Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 7
828 iles ins aist souris Na Shiga Aljanna...1 Ba wannan sharhin Hajiya ta so ba wanda ke nuna abinda take wa har yanzu gefensa ma Adamu bai bi ba, wato kulla kauna tsakanin Adamu da Salman, musamman kuma a daidai wannan lokacin da yake ta yi mata kururuwar aure yake so, tana da yakinin in dai an so zama lafiya to gara ma ayi masa auren a kuma zuba wa saraut Ubangiji ido. Cikin sanyin jiki ta mika masa nairarta dubu da take makale a hannunta, "Ungo wannan ka rike a hannunka ko zata bukaci kudin dinki, ka ga ba sai ka bada maza ba" Ya sa hannu ya karbe kudin ya kalmashe a aljihu yana tura wa Salma ashar cikin zuciyarsa, ya rasa da abinda wannan tulun yariyar ta rudi su Hajiya har'suke ganin bata da abokin rayuwa sai zukeken saurayi irinsa. Ya sake jaddada wa Hajiya godiya sannan ya sa kai ya fice da kaya a hannu zuciyarsa barkatai da tunani iri-iri duk na ba'a ga Salma wadda ya dinga rantsewa ko tayi kwalliya ba kyau take ba, lallai mijinta zai sha barnar kudi Maimuna Idris Sani Beli 83 Na Shiga Aljanna...1. kuma babu obiyan bukata, don ko Zinärin duniyar nan zata sanya ba zai mata kyau ba. YDSAEE s siluil otaw sd id lad uosbA ebinb s *********mis sb wsbA Tewwnd iy selay sb ginlol nsnnsw Husna kyakkyawar doguwar yarinyar da ta taso cikin s maraicias sakamokon rashin mahaifiyarta Zainab sanadiyar haihuwarta kuma haihuwar fari, ta sha hannun raino iri-iri tun daga kan hanun Kakarta Innaa mahaifiyar Zainab odin wadda ta dauke tat a cigaba da rainonta tare dastare da dan da take goyo Yunusa. Ita ma Allah ya karbi ranta Husna ná shekaru hudu, sai rikonta ya koma gurin yar mahaifiyarta mai suna Rakiya wadda shekaru biyu kacal tayi Allah ya raba zaman dalilin mutuwar auren Rakiyar kuma bata da Karfin cigaba damrikonta, wannan yasa ta danka amanar Husna ga autarsu Jamila, la, amımma ba'a yi sa'a ba halin Jamila tamkar ba ciki daya süka fito das'yan uwanta ba, sai ta dinga gasa Husna tamkar ba vjininta ba, yadda take matukar gallaza mata tun idaga unguwa här kafatin 交 Maimuna Idris Sani Beli 848 i net enhi srunish Na Shiga Aljanna...1 dangi babu wanda bai san irin mawuyacin halin da Husna ke ciki ba. Mahaifin HUsna Malam magini mutum ne mai tsananin kawaici, shi ne dalilin da yasa ma ya dauke hankalinsa daga kan Husna duk da kasancewarta 'yar fari kuma 'ya daya tilo day a mallaka a duniyarsa. Gashi kuma dangin Zainab sun baibaye shi da karamci, kana sun baibaye shi da lissafin hakkin rikkon Husna ahannunsu yake. Bayan rasuwar mahaifiyarta yayi aure har sau biyu, farko Suwaiba wadda da alama bat a da rabon haihuwa, suka shekara biyar tare kanwar son 'ya'ya ta kais hi auren Jummai, amma muguwar fitiharta ta sanya yayi mata saki uku da tsohon ciki ta koma gidansu ta haifo 'yan biyunta. 'Ya'yansa uku kenan a dangin matannsa matatciya da rayayyiya. Da aka sake diban shekara daya da rabuwarsa da Jummai sai ya sake auro Hajara, wadda tana zuwa ita ma ta ci karo da nata rabon, a auren Hajarar ne kuma ya fahimci ashe akuyar Jummai ce tayi kuka kawai, bambancin ya saba da rike mace daya ne Maimuna Idris Sani Beli 85 Na Shiga Aljanna...1 Zainab sannan Suwaiba, lallai rashin kyawun halin mace yafi bayyana idan tana da kishiya, wato dai ya yiwa jummai bahaguwar fahimta ita kanta Suwaiba baa rasa nata laifin. Wannan dalilin ya sanya ya rike su da halinsu ya kuma cigaba da hakuri haka. A shekarar da Hajara ta haifi 'yarta Khadija hakurinsa da kawaicinsa akan rikon da Jamila take way a gaza, ya shafe wa idonsa tokay a karbi 'yarsa, babu wani jan ido Jamila ta bashi abarsa, dama ba Kaunar rikon take ba kasancewarta mai muguwar karaya da kyashi. Da babu gara babu dadi, amma Husna ta baro wata wuyar ne ta fado wata, duk da akwai dan sassauci kasancewar a tsakanin kishiyoyin da ked a migun kishi take, wadanda kulawarsu gar eta bata motsawa sai idan zasu cutar da juna, in bah aka bata da sauran wani gata ko amfani a wajensu, sannan ko da sun cutar da ita idan idon mahaifinta ya kai kan cutar ya ka tsawatar daidai gwargwado. Sai dai wannan halin ko in kula da tare da Kalubalen da rayuwarta ta taso a ciki ya koyar da ita dabi'a gwagwarmaya tare da koyar Maimuna Idris Sani Beli 86 3 Na Shiga Aljanna...1 tsayuwa da kafafu., ta taso mace mai jarabar neman kudi kamar tayi sata, it ace wannan sana'ar gobe waccan, karshe dai ta tsayar da guda wadda ta fi kwarewa a kai kuma wadda tafi ko wacce kawo mata kudi wato dinkunan mata, kai har na mazan ma tabawa take idan ta sami rarar lokaci tun da dinkin matan yafi sauri tare da kawo kudi masu kauri. Wannan jarabar neman kudin nata ne ma ya sanya dakatar da karatu daga kamala babbar sakandare kawai, a cewarta ai karatun book dan sana'a kawai ake saboda haka ai ita ta sami sana'a yi. Sai dai nakasun da za'a duba a rayuwarta da gwagwarmayarta it ace, shegen sabo da kasha kudi, tana da kirki sosai amma yawancin alfarmarta ta kudi ce da kokarin kere sa'a. gat a 'yar kyakkyawa mai kyan diri don haka ta budi ido da farin jinin samari fiye da kima, ita kuma tayi amfani da wannan dammar ta dinga yashe duk saurayin da tsautsayi ya kawo shi shirgin ta saboda tana da dankaren wayo da iya tsara kalami bugu da kari gat a mace mai sanyin murya. Maimuna Idris Sani Beli 87 Na Shiga Aljanna...1 Wannan dabi'ar tata ta dami mahaifinta kwarai, kullum cikin fada da nasiha gareta yake tare da fatan ganin ta tsayar da miji ya aurar da ita amma ita sam hankalinta bay a kan auren, ta ci alwashin sai tayi wanki zata yi aure kuma ma dai har zuwa yanzu bata ga saurayin day a kwanța mata a rai ko kuma ya cika sharudan zamowarsa miji gareta ba. Amma wani hukuncin Ubangiji wanda ya sanya ta sakankancewa tabbas rayuwa ba abinda ka tsara tun fari zuciyarka ke dorewa a kanta ba kuma ko ana yi wa komai tsari to tabbas So ba a yi masa tsari kuma ba zabа masa muhalli ake ba, kawai shi yake canka ya zuba sheka. Tun ranar da ta hadu da Adamu a shagon kayan dinki sai ya bi zuciyarta ya mimmike, ya zamana dukkan mafarkinta a mijin aure kan Adamu yake fadawa da kudi ko babu, in ta wassafa shi a mai kudi sai ta hango musu wata aljannar duniya mai cike da kyawawan 'ya'ya da rayuwar jin dadi, in ta wassafo shi a talaka kuma sai ta hango rayuwarsu mai mutumci da karrama juna tare da son juna tsakani da Allah. A wannan gabar Maimuna Idris Sani Beli 88 Na Shiga Aljanna...1 har hango kanta take yi tana daukar nauyin gida a sana'ar da take shi kuma Adamu na ta kara sonta yana shi mata albarka tare da cin alwashin daga ita babu kari, kuma duk lokacin da Allah ya yassare masa sai ya jiyar da ita dadin da babu wanda ya taba jiyar da matarsa ko masoyiyarsà irinsa. Wannan jumurdar da ta sami kanta ciki ta rage mata kuzari ainun, so take ta fasa wannan son da zuciyarta ta kinkimo mata amma duk yadda ta kwaso fasawar sai ta ji ta kasa, sai fasawar ta rikede dubunnan soyayyar Adamun su hadu da fatan samunsa su yi ta faman wahalar da ita. Musamman idan taji faduwar gaban yadda za'ayi ta samu din tunda ba ta cikin duniyar da ake mutunta matar da ta ga namiji tace masa tana son sa. Cikin kwana biyun nan haka ta dinga tsirar zuwa shagon kayan dinki musamman dan ta ganshi, ko akan allura ne bazata aiko yaro ba sai dai ta wanko kafa ta taho amma bata taba katarin sake sanya shi a ido ba, kuma duk yadda sonsa yake gasa mata gujjiya a hannu ta kasa samo dabarar da zata yi wa mai shagon Maimuna Idris Sani Beli 89 Na Shiga Aljanna...1 kayan dinki ta nemi Adamun ko kuma ko da sunan Adamun ya tuna mata wanda ya kwanta mata a rai kafin zuciyarta ta zabe shi gwarzonta na har abada. ******* A gurguje kafin karasowar Salmanu Adamu ya fada wanka sai dai bai yi katari ba ya fito ya tarar da Salmanun har ya ya karaso yana kwance kan kujera yana jiransa tare da rera wakarsa ta Dauri kasancewarsa mai son wakokin mutanen Da. "Haba ashe ba banza ba Allah yayi maka ajiyar son wakokin su Dan anaci da su Duna, ashe Boka mai gani har hanji zaka zama" Da shegantakar da Adamu ya tare shi kenan. Suka tuntsire da dariya suka tafa. Salmanu ya ce, "Malam da fa kai na yi niyyar ka zama Bokan" Adamu ya kai masa duka a fusace, Maimuna Idris Sani Beli 90 Na Shiga Aljanna...1 "Ba na son rainin hankali, saboda ni na kawo shawarar kuma na san yadda ake yi?" "Saboda kai baki ne ni kuma fari, ka san ba a saba ganin bokaye farare ba..." Adamu ya sake kai masa duka cikin dariya, "Shege! Ni ne bakin? Ai nima ba baki ba ne malam" Suna kacamewa da dariya su duka Salmanu y ace, "Amma ai baki za a kira ka a kaina" "An ji, kuma nine mai masoyiyar da babu irinta ko, Husna mai sunan laarabawa" Adamu ya fada cikin raha. Salmanu ma ya zolaye shi bayan ya kawar da kai yana kunshe baki, "Allahu Akbar! Na rantse da Allah na zaci Salma zaka ce, ita ke sonka, waccan ba ta san bikin da kake ba kila ma matar aure ce ma'ana an yi mata miji". Fuskar Adamu ta nuna damuwa amma sai ya girgaza kai ya jefar da comb ya yi gaba ya dauko man shafawa ya nemi gurin zama, sai da ya fara shafa man ya amsa wa Salmanu, Maimuna Idris Sani Beli 91 Na Shiga Aljanna...1 "Salmanu, addu'ar da nake wa yarinyar nan ina tsaya wa dararena akanta, idan ka ga ban aureta ba ko kuma Allah bai jefa mata sona cikin zuciyarta ba, to ka tabbatar Allah ya ajiye min wadda ta fita wadda kuma zan so fiye da ita din" Salmanu ya saki wani ihu sannan ya dora da cewa, "Ka san abinda ya fi birge ni da kai?" Adamu ya girgiza kai. Salmanu ya ce, "Yarda da kanka wallahi" Adamu ya sake kada kai, "Ai ba yarda da kai ba ne, yarda da wanda ya ce idan an kira shi zai amsa ne, idan kuma aka tsaya a kofarsa ya ishe mu ne, shin a kai wa kuka na kuma ina da yakinin ba zai tankwabar ba. Irin wannan addu'ar na yi a karatun bokon da aka yi niyyar mayar min addni, ka ga cikin sauki Allah ya raba mu' Jikin Salmanu a sanyaye ya amsa masa, "Ai game da karatun nan gata ne yayi maka yawa Adamu, in ni na sami wannan gatan Maimuna Idris Sani Beli 92 Na Shiga Aljanna...1 wallahi ba zaka gan ni a wannan kwararon ko wannan sana'ar ba" Sai jikin Adamun shi ma yayi sanyi, ya basar lokacin da Husna ta mamayo zuciyarsa, wadda ya hakikance in dai akwai karatu nan a gabansa tabbas sai aurenta ya tsere masa. Zai yi Magana kenan ya jiyo motsi kamar daga cikin gida, zargin ko Hajiya ce zata leko ya sanya ya mike da sauri ya zo wajen Salmanu ya hau yi masa radar yadda suka yi da ita akan sabuwar sana'ar da suke son farawa. Cikin sakkani kadan Salmanu yayi hadda kuma zo aka wuce ne ma suka gane cęwa yara masu siyen Goro ne. Salmanu ya mike, "Bari na je na gaishe ta kafin ka shirya. Cike da fargaba da wasi-wasi iri-iri Adamu ya shirya har Salmanu ya fito. Salmanu ya nemi guri ya zauna ya fito da kudin aljihunsa ya hau kirga, kana ya daga kai ya dubi Adamu, "Ni an sami dubu goma ba dari daya a jikina, kai nawa aka samu a jikinka?" Maimuna Idris Sani Beli 93 Na Shiga Aljanna...1 Maimakon Adamu ya amsa kai tsaye sai ya fara kalubalantarsa. "Dari dayan ma na san fasa dubun ka yi ka sha sigari. Salmanu yayi dariya, "Kamar ka sani?" "Yo kama ce ma? Ai sani nayi kawai" "An ji, kar kuma ka ja mana zance mu yi abinda ya kawo ni lokaci na kurewa" Adamu ya kawar da kai, "Haka ne, to ni ban tara komai ba" Salmanu yayi masa wani kallon banza, amma ganin bai san yana yi ba sai a hasale ya ce, "Ba ka tara komai ba fa ka се?" Adamu ya juyo ya kale shi, "Eh, na je ba sa'a na matsa layar zanar na kasa bata" Salmanu ya shanye haushi ya dan yi murmushi, kamar zai basar amma sai ya yi dabarar tashi ya shammaci Adamu ya dakumi aljihunsa ya zaro naira dubu biyun da Hajiya ta ba shi kudin dinkin Salma, > "Makaryaci, wannan fa?" Maimuna Idris Sani Beli 94 "Tsakaninku kallo" Na Shiga Aljanna...1 Adamu ya kawar da kai ya fada. "Wallahi bata isa ba, sai ka bayar das u sun shiga cikin 'yan uwansu, na karba a haka ai da hanau gara mannau" Ya hada su da dubu goman wajensa ya mikawa Adamu, "Ungo ajiye mana ka zauna ka ji bayani" Ba musu Adamu ya karba ya cusa aljihu sannan ya gyara zama yana duban Salmanu. Salmanu ma ya zauna zaman nutsuwa ya fara koro jawabi. "Abu na farko da zamu tanada shi ne, Guri, wato muhalli da ya dace da malamai ko bokaye, dan guri kebаббe nesa da mutane, ko kuma cikin mutane inda ba a san mu ba" Adamu ya ci gaba da kallon Salmanu saroro da alamun rashin fahimta, kuma cikin alamun son nuna juriyar a dire ya fahimtar. "Wannan bos din na gama kashe shi tun daren jiya, ina gidan gonar Ogana da nake kular masa da shi na nan Zawaciki kusa da mu?" Maimuna Idris Sani Beli 95 . Na Shiga Aljanna...1 Da kyar Adamu ya daure ya kada kai saboda tsabar rudewa. Salmanu bai damu da rikitar Adamu ba ya cigaba da ba shi lissafi, "To dama tuni Alh. ya daina zuba Kaji a nan, sai kawai ya ce na sawa gidan ido na dinga kula da shi, ai mun taba zuwa ka ga girman gidan ko?" Nan ma Adamu ya kada kai, "To daya 6angaren za mu iya mayar da shi fadar tsubbunmu ba tare da wata mishkila ba, dama gashi Alh. yana shirin zaune wa a Japan har na tsawon shekara hudu, abin Allah jiyan nan yake min wannan albishir din" "Ikon Allah" Adamu ya daure ya tanka. Salmanu ya janyo jug ya tsiyayi ruwa ya sha, sannan ya dubi Adamu da kyau, "Wadannan kudin ko basu hada dukkan siyayyarmu ba na san zasu kusa, zamu sai kayan saki irin na 'yan bori, har da su tabarmi, kore, shantu da kaskwayen wuta, kai har da su tsaintsiya da faifai duk masu fenti irin na masu girka...." Maimuna Idris Sani Beli 96 Na Shiga Aljanna...1 "Har girkar zamu dinga yi kenan?" Adamu ya fada cikin tsura wa Salmanu ido yana hadiyar yawun fargabar yadda Salmanu ke son aikensu zunguro sama da kara. Salmanu ya tuntsire a dariya ya amsa, "Haba wa zai aike mu wannan danyen hukuncin? Mu fa Jabun ne, masu girkar asalin ne Orijinal, hanyarsu daban tamu daban kawai dai sunan sana'a kusan daya mu ke" "Shikenan, ina jin ka". Adamu ya fada cikin sallamawar da bata kai zuci ba. "Kana ji ko?" In ji Salmanu. Bai jira cewar Adamu ba ya. cigaba. "Wadancan kayan 'yan borin ba su ne kayan sana'ar ba, su ne dacoration din wajen yadda zai dace da sana'ar, amma dai zamu dan yi hake-hake a wajen yadda zamu jona butotanmu...." "Meye wani butotai?" Adamu ya fada kamar a kule. Har ga Allah maganar ba karamin gundurarsa da batą masa rai take ba.' Maimuna Idris Sani Beli 97 1 Na Shiga Aljanna...1 Salmanu ya buge shi a kafada. "Kai dallah malam ka ware, duk ka bi ka wani cukwikuye" "Ai kai ka cukwikuye ni, malam in zaka yi sauri ka ware ni, ka yi wallahi ka fara sa min ciwon kai" Salmanu ya dinga tuntsira masa dariya har sai da Adamu ya dinga barazanar bar masa dakin sannnan Salmanu ya riko hannunsa cikin tsananta dariya, "Ka ga in ma'anar Butotai ne zo in fada maka mu kashe wannan bos din mutumina" Yana cigaba da dariyarsa bai jira cewar Adamun ba ya cigaba, "Tiyo nake nufi da butotai, ko baka san an ace masa bututu ba? In ka je makaranta ai ka san za'a iya kiran jam'insa da butotai. To ba wai amfaninsa kawai tarar ruwa daga famfo zuwa tanki ba, a'a, a tamu sana'ar da shi ake maganar aljanu duk zaka gani idan mun je wajen" "To" ciAdamu ya fada domin ya hutar da zuciyarsa Maimuna Idris Sani Bell 98 A Na Shiga Aljanna...1 da-zucinta na jiran fahimtar Salmanu tare da kokarin cirewa ransa damuwar da ta addabi ransa. Amma sai ya dage ya mayar da hankalinsa ga Salmanu wanda ya zage yana yi masa bayanin yadda ake wannan sabuwar sana'a ta wankin ido ba tare da an je wajen wani malami neman sa'a ko siddabarunsa ba. Hankali kwance kuma a wanke bayin Allah. Adamu ya kwashi gayar mamaki da yadda salmanu ya kwatanta masa yadda ake binne hankali da azancin masu yawon neman asiri, yadda ko shi aka yi wa wannan siddabarun sai ya yi muguwar bayar da gaskiya. Kai tsaye Adamu ya gane wannan sana'ar sunanta damfara hakkun, amma tunda da tsoka kuma Salmanu ya baibaye shi da hujjar dama duk wanda zasu cuta ko su damfara Allah ya bari ya kama gaibu, ba laifi in an nuna masa yadda ya kama kafar wala. Wata hujjar da Salmanu ya gabatar masa it ace, sana'ar na kawo kazaman kudi, a saukake zasu kawo masa kudin da zai auro masa Husna cikin wata daya kacal! Maimuna Idris Sani Beli 99 Na Shiga Aljanna...1 Ko an juyawa dukkan hujjojin baya wannan kadai ta ishi Adamu, domin yana jin HUsna da darajar da ko ta wane hali ne ma ya kamata ya sami aurenta, kuma in ya samu shi ne abinda ya dace da shi duniya da lahira. "Amma idan Goranmu ya kamo katon kifi, akwai wata hanyar mai 6ullewa, ita ce ta tsakurar wani kaso daga abinda muka caji kostoma mu nemi Bokan gaske mu bashi aikin ya gabatar, maimakon namu da yake iska, ka gane?" Salmanu ya karkare dogon jawabinsa da wannan karin hasken. Cikin karsashi Adamu ya kada kai, zuciyarsa na kara karfin bugu tana hango masa samuwarsa Husna a duniyarsa. Ba su bata lokaci ba suka mike don fara daura damba, daidai lokacin kuma Salma ta kira Adamu a waya, kafin ya daga ya antayo mata ashar ta kai goma, sannan ya daga murya a cushe y ace mata. "Malama lafiya?" Ta hadiye jin haushin tambayar tasa ta amsa masa cikin tambaya, Maimuna Idris Sani Beli 100 "Lafiya da aka yi me?" A kufule ya amsa, Na Shiga Aljanna...1 "Da kika ishe ni da kira kamar ke kika sai min wayar" Ta yi dariya, "Ai ban san a saukar da ka'idar sai an sai waya ake kiran mai ita ba, in haka ne ni da nake da burika kan kiranka ai yakamata na sai 99 maka waya... Yayi tsaki cikin gundura, "Sai ki hada har ni ki siya, don in kin sai wayar ai kamar kin yi baki yi ba" Zata yi Magana ya tare ta, "Malama don Allah kar ki cika ni da hayagaga, me nene dalilin kiran?" Kai tsaye ta amsa, "Ankon nan, sati na sama ne bikin..." Kafin ta dire ya tare ta, "ki aiko a karbar miki zan fita" Ta dan yi ihun murna, "Da gaske, kudin ko kayan?" "Oho!" Ya amsa mata. Ba ta damu ba ta sauke ajiyar zuciya, Maimuna Idris Sani Beli 101 Na Shiga Aljanna...1 "Wallahi ga gidan babu kowa Yaya Adamu, ai na san hanya ne, me zai hana ka daure ka biyo min da shi?..."" "Ashe ba zaki sanya ba kenan" "To in fito kenan yanzu na karba? Gaskiya ina son karba yau na mik wajen dinki" Adamu yayi jim, ya tsani zuwan gidansu, haka kawai shi ko son ganinta ba ya yi bare ace wai takanas wajensa ta zo, saboda haka nan da nan ya tare ta a cunkushe, "Uwar gantali kenan, zan biyo miki das hi, mu kar ki wani kwaso kafa ki zo mana gida" Cike da murna Salma ta shiga gyada kai tamkar yana ganinta, "Haba dan albarka ko kai fa" Bata jira cewarsa ba ta sauke wayar. Shi ma ya ajiye cikin bata fuska yana sauke idonsa kan Salman wanda ya ishe shi da fuskar tambaya, ya hau bashi labarin abinda ke akwai game da Salma da ankonta. Suna ta hirarsu suka fito dan fara shiryeshiryen sana'arsu Adamu dauke da ledar kayan Salma. Maimuna Idris Sani Beli 102 Na Shiga Aljanna....1 Zancen Husna ne a bakinsa yana jaddada irin kaunar da yake mata. Salmanu ya fahimci lallai da gaske Adamu yake sai ya shiga karfafa masa gwiwa cikin karsashi. "Ka kwantar da hankalinka, mace fa ba wani wahalar farauta ne da ita ba, ko baka da ranyo in kana dad a tsari ka gama da ita" Cikin nuna karaya Adamu ya ce, "Ayya! Don kana da kyau ne ba sa yi maka wahalar shiga tarko Salmanu, amma ni, ai sai aikin sa'a kawai..." Ya katse maganarsa zuciyarsa na bugawa fat-fat har Salmanu na lura da dagawarta, ya daga kai da sauri yana kallon saitin da Adamu ya shanya ido da baki yana kallo, sai ya ga wata kyakkyawar doguwar halitta tana ratsowa, .shi kansa Salmanu sai da tasa zuciyar ta buga ko da kuwa ma'anar bugun tasa da ta Adamu akwai bambanci. Bakinsa na rawa ya ji yana tambayar Adamu, "Ba dai wannan ce Husna ba?" 99 "Ita ce Maimuna Idris Sani Beli 103 Na Shiga Aljanna...1 Adamu ya amsa a hanzarce kuma cikin nasa karkarwar harshen zuciya cike da debe kauna da fata, saboda.yadda ya ga Husna rai a bасе kuma sun hada ido ta kawar da kai, kawai sai ya kaddara fishinsa ne, ya shiga uku! Ta fara kin sa tun kafin ma ya furta yana sonta. Ya sami bakin Magana gareta karo na farko a matsayin yada manufarsa tun da sonta ya tsira a zuciyarsa, "Ranki ya dade" Ya ambata mata lokacin da ta zo giftawa, a idonsa tana ta faman shan kamshi kamar jira take a kula ta, ta zabga mari. Ga mamakinsa da raguwar fargabarsa sai ta dan dakata ta juyo kuma tana masa duban ina na san ka? Kwakwalwarsa ta yi shawagi kafin ta cafko makama, "Ko ba Telar nan ba ce?" Ta kada kai cikin saurin da ba dan Adamu ma a rude yake ba zai gane fuskarta daban, zuciyarta daban. Salmanu dai na kallonsu da nazari su duka. Maimuna Idris Sani Beli 104 Na Shiga Aljanna...1 "Ai na jima ina nemanki Hajiyata In, ji Adamu, yana Magana cikin wasa da zolaya. Husna ta yamutsa fuska da nufin dan rage damarar da ta yi wa fuskarta, ta yi murmushi sannan ta rausaya kai ba ta ce komai ba. "Halan baki gane ni ba" Ya fada da alamu karayarsa na nema ta - bayyana. Wannan karon kai tsaye ta amsa kuma a yangace, "Na gane ka maña, ba Malam mai maballi ba ne wanda muka hadu a kantin kayan dinki" Ya tari numfashinta da karsashi, "Yauwa kin tuno ni da kyau, to ya yau?" Ta dubi tsawon hanya da fuska mai nuna kosawa, "Alhamdulillah. Neman me kake min?" "Dinki ne da ni". Kai tsaye ya amsa. Ta ji kirjinta ya amsa, don ba ta so neman nasa gareta ya tsaya a dinki kadai ba, sai dai ta yi saurin jin cewar in dinkin yayi sanadi ma kila wancan ya zo da sauki. Maimuna Idris Sani Beli 105 Na Shiga Aljanna...1 Ta murmusa ta dube shi ta cе, "Na fada maka ba na dinkin maza" "Ai na mata ne, kin gan su ma Ya amsa kuma ya mika mata kayan Salma da zai kai mata. Salman yayi ta zarya cikin wata irin muguwar dariya, sai da Adamu ya yi masa alama sannan ya kama kansa cikin tu'ajibi ya cigaba da kallon wannan dirama. Husna ta karbi kayan ta buda cikin mugun sanyin jiki, tamkar ta bace a wajen take ji saboda tsabar fargaba da jin an ci ta da yaki. Ta sake daga kai ta dube shi ranta a dan bace. "Wa za'a dinkawa, ko kuma in ce ina measurement?" Adam ya dan yi turus sannnan ya waske ta hanyar kare mata kallo sama da kasa, "Ki yi kamar na jikinki komai d komai" Ta kasa daurewa sai da ta bi ba'asi cikin tsuke gira, "Kamar ni take kenan?" "Wace cе?" Maimuna Idris Sani Beli 106 Na Shiga Aljanna...1 In ji Salmanu da ya ji ya kasa hadiye dariya ko saka baki. Adamu ya saci idon Husna ya watsa masa harara, sannnan cikin tsabar yin fuska ya gyada wa Husna kai alamar amsarta Eh kenan. A ciwon matukar gajiye da zuciya da takaici Husna ta sake bude ledar kayan ta gani, sai sannan ne ma ta lura ashe ankon bikin aminiyarta Amina ne, wani mugun takaici yayi masifar turnuke ta, ba dan ba ta sai ankon ba, a'a wajen samari hudu ta karbi kudin ankon a wajensu amma a ganinta babu na birgewar da ya kai na Adamu wanda dinki ma sai ya kai wa budurwarsa don tsabar gatantawa. Kodayake ita kanta ta san a baibai ko a tarkon So take yanke wannan hukuncin, in kai dinki gata ne, fiye da shi ma tana samu a a wajen masu sonta, amma dai ta ji yaji da bata sami ko kasa da haka a wajen wanda ita take so ba. "Ai ankon aminiyata ne ma Ta hakura da kallon kayan ta mayar da ganinta gareshi tana hadiye hawayen da ke son kunno mata. Maimuna Idris Sani Beli 107 Na Shiga Aljanna...1 Cikin zumudi Adamu ya ce, "Allah ko? kawai k ice an sara akan gabа?" Ta koma duban hanya cikin cin magani. A zatonta duk wannan fara'ar tasa ta zai bayar da dinki masoyiyarsa ne. Ta nisa ta се, "To ni zan wuce, yaushe ake son dinki?" "Kin fi ni sani tunda kin san ranar bikin" "Haka ne, to yanzu yaya za'a yi? Baka san gidanmu ba bare ka zo karba, kai ko tsoron in gudu maka da kaya baka ji ba?" Ta daure ta karasa maganarta da dariyar 5 zolaya. Kai tsaye kuma fuskarsa na nuna yakini ya amsa mata, "Haba dai, wallahi kin fi karfin wannan. Ke dai kawai ki je da kaya ki yi min dinki mai dankaren kyadaidai jikinki, yadda za'a yin a karba na san Auah zai kawo" Ta yi saroro tana kallonsa. Abinda ya sanya numfashin Salmanu bugawa. Sai ga Adamu ya kutsa hannu a aljihu ya dumbuzo kudin da ya bashi riko ko kirgawa ba yi ba ya mika mata. "Ga kudin dinki? • Maimuna Idris Sani Beli 108 Na Shiga Aljanna...1 Ta dan rusuna kadan ta karba fuskarta babu walwala ta yi musu sallama ta wuce. Adamu ya bita da kallo cikin shanya baki Salmanu ya danki hannunsa wanda ya mayar aljihu suna taba ragowar kudin da ya bari. Cikin fishi ya ce, "Ina fatan wannan matsiyaciyar dubun naka ka bata?" Adamu bai bashi muhimmmanci ba sai daya tabbatar Husna ta gama bacewa idonsa sannan ya juyo ya dube shi, "Me ka cсе?" "Nawa ka bata?" Salmanu ya tambaya cikin fishi. Tun daga zuciya Adamu ya fara shiryawa rikicin Salmanu, cikin dakewa y ace, "Sai dai mu koma ciki a kirga" Bai ma jira cewa Salmanun ba ya wuce ya koma cikin soro ya hau buďe dakinsa. Salmanu ya biyo shi yana

Chapter 4 of 7