Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 7
da yafitowa. Lokaci guda ya nemi danshi a makogwaronsa ya rasa, don haka lamarinsa ya zame wa Hajiya bambarakwai tunda ta san ya saba fadin gaskiyarsa kai tsaye in yaso ko me za'a yi, a yi. Cikin sabbata juyyata ya aro fuskar kunu ya yafa, "Me yasa kika yi min wannan tambayar?" Ta rausaya kai cikin yanayi na saduda a matsayinta na 'yar masani a cikin halayyar Adamu, zuciyarta ta tsinke. da ambaton sai yadda Allah yayi shiyasa gangar jikinta ta dauki barin jimamain abinda Allahn ya 6oye mata, hakan ya sa duk da ta nemi guri musamman ta zauna bata kasa jin jiri daga zaunen ba. "Shazali na tuna" Maimuna Idris Sani Beli 55 Na Shiga Aljanna...1 Ta fada cikin rawar murya tare dą kurawa Adamu ido saboda ta canki amsa da kanta ko da shi zai mata karya. Ya kawar da kai yana sake cin magani. "Nima Na-Allahn kaina ne Hajiya, bana son zarge-zarge" Sai Hajiya ta sa masa ido sagwalo tana kallonsa amma zuciyarta cike da hirji da neman tsarin ubangiji. Suka dauki tsawon wani lokaci a haka kowa da abinda cuciyasa ke sakawa. Can Adamu ya dago ya dubeta fuskarsa na kokarin shaye fargabarta ta dazu, "Yanzu yaya zamu yi da maganar sai wa Salma ankon nan, hakuri zan bata ko kuma za ki ara min na sai mata kafin na fara aiki?" Kirjin Hajiya a nauyayae ta kada kai, "Ba komai zan bayar a siyo sai ka karba ka kai mata, don kar na baka kudin ka kashė ka ki sai mata" Ya mike yana dariya ba tare da zuciyarsa ta iya tantance abinda yake ji cikin ransa ba. Maimuna Idris Sani Beli 56 Na Shiga Aljanna...1 "Dama haka rayuwa take, in baka da kudi to duk zantukanka kila-wa-kala ne wajen mutane Cikin yanayin tunani ta amsa, "An ji, je ka" ******* Da sanyin yamınacin Alhamis ya dogara ya fito waje da kwalin sugansa mai kwara-kwara a hannu. Ban da dolen an ce a yau din nan kafin faduwar rana zai yi sadakar babu abinda zai fito da shi har sai ya sha ruwa. Shi dama can a ibada ba mai bashi wahala irin azumi, don haka ban da azumin Ramadan da ya zama farilla baya taba tarkar wani na Nafila, to yau neman rufin asirin duniya ya kai shi ka'idar da ta gindaya masa azumi bayan kwanan zaunen wurudi, sannan ya rufe ranar azumin da wani raya daren wurudin. Wuni yayi yana bacci amma abin mamaki bai hana shi jin wuyar azumin ba, in ma ba rudewa yayi ba sai ya rantse da Allah bai taba azumin da ya bashi wahala irin wannan ba. Maimuna Idris Sani Beli 57 Na Shiga Aljanna...1 Gashi dai a kwance yake, amma a kwancen yake jin zai fadi. Kamar ya kwanta a dakalin kofar gidansu yayi rabon sugan a haka lokacin da ya sanya yara suka yi masa layi, haka dai ya daure ya cije yayi rabon sannan ya raba ya kwanta. Kwanciyarsa ke da wuya ya hango abokinsa Salmanu na doso shi cikin kuzari kamar ya tashi sama. Shi ma wani matsanancin kuzarin ya motso masa bai san lokacin da ya gan shi zaune ba. Salmanu abokinsa ne na bani da wani sai shi, asali a nan unguwar suke zaune kafin Allah yayi wa mahaifiyarsa rasuwa mahaifinsa ya auro wata fitinanniyar mace, wadda babu shakka dalilinta Salmanu ya kangare har ya gagari kowa. Karshen barinsa gidan mahaifin nasa ma wuka ya dauko sai ya yanka matar uban nasa da kyar mahaifin nasa dad a jama'ar unguwa suka taru suka karbe matar, dalilin day a sanya ita kuma t ace in dai da Salmanu zata ci gaba da zama a cikin gidan to ta gama auren ubansa. Ta yi yaji ta tafi gidan ubanta, daga Maimuna Idris Sani Beli 58 Na Shiga Aljanna...1 bisani ta dawo bayan Uban Salmanu ya tara mutane har da 'yan sanda ya sanar musu ya sallama Salmanu ya yanke diyancin da ke tsakaninsu komai, ya dauko babu hannunsa, ciki kuwa har da sharadin ko gidansa aka gan shi ya shigo zai iya zuwa hukuma ta bi masa hakkinsa. Hajiyan Adamu da ta san ciki da bai na maraicin Salmanu da kuma sanin wani abu daga cikin muguntar matar babansa, sai ta - amince da zaman salmanu cikin gidanta tare da yarda ai Da na kowa ne, kuma idan da rabo in Salmanu ya sami rikon kirki kila ya shiryu. To amma me? Ba a shekara ba sai maimamkon Salmanu ya shiryu' sai ya kasance ya fara bata mata Adamu da tsayayya, don haka babu shiri ta sallami Salmanu cikin dadin rai inda ta kora shi dangin mahaifiyarsa can hannun kanin mahaifiyar tasa a Unguwar Panshekara. Amma wannan bai raba zumuncinsu da Salmanu ba wanda lokaci lokaci yana zuwa gaishe ta kuma bashi da abokin sirri sai Adamu. Maimuna Idris Sani Beli 59 Na Shiga Aljanna...1 Tun kafin ya karaso wajen Adamu ya fara kora masa kirari, "Ruwan rijiya mai wuyar raba gado. Gawo ba a hawanka ta reshe. Gonar nesa mai wuyar kai taki. Buhun Kaya ba a cika ka a danna. Buzun Bushiya Malam na kallonka yake salla a kasa. Gonar nesa mai wuyar kai taki. Dakalin majina a hau ka a zame, ka hau mutum ka zauna daidai. Kutu-kutu mugun Icce, tsohuwa na kallonka ta kwana da yunwa. Fagen gyada ba a rasa kala....." Salmanu ya karaso suka tafa cikin ihu irin nasu mai bayyana murnar ganin juna. "Ya aka iya, ya za a yi?" Inji Salmanu lokacin da ya zauna kan Dakalin kusa da Adamu. "Ka zo a lokacin day a dace Salmanu, Sama ta turnuke da hazo, kasa ta dauke ni ta cilla mata Maimuna Idris Šani Beli 60 3 Na Shiga Aljanna...1 Adamu ya fada cikin gyara zama zuciyarsa na farin cikin jin kamar matsalolinsa sun zo karshe. Salmanu ma ya tari numfashinsa. "Nima da tawa na zo, shiyasa kirarin da kake min bai taba yi min dadı irin na yau ba, lallai ka sami guri ka adana shi, domin amfaninsa ya zo. "Allah ko? To da me kazoo? Adamu ya tambaya cikin zumudi. Salmanu ya kada kai, "Ai kai zaka fara saukewa, don da alama ka fi ni abin fada, ni nawa Caca ce kawai, ko a ci riba ko kuma a fadi... me ya faru ma nag a idonka ya fada? Kai ka ma rame gaba dayanka fa!" Adamu ya kai hannu yana shafar kundukukinsa tare da kurawa hanyar da yake yawan ganin Husna ta bullo ido tsawo wani lokaci sannan ya juyo ya dubi Salmanu, "Kududdufin soyayya na fada, wanda kifin da ke cikinsa giwaye ne....." Salmanu ya kawar da kai cikin bata fuska, Maimuna Idris Sani Beli 61 Na Shiga Aljanna...1 "Ka ji wani Ajawo! Kai baka dauki kanka Zaki bane shiyasa kake tsoron Giwa. Macen banza da har zata iya zama kududdufi a duniyata, dan uwar kakanta ta ma isa..." "Kar ka ja ta da nisa cikin rashin sani Salmanu" Adamu ya fada cikin jin ciwon zagin mata da salmanu ke yi, da ma ya tsame Husna cikin zagin to kalas! ya mayar da matan zogale idan ya so. Salmanu zai yi Magana Adamu ya tare shi, "Kar mu ja ta da tsawo, ka tsayar da zafin kanka dan mu fahimci juna" "A'a tafi kawai, na ji ka fada maliyan so, kar a raina son in ka ce kududdufi" Adamu ya kada kai cikin murmushin shanye ba'ar ta Salmanu, a takaice kuma ya kwashe labari tsab ya bashi. Babu abinda yayi wa Salmanu dadi sai ritayar Adamu daga karatun boko, labarin ya yi masa dadi ba dan kadan ba har bai iya boyewa ba ta kansa ya fara sharhi, ? Maimuna Idris Sani Beli 62 Na Shiga Aljanna...1 "Gaskiya barinka karatu yayi min mugun suga" Adamu ya sanya masa ido kawai. "Zuwanka wajen Malam-na-Allah kuma ya bakanta min, da gaske ne fa shegen Malamin nan fa yana sunkuyar da 'ya'yan mutane, ni kuma ko komai nama ne a wajena wannan harkar ina mugun ganin kazantarta" Fuskar Adamu ta fara nuna jimami, nan da nan ya ci laya, "Na rantse maka da Allah ni bai taba yi min maganar ba, na san dai fara'arsa da habahabarsa ta sanya ni jin lallai banza bat a kai zomo kasuwa, na kuma yi kudurin da zarar bukatata ta biya zan ari takalmin kare, nima ina ganin kazantar haka Salmanu ka yarda da ni" "To ka manta da shi, azumin nan ma ka karya shi, ba fa karya ba ne wurudin nan na haukata mutane, don in baka tsinto kudi ba na rantse da Allah hauka zaka tsinto, kuma a daren irin wannan ranar ne a zaman wurudin nan suke haukacewa" Sai wani mugun tsoro ya runtse Adamu, ko kowa yana karya a wajensa to ban da Salmanu, Maimuna Idris Sani Beli 63 Na Shiga Aljanna...1 ba a bakinsa kadai ya fara jin maganganu a akan Malam-na-Allah ba amma shaci fadi ya dinga daukar maganganun. Ba wai tsarkin niyya ko ayyukan Salmanu ke janyo masa yarda a wajen Adamu ba face don ya hakkake babu matsi a ra'ayoyin Salmanu, saukakan fatawoyi yake bi wadanda ba zasu matsa wa numfashinsa da farin cikinsa ba. Adamu ya lula can duniyar canki-canki ya balla azuminsa wanda bai rage masa cikakkiyar awa daya ayi kiran sallar magariba ba ko ya bar abinsa? Sai juyowa yayi ya ga Salmanu da karan sigari yana zuka, a firgice zai yi Magana Salmanu ya riga shi tare da miko masa sigarin yana dariya cikin karkace lebe, "Don Manzon Allah kafa tarihi ka ja abar nan sau daya ka karya azumin nan da ita, nima agurina ta tarihi ce don karan karshe nake zuka". Adamu ya fizga yayi cilli da ita cikin tsoro da 'fusata yana kallon soron gidansu kana ya dubi hanya, Maimuna Idris Sani Beli 64 2 Na Shiga Aljanna...1 "Zaka janyo min masifa Salmanu, ka manta sa idon unguwar nan.... Salmanu ya tare, "Shikenan ya wuce, yanzu mu koma abinda دو ya fi kyau da mu... Adamu ma ya tare, "Mu fara ta kan yadda Husna zata shigo rayuwata cikin sauki, don kirjina na fada min kamar gaba daya ita ce rayuwar tawa ma "Macen ka mayar haka? Na fada maka in ka basar su da kansu suke kawo kansu in dai mata ne, kawai kai dai ka nemi karafa" In ji Salmanu cikin Gadara. Adamu ya dinga kada kai cikin jimami, "Ni ba fari dogo kyakkyawa kamar kai ba ne da mace kalar da nake so zata kawo kanta gurina, duk sai jagwal irin su Salma. Kai na ma fada maka ni ba mata nake so ba, Husna kawai יי nake so Suka tuntsire da dariya su duka sannan suka tafa. Salmanu ya yafito wani mai lemon fata da ya zo wucewa ya sai musu. Cikin saduda da jin ba shi da zabin da ya fi wannan Adamu ya Maimuna Idris Sani Beli 65 Na Shiga Aljanna...1 karbi lemo ya karya azumin musamman da Salmanu ya cigaba da kururuta masa yawan mutanen da suka haukace bayan sun kai azumin sun kuma zauna lazumin dare. Salmanu ya cigaba da ce masa, "Kai ni fa duk namijin da na ga ya kwanta yana jiran arziki daga kwance kallon gara nake masa, Allah Wallahi, Kwanji ai ba karya ba ne nemowa kai ake har a sam wa wasu, دو musamman kai da kake da wasun... "Kai baka das u?" Adamu ya tambaya yana dariya. Salmanu ya dauke kai yana cin magani, "Ni babban burina in na yi arziki shi ne in dinga tula wa wancan tsohon banzan kura da mota, ita kuma wannan kilakin da ya 6оуе а gidansa yake wa kallon mace sai na ci kan ubanta wallahi, na rantse sai nayi sanadin da zata mutu a daure shi kuma mijinta ya mutu a hanyar zaryar ganin ta kubuta, na rantse da sarkin da ya kage ni" Dariya kawai Adamu yake idan Salmanu na cin irin wadannan layun mahaifinsa da Maimuna Idris Sani Beli 66 ? 2 Na Shiga Aljanna...1 matarsa, da can yana dan kwabarša, amma tun da suka raba gari akan haka yà sanya ya daina kula shi sai dai kawai ya dinga yi masa dariya. Suna ta hirarsu har magariba ta karato, bisa dabi'ar Adamu da sallah bata wuce shi Salmanu da sallar ma gaba dayanta bata dame shi ba dole ya bishi masallaci. Dukkansu dama suna da kiyaye girmama bukatun juna. Bayan sun dawo suka wuce cikin gida Salmanu ya gai da Hajiya, suka dan jima tare da ita suna hira tana kara yi musu nasiha kamar yadda ta saba, ta yau har ta fi ta kullum kasancewar tana cikin firgicin halin da Adamu yake shirin fadawa. Bayan sun dawo dakin Adamu suka ci abinci suka cigaba da hira. "Wai me yasa na ga Hajiya a firgice? Ina fatan ba zuwana ba ne?" ne" Salmanu ya tambaya. "Kan zargin na je wajen Malam-na-Allah Adamu ya amsa. Maimuna Idris Sani Beli 67 Na Shiga Aljanna...1 "Tana da gaskiya, kuma da na san haka ne, da na kwantar mata da hankali na fada mata gaskiya" "Gara da baka sani ba din, yanzu mu je ga abinda ya kawo ka" Salmanu ya gyara zama cikin jin kumaji da nishadi, "Faduwa ce fa ta zo daidai da zama, hanyar neman kudi da samunsu cikin sassaukar hanya na kawo mana, dabararmu ce kawai zata yi aiki.." "Kai da ka ce baka son ganin Kato na jiran kudi a huce?" Adamu ya fada cikin gwasalewa. Salmanu ya girgiza kai, "Ai ba irin naka ba ne Adamu, ku da kuke jiran Aljanu su sato na mutane su kawo muku kuna kwance, akwai bambanci da sana'ar da kana zaune mutane ne zasu tako sayyadarsu su kawo maka, hasalima sai ka zuba jari, ka ga da bambanci?" Adamu ya rausaya kai, 3 Maimuna Idris Sani Beli 68 Na Shiga Aljanna...1 "Uhum ina jin ka, kar ka manta ka dai sa ni na karya azumi, da ka bar ni na kai abina ai in nayi kudin kai ma ka huta...." "Allah ya kiyaye, me zan yi da kudin jini" Suka sa dariya sannan Salmanu ya dora, "Ka na ji ko? Muma malaman tsubbu zamu zama a yanzu babu sana'ar da ta fi ta kawo kudi...." An ki cin Biri an ci Dila...." Adamu ya fada cikin dariya. "Na fada maka da bambanci, mu fa har jari zamu zuba, kuma harkar mu ba ta shirka ba ce" "Hmn" Ragon nishin da Adamu ya iya saukewa kenan. Salmanu yana dubansa y ace, "Allah kana daukar lamarin nan wasa, ka yi shahada ka sa kai kawai, a gaba zaka yi dariya ka gode min' Adamu ya yamutse fuska ya mike tsaye, "To ni wallahi kaina ya fara ciwo, kawai ka je gobe ka dawo, ga kiran sallar isha can ma an fara" Maimuna Idris Sani Beli 69 Na Shiga Aljanna...1 Salmanu ya daga kai ya bi shi da kallo kamar zai kulu, amma sai ya dake, shi ma ya mike tsayen, "Banza gwangwani kawai" Adamu ya ki tanka shi, don tsakani da Allah da gaske kansa ya fara ciwon, wannan saki na dafe da Salmanu yayi masa ya rasa da abinda zai gwada shi. Salmanu ya kulun, a fusace ya nufi kofa. Adamu ya daga murya, "Sai ka zo da wuri goben Salmanu yayi tsaki, "Zuwa goben kai ma ka tanadi dubu goma wadda za mu hada mu zuba jari" Ya shafa aljihun wandonsa, "Ni kaga tawa na tanado" Adamu ya kebe baki, "To babu laifi. Ga duhun dare ga bindiga, al'amuran duk sun zo da sauki..." "Ga kuma layar zana ba" Salmanu ma ya rama bakar maganar. Adamu ya tuntsire da dariya yana cewa, "Allah baka hakuri, ka jira mana mu je sallar Isha sai ka wuce Maimuna Idris Sani Beli 70 Na Shiga Aljanna...1 "In na je tamu Unguwar na yi, dama bana son bin sallar 'yan kabalu". ********* Salma ta kwana da damuwar halin da take zargin Adamu na neman jefa kansa, ta yi tunanin duniyar nan dan samo masa mafita ko kubutar da rayuwarsá daga mutuwar tsaye a duniya tare da zuwa lahira fankan fayau ta rasa, shi dai Adamu ba wani yake shakka ba bare ta dogara das hi ta kai masa kararsa. A zahirin ido Alh. yake tsoro amma shi din ma tuni ta fahimci tsoron na ta gina bata shiga ba ne, domin duk abinda ya hana shi ko kuma ya sa shi a gaban idonsa zai nuna ai ya hanu har abada, amma Alh. na 6acewa zai hau mita da jefar da bakar Magana har da cin alwashin in yayi kashe shi za'a yi? Wai ma Alh. haifarsa yayi da zai dinga sa masa ido alhalin uwarsa da ubansa basu sa masa idon ba? Kai kankat ma yadda ya ci lagon Alh. akan gudun makaranta ya tabbatar mata babu abinda Adámu ke bukata illa addu'a. Maimuna Idris Sani Beli 71 Na Shiga Aljanna...1 Kwana biyun nan Sa'adatu ta fahimci sam Salma ba ta cikin walwala, kuma dama tuni ta dade da sanin matsalarta bata wuce Adamu ba, amma abinda yake shake mata makoshi bai wuce kaukauce wa iyakar hanyar da zata iya taimakonta ba. A wajen Sa'adatu duk abinda kake so a rayuwa ko wani baya so zaka iya samun abin in dai ka san hanyar da ake bi a samu, to ita ta san hanyar saboda haka duk abinda ta nema a rayuwarta ita ta same shi, ta sami mijin nuna wa sa'anni wanda bay a tsallake bukatunta, ta sami kudi ta silarta da ta silar sana'o'inta, ta sami 'ya'yan da ko mutuwa tayi dole an san ta bar Iyali, 'ya'ya takwas ba wasa ba, ta cusa wa kowa soyayyarta yadda mutane na nesa da na kusa ba sa ganin laifinta ko da tayi. Duk da dai ta hakkake ba waccan dabarar tata kadai ta bata ba har da Kokarinta na kyautata kowa daga fuskarta zuwa aljihu. Hakan ya toshe ko da zaginta wani zai yi a gaban mutanen da take kyautatawa sai ta sami me karba mata. Maimuna Idris Sani Beli 72 Na Shiga Aljanna...1 Ta zari jiki ta sami Salma kwance kamar ruwa a daki. "Waj Adamun ne yayi miki irin wannan raunin haka?" Saima ta dago ta dube ta a jahilce, duk da ta san ta dauki turbar kwance abinda yake faruwa a ainihin zuciyarta. "Wanne rauni kuma Anti?" Sa'adatu ta nemi guri na zauna. "Na fahimci son da kike wa Adamu ya fara kai wa mizanin da ba zaki iya rike shi ba" Salma ta kawar da kai ba dan ta saduda da fasawa Anti Sa'a cikinta ba sai dan tana jin kunyar ta karyata abinda yake gaskiya. A labarai da fina-finai ta saba ji da ganin irin son da ke makare cikin zuciyarta bata taба tsammanin ko da mafarki akwai shi a zahirin rayuwa ba. "Haka ne?" Anti Sa'a ta sake tambaya da fuskar neman tabbaci mai kuma bayyana ta riga ta tabbatar tuni. Maimuna Idris Sani Beli 73 Na Shiga Aljanna...1 Salma ta tashi kwance daga kwanciyar da take cikin matsanaciyar kasalar da take tasowa tun daga zuciya. "Ba ni da tabbas Anti Sa'a, har yanzu cikin karyata zuciyata nake, abinda nake ji a cikin raina kamar ba shi ne son da aka saba ji ba, in ma an saba ba'a taba tarar wa mace ce take irinsa a inda ba a san darajarta ba". "Kar ki sare wa kanki gwiwa da wannan hasashe-hasashen Salma, ni ban goyi bayan mutum ya tauye wa zuciyarsa abinda take so baa matukar zai amfane shi. Adamu yà cancanci a so shi kuma ya cancanci zama miji saboda haka sarewa kai gwiwa ne ki dinga sonsa tare da kallon taki gazawar ko wacce iri ce" Tun da Sa'adatu ta ambata Adamu ya cancanci a so shi Salma ta saki baki tana kallonta cikin shakku da alamun neman ba'asi. Sa'adatu ta lura da ita don haka ta amsa mata kai tsaye, TEROL"Kyautata wa iyali a tsatso Alh. ya tsinta, haka kakansa yayi, haka babansa yayi shi ma gashi ina sahun farko na matan da ke jin dadin miji, ina kuma da yakinin Adamu ba zai yar a Maimuna Idris Sani Beli 74 Na Shiga Aljanna...1 kasa ba, wannan yasa tun kafin ma ki fara sonsa nayi miki sha'awar aurensa. Salma ta rausaya kai kawai ta nemo abin cewa ta rasa, amma dai zuciyarta na raya mata ko babu abin moro a Adamu ita dai ta fada tarkon sonsa ba tare da sa ran ko a tukwici ya kyautata matan ba. "In kuma kin ga na kyale tawa hobbasar shikenan, amma ina da yakinin in na sa hannu ko Adamu ya ki Hajiya sai ya aure ki...." Cikin faduwar gaba da dukan zuciya Salma ta sami kanta da rawar jikin kada wa Sa'a kai baki na rawa ta ce, "Na amince ki sa hannun Anti..." "To ba ni sati biyu ki gani" Anti sa'a ta fada cikin karsashi da yarda da kai. Sai karfe sha daya na şafiya ya sami shiga gidansu don ya gaishe da Hajiya, suka gaisa ya ci abińcinsa suna hira. Maimuna Idris Sani Beli 75 7 Na Shiga Aljanna..3. Wajen sha biyu sai ga kiran Salmanu ya shigo, sai a sannan ma ya tuna yadda suka rabu. Yana ta faman tuntsira dariya ya daga wayar, "Malam gobe-da-nisa" Salmanu ma ya tuntsire da dariya y ace, "Kai na fi haka mukami, Malam ba-jira kawai zaka kira ni" Adamu ya sake tuntsirewa da dariya, kafin yayi Magana Salmanu ya tare shi, "Kai babu sanya fa! Ina hanyar gidanku da fatan ka tanadi kudin nan?" "Sai dai in ni zaka kai kasuwa ka siyar, amma ko na tauna goro ni kam ba ni da shi" Salmanu ya sauke dogon tsaki y ace, "Malam Yawa kake wallahi" Kafin Adamu yayi Magana ya kashe wayar. Shi ma Adamu ya sauke tasa yana bin ta da kallo da murmushi. ido, Jikin Hajiya a sanyaye ta kurawa Adamu "Da wa ka yi waya?" "Salmanu ne" Kai tsaye ya amsa Maimuna Idris Sani Beli 76 2 "Salmanu da ya zo jiya?" Na Shiga Aljanna...1 Ta sake tambaya cikin alamar tuhuma. Cikin dauriya Adamu ya kada kai. Ya san Hajiya na son Salmanu amma sam bata son mu'amalarsa da danta don haka yanzu duk sai ya tsure, gani yake kamar zata iya shiga zuciyarsa ta ramfo kasuwancin da suke shirin Kullawa ta kafa musu kusa. Hajiya ta sake sanya masa ido cikin shakku, "Amma maganar kudin me na ji kuna yi?" Ya fara hirji cikin zuciya kuma yana iyakar kokarinsa na boye damuwar fuskarsa lokaci guda kuma zuciya da kwanyarsa na saka wa Hajiya amsa, "Kamar ya san ina cikin halin ha'ula'in neman sana'a, jiyan nan sai gashi ya zo min da maganar mu fada aikin gini maná? Shi ma ana samu kudi musamman na kwangilar tituna ko gine-ginen gwamnati da ake samu, a wuni daya kusan kullum sai 66 mutum ya sami dubu biyar zuwa sama.... Hajiya ta ji hawaye na neman kece mata amma ta danne shi. "Sai kai kuma ka ce masa me?" Maimuna Idris Sani Beli 77 Na Shiga Aljanna...1 "Ni kawai sai na amince, don dama akan gwiwa nake da neman sana'ar Hajiya ta sake jin wani yaji ya shake ta na tausayi da takaici, ba tare da ta shirya ba ta ji ta tambaye shỉ, "To kudin da naji yana Magana na meye? Cin hanci zaku bayar kafin a dauke ku aikin?" Nan ma bai yi kasa a gwiwa ba ya amsa mata yana dariyar yake, "Haba dai, wannan ai sai aikin gwamnati. Wukar sumunti zamu siya kwangiri da sauran kayan aiki, in masu daukar aikin suka gan mu da shirinmu sai sun fi gane cewa da gaske muke, saboda ba ma so mu je a kananan leburori" Hajiya ta saci idonsa ta goge kwalla. Cikin shanye damuwa a murya ta juyo ta dube shi, "Wannan sana'ar da wannan rayuwar sun fib aka sha'awa ko Adamu? Kaico baka iya zabi ba kuma tsaurin ra'ayinka aikin banza ne da wofi tun da bai san inda gata da kamata وو suke ba bare ya nemo maka su Yayi fuska ya kawar da kai, kamar zai yi Magana sai kuma ya hadiye abarsa. Maimuna Idris Sani Beli 78 Na Shiga Aljanna...1 Hajiya ta daure shakar hanci. "Menene wahala a karatu da yi wa kai kyakkawan gini har da ya fi aikin leburanci wahala ko jiran tsammani..." Kamar Adamu zai cigaba da yi mata kunnen uwar shegu, amma da ya tuna cewa in ya dauki wannan matakin ita kuma zata cigaba da kwakkwafarsa sai kawai ya murje ido ya fara shirin yi mata bore, "Sau nawa kika yi min alkawarin cewa ba zaki sake yi min maganar karatu ba? Hajiya in gani na ne ya isheki ki sha kuruminki ina fara sana'ata sai ki wuni ki kwana ma baki sanya ni a ido ba...." Ya fara kokawar tashi yana barazanar tafiya kamar yadda ya saba yi mata. Da alama ta rasa abin yi yau, a maimakon kira shi tá lallaba kamar kullum yau kawai sai ta sanya masa ido. Shi da kansa ya ji kamar bai kyauta ba sai ya dan dakata a kofar daki yana cigaba da mita cikin yanayi kamar zại yi kuka. "Ko ban fada wa kowa dalilina ba aike dai ban boye miki ba Hajiya, na ce aure nake so an Maimuna Idris Sani Beli 79 Na Shiga Aljanna...1 ce sai na yi karatu, shin a duniyar nan ni kuwa in ban tsani karatu na tsine masa ba anya akwai wanda zai tsine masa?" Har yanzu kwányar Hajiya ta kasa dawowa kan doka da oda bare ta yanke hukunci, kallon Adamu kawai take zuciyarta cike da fargaba iri-iri. Shiru duk sun yi jingo-jingum shi yana dogare nauyi da kunya sun hana shi tafiya ita kuma tana ta faman kallonsa cikin hada kan kare da na doki. Sai daga can ta nisa, "To kayi tafiyarka mana" Ya ji wani turus don bata taba yasar da fishinsa ba sai yau. Har yayi gaba kamar zai tafi cikin rashin kkwarin gwiwa sai kuma ya dawo cikin sanyin jiki, da muryar tausayi yace mata, "To kin amince in je?" "Ina?" Ta tambaya cikin rashin fahimta. Ya amsa, "Kwadagon ginin " "Ina da wannan mutuncin ne?" Ya dube ta saroro, Maimuna Idris Sani Beli 80 Σ ス Na Shiga Aljanna...1 Ta kada kai mai nuna yakini, "Kwarai da gaske, na san da ina da wannan mutuncin ko alfarmar a wajenka da kafin ka zartar da hukuncin sai ka zo ka same ni ko ka 99 sami yayanka, to yanzu me kake son in ce Ya dawo cikin karfin gwiwa ya nemi guri ya zauna yana dubanta kai tsaye, "Idan na ci baya a rayuwa ko na kasa albarka ina da yakinin da sanya hannunki Hajiya, duk al'amurana sai kin kushe kin turbuda musu kasa kuma ba haka na ga kina yi wa Alh. ba......" Sai ya zarce da shasshekar kukan da yanzun nan yaji zuwansa makogwaronsa, ba dan tausayin Hajiya ba sai Husna da ta dan kawo shawagi kirjinsa daidai wannan lokacin. Dole ya baibaye Hajiya da tausayi ita ma ta ji kukan na neman kamata, nan da nan ta hau girgiza kai t ace, "Sam ba haka ba ne karka tauye wa kanka 99 albarkar mana... Ta katse maganarta saboda shagala da kallonsa yana matsar hawaye, sai ta hau Maimuna Idris Sani Beli 81 LGugsilA suide З Na Shiga Aljanna... tunanin me ya sarsh kakanBuka gina shaka har egaji yoishareshawaydnsa etkinmatitwa kuma ya,dube da yafara yismatá kalalmaionutum Tamikaeikin sanyini jikiitanaiedakatasrda shi, "ao m uoe ekak em usnsy of sinevay ime2 "Tsaya ka karbi wani sako" Batarjira cewatsagbaita: fashlita ownde aiwar daka. Ba jimawa ta fito dankoldå lodamainyaky da bakis da alamatufa ce eveikiidlana ankiä ta mika mase. svnea sb ainidsy sb sni asds Ya karba fuskarsa cikerda lalamun rashini fabimia ya karbesya buda, saesyh tarar sordin atamfa da na leshi ne. ya sake, dawo daAido kanta çikinalamar tarnbayada sh sOTSX BY In2 Da alamuna kassashi Hilajiyazta.coms OYAnkon da Salmadalbakaskassiysi mateszre wanda nadauki nauyin sai makska jbnlaggashia nan sai kai kai mata kar ma kaooedidassiyaö Zuciyarsa eta hugatdasjimswanann siyashr amma fuskarsa ta shanye, nan domnisyasfarag murmushin yakeuvarsamadrawhadye?" "Ai kuwa kin ceto ni Hajiyaşnmı sanradis zhumet ffe wabwdnnapmlar şatrihyad ta kawa min kyallonwanko ets susy sanolis Maimuna Idris Sani Beli

Chapter 3 of 7