An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels
MARMUNA DRIS SAR
NA SHIGA
ALJANNAm
Na Shiga Aljanna...1
NA SHIGA AI AN
ajiya Uwa na zaune kan tabarma a
H
dakinta. A gahanta weni katon daro
ne cike da daushen goro tana ta
faman dauri tare da 'yan wake-wakenta
Kamar daga sama aka watso Adamu ya
fado dakin dafe da ciki yana kugi, babu batuu
ma yayi sallama kenan. Ya zube gaban Hajiya
tare da ambaton.
"Na shiga uku Hajiya.
Ta tsayar da kullin goron tana bin sa da
kallon, fuskarta na nuna yanayin takaici.
"Na shiga uku ce sallamarka yanzu
Adamu?"
Ya kwanta kan ledar tsakar dakin yana juyi
cikin kama ciki,
"To ina ma laifi Hajiya, ai 6arar dankali
samun dama ne, ni tara ma na shiga ba uku ba
don dai na soke farashin ne..."
Hauşhi ya kara kama Hajiya, amma sabo da
yi wai gawa da gatsine ya sanya ta yi kokarin
hadiyewa har ta yi masa magana cikin mutunci
da aminci,
Maimuna Idris Sani Beli 4
Na Shiga Aljanna...1
"Ka shiga ukun ya fi sallamar mutunci a
wajenka Adamu?"
"Na fada miki tara na shiga ba uku ba
Hajiya"
Ya tari numfashinta tare da tankwabe
hannunka mai sandan da take masa.
Da takaici ya ishi hajiya kawai sai ta
rausaya kai ta ce,
"K! Ai shikenan."
Ta mayar da kai ta cigaba da aikinta cikin
6ata fuska,
Sama da minti biyu babu wanda ya tsinka a
tsakaninsu, ba ta bar aikin gabanta ba shi ma
bai bar juyi a tsakiyar dakin yana kama ciki
yana kuma kugi ba.
Hakurin Hajiya ya kai makura, ta dago a
fusace ta dube shi,
"Ka san Allah? Matukar ba ka tashi ka fita
tsakar gida sannan ka shigo min da sallama ba,
ba zan saurare ka bа".
Ya tari numfashinta cikin numfarfashi,
"Yanzu Haj. don Allah da me zan ji?"
"Kai ka sani."
Ta amsa a fusace.
Maimuna Idris Sani Beli 5
Na Shiga Aljanna...1
Ya yunkuro zai yi Magana ta tare shi,
"In ba haka ba kuma in tashi in bar maka gidan"
Yana jin haka ya yunkura da kyar ya mike
cikin kama ciki da numfarfashi, dan ya san ba
karamin aikin Hajiya ba ne ta fita ta bar masa gidan. A dudduke ya fice daga dakin yana
cewa,
"Ai shi ya sa na ce ni gayana nake a duniyar
nan ba ni da kowa"
Ko kallonsa Hajiya ba tayi ba bare alamar
zata tanka masa.
Dan tsabar shegantaka sai da ya fice daga gidan gabadaya, sannan ya shigo ya dinga
kwada sallama tun daga zaure babu
kakkautawa, ya yi ta kai sha biyar, tun Hajiya
na amsawa har ta gaji ta tsuke bakinta.
Da ya zo kofar daki ma a jere yayi ta kai
takwas.
Hajiya tun da ta amsa daya ba ta kara
saurararsa ba, illa cikin ranta da take nemar
masa shiriyar Ubangiji. Mutum shekaru kusan
talatin amma har yanzu bai watsar da tashen balaga da shaidancinta ba.
Maimuna Idris Sani Beli 6
Na Shiga Aljanna...1
Ya shigo a dukensa kuma ya koma
makwancinsa na dazu ya kwanta ya cigaba da
kama ciki yana kuginsa.
Hajiya ta so ta bata rai, amma da ta san in
ma tayi a banza wai man kare sai ta hadiye
kawai ta fuskanci Adamu,
"Wai don Allah Adamu yaushe zaka yi
hankali, kana tuna cewa a shekaru talatin
watanni uku kake jira..?"
Ya katse ta cikin daga murya,
"Amma dai Inna kin san ita yunwa babu
ruwanta da babba ko yaro ko?"
Takaici ya hana Hajiya Magana sai kawai ta
sanya masa ido tsawon wani lokaci sannan ta
jinjina ta cigaba da sabgar gabanta.
Adamu ya fahimci ta shaka saboda haka ya
bar kungin da yake ya tashi zaune yana faman
jan doguwar hamma, kana ya kai hannu ya
dauki kwalelen goro a daron gabanta ya basga,
"Waccan banzar matar Sa'adatu ce ta zuba
min abinci kadan, Hajiya sai ki rantse da Allah
ubanta ne ya nemo abincin ya kawo"
"Da dai kana da mutunci ko cokali guda ta
baka abincin sai in ga kamar ta fi karfin zagi a
Maimuna Idris Sani Beli 7
Na Shiga Aljanna...1
wajenka, ai ko guga bai ci arzikin komai ba
yakamata ya ci na igiya bugu da kari kuma ba
Karenka ne ya kamo ba" Kama
In ji Hajiya wadda da farko tayi kamar ba
zata tanka masa ba.
Ya fara taunar goron tamkar mai cin kashi
yana kallonta uisb
"Wai tsakanin ni da Sa'adatu wa kika Haifad
Hajiya?"
Kai tsaye ta amsa masa cikin nuna da gaske
takeed swnuy sti nse nil snul isb sMA"
"Kai na Haifa asuna, ammasitabmijintan
kawai na Haifaosai mahaifiyarta da tai kasance
yayata amma ta dauke ni mahaifiya!. sesm яүп9г
"Shiyasa ta sami lasisin kashe nida yunwa
kina kallo Hajiya?eda si iomidst sy umsЬА
Hajiyanta sake dakatar vda kullin igorontad
tana kallonsa sakare,sdaxalamantabararAdamu
ta sha kanta, ta nemi abinda zata celtásrasa saib
da kyar ta fizgosbs 62 161 Tsnap necsW"
Yanzu donsgirman Allah ba kalji kunyarn
cewa an bar ka dalyunwa ba? In zamanin bayau
ne fa har jikaka kusa dauka karewar daukar
nauyin mace daifya'yasl вg ni ise nionide eкяр
Maimuna Idris Sani Beli 8 ile8 inc2 sinht soumisM
Ya tare da kunkuni,
Na Shiga Aljanna...1
"A yanzu ma ko ban dauki jika ba ya ci a ce
an gan ni da mace da 'ya'ya, sai dai kawai don
tawa rayuwar lito take a jikin taku. Da alama
an turo ni duniyar ne domin ku zabi tsarin
rayuwarku kuma ku zabi tawa"
Da haushi ya ishi Hajiya kawai-sai ta nuna
masa wata kular abinci,
"Don Allah dauki ka ci ka tashi ka bar min
daki"
Bai tanka ba, cikin hanzari ya mike ya
janyo kular abinci ya bude.
Hajiya na lura da shi, maimakon ya ci
abincin tunda yace yunwa na neman kashe shi,
kawai sai ya shiga tsince nama kai yana
cinyewa har ya cinye ya ture abincin.
Kada kai kawai tayi ta cigaba da nemar
masa shiriya. Yanzu da bata san halinsa ba,
shikenan ya hada ta da surukarta Sa'adatu, don
ma dai tuni an zama daya, shekarunsu sha
bakwai tare, kai hasalima Sa'adatun 'yar yarta
ce, duk abin na gida ne, don haka ne ma babu
abinda itama Sa'adatun bata sani ba a halin
Adamu.
Maimuna Idris Sani Beli 9
Na Shiga Aljanna...1
"Da alama yau ma ba ka je makaranta ba"
Ta fada tana duban keyarsa lokacin da ya
kamfato ruwa a randa yana maka.
Yana ajiye modar ya amsa mata,
"Eh, ai in an hana ihu ba a hana aha! Na ce
ni babu abincina a karatun boko, duk wanda ya
dage sai nayi kuma, to kamar ya dage yin
asarar bakinsa, lokacinsa da kuma kudinsa ne'
Hajiya ta dan ja fasali sannan ta rausaya kai,
"In sha Allah ba zan kara sanya bakina a
maganar ka je maakaranta ba, shi ma Yayanka
da ya matsu sai ka yi karatun zan fadakar da
shi cewa da gaske kake asarar kudinsa yake"
"Yauwa! Da kin kyauta wallahi"
Hajiya tayi shiru cike da jin haushi tare da
debe kaunar in Adamu zai fahimci gatan da
Yayansate masa, Yayan da samun irinsa a
wannan lokacin yake wahala. Ta shafa dalilin
da ya sanya Adamun kin jinin Yayan nasa ta
rasa.
Kamar Adamu ya san abinda ranta ke
rayawa sai gashi ya zo da amsar cikin yanayin
halin ko in kula,
Maimuna Idris Sani Bell 10
Na Shiga Aljanna...1
"Sau nawa na nemo aure ya hana ni yi, 'yar
rikonsa yake neman matsa min na aura ni kuma
na ce bana so, wallahi Tallahi babu shegen da
ya isa ya aura min wannan kundubar 'yar"
Da gudu Hajiya ta saki baki tare da kame
haбa.
Adamu ya mike cikin fishi, ya sunkuya ya
dauki kullin goro 'yan dari uku-uku guda hudu
ya sa kai zai fita.
Dole Hajiya ta magantu cikin daga murya,
"Ina zaka kai min goro har na dubu da dari
biyu?"
Ba tare da ya juyo ba ya amsa,
"Kyauta zan yi da shi"
Bai bata damar Magana ba ma, don tuni ya
fice, dole ta sauke kai cikin yanayin alhini.
Gangar jikinsa ke zaune kan dakalin kofar
gidansu rike da sabon littafin Maimuna Beli
mai suna MAFARKIN KHADIJA, zuciyarsa
da kulliyar lissafinsa na can duniyar jaruman
littafin.
Maimuna Idris Sani Beli 11
Na Shiga Aljanna...1
Ya dinga cakuda rayuwarsa da ta jaruman
littafin tsawon wani lokaci sannan ya koma
faman tsintar abubuwan da suka yi dai dai da
tasa rayuwar. Muhimmi a ciki shine, zazzafar
soyayyara da ke tsakanin Sunusi da Khadija, ya
hakikance irinta ce ke cin wuta a kirjinsa ga
yarinyar da ko sunanta bai sani ba, shi yasa ya
kuma gano bambance-bambancen da ke
tsakaninsu su ne, Khadija da Sunusi tare suke
son juna, amma nasa son shi kadai yake wa
tsalle a kirji yana ji masa raunin da kila wadda
ake wa ko ta sani ba zata taya shi jinya ba.
Abu na biyu shi ne, Khadija da Sunusi
Mahaifin Sunusi ne yayi musu karan tsaye, ko
banza yana da kwanjin da idan yayi hakan za a
zaci ya isa kuma da guminsa Sunusi ke
rayuwa, amma shi fa? Yayansa ke gwada masa
kwanji babu sidi ba sadada ya hana rayuwarsa
rawar gaban hantsi da hujjar kawai ya dauke
masa kwanon abinci ko kudin kashewa idan ta
kama, sai shegiyar takurar tura shi makaranta
da yake tun tasowarsa.
Abu na gaba shi ne, sunusi ya dauki Khadija sun yi auren sirri saboda yana da
Maimuna Idris Sani Beli 12
Na Shiga Aljanna...1
kwabbai a aljihunsa, to shi idan ya dauki hakan
mafita, in ya auri matar ya boye uwar me zai
dinga bata tana ci? Wai ma idan abar son nasa
ta goya bayan ta zama Khadija ma'abociyar
sadaukar wa so.
A guje zuciyarsa ta tsinke tunanuwanta da
kasafce-kasfcenta lokacin da ta hango wadda ta
ke yi don ita.
Can nesa ta fullo tana tafe cikin rausaya
tamkar reshen bishiyar da ke jin nishadi a
lokacin damina.
Adamu ya ajiye littafi gefe ya rafka uban
tagumi yana kare mata kallo tana kusato shi.
Wankan tarwadar mace doguwa sambal,
mai matsakaicin kauri komai nata matsakaici,
bai yawa kuma bai yi kadan ba, mai
kyakkyawar fuska dauke da madaidaicin dogon
hanci..... kai kyawawan idanuwanta ma sun
Kawata fuskarta.
Ko hauka ne Adamu ya yarda yayi, duk
duniya bai taba ganin mai kyau sama da ita ba,
bai taba ganin wadda yakamata a so sama da
ita ba, sai an rasa ta za a nemi da sunan maneji.
Maimuna Idris Sani Beli 13
1
1
Na Shiga Aljanna...1
Ya sauke kai daidai lokacin da ta yi
kusatowar da zata iya gane kallon kurillar da
yake mata.
Ba ya jin sautin takunta har ta bace, amma
zuciyarsa na bugun da yafi na karar fasa
duwatsu a nasa kunnuwanwa.
Sai da ta yi nisa da wucewa sannan ya iya
daga kai ya hange ta lokacin da take shigewa
wani shagon sai da kayan dinki. Dama kusan
kullum in ya ganta a unguwarsu shagon kayan
dinkin take zuwa, duk da haka ma yana da
tabbacin ko ma dai ya ya ne in ba a nan
unguwarsu Kurawa take ba to tabbas ba za'a
rasa ta kusa da su ba.
Ta jima a shagon kamar yadda ya jima
zaune kan dakali suna ta faman kokawa da
zuciyarsa wadda ke tunkuda shi wajenta dan ya
bayyana kai, lokaci guda kuma yana hango
Yayansa ya tsare shi da kabli da ba'adin hana
shi aurenta. Kila ya ci nasarar janyo wannan
santalar yarinyar ta tsane shi kuma ta sanya shi
kwandon shara kamar sauran 'yammatan da ya
sha neman aure Yayan nasa na tankwabe masa
hannun da yake mika wa neman aurensu.
Maimuna Idris Sani Beli 14
Na Shiga Aljanna...1
Duk zagaye-zagayensa, a yau sai da
zuciyarsa tayi nasara a kansa, ya gan shi a
hanyar kantin kayan dinki ya tunkara da
jarumar zuciya lokaci daya kuma yana shafar
aljihunsa don tabbatar da cewa nairarsa fari
wadda ta kamata ta sadar das hi da kantin
kayan dinkin tana nan a muhallinta.
Ya dinga hadiye barin da jikinsa yake yana
bayani ga mai kantin tare da mika masa darin,
"Tukur zare da allura da maballi zaka ba ni,
wai kawai na fito wanka, in dauko kaya zan
saka sai na tarar babu maballai. Bayan karya
alkawari kuma teloli sun fara tauye mudu"
Ya dauki wannan salon ne dan janyo
hankalin tauraruwar tasa da ke cikin shan
sharafin sayen kayan dinki iri-iri, da haka ya
zaci duk yadda aka yi madinkiya ce, duk da
cewa bai tantance kayan da suke zaba nata ne
ko na kawarta da ya same su tare ba, wadda
yake da tabbacin a katin ta same ta tunda bai ga
shigarsu tare ba.
Ko dai ya ja hankalinta a maganar da yayi
ba ta nuna ba, sai Tukur ne ya bushe da dariya
ya ce,
Maimuna Idris Sani Beli 15
Na Shiga Aljanna...1
"Adamu maballi a me yake da har ya zama
mudun da za'a tauye?"
Kai tsaye ya amsa,
"Sa wasa! Ai aikin lada da zunubi ba
wahala yake ba, idan daurin aurena za'a tafi na
tarar da kayan babu maballi me kake
tsammani?"
Yayi maganar ne yana satar kallonta bayan
ya fahimci sun kawo hankalinsu kansa.
Kamar wasa sai gashi ta tanka cikin fara'a
da dariya'
"Don ma ko babu kai ba fasa daura auren
za'a yi ba in dai ka tura sadaki da waliyyi"
Ya sha kokawa da nutsuwarsa kafin ta bar
shi amsawa a nutse da alamar raha,
"Hajjaju amma dai ba haka aka so ba, wai
kanin miji ya fi miji kyau, in ji Karin
maganarku ta mata ko?
Duk suka yi dariya, sannan jarumar tasa ta
mayar da hankali kan aikin gabanta na duba
kayayyakin da take siya.
:
Tukur ya се,
Maimuna Idris Sani Beli 16
Na Shiga Aljanna...1
"Zaka jira na karasa bata kayanta sannan na
nemo maka? Allurar dinka maballin ce nake
tsammanin ba ni da ita a kusa.
Ran Adamu tas! Ya nemi guri ya zauna
yana cewa,
"In zaka yi sauri babu matsala"
Nan ma ta sake tsomo baki'
"Haba da ya amsa cewa a fara bashi kafin
mu, da na tabbatar da cewa ko shi ya sami
mudun sai ya tauye, kila fiye ma da maballi"
"Allah ya sa dai ba haushi kika ji ba"
In ji Tukur yana dariya kuma ya juya ya
dubi Adamu,
"Zata wakilci Teloli 'yan uwanta ta nuna
maka su fa ba sa tauye mudu sai dai saba
alkawari ko?
"Shi ma Allah ya tsare"
Ta sake fada cikin fara'a
Murmushinta kawai tamkar ya barar da
Adamu a shagon, don haka duk karfin halinsa
sai ya kasa tankawa, in kuwa ya dage sai ya
tanka ya tabbatar yanzu zai bayar da maza.
Kila shirunsa ne ya janyo fishin kawarta,
Maimuna Idris Sani Beli 17
Na-Shiga Aljanna...1
'Ke matsalarki kin cika arahar hakora
wallahi'
Ta ki damuwa,
"A'a bari na 6ata fuska, tamkar kunun da
babu suga babu gasara
Adamu ya sake laluba abin cewa ya rasa,
amma wannan karon faduwar gaba ce ta hana
shi.
Kawarta bat a tanka ba ita ta sake jan
maganar,
"Bakeken mata irinmu in muka ce kunu
zamu dinga ci ai zamu gamu da kwantai
Amina"
"Eh, haka ne, gara ku dinga hadawa da
tallar kai"
وو" Ba na son bakar Magana"
"Amma kika nema
Ta sake tuntsirewa da dariya ta ce,
"Ke matsalarki baki iya siyasa ba Amina,
zaki rasa masu yi miki shaidar arziki bayan
99 mutuwa
A sanyaye Amina ta ce,
"Ai haushin da kike bani ne yake shafar
kowa Husna, yanzu don Allah ina ke ina
Maimuna Idris Sani Beli 18
J.aansA egide a Na Shiga Aljanna...1
sauraron Sani mai Injin markadeda sunan
soyayya?" y nos inwsk iuk nus
o:Guduma biyu ta dake shigaikahon zuci ta
farinacikin tsintar sunanta Husna, ogaskuma
waddal tà afi sta,sewátorumagánar Sanima!
markadesri sgik evaat e'es sb nuler isl sie ED
Sn Kwatsam! sai ga wadda ta fisu tsaurita fito
daga bakin Husna,rsd szob at ebi eb enaldEkIB
udf Kisbars Sanilya cigaba da amfana da furtai
Kalmarı yana sona yańa cikawanicabun daga
burinsa, oni kuma ya cigaba datattaro cinikini
markadensal yanaabani tükwicinušoshinsaka
hana masa wannanlan tauye hakkinsai da yawа
tunda ba zai iya tarackudinsaurena sbajs bain
kamata a hana shi furta abinda yake ji gaméda
nia kirjinsa balbl sy BD Ssiem sвy аb пог sh
swCikinedariya Amina tarce, ed noa Tsisddst sy
sh "Barki da mutunci Husna'sied sbodsa on sd
Ita ma tana dariyar ta amsaz nob ide sws stss
"Barashin mutinci ba ne, saukinckai ne da
iya zama da mutane. Sai dai hakan ba yà hanas
kokarin cimma burinanbałzan sáuríbmára
sanata baskumá ba zani auri mai karámar sana'a
ni
Hnans bs esi de loknoi weni taswon ds КSntin
Maimuna Idris Sani Beli 19. و من sim yhsiaالمن
Na Shiga Aljanna...1
ba, ban taba tunanin yin auren soyayya ba ni
auren kudi kawai zan yi"
Adamu ya dinga yarfe gumi a saye ba tare
da lurar kowa ba. Macen da yake so sunanta
Husna, yau ga shi zaune kusa da ita da tazarar
da bata kai takun da za'a tsaya kirga ba, sannan
tayi magana, maganar da za'a iya gane
alkiblarta da inda ta dosa har karshen rayuwa.
In babu irin son da yake mata lallai akwai aibu
cikin maganganunta, sai dai shi mai rufaffen
ido a so ya mayar da aibun nata yabo, sai ya
mayar da dukkan aibun kansa da kan yayansa
wanda shi ne bai so Husna ta gan shi a a layin
mazan da zata iya aure ba.
Rauni a zuciyarsa yanzu shi ne, yaya zai yi
da son da yake mata? Da ya laluba zuciyarsa
ya tabbatar son ba irin wanda ake iya yafewa
ba ne, saboda haka ina za shi ya samo kudin da
zata aure shi don su?
A kwanakin da suka gabata burinsa daya ne,
shi ne Husna amma a yau ya kara na biyu, shi
ne kudin da zai farantawa Husna.
Bai san hakikanin abinda yake wanzuwa a
kantin ba tsawon wani lokaci har sai da Husna
Maimuna Idris Sani Beli 20
2
Na Shiga Aljanna...1
ta farkar da shi da zazzakar muryarta cikin
yanayin barkwanci,
"Ranka ya dade za mu wuce, da fatan zakaа
yafe wa telan da ya tauye maka mudun, in
kuma ba zai yafu ba ka je ka kawo rigar na
daura maka maballin a madadinsa".
Ya dage iyakar dagiya ya wurga damuwarsa
can bangon zuciyarsa, ya dago da murmushin
yake,
"An yafe masa"
Yayi saurin kawar da kai saboda zaton
dakewarsa ba ta cika mizanin da zata 6oye
damuwarsa da rikitarsa ba.
Ya ji wani kwarin gwiwa da kyau lokacin
da cikin dariya Husna ta amsa masa,
"To madalla da karimi mai kyautar yafiya"
Bai shirya ba ya sami kansa da sake се
mata,
"Da alama kin bambanta da telolin
zamaninki, ni da kin iya dinkin maza wallahi
sai ki zama Telata"
"Ayya ban iya ba, amma idan ka tashi kawo
dinkin amaryar taka ina maraba"
Maimuna Idris Sani Beli 21
Na Shiga Aljanna..,1
nixTa amsa masa lokacin da suke 'ficewa daga
kantin, matakin da ya tabbatar masa dabi'ar
Hisnacel kawai tayiaiki akansa ba đơn ya
zamanvani abu a zuciyarta ya sanya shi samun
matsayin shimfidar fuskarta basy is d a
Nan ya shiga caje kansa ciki da bai, don
ganirvme ya rasa a kyaunhalittagsb BY
niBakinnesosai mai matsakaicin tsawo amma
kakkaura, mai dogon hanci da manyan
idanuwa wadanda suka dace da tsarin fuskarsa,
yanasdasbtsararren Saje da hashin baki wanda
yakeü saisımasa nkwarjini; musamiman saboda
sumar kai da yake Tarawa wadda tun Hajiyarsa
naifadaihart a gaji ta dainatirawa inaw iH sY
A tsarin. halittarsas yastabbatar babu abn
kušhen da Husná izata ki matsalarsa kudi ce,
kuma dolebzainemoisu in dai szasu bas hi
abinda yake so, wati Husna. E6
nilolst sb sinsded ail ssis
idsllaw ex****** ** in blainss3
"sisisT cmes il is2
vAdamu dutkuslies gabane Malam-na-Allaň a
dakinsa mai karancinahaske ko dad a hasken
Maimuna Idris Sani-Beli 22 ils8 inse anbi srumisM
E
2
Na Shiga Aljanna...1
rana balle daidai wannan lokacin na duhun
magariba
Da kyar ake iya gane abinda dakin ya
kunsa, tarin litattafai ne zube a ko ina nan da
can a dakin, sai kuma jeren allunan rubutun
sha suma birjit jingine jikin bangwayen daki,
akwai raki rataye dad a kayayyakin malamin
sai kuma kala-kalar carbi manya da kanana su
ma rataye a jikin rakin.
Daga can kusurwa akwai wata karamar
kantar katako mai dauke da kwalaban
turarukan wurudi su ma kala-kala.
Bayan gajeruwar gaisuwa Adamu ya
gabatar da bukatarsa,
"Malam zuwa na yi ni ma a ba ni wurudin
nan da aka ba Sulaiman, yanzu na gane mutum
bas hi taba kwanciyar hankali in ba kudi ya
mallaka ba?"
Malamin yayi gajeren murmushi ba tare day
a tanka bay a bude wani kundi dake kusa das hi
ya zaro takarda mai kunshe da rubutun ajami,
da kuma bayanin da fassarar boko a bayan
takardar.
Maimuna Idris Sani Beli 23
Na Shiga Aljanna...1
"Gas hi, kamar dai wancan ne da nab aka ka
dawo min da shi"
Adamu ya karba ya shiga dubawa, sai can
ya dago ya dubi Malam,
"Eh na gane irin wancan ne?"
Malam y ace,
"Ai dama ba ka kawo min turaren ba, ko ka
salwantar nab aka wani?"
Adamu ya girgiza kai,
"Yana nan Malam"
Malam ya dubi agogo,
"Shikenan sai ka je, abinda baka gane ba ka
dawo gobe, yanzu dab ake da fara kiran sallar
magariba.
Adamu ya fara godiya yana kokawar sa
hannu a aljihu,, cikin ransa yana fatan Allah ya
sa kamar wancan lokacin Malam y ace ya bar
shi, don Allah ya sani duk bogi ne sa hannu a
aljihun, naira hamsin ce a aljihun nasa.
"A'a ka bar shi kawai, zamu hadu wani
lokacin?
In ji Malam, addu'ar Adamu ta ci kenan.
Ya kara wata godiyar sannan suka tashi
gaba daya Adamu na yi masa sallama.
Maimuna Idris Sani Beli 24
ร
Na Shiga Aljanna...1
**********
"Na kira ka ne in ji yadda aka yi ka san
gaibu"
Ko gaisawa da Yayansa ba suyi ba, ya tare
shi da wannan maganar cikin daure fuska,
alhalin takanas ya aika aka yi kiransa.
Ya zaci ma wani abin kirkin ne ashe
wulakancin da aka saba za'a yi masa.
Kansa na sunkuye yana zaune kan kujera
yayin da Yayan nasa ke tsaye kerere a kansa.
Sai dai duk bacin rai da rashin kunyarsa ya
hadiye kayansa a ciki. Jiki a sanyaye ya daga
kai ya dube shi,
"Alh. Ban gane na san gaibu ba fa, a ina na
fadi hakan?"
Yayansa ya amsa masa ba tare da ya juyo ya
dube shi ba,
"Shekaranjiya ka fada wa Hajiya"
"Na ce mata gobe za a tashi kiyama?"
Ya amsa cikin cin mur da dakewa.
Maimuna Idris Sani Beli 25
Na Shiga Aljanna...1
Dama tun shekaranjiya bayan ya ji kudurin
Husna na kin auren mara sana'a ko kuma mai
karamar sana'a ya ji-ya tsani kowa a duniyarsa,
musamman ma Yayan nasa wanda ya fi kowa
gina masa Katanga da sana'ar, kuma tun
shekaranjiyan yake atisayen yi wa kowa bore,
bai yarda a shigo rayuwarsa a tauye masa
Husna a cikinta ba.
"Karatu ne na bar shi kuma babu shegen da
ya isa ya kuma sawa na yi"
Kalmomin da yake ta maimaitawa kenan
tun daga jiya zuwa yau, da ma yanzu da yake
gaban Yayansa cikin zuciyarsa.
Yayan na sa ya sha mamakin wannan bakar
maganar da Adamu ya yarfa masa, amma dai
ya hadiye yadda ta bata masa rai, yana kallonsa
kai tsaye ya ce,
"To ko hakan ma ka fada mata ne? gaskiya
na gan ka da wannan zabgegen carbi mai
'ya'ya dubu kana neman gafarar ubangiji....."
Takaici ya kama Adamu na ganin an canja
masa ma'anar wuridi.....
"Ni ba Istigfari nake ba".
Ya tare Yayan a kuntace.
Maimuna Idris Sani Beli 26
3
Na Shiga Aljanna...1
"Oh Hailala kake kenan, musamman tunda
gobe za'a tashi kiyama, shi ne kake sabunta
shahada?"
Adamu ya sake yin fuska yana murza
'ya'yan carbin hannunsa daya bayan daya tare
da yin mus-mus da baki
"Kalas! Da alama ta wannan hanyar kake
iya hango abinda zai faru gobe".
In ji Yayan cikin nuna halin ko in kula.
Har yanzu Adamu yaki ya tanka illa
fuskarsa da take iyakarta na cin magani
bakinsa kuma ya dukufa da motsi.
Yayan ya basar inda ya jira shi yayi adadin
da yake bukata yana yi masa kallon tura aniya,
sai da don kansa ya gaji da kallon da kuma
murza carbi sannan ya ajiye, sai dai bai ce
komai ba.
Yayansa ya ya fara safa da marwa a tsakiyar
falon cikin yanayin mazantaka,
"Hajiya ta sanar da ni cewa wai ka hango
baka da abinci a karatun boko, haka ne?"
Adamu ya jima kafin ya tsinka. Har yanzu
yanayinsa na nuna akule yake,
"Duba na yi kenan?"
Maimuna Idris Sani Beli 27
Na Shiga Aljanna...1
"Ah! To wa sani? Abinda nake tambaya tun
dazu kenan rashin muhimmancina ya hana ka
bani amsa".
Adamu ya dan fara mutsu-mutsu yana
kunkuni,
"Ai ka ji matsalar, shiyasa ma babu amfani
na batawa kaina lokacin yin karatu,