Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 7
maimaita tambayarsa cikin fishi. Bayan sun shiga ma Adamu na neman guri musamman ya zauna sannan ya fito da kudin don ya san ba karamin aikin Salmanu ba ne in Maimuna Idris Sani Beli 109 Na Shiga Aljanna...1 Barnar da yayi wa kudin ba ta yi masa dadi ba yayi masa mahangurba yanzu. Ilai kuwa, hana shi zama Salmanu yayi sai ture shi yake yana hayaniya. Haka dai ya daure ya fito da ragowar kudin, sai ga shi dubu uku, wato ya ba Husna dubu takwas. Salmanu ya kasa Magana don haushi, sai kawai Adamu ya basar ya ce, "Mu cancana wannan mu yi da su, na san albarkacin sadaukarwar da na yi wa soyayya وو zaka ga Allah ya buda mana.... Bai kai ga rufe baki ba Salmanu ya sakar masa wani wawan naushi a ciki, wanda ya sanya shi zubewa kasa wanwar a sume, jini na fitar masa ta hanci. Ko kadan Salmanu bai yi nadama ba, domin neman guri yayi ya zauna yana ta kunno ashar, "Dan iska, wannan dukan ma ka sadaukarwa soyayyar" Maimuna Idris Sani Beli 110 Na Shiga Aljanna...1 Ba a son ran Salma ta bi Anti Sa'a unguwar da ta gayyace ta ba saboda saka ran Adamu yana dab da iso mata da ankon da ya sai mata, kamar yadda ya sanar da ita. Ta yi gardamar zuwa unguwar, ita ma Anti Sa'a ta yi lallashin har sai da ta kai ga zagi sannan Salma ta hakura ta shirya suka tafi. Anti Sa'a na ta faman mita, "Banza ce ke wallahi, na rantse miki da Allah idan muka je muka dawo, zai yi wahala Adamu ya kwanta bacci ba tare da ya dawo ya nemi inda kike ba" Wasi-wasi da mamakin duniya ya ishi Salma, bayan wani tsantseni da bai taka kara ya karya ba wanda yake kawo wa zuciyarta shawagi. Antinta ta wayar mata da kan inda zasu kai Adamu, gidan wani boka ne mai aiki kamar yankan wuka. A duniyar soyayyar Salma Kauna bata ce haka ba ko da kuwa haramci ya kau, to amma dai tunda mutuwar yawa kaka ce sai ta bi ayari, a yadda Anti t ace mata duk matar da ba kai mijnta ko saurayinta gidan Maimuna Idris Sani Beli 111 Na Shiga Aljanna...1 boka a wannan marrar to tabbas ita take zaman hakuri da shi. Da alama kalaman karfin gwiwa ne Antin ke mata, amma tsoronta ya ci dubu sai ceto, don ta shafa karfin gwiwar ta rasa. "Kuma mutane ba zasu ga bekena ba idan aka gan ni budurwa wai na kai saurayi gurin boka dan ya so ni?" Ta furta cikin rawar murya bayan ita da zuciyarta sun gama sakankancewa sun shiga uku. Anti Sa'a ta tuntsire da dariya tana yi mata kallon mamaki, ta ce, "Lallai Salma kanki a tukunya yake har yanzu. Shin baki san yanzu 'yammata ma sun fi matan aure gane aikin boka ba? Zura ido ki kirga min matan aure da 'yammata in mun je" Da haka Salma ta saduda ta bayar da gari, yayin da bangaren shirya mafarki a zuciyarta ya lula shirya mata auren Adamu da kama mata shi a hannu yadda zai amince su shirya iyali masu kyau da soyayya. A can cikin kauyen Bunkure suka iske gidan Bokan. Kamar yadda Anti ta labarta Maimuna Idris Sani Beli 112 Na Shiga Aljanna...1 mata yammata sun fi matan aure yawa a wadanda suka tarar a alayi, sai ko dima-diman motocin da suka cika farfajiyar unguwar bokan. Da Salma ta tambayi Anti Sa'a game da manyan motocin sai ta amsa mata da cewa, ai motocin 'yan siyasa da 'yan kasuwa ne, don ko 'yan siyasa sun fi mata lakantar zuwa gurin boka da matsafa, ta kare da cewa, "Mata na hada kafada da 'yan kasuwa da kuma 'yan sane" Sai Salma ta ji zuciyarta ta yi wani irin rauni, kamar hawaye ya zubo mata jin cewa har da 'yan sane tana hada kafada ba ma 'yan kasuwar ba, kai! Maza ba su yi ba aradu tun da ba sa abinda ake so sai an shako su ko an biyo musu ta bayan gida. Ta bar damuwarta a zuci da fuska kadai, ba tare da gangar jikinta ta kasa aikin bin Anti Sa'a ciki suka hau layi a bencinan dake jere a soro cike da mata. Akwai kuma wani Katon soron wanda maza zalla ke bin nasu layin. Salma na ta rarraba ido tana shan kallon kosassun matan da idan ta gan su a gari sai taci layar duk inda matsala take ba su san ta bare su Maimuna Idris Sani Beli 113 Na Shiga Aljanna...1 je gurin boka neman warakarta, a ganin Salma ga su da kyau, ga kudi, to me suke nema? Kamar Anti Sa'a ta san abinda Salma take rayawa a ranta sai ta hau kara mata bayani duk dai dan ta karfafa mata gwiwa. "Wasu matan ba wai matsalolin miji kadai kan kawo sun nan ba, zaki sami ma'aikata da masu matsala da dangin miji ko kuma son mayar da kishiya bora, kai wata ma bata dakishiyar sai 'ya'yan miji, sabda haka su ne kishiyoyinta kuma in ba shan kansu tayi ba to ba zasu ta6a barinta shakar numfashi a gidan aurenta ba... Kin ga, dubi waccan!" ta katse bayanin da take mata tana nuna mata wata zankadediyar farar budurwa cikin rage murya, "Kin gane ta?" Cike da mamaki da shakku Salma ta kada kai, "Na gane ta, shahararriyar "yar fim din nan ce, amma na yi mamaki.. kodayake kila ta kusa دو aure Anti Sa'a ta tuntsire da dariya tana cewa, "Ana baki kin a kin karba, maganar me nake miki yanzu? Ba batun da ke sa mutane Maimuna Idris Sani Beli 114 Na Shiga Aljanna...1 bin malamai muke ba? Kuma n ace miki ba wai sai matsalar miji ko ta saurayi kawai ke kawo mutane ba, na saba ganin 'yan fim maza da mata a wajen nan suna neman daukaka da farin jinni, ke fa nake gaya miki wallahi wata ma mijin makociyarta zaki ga ta kawo. Rayuwar ta yanzu gaba daya ta neman dafa'I ce, in kuma ka matse hannun nema to kuwa sai dai ka zauna a rayuwar kana ji gani gani ka zama mara sa'a, talaka mai bakin jinni da mummunar fuska" Sai da Salma ta daga kai ta dubi Anti Sa'a bayan ta diga wa zancenta aya, ta dubi fuskarta da kyau sai ta tabbatar da gaske take a maganar da ta karkare batunta da ita, Salma ta ji hanjin cikinta na wani mugun kadawa da dalilai biyu, na farko in bata nemi wannan dafa'in na zuwa irin wannan kazamin gurin ba zata zama talaka mai mummunar fuska da bakin jini kuma mara sa'a a rayuwa, na biyu idan ta nemi dafa'in tabbas tana shirin canjawa ne daga asalin Salma da ta dade da sanin kanta zuwa wata daban da ba ta gama ammana da irin rayuwar Maimuna Idris Sani Beli 115 Na Shiga Aljanna...1 da ta tsoma kafa ba kuma bata san inda zata riska in ta nade hannun zani ta fara tafiya ba. Tana ta wannan tuntuni har layi ya zo kansu, kuma karin gargaba da bugun zuciyarta, mutum daidai ake shiga dakin bokan, bare ta shiga da Anti Sa'a tayi mata jagora. Haka dai Anti Sa'ar ta yi ta tausar ta sannan ta tura ta. Daga bakin kofa kafin ka shiga akwai wani dogari tsaye rike da wani bakin koko cike da kananun layu, duk kostoman da zai shiga sai an bashi guda ya hadiya sannan ya shige ciki. Har ga Allah ba da son ran Salma ta hadiyi layar nan ba, don dai kawai ta kawo kanta ne, kuma ma dai ta ga gomomin mutane sun hadiya sun shiga sun fito kalau, kuma gobe ma suna dawowa kamar dai Antinta Sa'a. Tun daga kolin kanta har tafin kafarta karkarwa suke, ta bankada labulen dakin ta shiga tare da rafka sallama. Ba kamar yadda ta tsammaci ganin bokan ba, wato sanye da kayan tsafi ko tarkacen kayan bori rakwacam! Maimakon haka sai ta ganshi hakimce kan kujera ya ci manyan kaya tamkar wani saraki har da rawani, fari tas da Maimuna Idris Sani Beli 116 Na Shiga Aljanna...1 shi kamar shi ya zabo kansa musamman da yake yana da alamun yanzu yake dosar shekarun tsufa ba a cikinsu yake ba. Sai dai fuskarsa a matukar murtuke ya zubo mata ido ba tare da ya amsa sallamarta ba. Tamkar Salma ta yi girgiza ta zama ba ita ba saboda tsabar firgici da fargaba, ta yi diradira tana cigaba da yi masa sallama. Ya ci gaba da kallonta rai a bace ba tare da ya tanka mata ba, har sai da dan kanta ta yi wa kanta wajen zama ta kuma ja bakinta ta tsuke kai a kasa, amma tana samun damar kalle nan da can a kusurwoyin dakin wanda yake shaida kasancewarsa dakin bokanci. Bangwayen dakin duk an lanyace su da zannnuwan shudin saki da fari, ga kuma hatimin gidan sarauta a guraren da ba su sami adon zannnuwan sakin ba, abinda kuma ya daure kan Salma kenan. Amma dai ta ci gaba da kallon yadda dakin ya sha korai masu fenti shantuna da sauran dangin kayan duma, sai layu bankwala-bankwala rarrataye bakake da jajaye hade da wuri tare da wasu karafa da Salma ba ta san sunansu ba. Sannan akan ko Maimuna Idris Sani Beli 117 Na Shiga Aljanna...1 wacce kusurwa ta dakin daga kasa akwai katuwar kwarya zaune kuma daya cikinta wani hayaki ke fita tamkar dai an kunna turaren wuta, wannnan gaskiya shi ya fi tsorata Salma, dan tana da yakinin sai tsabar sihiri ne zai zaunar da garwashi cikin kwarya ba tare day a kona kwaryar ba....." Bata gama shan kallonta da nazarin dakin bokan ba gajiyayyiyar muryar bokan ta katse mata hanzari, "Yanzun haka Adamu na kwance gadon asibiti" Abinda bokan ambata kenan ya sanya ta razanar dagowa ta kalle shi duk da kuwa kunnuwanta ba su gama tantance abinda ya fada ba illa sunan Adamu da ya bata mamakin ji a wannan muhallin. Ta zuba masa ido da kallon tsoro da rashin fahimta, shi kuma bai yi kasa a gwiwa bay a sake maimaita mata, "Masoyinki Adamu a halin yanzu yana kwance a gadon asibiti bai san inda kansa yake ba" "Inna lillahí wa inna ilaihi raji'un" Maimuna Idris Sani Beli 118 Lusensita de БИ Na Shiga Aljanna a, lada.bda munacrazanale fuaka amma cikin zuciyarta tana karyata bokan jayas Adamun da suka sabusdafiyalafiya zabaidada mata mummunan labari a kansa mara dadiр irin haka Wai me har da maĝailar bai gaida kansa yake ba saboda tsabaririuguh fatab sb s ksasbi ki je gida shi kinhtarar da abinPA faga kinigamsu sannan kindawo kisan sitrd kike nemaja kansab ustsm aianij s ibl aa sdst iss evSalinacta kara rudewa dastargane bakan ha gang har ahinda ke cikin ztrciyarta, mirda niad ta hayicin laya Sa shud as staddst st ideWallahisgrapkaa yas dads stin ifyanzusgisb gamsnu ka yi min rai karsaurafisabindalzts shi" serbleds s usber usbA asnue siasl Ya jimathaintankaaibmyeammiasidonsalda kantabrs os kr agked iomidst sT sDuksta bii td lirkiaes ndiyaetasvhausonnilsd kamo tashar dana-sanin zuwanta, amnd ca tsoron hatsabibin bokan: ya shigalzudkiyasta ya gang abindasta erayeh doio hakaura oicanaHsy kakkacewa tashoshi dåssuky dongandsd bokankarshevmarkawaiisailtayl dabaarea 76267 68 sinobi s vist st sliswal ted SPISTIOUS Maimuna Idris Sani Beli 110lsd ia62 zirbI GnumisM Na Shiga Aljanna...1 tashar mafarkin soyayya da Adamu ta zama gaskiya. Dai-dai wannan gaßar ne kuma Bokan ya tanka, "Adamu ya fada wata zazzafar soyayya ba tare da dalili ba, duk wata mace a duniya yana kallon kawai wadda yake so ta rako duniya, lallai ba don kin zo nan ba har abada Adamu ba zai taba sa ki a jinsin matan da zai so ba" Yanzu tsakani da Allah Salma ta ba wa Boka dukkan imaninta, ko bai san gaibu ba to ta tabbatar an buda masa wani abu da ya dangance shi. Ta zo wajensa ba sanar da shi abinda ya kawo ta ba, amma ga shi yana batu a kanta, sunan Adamu radau a abakinsa. Cikin sakankancewa ta muskuta ta ce, "Na fahimci hakan, ranka ya dade tunda da bakinsa ma ya sha fada min ni ba irin matar da 99 za'a so ba се... "Ki bar shi kawai, da mu yake zancen. Ba shi yau ya farfado zuwa gobe duk tsiyarsa sai kin yagi wani abu a soyayyarsa" Salma ta ji wani irin rauni ya mamaye zuciyarta har kwalla ta taru a idonta. Ba yagar Maimuna Idris Sani Beli 120 Na Shiga Aljanna...1 wani abu take son yi a soyayyar Adamu ba, kulliyar soyayyarsa take so saboda haka ta ji sanyin gwiwar yadda bokan nan mai gani har hanji yake batun zata yagi wani abu soyayyarsa. "Kin fiye garaje" a Bokan yace mata lokacin da ya miko mata wani kunshin hoda da ba ta san yadda aka yi ya zo hannunsa ba. "Duk mai hulda da ni sai ya yi yadda yake so a rayuwarsa kar ki dinga zatawa aikina ragontaka, Ungo nan!" Ya cilla mata kunshin hodar. Jikinta na karkarwa ta sa hannu ta dauka tana bin sa da kallo, "Ta zama hodar sawar ki duk lokacin da ki ke hasashen zaku haďu da shi" Ya sake cillo mata wani daurin magani. "Wannan duk yadda za'a yi ki bashi a abinc ko a ruwa ko da sau daya ne, Adamu ya zama naki in kin yi wannan... ajiye sadaka ki tashi-ki وو tafi sai kin kawo min goron daurin aure' Jikin Salma sai bari yake ta zuge jaka ta kwanto dubu biyar din da Anti Sa'a ta bata ta ce Maimuna Idris Sani-Beli 121 Na Shiga Aljanna...1 ta bashi, ta mika masa yayi mata inkiyar ta zube kan dardumar gabansa. Ta ajiye ta mike tana faman sharara masa godiya ta fice yana bin ta da wani irin kallo da har keyarta ta ji shigar kallon. A waje ta yi jiran Anti Sa'a wadda layin ya zo kanta, ta dinga mamaki da al'ajabin jin cewa ashe wai duk so da kyautatawar da Alh. ke wa Anti Sa'a ba so da kirkinta ne ya janyo mata ba? Dama wajen boka ta ke kai shi? Shiyasa ake ganin tana samun kudi amma a rasa inda take kai su? Yanzu ita ma haka zata sami irin wannan gatan na kwatance a Adamu? Amma kuma ta rasa ajiye abin kanta? Ta binne wannan mamaki da tunane-tunanen bayan Antin tata ta fito, suka dauki hanya cikin tattauna tadin Bokan, a nan ne Salma ta ji abinda ya ruda zuciyarta ya kuma so ya sanya ta sauka daga wannan turbar ta bin bokan, wato Anti Sa'a take kara mata bayanin dalilin da ya sanya aikin bokan ke matukar ci kamar yankan reza, inda ta ce mata, "Na taba jin bayanin cewa aljanu na yi wa bokaye biyayya ne gwargwadon yadda suka shata maka sharadi ka bi, shi wannan Bokan Maimuna Idris Sani Beli 122 Na Shiga Aljanna...1 babban hadimin aljaninsa dan sarkin agadas ne, an ce kafin ya bashi aljanun da zasu dinga yi masa hidima suna yi masa biyayya ido rufe sai da ya ba shi sharadin zai daina sallar la'asar kwata-kwata kuma zai daina halartar sallar juma'a cikin jam'i sai dai yayi tasa a gida, sannan wannan karagar da yake zaune a kai karkashi shimfidar akwai kur'ani izifi sittin. Wannna shi ne sharadin da ya cika ake biya masa bukata, don haka duk wanda ya ce miki ya zo wajen malamin nan bukatarsa ba ta biya ba, na rantse miki da Allah ya ci karya ya kwana da yunwa" Wannan bayanin sai da ya so sanya jiri ya kai Salma kasa, duniyar ta dinga juya mata cikin jin tsananin mamaki tana duban fuskar Antinta wadda ke halartar islamiyya duk asabar da lahadi, amma wai ta dage tana yi mata bayanin bajintar nan ta boka a wajen saßawa Allah da sunan labarin birgewa. Ba ta farko daga rudaninta ba Anti Sa'a ta sake kashe ta da wani labarin takaicin, Maimuna Idris Sani Beli 123 Na Shiga Aljanna...1 "Amma dan tsabar son yada jita-jita irin na mutane, rannan na ji wani malamin addini a radio yana ba da misalin bokan a fakaice ba tare da kama suna ba, wai shi a dole masanin bokaye da sirrin aljanu, yake cewa, wai layun da maziyarta gurin bokan nan ke hadiya kafin ganawa da shi ta wannan hanyar yake zaunar musu da aljanu a zuci da sauran sha'anoninsu wadanda zasu zama 'yan sa ido kansu da wadanda suke son a yi wa sihiri, kuma wai ta wannan hanyar ne yake sanin abinda ya faru da mutum kafin ya sanar da shi, kuma ta wannan hanyar ne bokan ke ribace imanin masu zuwa gurinsa har suke ganinsa kamar wanda ya san gaibu, ... ki ji don Allah, hassada kiri-kiri, shin Allah ba zai yi baiwa ga mutum ba sai da wani dalili?" Wani tsinannen takaici ya cunkushe wa Salma a makoshi, ta yi kokarin ta hadiye shi ya faskare, dole ta ji ko yaya ne yakamata ta rage wa bokan nan karfi a fuskar Anti Sa'a ko da kuwa da fatar baki ne kuma ko da ragewar ba zata tsinana komai ba na janyewar su ga bokan, ita kanta ba ta fara mafarkin ta guji bokan ba, Maimuna Idris Sani Beli 124 Na Shiga Aljanna...1 musamman saboda furucinsa na cewa duk mai hulda shi sai yayi abinda yake so a rayuwarsa, ita Adamu take so a rayuwarta kuma da alama ta hanyarsa zata same shi. "Kila maganar malamin da kika ji a radion gaskiya ce, tunda ko kin ce ai ajanu ne suka tsaya masa, mu dai mu je ya biya mana tamu bukatar in ma da laifi sai mu dawo mu yi istigfari "Ai shiyasa nake yawan sadaka Salma, ni ma ai na san akwai laifin, akwai lokacin da nake jira na dena musamman kwanaki da boka ya sa ni hada wani asiri, ni da kaina na san akwai kaucewa a ciki, sai dai kawai mu yi ta rokon 29 Allah ya yafe mana "Amin" Salma ta fada a darare, domin ita kanta ta san wannan ta'addaci ne aka kinkimo aka kai wa Allah b "Ko me ya sami damu? A tsorace nake wallahi" b In ji Anti Sa'adatu, kum fadar tata ce ta dawowa da Salma damuwarta da ta sanya ta kasa ko tankawa. Maimuna Idris Sani Beli 125 ******* Na Shiga Aljanna...1 Salmanu yayi jiran farowar Adamu tsawon fiye da mintina talatin, da bai farfado din ba ne kuma hankalinsa ya tashi har ya fara sambatu. "Ka ga dan iska, idan ka zarce ai ka yi wa soyayya asara, ni kuma ka janyo min jafa'i a се ni na kashe ka" Yana ta faman irin wadanna sambatun ya debo ruwa ya shafawa Adamu amma kamar an shuka dusa, sai hankalinsa ya kara mungun dugunzuma, ya kame kugu yayi tsaye tsakiyar dakin yana shawarwari, duk hange hangensa ya rasa tudun dafawa, can sai ya sake debo wani sambatun, "Dama ni bokan gaske ne ba sai na fara aikina ta kan wanna shegen ba, daga wasa sai ka kama ka macewa mutane, tun farko ma ban da kai wani shegen tunku ne uban waye yace ka bayar da kudin, yo ko ubana ne yayi min abinda ka yi ba sai na dirka masa naushin da zai ziyarci Maimuna Idris Sani Beli 126 ☑ Na Shiga Aljanna...1 barzahu bai shirya ba, kai ma sa'a ta ka ci wallahi" Maganganun da yake fada ba su yi kama da fuskarsa mai nuna tsananin tsoro da fargabar yadda abokinsa ke kwance hanyar rasa rai ta dalilinsa ba. Ya sha hange-hange kafin ya kullo dabarar da zai je Hajiya da ita, ya fito dakin yana hawayen karya amma bakinsa bai fasa kuri ba, "Dan iska kawai, na rantse da Allah ban da wancan furojet din namu na sana'a in ka mutu zan jima kafin in samu madadinka, Kur'anin Ubangiji da bar ka zan yi ka tafi kawai" Ya karasa maganarsa a ciki lokacin da ya shiga cikin gidan, aka yi sa'a suka yi kacibis da Hajiya ta fito daga kicin rike da galan din kananzir, Tana kallon Salmanu idonta ya shaida mata tashin hankalin da yake ciki, ita ma nata hankalin a tashe ta hau baibaye shi da tambayoyi, "Lafiya kuwa, ina Adamun?" "Yanzun nan wani la'anannen tsinannen matsiyacin direban babur ya make shi ya tsere, Maimuna Idris Sani Beli 127 Na Shiga Aljanna...1 na kwaso shi mun taho gida bai san inna konsa yake ba saboda sisin kobo babu a aljibuna Sai ya karasa maganarsa ta hanyar barkewa da kuka. Kafin ma ya dire Hajiya ta yi hanyar soro tana rafka salati gami da hirji. Salmanu ya bita a baya yana ta faman kwashe wa direban babur albarka kuma yana kuka haikan tare da bawa Hajiya labarin Karya akan hatsarin, ya ce mata ta cikinsa ya kusa bi da tayar mashin din, duk yadda-aka yi a ciki ya sami matsalar. Hajiya na jinsa tana ji da danta, ba ta tankawa Salmanu ba sai da ta bugawa Alh. waya ta sanar masa komai ya taho daga unguwar da ya je a gigice sannan ta juyo ta fuskanci Salmanu cikin tausayawa ta ce, "Halinku daya dai da abokin naka Salmanu, kun fiye amfani da munanan kalmomi, yanzu don Allah wadannan alkaba'in da kake janyo wa mai laifin nan da wannan tsine-tsinen da kake masa duk ya cancance su, yaushe laifin nasa ya kai haka Salmanu? To ka yi hakuri don Allah ka yi masa addu'a tagari wato addu'ar shiriya, shi Maimuna Idris Sani Beli 128 Na Shiga Aljanna...1 kuma abokinka sai ka dinga yi masa ta fatan samun sauki" Salmanu ya hau matsar hawaye yana kada kai ba tare da ya tanka ba. Alh. na zuwa aka kwashi Adamu asibitin Murtala a sume. "Kar mu ce bigewar mashin ce, yanzu sai su sanya mana ka'idar sai mun zo da 'yan sanda" Alh. ya kawo shawarar nan, ta yi wa Salmanu dadi ainun, cikin doki da garaje ya ce, "Nima na yi wannan tunanin Alh. kawai sai mu ce faduwa yayi kan kwalbar lemo" "Haka za'a yi" Alh. ya amsa zuciyarsa daya. Bayan sun kai asibitin Salmanu na kan gaba wajen kurda-kurda da kuka shaße-shaße da hawaye, babu wanda bai ji tausayinsa, don haka ne ma da aka baAdamu gado, Alh. ya bar Salmanun ya tafi gida shaidawa iyalinsa da kuma kwamtar da hankalin Hajiya wadda yayi dabarar kin tafiya da ita don kar ta zo ta daga hankalinta. To ya manta ma iyalin nasa ta je unguwa, don haka kawai sai ya je ya kara rarrasar Hajiya sannan ya koma asibitin. Maimuna Idris Sani Beli 129 Na Shiga Aljanna...1 Har yamma suna tare da Salmanu wanda ya fi shi tarin damuwa da cutar, don haka ne ma sai ya zama kämar shi ne dan uwan Adamun a idon likitoci shi suke kira don karin bayani ko neman wani abu kasancewar asibitin ba'a ganin mara lafiya sai lokacin ziyara. Wannan ta sa shi kansa Alh. a bakin Salmanu ya ji cewa Adamu ya farko kuma jikinsa da kyau yana baccin gajiya, duk suka taru suka yi ta farin ciki. "Sun ce zuwa dare ma zasu sallame mu In ji Salmanu. Alh. ransa yayi dadi, ya ce "Abin yayi kyau, dama ina zaman asibiti ya ga dadi, ga mahaifiyarsa can hankali a tashe, gara a kai mata danta ta ga lafiyarsa Lokacin ziyara na yi Salmanu ya yi dabarar silalewa ya riga Alh. shiga dakin da Adamu ke kwance, ya same shi zaune jingine da filo yana kurbar maltinar da Salmanu ya siyo masa tun yana mace. Ya zauna bakin gadon daga gefensa suna yi wa juna kallon kuda, da alama kowa bakinsa cke yake .da zance, amma sai Salmanu ya riga shi Maimuna Idris Sani Beli 130 Na Shiga Aljanna...1 furtawa cikin murya kasa-kasa kasancewar dakin ba Adamu kadai ba ne mara lafiya. Babu alamar ciwo a tare da shi yanzu amma fuskarsa ta nuna jigata da farkowa daga ciwo. "Malam ka daga min kafa, na ce Mashin ne ya bige ka, banza kawai daga naushi daya sai ka macewa mutane?" Adamu ya jima bai tanka ba. Salmanu ba ya shakkar in Adamu zai kasa goya masa baya, ba yau yake da shi ba ba jiya ba Hasashensa kuwa ya ci, domin sai gashi cikin murmushiAadamu ya се, еек y en t "Ка сci sa'a ban mutun ba Salmanu, in na mutu ni đa Hüsna ba zamu taba yafe maka ba, don ba ka bar mu a duniya mun auři juna ba ihu, Salmanu ya kai masa bugu cikin murna da ed uobs'2 "Au har ita ba zata yafe min ba? Ita da bata ma san kana yi ba?" revAdamu ya kawar da kaiyslaw i umbA EhAmana, ruhinta ba zai yafe ba domin akwai ranar da zai san a duniya yayi rashin wanda ba zai taba samun wanda ya so shi haka ba sy sb diA ad in sted sy sbbsy blerd no Maimuna Idris Sani Beli 131 Na Shiga Aljanna...1 Shigowar Alh. ba ta hana Salmanu ya ansa masa cikin murya kasa-kasa ba, "Da ka mutun ai zan kai mata wannan canjin a matsayin diyya, su suka kashe ka su suka hana ka auren abinda kake so" Suna dariya tare da tafawaAlh. Ya karaso cikin fara'ar nuna farin ciki da murnar yadda ya sami jikin Adamu, "A lallai jiki yayi kyau, Alhamdulillahi" Cikin ladabi Adamu ya rusuna kai ya gaishe da yayansa. Salmanu ne ya amsa, "Wallahi kuwa jiki yayi kyau Alh, kawai su יי zo su allame mu a kai wa Hajiya danta" Suka yi dariya su duka. Alh. ya duba agogo y ace, "Sa'adatu ba ta gida ne tún safe, amma mun yi waya da ita ta ce min ta dawo gida har sun yi abinci suna hanyar zuwa ita da Salma" Adamu yayi walankeluwa da bayanin yayan nasa don ya ji suna Salma a ciki, har ga Allah ya tsani Salma, tsana mai yawan da ya sha tambayar kansa dalilinta alhalin ta kasance 'yar'uwarsa. Don haka yadda ya bata rai ba Alh. da ya san Maimuna Idris Sani Beli 132 Na Shiga Aljanna...1 akwai tsama a tsakanin Salma da shi ba, hatta Salmanu da yake daukar tsanar da Adamu ke wa Salma a matsayin shakiyyanci sai da ya lura da hakan, Suna ta 'yan hirarraki a tsakaninsu, Da Adamu aka taru aka dinga zagin mai mashin da ya buge shi har Allah ya kawo su Sa'adatu. Aka gaisa a mutunce tare da yi wa juna jaje da Allah kiyaye gaba. Kasancewar akwai Alhaji a wajen Adamu ya dake bai nuna tsama ba, Salma ma ta rakuye a can gefe rungume da hannu tana satar kallon Adamu wanda ta lura yana ta faman buga mata shan kamshi ko kadan bai yarda ma sun hada idoba, alhali a yanzu babu abinda take nema irin su hada idon ko hodar Boka zata rallo mata shi, tana son ta ga yadda za'a kare saboda haka zuciyarta ta kasance cikin matsanancin bugu. "Zo ki zuba masa abinci Salma, mun gode Allah Adamu an auna arziki" Anti Sa'a ta farko da ita daga fargabarta, a hanzarce ta yunkura ta nufi ledar kayan abincin ta janyo. Maimuna Idris Sani Beli 133 Na Shiga Aljanna...1 Tana zuba abincin cikin kasala da fargabar yadda maganin zai yi aiki akan Adamu kadai duk da ba shi kaďai zai ci abinci ba, Anti Sa'a ta fada mata a tukunyar gidan yawa ma ana zuba maganin Boka kuma ba wanda zai kama sai wanda aka nufa. Adamu bai yi niyyar kin karbar abincin ya ci ba, sai da Salmanu ya zolaye shi ta hanyar yi masa inkiyar ga amaryarshi fa na hidimar zuba masa abinci. Da Salma ta mika masa filet din abincin sai ya kawar da kai yana cin magani, "Ke na koshi" Suka dubi juna ita

Chapter 5 of 7