmanu wani wawonkmari, Allah taimake shi ya kauce yana darrya "Kai wallahi kwankwararren mugu ne, ka san da hakan sai da muka cinye zaka fada min?" Salmanu yа сe, Maimuna Idris Sani Beli 148 Na Shiga Aljanna...1 "Kai ma yakamata ka san hakan don kai kadai ka san abinda kake ji a kirjinka game da Salma" Sai kuma Adamu ya ga gaskiyarsa, amma daga daren jiya zuwa yau zuciyarsa ba ta da zabin tunani na kanta sai abinda aka zaba mata, ko ta fara sai ta tsinke, don haka yanzun ma tsinkewa tayi daga gaskata Salmanu da ta fara. Sai Salmanu ya canja bari, "In muka fara sana'ar nan zaka ce na sanar da kai, zaka gane halayen mata da yawa" Adamu dai yayi shiru, daga shi har zuciyarsa ba a nutse suke ba, ko ragon tunani ba za su iya ba bare su yi wanda za'a yaba. Sati daya a tsakani Adamu na shan wahala iyakar wahala, tun daga zuci har zuwa gangar jiki. Duk wáni tsari da fata wanda yayi shekaru yana shiryawa a matar aurensa da iyalinsa cikin sati daya sun bi ruwa. Zuciyarsa ta zama fanko babu wani tanadi a cikinta sai jiran tsammanin abinda rayuwa zata zabar mata. Maimuna Idris Sani Beli 149 Na Shiga Aljanna..... Zuciyasa ta bude makeken fili ta share a son Salma ko ciwon shigowarta rayuwarsa, Husna na can loko sakaye da tata matsananciyar kaunar wadda ya fara jin yawa ne da ita kawai, amma tabbas zuwa yanzu ba ta da tasiri, tare da yakinin rashin tasirin nata nakasu ne a kulliyar tasa rayuwar. tS ts RO Abin ya zo masa da sauki ne, kasancewar tsawon satin suna ta fama da kujiba-kujibar harkallar da suka cacimowa kansu, shiyasa dare kawai yake mallaka yayi kukansa yayi rokonsa ga ubangiji kuma ya tunana abinda zai iya tunanawa a mafiyayyen son KOIS Salma da kuma dan asalin son Husna. se sbnsw ty na sied sd Sun gyara muhallin da zasu fara bokancinsu, yanzu suna cikin atisaye ne na dabarun karbar kostomomi yadda bokayen gaske suke, da kuma koyar rufa idon da zasu dinga yi wa maziyarta, ga Adamu kenan wanda bai san kan garin ba. Zuwa yanzu dai ya haddace rufa idon da ake da kwai, Tiyo, kyandir da kuma karkashi. Sun samo wani abokinsu takadari irinsu mai suna Tanimu, tafiyar ta koma ta mutum uku, Salmanu ne Boka, Adamu zai dinga aiki biyu, Maimuna Idris Sani Beli 150 ls8 in62 ainbI snumisM Na Shiga Aljanna...1 muryar aljanu yayin da yake boye, in ya bayyana kuma ya zama dan kore ga Boka, Tanimu kuma shi ne mai nemo kostomomi, wataran kuma yayi shigar burtu a zuwan kostoma ya yi ta koda boka a gaban bakin kostomomi, sun shirya in harka ta kankama zasu nemai karin yara. Yadda suka dauko tafiyar sun hango mata samun tsabar kudade da nasarori, don haka dukkansu hankalinsu kwance suke komai. ******** Ranar juma'a da yamma yana zune a dakalin kofar gidansu zuciyasa a mugun kuntace, ya dinga ayyana, ina ma shi yaron goye ne, tabbas yau da uwarsa ta shiga uku da tsinannen kukan da zai balle mata hancinsa, a yau sai ta gwammace bata haife shi ba: Kuma da girman nasa ma ya so ya kwantanta har ya shiga daki ya fara gwaji, amma da ya fahimci aikin baban giwa yake babu wanda ya san yana yi kawai sai ya share hawayensa ya fito waje yana rarraba idanu. Kamar daga sama ya hango Husna ta nufo shi kai tsaye, ta ci kwalliyar da bai taba ganinta Maimuna Idris Sani Beli 151 Na Shiga Aljanna...1 cikin irinta ba, kai bai ma taba ganin wata 'ya mace mai daura zani a hannun hagu ta yi ba. Kawai sai ya saki baki yana kallonta cikin matsanancin bugun zuciya har ta karaso gare shi, sannan ne ya lura tana dauke da wata leda kunshe da kaya. Ya sauke wata wawuyar ajiyar zuciyar da ya so hadiye ta amma ta sanya masa karfi, ya kawar da kai cikin jin gaba daya ma ya san ya gama bayar da maza. Da sassanyar muryarta ta yi masa sallama. Ya amsa da tasa dakusasshiyar muryar ba tare da ya dube ta ba, ya kuma rasa dalilin da ya sa ya kasa duban nata. "Ranka ya dade wannan gimbiyar taka kuwa tana gari? Na ga ba ka nemi dinkin nata ba gashi kuma tun jiya muka fara bikin" Ta fada cikin matsananciyar fara'ar da tayi awon gaba da dukkan fargabar da ke kakale a zuciyarta Cikin kumaji ya juyo yana dubanta kai tsaye, kirjinsa na dakan uku-uku amma karfin halinsa ya gama bayyana ilahirinsa, yayin da soyayyarta ta fito daga sakon da kaddara ta bayar da ajiyarta Maimuna Idris Sani Beli 152 Na Shiga Aljanna...1 tayi awon gaba da ta Salma wadda ta yi gida ta tare, "Duk wata gimbiya ai bayanki zata bi ranki ya dade" Ya fada cikin sanyin murya yana yi mata kallon da shi kansa ya san karya ne a ce bai bayyana tsantsar kaunar da yake mata ba. Ta dora dan alinta a kirji tana bude da baki cikin shauki da yi masa kallon mamaki, amma bakinta ya kasa furta kalma, Ya kada kai mai nuna tabbatarwa, "Na rantse da Allah dama kayanki ne Ta ji tsaiwa na neman gagararta, sai ta doge, ta rausaya kai har yanzu ta rasa bakin Magana. "To yaya hidimomi?" Da kyar cikin sarkewar numfashi yanzu ta daure ta tanka, "Alhamdulillahi, komai na gudana yadda ake So "To masha Allah, dama yanzu da nake zaune tunanin yadda zan riske ki gidan bikin nake" Ta sake dubansa galala. Shirunta ya cigaba da bashi karfin halin Magana, musamman yadda take dubansa cikin Maimuna Idris Sani Beli 153 Na Shiga Aljanna...1 sanyin jiki yana da yakinin tabbas ita ma So yayi mata wawurar da yayi wa zuciyarsa da ilahirinsa. "Zuwa yanzu na gama juriyar hadiye soyayyar da zuciyata take miki, in ban samu na furta ba ina da tabbacin zamu iya shari'a da zuciyar" Tamkar jiri zai tika ta da kasa ya fasa, garin kuma ya dauki haramar zagayawa da ita. Cikin haka ta kwato furucin, "Ni ka ke so?" Ya amsa, "Menene na shakka?" Ta yi saurin girgiza kai. "Ba shakka nake ba, amma me yasa sai na zo kofar gidanku zaka fada min? ka ragewa son da ka ce kana yi min daraja" Ya girgiza kai cikin sanyin jiki, "Kar ki fadi haka, son da nake miki ina da yakinin ba a taba irinsa ba, amma sai jiya na san gidanku kuma a yau din nan naked a niyyar zuwa" Farin ciki ya rufe Husna, sai ta kasa tankawa. Suna tsayen nan kowa sai numfarfashi da murmushi. Maimuna Idris Sani Beli 154 Na Shiga Aljanna...1 Kwatsam sai ga Salma tamkar an jefo ta, ita ma ckin kwalliya tana sanye da irin kayan dake jikin Husna. Adamu na ganinta ya ji tamkar an ruguzo masa dutsen dala a kirji, jikinsa yayi sanyi kalau, zuciyarsa kuma ta dakata da zabі, Aka yi gaisuwar mutumci tare da ambatar sunan juna tsakanin Husna da Salma na shaidar an san juna, kai tsaye kuma Salma ta fara gabatar da Adamu a wajen Husna a matsayin dan uwanta, sannan ta zarce da cea, "Kuma shi ne wanda zan aura in Allah ya so" Duk da Husna macace mai siyasa, amma siyasar tata ta kasa galaba a wannan muhallin, sai da idanunta suka kankance suna shirin fara zubar da hawaye, ta bi Salma da kallo wadda fuskarta ta nuna alamar da gaske take. Da ta juya ta dubi Adamu shi nasa arzikin ma sai ya ci uban na jiya, domin kada mata kai yayi cikin tabbatarwa ya kuma amsa mata da baki. "Haka ne, za mu yi aure cikin kankanin lokaci" Maimuna Idris Sani Beli 155 Na Shiga Aljanna...1 Husna ta dauke kai daga kallonsa lokacin da wani malalacin hawaye ya sulmiyo mata ta yi dabarar goge da mayafi. Ko Adamu ya san tarkon sonsa ta fada ne shiyasa takanas ya shiryo mata wannan cin fuskar? Sai ta daga kai ta cigaba da tsura musu ido su duka dan ta gane siyasar ce, cin fuska ce ko kuma iyakar gaskiyarsu kenan? Kamar sun manta da ita sai suka lula cikin hirarsu da ke bayyana son da suke wa juna kai tsaye. Zan cigaba a kashi na biyu. Taku Maimuna Beli Ga kadan daga littafina mai zuwa nan ba da jimawa ba. RIGAR SILIKI.. "Gwajin HIV?" Maimuna Idris Sani Beli 156 Na Shiga Aljanna...1 Mujahid ya jaddada cikin kallon likita da haushi da kuma mamaki. Likita ya kada kai yana tsura masa ido cikin tabbatarwa da nuna babu fa canji. "Haka na ce Mujahid ya cakumi wuyansa kamar zai gwara kansa da bango, amma sai ya sake shi cikin huci ya shi hargagi, "Haka ka ce din addini ne, ko fadar Allah ce da ba'a gogewa? Likita ya shiga gyara wuyar rigarsa da Mujahid ya cukwikuya, fuskarsa na son nuna hakuri da shanye damuwa, ya dubi Mujahid da kyau ya ce, "Abinda ka yi bai yi maka kyau a zamowarka lauya ba, yanzu in na tafi neman hakki bisa wannan cakumar da ka yi min, me kake tsammanin zai biyo baya... a kan aikina kake cin zarafina?" Mujahid ya tare cikin hargagi, "Komai ma ya biyo bayan mana, ka tafi kotun duniya in ka so. Ban da kai dan iska ne, matar auren zaka kawo wa maganar gwajin HIV? In zargin hakan ne me yasa ba zaka ce ni mijinta Maimuna Idris Sani Beli 157 Na Shiga Aljanna...1 zaka gwada ba? In dai ba shirin tozarta min iyali dama ka yi ba" Likita ya dinga duban Mujahida cikin takaici, kawai sai ya watsa masa sakamakon gwajin HIV din da suka yi wa matarsa Binta. "Gashi nan, ai yanzu ma bata baci ba, in ka gama duba wannan kana iya zuwa Lab kai ma mu gwada ka" Jikin Mujahid a salube ya shiga dakin da Binta ke kwance. Bai tarar da Salima ba sai Binta kawai zaune kan gado ta kwanta jikin filon da ta jingina da bango. Fuskarta nan nuna farfadowa daga cuta, idanunta sun yi zuru-zuru, sai dai fa ko kadan babu wani annuri a tare da ita wanda zai sa a zaci tana cikin tashin hankali ko kuma nadama, kallon iskar da ta saba wa Mujahid da shi ta karbe shi yau ma. Shi yau tasa fuskar babu walwalar da ya saba tarenta da ita duk irin yadda ta kai ga bori, hasalima bata taba ganinshi cikin bacin rai irin Maimuna Idris Sani Beli 158 Na Shiga Aljanna...1 na yau ba tun saninta da shi, amma a hakan ta debe shi ta watsar. Ya ja kujerar gaban gadon ya zauna yana mika mata takardun da likita ya watsa masa cikin kallon fuskarta kai tsaye. A wulakance ta karbi takardar ba tare da ta duba ba ta yasar gefe, kuma cikin shan kamshi ta dube shi da kyau ta се, "Ni ya fara kawo wa na gani kafin ya baka" Sai ya sake dubanta cike da mamaki, ya ce, "Kin kuma duba takardar kin ga rainin hankalin da take dauke da shi?" Ta sake watsar da kai gefe tana cona baki, "Na gani, ai ba rainin hankali ba ne, iyakar gaskiyar kenan" Yanzu duban mahaukaciya yake mata. Dan ta nuna masa da hankalinta ta juye ta dubi kwayar idonsa fes! Ta ce, "To wai kai meye na tashin hankali don an ce ina dauke da cutar kanjamau? Ko ka manta tuni ka ci alwashin ko yaya zan kasance kana so? Ai baka zabi in na zo da kanjamau baka so ba, in kuma zaka zaba yanzu ma bata baci ba" : Maimuna Idris Sani Beli 159 Na Shiga Aljanna... Mujahid ya jima da hankalinsa tsakanin Kary da gaskiya a tunani da hasashe, sai can ya mike cikin nuna yakini da kumaji ya ce, "Na tuna an yi hakan, ban zabi kanjamau ba amma yanzu na zaba... nan gaba ma in zaki zo da abinda yafi kanjamau ke da su duk ina so.. kar ki damu, ki ji sauki ki zo mu koma gida mu cigaba da jinya... in ma lahira kika tafi zan nade Kafar wando na bi ki" Rigar Siliki...!!! Sadaukarwa ga Mujahid Muktar Misau. Maimuna Idris Sani Beli 160 An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke

Chapter 6 of 7