Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 7
domin idan zan zama Mongo park ba zaku taba yarda an halicci kwanyata da iya kirkirar abin kirki ba" Yayan ya kara janye annurin fuskarsa yana duban adamu, "Uhum! Cigaba ina jinka" Adamu ya sake muskutawa rai a bace yana gyarawa carbinsa zama, ba tare da ya dubi Yayansa ba ya ce, "Alh. Yadda kuke kaddarawa ni ban iya wani abin arziki a duniya ba, haka na kalli kwanyata da rayuwata na gane sam babu abincina a karatun boko, don haka a daina yi min kagen cewa na san gaibu", "Kage? Uban wa yake maka kage Adamu?" Adamu ya motsa ya sake motsawa cikin dauke kai, amma bai tanka ba. 'Maimuna Idris Sani Beli 28 Na Shiga Aljanna...1 Alh. Ya jima yana yi masa kallo mai fassara iri-iri, bai gamsu ba sai gashi a gaban Adamu cikin zafin nama, ya sunkuya ya dago habarsa ya shinshina tsawon wasu sakanni sannan ya ture shi ya mike yana ja da baya cikin kallonsa, "Babu alamun shaye-shaye a numfashinka Adamu, amma me yake cin kanka yau?" Adamu ya sa sake cin magani ya cigaba da jan carbinsa, sai jikn Alh. Yayi sanyi ya jima tsaye yana nazarinsa cikin kasa hankula, bai kai ga warwara ba ya zauna kujerar kusa da Adamun ya dafa hannunsa yayi masa Magana da tattausar murya, "Ka kasa gane nufina Adamu, kudurorina akan ka sami kyakkyawan ilmi mai zurfi duk ba ni zasu amfana ba kai zasu amfana, babbar sakadanre bata isa komai bad a har zaka mallaketa ka ja ka bame, ina laifin ko 'yar diflomar ka yarda ka samu tunda ka fara?" Yayi jiran cewar Adamu, amma har yanzu babu alamar zai tanka, sai dai ya rage cin magani da yake. Maimuna Idris Sani Beli 29 Na Shiga Aljanna...1 Alh. Bai yi fishi ba ya cigaba da magana cikin taushin murya da sassaukan harshen fahimta. "Hajiya Uwa da mahaifinmu Mal. Musa mu biyu kadai suka mallaka wato ni Kabiru da kai Adamu wanda na bawa tazarar sama da shekaru goma. Lokacin kuruciyata kafin kai kai bai waye da neman ilmin boko sosai ba don haka ban sami hasafinsa ba, lokacin taka kuruciyar kuma kuncin rayuwar talauci ya hana su maida hankali akan karatunka" Adamu ya muskuta alamar nuna gajiyawa da gundura da wannan dadaddan tarihi da kullum Yayansa ya tashi yi masa nasiha sai ya hado masa da shi, sai ka ce mai gwada masa shiga kabari a fito. Alh. Ya fahimci gundurar ta Adamu amma sai ya share shi ya cigaba da maganarsa, "Tun kana mitsitsinka na fara buga-buga ta neman kudi, yau wannan sana'ar gobe waccan har ajalin mahaifinmu ya riske shi. Duk da ina da sauran kuruciya bai hana nauyinku kai da Haj. ya dawo kaina, wanda hakan ya sa ni kara Maimuna Idris Sani Beli 30 Na Shiga Aljanna...1 zage kwanjin neman na kai, Allah kuma ya dafa min har ya tsayar min da sana'ar nan ta safarar Goro daga kudu zuwa arcwa, har kawo yau da rufin asirin Allah ya lullube mu ta silarta har ni da Haj. mun shiga sahun wadanda za'a kira Alhazai" Ya dan nisa kamar alamun rashin alamun abin fadar ne ya kare har Adamu yana murna da tsaki cikin ransa, amma sai murnar ta koma ciki lokacin da Alh. Ya sake nisawa, "Ba gorin kushe nake maka ba Adamu, amma tabbas na. ci kashinka yadda idan ka bijire min ko kayi min butulci Allah zai bi kadin hakkina, na soka shigen son da Uba yake wa dansa, shiyasa burikana akan ganin cigaban rayuwarka suka yi kamari. Burina ka zama likita,, amma da naga hankalinka baya kan karatun sai na sauke farashi, akalla ko malamin makaranta ka zama. Haka kawai ni dai naji akwai bukatar ka tanadi ilmin ko da kuwa kafi sha'awar zama dan kasuwa, shiyasa ma na bayar da shawarar ka karanta kasuwanci kamar yadda ka yarda ka fara bayan ka share shekaru da dama kana zaman kasha wando. Maimuna Idris Sani Beli 31 Na Shiga Aljanna...1 Na ci burin ka tsaya da kafarka yadda ko bayan raina zaka iya cigaba da daukar nauyin kanka da mahaifiyarmu sannan ga nawa iyalin wadanda bas u da kowa sai kai......" Adamu ya muskuta cikin mita da kunkuni, inda yake cewa, "Kana tunanin abi maka kadin hakkinka a kaina, amma ka kasa tuna za'a bi nawa hakkin a kanka saboda takurawar da kayi min da cukwikwiye ni sai nayi wata rayuwa wadda bani da sha'awarta saboda kawai na dauki nauyin rayuwar iyalinka in ka rasu.... "Me kake cewa?? Alhaji ya tambaya cikin fuskar mamaki. "Cewa nayi Allah ne kadai ya san gawar fari" Adamu ya amsa cikin nuna gundura. Alhaji Yayi kasake yana kallon Adamu, ya shafa abin dorarwa ya rasa, sai kawai ya rangwada kai yayi shiru. Hakan da Adamu ya gani ya sanya jikinsa yin sanyi, ya dan yi kame-kamensa sannan ya fara magana, Maimuna Idris Sani Beli 32 Na Shiga Aljanna...1 "Wallahi duk na fahimce ka Alhaji Amma kai ma abind aka kasa ganewa shi ne, shi karatu ba a sanya masa karfi dole sai kwanya da ra'ayi suna da sha'awa, Ni kwata-kwata idan ina da ra'ayin karatun boko Allah ya tsine min, shiyasa ma shekarun nan biyu na dinga samu n kari oba, kuma wannan shekarar ma idan an matsa min kila abin sai yafi haka.." istAllah ya kyautam BRESE uAlh.Yafada cikin alamun gajiya da takaici.AE no Sukajima cikin shiru kafin alh. Yamisa, susI Shikenan maganar karatu an barta in Allah ya so, amma fada min, menene kudurinka menene burinka, menene abindaskwanya da ra'ayinka eys suke sha'awa one is baswanda As sape As ake musus Kingi Asgo Da sauri adamu ya amsa, 626П Nilsana'a make so, Allah yausani ina so nayi aure3 вр якпог sn smls? iA sks sweС Zuciya ta zo wa Alh. Wuya, amma ya dingav shanye kayarsa harya hadiye fiye da rabintáA "Na san kana sonsaure Ctunsfuni, amma a tsammanina zan iya tare ka har lokacin da idan Maimuna Idris Sani Beli ewеlUь сsa sY IA 33E iled ins2 ainht sauoisM Na Shiga Aljanna...1 kayi ba zai zame mana matsala ba, ban sani ba دو ashe karya naci na kwana da yunwa" Adamu yayi shiru. Can.jimawa Alh. Ya sake nisawa, "An ce min Salma na sonka, in haka ne gara ayi 'yar gida musamman da yake baka da kwakkwarar sana'a sannan ka san komai akanta, 'yar yar mahaifiyarmu ce da ta rasu tun tana karama rikonta ya dawo hannuna don haka ta san ciki da bai a samu da rashinka kafin sana'arka tayi kwari". Ba don wata fuskar tafi gaban mari bă babu abinda zai hana Adamu tura ashar. Sai kumburi yake kamar ya fashe ya tari numfashin yayan nasa, "Wa yayi min sharrin cewa ina son Salma?" "Cewa aka yi Salma na sonka, ba cewa aka yi kana son Salma ba" Alh. Ya amsa cikin tausasawa. Adamu ya kara bata rai, "Wa ya fada? Ni bata taßa fada min ba" Alh. Ya sake daurewa, こ Maimuna Idris Sani Beli 34 "Sa'adatu ta sanar da ni Na Shiga Aljanna...1 Babu kunya Adamu ya sake tare numfashin Alh. a sike, "Gaskiya ni bana sonta, ba mace nake so da aure kawai ba, wata yarinya nake so na aura' Alh. Ya gama kai wa bango, tsawon lokaci yana jinjinawa, "Ba ka sonta?" Adamu bai tanka ba, iyaka ya cafko carbinsa ya fara ja. Alh. Ya sake kada kai, "To da kyau! Nan ma an wuce, na yarda kaje ka auro yarinyar da kake so kuma kake son aure. Sai mu fado maganar sana'a, wacce kwanya da ra'ayinka suke sha'awa?" Hantar cikin Adamu ta kada day a fahimci turin Jeka-ka-mutu Alh. Ya shirya yi masa, ko kuma debi in ga hankalinka. Ta ina zai sami sana'a babu hannun yayan nasa a ciki, in sana'ar ba ta aikin karfi bace ina zai nemo jari? Yana tuno tauhidi sai ya sami harshensa na bawa Alh. Amsa, "Muna nema wajen Allah?" Maimuna Idris Sani Beli 35 Na Shiga Aljanna...1 "To babu laifi, Allah ya zaba mafi alkhari. Idan an samo sana'ar a sanar da mu mu taya murna. Tashi ka je" *** ********* Garin Kano garin kasuwanci, unguwar kurawa unguwar sarakai kuma unguwar makotaka da kasuwar rimi bakin asibiti. An ce duk mai makotaka da kasuwa baya tsiya, amma da alama wannan kaulin ya tsame, Adamu ciki, domin a Kurawa aka haife shi, ya girma a cikinta amma yau ya laluba sana'ar yi ya kasa ganowa ko kuma ita ta kasa ganinsa, saboda haka kamar makotaka da kasuwar ta kasa yi masa rana. Bayan alhinin awa daya kacal~ wanda yayi bayan turin je-ka-ka-mutun da Alh. Yayi masa, ya dawo gida ya dinga cakuda rayuwa da mutuwa a hakuri da son Husna da kuma sauran rayuwarsa, da kyar ya wafto jarumtar tashi ya nemo sana'a don kar ya mutu a matsayin ragon soyayya da rayuwa, tunda aikin malam ba lallai nan take zai ci ba. Maimuna Idris Sani Beli 36 Na Shiga Aljanna...1 Amma kaico! Kwana da yini kenan ya kulla lissafin sana'o'l sun fi a kirga amma har yanzu ya kasa fitar da amsar ko guda, ba don rashin iyawa ko rashin sanin makamarta ba face don wadanda suke da saukin samu shi sam! Basu dace das hi ba kamar dai yadda me markade bai dace da zama mijin Husna ba. Ya yarda tun daga yammacin jiya bayan sallamar da yayansa yayi masa kawo yammacin yau, kwakwalwarsana ajin washi, ta fara karaiun nemo mafita, har tayi digirgir amma ta fito fanko! Kwance yake rashe-rashe kan doguwar kujerar dakinsa da yammacin ranar cikin tunani a halin yanzu, sai gashi a halin zahiri an wangale kofar dakinsa an shigo "Ho! Gayun gidan nan suna kusa?" Wani shegen takaici ya kume shi, amma a halin shanye shi ya dago kai ya dubi mai shigowar lokaci daya kuma zuciyarsa ta rubuto wata addu'a tana biyawa, "Ya Allah ka tsari gatari da saran shuka, Ubangiji ka tsare ni ko hada hanya da gajeriyar mace bare ta kai ga gina mata gida in ajiye a Maimuna Idris Sani Beli 37 Na Shiga Aljanna...1 matsayin matar aurena, Allah ka san ni baki ne, amma bana son macen da ta fiye baki Allah ka tsare ni da ita. Idan na ga 'ya'ya masu idanuwa dakwa-dakwa Allah ka sani har jaje nake wa iyayensu to Allah ka tsare ni da macen da zata haifa min irinsu. Duk mace mai saurin murya bana kaunarta, Allah ka san wannanin ka jarrabe ni da irinta zuciyata zata iya fashewa.... Gaba daya Allah ka san doguwar mace nake so wankan tarwada mai kyakkyawar fuska da kyakkyawan murmushi bana son mai yake, ina son mai kyawawan idanu mai dogon gashi, mai fara'a in so samu kuma mai suna Husna.... Ita nake so, Allah ka mallaka min kayi min tsari da wannan da take tsaye a gabana yanzu Salma ta karasa shigowa dakin sosai tana nazarisa tamkar wani bakonta. Dakin ya wadata da duk wani kayan more rayuwa daidai matashi mai matsakaicin rufin asiriirin Adamu. STEVIOUS Saul sysh igndol mewogida Dakin na shimfide da shudin kafet, akwai dindimemiyar katifar sauko mu gaisa daga can Kuryar dakin waddaEDSIT ta cika OELI da shirgi kama da bargo, kayan sawa wankakku da masu dauda Malmuna Idris Sani Beli 38 RON HML 2 Na Shiga Aljanna...1 litattafai har da wasu allunan rubutun sha guda biyu kamar yadda suke watse ciki da gefen akwatunan dake jere a nasu gefen ba. Daga wani gefen kuma ga fakej din kayan kallo masu dirma-dirman sifiku da kuma karamin firji a gefe. komai dai a dakin baya cikin hayyacinsa duk kyau kuwa da tsadarsa, can kwalbar turare nan filasan abinci, can bel nan kwalaben lemo. Abu bako a idanun Salma cikin dakin shi ne, wata shimfidaddiyar sallaya daga can bangaren gabas a karshen dakin sannan ga wani jibgegen carbi zaune kan salllayar yana shan nasa sharafi. Kodayake iyakar sanin da tayi wa Adamu ma abocin son ibada ne wato sallah akan lokaci da kuma yawan nema a wajen Allah, idan duk halayensa na kushewa ne to tabbas a nan bangaren ya sami na yabo. Ta dade da sanin Adamu tun suna yara, in dai yana jarabar son abu, to ya dinga kafa goshi yana fadawa Allah kenan ba dare ba rana. Lokacin da yake neman tsarin Allah da ita cikin zuci, ita kuma daidai lokacin take nazarin dakinsa, sai aka yi sa'a suka gama kusan lokaci Maimuna Idris Sani Beli39 Na Shiga Aljanna...1 guda, kuma kamar masu tseren Magana suka dago suka fuskanci juna, "Ke matsalarki fadowa dakin mutane babu sallama" Ya riga ta Magana cikin matukar daure fuska. Duk da kusan a tare suka yi maganar ita ma ce masa tayi, "Lafiya kai da dakin naka na gan ku duk a hargitse?" Dayake kafin ta dire taji nasa furucin sai ta zarce da amsa masa, "Au yanzu ban yi sallama ba na shigo? Kawai dai ka ce baka ji ba ka lula cikin tunana di". Haba ya ji kamar zai tura mata ashar, amma ya maze ya kawar da kai, "Kin manta ne, ai ba daki kika shigo ba, Turu kika shigo... Ta wuce ta zauna kujerar dake kusa da kafarsa tana dariya, "Allah ya baka hakuri Akaramakallahu..." Ya tare ta a kufule, don bai gama fanshe maganarta da ta zoza masa gyambo a kirji ba, Maimuna Idris Sani Beli 40 Na Shiga Aljanna...1 "Tunanainki? To kila ma ni gabadaya ba a halicce ni da zuciya ba bare a bata lokacin da zata bata wajen tunaninki" Salma ta katse si cikin dariya da mayar da komai ba komai ba, "Kar ka damu, tawa zuciyar ta ishe mu tunana komai da ya shafe mu, yadda nake bata lokaci wajen tuna ka haka nake bata lokaci wajen tuna maka kaina......" "Ba na son iskanci da wulakanci Salma..." Ya sake tare ta a zafafe saboda tsakani da Alla hadiyar bakin cikinta ya fara gagararsa. Salma ta shafe sama da minti biyar tana dariya cikin kallonsa kafin ta shanye dariyar cikin goge hawayen da dariyar ta samar mata. Ta jima tana kallonsa a nutse sannan ta tanka, "Komai ya ji a kai Adamu, gaye har gaye matsalarka daya baka san wasa ba. Wai kai a zatonka ko daura min kai a kafa aka yi zan ja? Ai gara na yanke kafar ko ta katako ce na aro na yafa" Ya tashi zaune cikin rage damuwar fuskarsa yana sauke numfashi, Maimuna Idris Sani Beli 41 Na Shiga Aljanna...1 "Ai kece kike neman zunguro wa mutane sama da kara, 'yar wannan rahar da kike kin janyo manya sun sa mana ido, suna zaton son juna muke. Abin ma sam babu tsari, ko ina zan dauki gundumemiyar mace irinki in kai a matsayin mata?". Duk kawaici da kai zuciya nesa irin na Salma sai da wannan maganar ta Adamu ta bata mata rai, don haka ta jima kafin ta gama hadiye ta. Cikin murmushin yake ta ce, "Kar ka damu, kai zaka samo wanda zai iya daukar irina a matsayin mace ka aura masa, na san kila kai ne waliyyin don haka in ka tashi tallata ni sai ka dinga dawajewa, Baka ce kuma gundumemiya" Adamu ya dan yi saroro da jin wannan bakar maganar tata, amma dai ya takura fuskarsa kar ta bada maza, sai ma ya kada kafada nuna halin ko-in-kula, "Ba ba'a ce ta kar uwar gizo ba karar kwana ce, ni ba kushe ki nayi ba, ainihin halittarki na fada menene na jin haushi na? in ni baki yi min a matsayin matar aure ba wani ai yana nan yana cin layar in ba ke ba sai rijiya" Maimuna Idris Sani Beli 42 Na Shiga Aljanna...1 Salma ta so ta hasala, amma sai ta binne da siyasa, "Haushinka na ji Adamu?" "Ni bana son janjanin magana don Allah" "To an bar maganar" Ta fada cikin saduda sannan ta koma bin dakin da kallo kusurwa bayan kusurwa musamman shimfidar sallayarsa mai jibgegen carbinsa a kai. Adamu na biye da ita da nasa idon tamkar yana gadinta ne, zuciyarsa a kuntace domin yakinin wannan kallon Allah tsine uwar mai karyar da take wa dakinsa sai ta jangwalo abinda sam bata da ruwa a cikinsa. Don haka ya katse mata hanzari, "Kin ga malama duk maganar da zata fito daga bakinki ya zamana ni da ke duk muna da hakki a cikinta, idan ba ruwanki ko ba ruwana to kar ki kawo mana ita, ato!" Ta sauke ido a kansa cikin murmushi tana jin ciwon hanzarinta da ya katse. Idan ba idonta ke gizo ba a can kusa da jibgegen carbin nan ta hangi kwalbar turaren wurudi, cike take da fargaba, amma dokokin Adamu na mata Maimuna Idris Sani Beli 43 Na Shiga Aljanna...1 burkin tambayoyin da zata fanshe, dole ta tattare ta hadiyc da cin alwashin jiran wata haduwar kafin ya kafa dokar. Ta ciro Jakarta da ke rataye a kafadarta ta zaro wasu kyallaye guda biyu na les da na atamfa ta mika masa, "Amina kawar nan tawa! To bikinta ne ya taso saura sati biyu, wannan anko ne na kawo ka sai min, kunyar Alh. nake ji wallahi kullum na dinga damunsa da dawainiya” Da Adamu ya kalle ta sai ya fahimci tsakaninta da Allah take Magana, don haka ya yayyafawa ashar din da ke turereniyar fitowa daga makogwaronsa ruwan salama ya hadiye su. Yana bin hannunta da kalllon gefen ido ya се, "To ajiye su nan, dama jiya-jiyan nan na siyo sabuwar Gariyo tare da AK 47, dare kawai nake jira ya tsala na fita" Duk da ta gane bakar maganar da ya cinna mata sai tayi fuska, "Ban gane nufinka ba" Kafin ta rufe baki ya mayar mata, Maimuna Idris Sani Beli 44 Na Shiga Aljanna...1 "Dama kin zo ne ki gane nufina ko kuma dan na sai miki anko?" "Anko ya kawo ni" Ta fada a sanyaye. Ya nuna mata kofa, "To ki ajiye ki je za a siyo" Ta bi umarninsa ta hanyar mikewa tare da yi masa sailama, amma maimakon ta nufi kofa kai tsaye sai ta zarce kan sallayar nan ta sunkuya ta dauki turaren wurudin nan ta hau sunsuna. Adamu ya kara cin magani ya kawar da kai daga kallonta, can ta juyo ta dube shi, tana kallon fuskarsa ta tabbatar ashar dinsa a kan harshe take karamin motsi bakinsa yake jira ya antayo ta waje. Ta so su hada ido ko dan ta gaskata zatonta, da ya ki sai ta hakure tare da ajiye turaren ta juyo a sanyaye kai tsaye kuma ta nufi kofa ta fita ba tare da ta sake tankawa ba. A soro ta tšaya domin bawa kwallar da ta cika cikinta dammai fitowa ta wataya. Wane irin mugun ciwo ne ya kama kirjinta? Ta tambayi kanta ba tare da sa ran samun amsa ba Maimuna Idris Sani Beli 45 Na Shiga Aljanna...1 don ta sha kai wa kirjin nata duk wani lissafi a akan Adamu. Adamu ban da son sallarsa kulliyarsa bai cancanci a so ba, ashe ma bayan wannan ita kanta bai dauke ta a matsayin mace. ba, Baka gundumemiya, wannan ce inkiyarta a wajen Adamu wanda ta kwashe shekaru da saninsa saboda haka ta ga ko wane irin aibu nasa daga halittar jiki zuwa hallitar hali amma duk da haka ko kadan kirjinta bai ji rauni a sonsa ba. Ta ci kuka mai hadiye shassheka a ciki sannan tà goge hawayenta daidai lokacin da zuciyarta ta cilla lissafin Adamu da zabgegen carbi hadi da turaren wuridi, nan da nan kwanyarta ta rushe da canki-cankin Allah ya sa ba zargin da zuciyarta tayi ya tabbata da Adamu ba. Tana cikin share hawaye Adamu ya fito daga dakinsa da nufin shiga cikin gida. Ya kula hawaye take tana sharewa, amma sai ya basar, "Au ashe ke ce baki tafi ba, haba tun dazu nake jin kwashar-kwashar". Maimuna Idris Sani Beli 46 Na Shiga Aljanna...1 Ta fara girgiza kai cikin rudewa da kokarin kwato furuci daga kwanyarta, amma ya gagara kawai sai ta sa masa ido da kallon kurilla. Suka yi kallon-kallo tamkar kowa na hango cikin zuciyar kowa, amma shi sai ya basar ta hanyar kawar da kai yayi fuska, "Ina abincina, kin taho min da shi?" Ta amsa da kyar cikin numfarfashi tana nuna masa cikin gida, "Tun dazu Sajida ta kawo maka ina tsammanin ba ta san kana ciki ba ta kai wa Hajiya" Ya kada kai ya wuce cikin gidan ba tare da ya tanka mata ba, ita kuma ta bishi da kallo zuciyarta na kade-kade iri-iri wanda ko daya gangar jikinta ta kasa zabar daya ta taka masa rawa, sai daga karshe ita ma ta zabi kada kai ta fice tana kara goge hawaye. ********** Yana ta faman wurga loma tamkar mai shiri hadawa da harshensa ya hadiye, idan ya ajiye cokali kuma kafin ya cinye na bakinsa sai ya Maimuna Idris Sani Beli 47 Na Shiga Aljanna...1 cafko carbinsa ya hau ja, a haid kuma mafici ne yana ta faman firfita. agu Ga kwanon abincinsa ga kyallayen ankon Salma a gefensu, shaida ce ta ya kuduro batu a akansu ya kawo wa Hajiyarsa wadda ke ta 'yan hidimominta daga tsakar gida zuwa daki. Da alama ita ma Hajiya hankalinta a kansa yake, tun bayan da babban danta ya je maía da batun ya sallama Adamu da maganar karatu sai duk hankalinta ya bi ya dugunzume, ta san Adamu da kyau! Bai iya zaben komai ba bare ya zabi makoma tagari a rayuwarsa wadda babu hannun yayansa a ciki, sannan ta san kafiyarsa kan abinda ya zabowa kan nasa komai muni shi baya gani. Kari kan damuwarta bayan wannan shi ne yadda ya zaune mata yanzü yana cin abinci bakinsa a dinke, ta dade da sanin shirun Adamu sai da dalili don haka tuni ta fara neman tsarin Allah da jin dalili wanda zai shafi farin cikinta ko wanda zai sanyata zance da karkata kai. Ta cigaba da shige da ficenta tana sakar abinda zai bugar mata cikinsa ta ji me ya hadiya, bata yi aune ba kawai sai ta ji ya Maimuna Idris Sani Beli 48 Na Shiga Aljanna...1 kwarma ihu tare da furzar da shinkafar bakinsa kana ya furta, "Na shiga uku!" Ta girgije tsoron da ta ji karon farkon ihunsa a hasale ta yi kansa da tsintsiyar hannunta, "Menene haka, kai wane irin mahaukaci ne?" Ya nuna mata shinkafar day a furzar daga bakinsa, "Wata shegiyar tsakuwa na gurza, in Sa'adatu ta iya girki Allah ya tsine min" Hajiya ta dinga motsa baki alamar takaici na neman hana ta Magana, amma dai ta daure ta warto, "Wato Adamu bakinka ba zai zama mai yawan ambaton alkhairi ba ko? Ka kwarma ihu ka biyo shi da na shiga uku an bi ba'asi kuma ka nemi Allah ya tsine maka. Adamu fata nagari fa lamiri ne...." Alamar nasihar tata ta bayan kunnensa take shiga, kawai sai ya hau kakari tamkar mai shirin finciko 'ya'yan cikinsa a matsayin amai sun ki fincikuwa. Maimuna Idris Sani Beli 49 Na Shiga Aljanna...1 Da haushi ya ishi Hajiya kawai sai ta bi bango ta yi zaman dabaro tana kallon Adamu har ya gaji da kakarinsa ya dago ya dube ta ido jawur, "Wai Ibtila'I ya afkowa mutum amma sai ki ce sai ya ce ya shiga aljanna a madadin ya shiga uku, aljanna ba dadi ba ce? Wata masifar kuwa in ana shiga dubu mutum ma ba sai ya ce dubu ya shiga ba..." Cikin sikewa Hajiya ta katse shi, "Ka'idar daidai ce sai ka ji dadi zaka godewa Allah Adamu...?" Shi ma tare ta cikin nuna mata carbin hannunsa, "Mu da muke neman kusaci da Allah har a fada mana godiyar Ubangiji Hajiya? Ai kar ki damu kawai, Allah na kowa ne kowa ma azurtawa yake. Aljanna kuma ta mai rabo се" Furucinsa da carbin hannunsa ya sanya shakku ya dabaibabye zuciyar Hajiya ta ji numfashinta ya fara gudu a guje! Nan da nan Shazali dan gidan Hajiya Dudu da Malam mai almajirai suka fado zuciyarta. Maimuna Idris Sani Beli 50 Na Shiga Aljanna...1 Wani malami ne a Warure da labarinsa tsakaninsa da matasa ya fara karade bakunan jama'a, ana zarginsa da neman matasa maza, wadanda yake yaudara da basu wurudin neman kudi, an ce wasu na tsallakewa su yi kudin wasu kuma su zama bayinsa da sai yadda yayi das u yayin da wasu idan sun kuskure wurudin suke haukacewa kamar yadda Shazalin ya haukace kuma kwararo-kwararo yake bawa mutane labarin abinda ya faru da shi a daren wurudin tare da bayyana matasan da suka yi kudi ta hanyar wurudin, kowa a Kurawa da zagayenta ya san da wannan batun ciki kuwa har da Adamu wanda bai dauki hakan abin kyama ba don lokacin da labarin ya zo musu suna tare da Hajiya da yayansa da Sa'adatu har ma da Salma. Suna ta jinjina labarin amma budar bakin Adamu sai cewa yayi, "Ni ban ga abin jinjina lamarin nan ba wallahi, ai wurudi ka nemi kudi ba laifi ba ne in dai ba shirka zaka yi ba, shi ma Shazali akasi aka samu" Salma t ace, Maimuna Idris Sani Beli 51 Na Shiga Aljanna...1 "Ko babu laifi Yaya Adamu ai kasada da rayuwa ganganci ne, yaushe mutum zai saka hankalinsa a caca yana ji yana gani a bashi zabin kudi ko hauka...." Ya mike yana amsa mata cikin gwasalewa, "Ke ai wata Dumfa ce wallahi, ai dai kin san matsaroci baya taba zama gwani. Dama rayuwar ai kamar caca ce, zubi ake ko a samu ko a rasa.... "Sannu Kala-Kato!" In ji Sa'adatu Adamu ya so ace ba Yayansa a wajen ya yarfa wa Sa'adatu Magana, idon yayan nasa ya sa ya bige da cewa, "Yauwa akarambana, sarauniyar shiga abinda babu ruwanta". Ya sa kai ya fice daga gidan. Hajiya ta dawo daga tunaninta cikin taruwar fargaba, ta dade tana duban Adamu wanda yake ta faman tsince-tsince a abincin da yake ci cikin yatsine fuska har ya kamala cin abincin ya ture kwanon. "Wai me kake ja da carbin nan Adamu?" Maimuna Idris Sani Beli 52 Na Shiga Aljanna...1 Ta ji muryarta na tambayarsa ba tare da tayi shawara da zuciyarta ba. Ya dan yi jim, sannan ya amsa cikin murmushin da-biyu mai alamar waskiya, "Waccan Kundubar yarinyar ce tana gani na ba Cas! ba As! Wai ta kwaso kyallayen anko har guda biyu ta kawo min, dan kar aji kunya na karkade kundi na dukufa gaban Allah rokonsa ya hore abinda za'a fita kunyar..." Har ga Allah Hajiya ta yarda da shifcin gizonsa. "Wacce Kundubar yarinyar?" Ta tare shi cikin rashin fahimta "Salma mana". Ya amsa mata cikin karsashi tare da mika mata kyallayen, Ta karba ta shiga juya su tana kallo. Zahiri kwayar idonta ce kawai take kallon kyallen amma zuciyarta da kwanyarta sun fi na'ura mai kwakwalwa tara aiki. Can jimawa suka samo matuntuba daya, cikin raunin murya ta daga kai ta dubi Adamu, "Yanzu kai tsakani da Allah da ka san akwai addu'o'in da zaka yi domin canja hagu Maimuna Idris Sani.Beli 53 Na Shiga Aljanna...1 ta zama dama amma ka kasa yi wa kanka gatanta a rayuwarka da neman ilmi wanda kamar ya zama shi ne tsanin sana'ar mutanen wannan zamanin in ma an ture wayewar rayuwa?" Yana sane ya mike yayi kicin-kicin yana fuffukar tafiya, "Ni wallahi Allah ne gatana, kar a daga min hankali akan batun da tuni nayi jana'zarsa na binne" A gajiye da takaici Hajiya ta yafito shi sannan ta shafa hannu a fuska, "To fatiha, an gama binne karatun boko, zo mu yi wata maganar daban" Ya dawo ya zauna yana kumburin karya. Sai kawai Hajiya ta watso masa tambayar da ta kusa tarwatsa masa numfashi duk da ya ji alamar ita kanta Hajiyar tambayar bata shirya mata ba ta fado harshenta. "Ina fatan ba ta tsanin Malam-Na-Allah ka hau domin kusaci da Allah ba...." Ragowar maganar ta makale a makogwaronta shaidar a cikin tsoro ko abinda yayi kama da shi tayi maganar. Maimuna Idris Sani Beli 54 Na Shiga Aljanna...1 Ya jima yana tattare yawun bakinsa yana hadiyewa da kyar ko dan ya sami kofar da sautin zance zai fito daga huhunsa. Ba ya shakkar Hajiyarsa ko kadan amma ya tabbatar a cikin sha'anin Malam-Na-Allah ko tsoron sata ne ya sami kansa

Chapter 2 of 7