kalleshi tana cewa, "Tabb to kafff duniya babu wanda yasan ni karuwa ce , kuma yanzu na kai shekaru da da ma domin duk taron legos ina zuwa baya wuce ni ,
zan cigaba da rayuwata a hakan ."
Ambassador ya mike tsaye ya matsa gabanta ,
kafin kace uffan Fadeela ta jawoshi kan gadon ya fad'a kanta .
Bayan ta gama duk shed'ancin da ta gadama Ambassador ya rakota ta dawo gida
cikin sand'a Fadeela ta fara taku dan gudun farkawar Inna a bacci
tana shiga falon ta ga Inna tana zaune tana kallonta ,
cikin firgici Fadeela ta kalli Inna tana cewa, "Inna jikin ne? me kika fito yi falo."?
Inna ta mi'ke cikin mummunan yanayi tana kallon Fadeela da cewa , " Ina kika je Fadeela, naga fitar ki tun d'azu sai yanzu kika dawo ."
Fadeela cikin tashin hankali ta matsa kusa da Inna , tana sosa 'keya zata fara magana
a wannan lokacin ne Inna ta hangi jikin Fadeela samm babu kaya a jikinta ,
"Inna da ma akwai wasu kud'i ne...."
Inna ta dakatar da ita cikin mugun yanayin yadda ta ga fadeela a wannan hali
wasu zafafan hawaye ne suka zu'bowa Inna , ta kalli Fadeela tana cewa, "Yanzu Fadeela fita kikai cikin daren nan ki ka je siyar da mutuncinki , tsirara kika fita Fadeela,
innalillahi wa innailaihir raji'un".
Inna tana gama fad'a ta fad'i kasa a karkace , da sauri Fadeela tai kanta , Inna ta dakatar da ita da hannunta tana wani irin haki tana cewa, " Bazan yafe miki ba Fadeela. "
Inna ta karasa kaiwa kasa cikin hawaye ko shurawa Inna ba ta sake yi ba ,
tafiyar ke nan , haka Fadeela ta ringa tsandara ihu cikin darennan har ma'kota sai da suka fito suka zo , suka sami gawarta.
Washe gari da safe sai ga Amina Salisu da Zainab da Ruma da Ummi baby sun had'u
matukar tashin hankali Zainab da Amina suka sake shiga ganin video da su Ummi baby suka nuna mata,
Ambassador ne da Fadeela,
abin ya zuzuta su matuka
hakan ya hassala Amina Salisu wai dole sai taje ta sami Fadeela
da 'kyer Zainab ta hana ta sakamakon rasuwar Inna ,
amma ita ma Ummi baby abin da taso ke nan kawai suje ayita a gama
saida Ruma taja hankalinsu kan wani shiri da tai hakan yasa duk suka sami sanyi cikin ransu
wayar Ummi baby ce ta fara ruri ta kalli wayar tana cewa, "Mene kuma Ambassador."
wayar ta kara a kunnenta tana cewa, "Ya akai."
Daga can Ambassador cikin tashin hankali ya fara cewa , "Karfa ki fitar da wannan videon ba a rufe fuskata ba ."
Ummi baby ta kwashe da dariya tana cewa, "Ambassador na fadeela, ai karma ka damu , har inda bai dace al'uma su gani ba wanda Fadeela ta bayyana a jikinta zamu rufe , duk da bataji kunyar Allah ba zan mata adalci ."
Ambassador yace , "To shi ke nan ."
ya kashe wayar
Amina Salisu tace , "To ita dabba jaka taya gar yay mata video bata sani ba."
Dariya Ruma tasa tana cewa, "Lallai ba zaki gane kan abinba , tana can tana jin dad'inta ai komai zai bazata gane ba."
Zainab dai da zancen ya matukar rud'ata tace , "Allah ya kyauta."
Amina Salisu tace, "kuma wallahi yau d'innan saina sanar da ita Zakariyya, Zainab zai aura kafin mu jefata cikin wani bala'in."
Ita dai Zainab shiru tai tana juyayin mutuwar Inna tare da tunanin da baba Aminu na duniya data jefashi cikin tashin hankali, sai Allah yasa yabar mata duniyar .
Bayansu Ruma sun koma gida ,suka sami Kalid yana jiransu
a yau suka ziyarci Gombe state suka nemi gidan su Farida, suna zuwa wata mahaukaciya suka gani a cikin gidan tare da wasu yarah kuma suna ta wasa , daga bisani bayansun sami mari'kin Farida suka sanar da shi duk irin rayuwar da Farida ta yi harta koma ga Allah,
yaci kuka sosaii yayi nadama duk da ba laifinsa ba ne , ya dad'e yana zuba idon shigowar Farida gida , amma a halin yanzu ya cire rai ,
haka shima ya basu labarin irin rayuwar wahalar da Farida tai a cikin gidansa , ga rasuwar 'kanwar mahaifiyarta wanda ita ce yake aure ta kuma d'auki Farida sanadin rasuwar iyayenta, su dai su Ruma sun san komai domin ta basu labarin
a lokacin mutumin yake nuna wannan mahaukaciya yake sanar musu ita ce azzalumar da tai sanadin komai da ba'kin halinta , domin ma ana zargin da hannunta wajen mutuwar'kanwar mahaifiyar Farida.
Da kuka suka rabu da juna Ummi baby kamar yarinya sai da ta d'auki dutse ta kwalawa wannan mahaukaciyar aiko ta fara ruwan ashar , Ummi ba ta sake bige Mata baki .
Sun yi matukar dare suka dawo cikin kano.
Amina kam kamar yadda ta fad'a
tasa Fadeela cikin mamaki a yanzu ta gane Zakariyya Zainab zai haura shi yasa ta ga da yazo gaisuwa ko sauraranta bai yi ba .
Washe gari da safe su Ruma suna karyawa sai Ruma take cewa , "Ummi ni a ganina a maimakon yiwa Fadeela hakan , me zai hana kar mu fitar da video, kawai mu mata bazaranar ta fito ta nunawa duniya ga irin halinta , domin kinga ita mace ce abin zai ta siri cikin rayuwarta sosai."
Cikin 'bacin rai Ummi baby ta kalli Ruma tana cewa, "ke kinma isa , kamar yadda nai alwashin tozartata to wallahi sai nayi, tana tare damu tana cin dunduniyarmu
kuma ke kinsan shekararta nawa a matsayin karuwar sirri , to wallahi ta rugamu farawa ,
kuma da kike maganar mu sata ta amsa , duk mutane sun san 'kawar mu ce , hakan yasa ake kiranta da 'kawar karuwai
to idan mukai haka kowa zai ce mu ne muka jawota ciki
gwanda kowa ya ganta 'kiri-'kiri ."
Ta aje maganar cikin huci tana kallon Ruma .
share and comment.......🙏
'KAWAR KARUWAI💃💃💃
BY
AUTAR MARUBUTA
_______________________________________
page 29&30
Fadeela bayan an sake kawo mata notice yasa cikin dare ta kwashe kayanta , har yanzu babu inda kanta ya kawo mata da zata je
domin ko 'yan uwan babanta na Kaduna sun ce ta shirya ta koma can , amma tace dasu idan sun tafi bayan tayi bankwana da mutane zata taho , hakan yasa suka tafi suka barta .
Gidan Sadiq ta wuce domin zama , aiko yayi murna sosai da ganinta a wannan lokacin,
shi kawai bukatarsa ayi abin da aka saba domin kwana biyu basu ha'du ba
duk da Fadeela na fama da zazzabi da ciwon ciki hakan bai hana Sadiq yin yadda yaso da ita ba ,
aiko ta ci wahala shi kam ko a jikinsa domin ya yi abin da yake so bayan ya fito daga wanka ya sameta shan'bar a kwance jikinnata ya yi tsafi sosai , a lokacin ne mahaifiyarshi ta kirashi a waya cikin murna take sanar da shi gobe yayansa zai dawo don haka ya shirya dawowa gida ya kuma gyara masa gidansa kafin ya sauka,
shi dai Sadiq damuwarshi rashin lafiyartaa a halin yanzu , hakan yasa ya nemi kaita asubiti.
Washe gari ma'kotan Fadeela suna shirin kai mata abincin rana suka ga gidan a kulle , babu jimawa suka ga anzo ana rushe gidan , bayan sun bincika aka tabbatar musu da ansiyar da gidan , hakan yasa suka fara tunanin ko ina Fadeelan yanzu,
wata mai kimanin shekaru iriin na fadeela ce ta fito daga d'aki tana cewa, "Umma !
Ai dole a nemi fadeela a rasa kinga videon ta."
Abin ya matukar basu mamaki sosai ji da ganin Fadeela a wannan yanayin.
Fadeela na cikin asubiti ita da Sadiq samm basu da labarin video da yake yawo na Fadeela, musamman cikin makarantarsu kowa malamai da d'alubai yasan halin da Fadeela ke ciki
Sadiq yana gabanta ri'ke da takardar da dactor ya basu tabbacin wata rashin lafiya dake tattare da Fadeela.
Kuka take sosai cikin tashin hankali tana kallon Sadiq tace , "Ka mai dani gidanka Sadiq ni tawa ta 'kare."
Sadiq ya kalleta cikin tashin hankali yana cewa , "To Fadeela ke da ba matata ba ni yanzu ina zan kai ki , sanin kanki ne gidan da nake gidan yayanmu ne kuma yanzu ya dawo , nima gidan mahaifiyarmu zan koma , kawai kiyi hakuri ni zan tafi ki nemi wani gun."Ya aje mata takardarta
Sauri Fadeela tai ta ri'ko masa riga cikin rurucewa da kuka tana cewa, " Haba Sadiq kar ka mini haka dan Allah ".
Sadiq ya fincike rigarshi yana cewa, " Sake ni dallah ni babban tashin hankali na ma wayasan tarin cutukan da kike dasu da likita bai gano ba ."
A lokacin Fadeela tai tunanin tun rasuwar Inna ,Alaji Mansur da Aliyyu basu sake waiwayarta ba , hakan yasa ta kalli Sadiq Sadiq tana cewa, "To ara mini wayarka nai kira."
Ya cilla mata wayar yana kauda kai , niko nace anci moriyar gan-gan...
Ta fara sa number taji an yi sallama hakan yasa ta aje wayar tana kallon masu shigowar cikin kuka
Ruma ce ta shigo da Ummi baby sai Alaji Mansur, Aliyyu, Ambassador, Zainab, Amina Salisu.
Fadeela ta rasa me zatai murna ko tashin hankali ne yake tunkarota domin tunda ta ga Ambassador a cikin su abin ya d'aure mata kai , kowa shiru ya yi
amma Ummi baby zuciyarta tafasa take sosai idan tana kallon Fadeela
"Nasan za ki mamakin ganinmu haka to ,sharrin da kika dad'e kina shukawa yau za ki kwashe".
Ruma tai maganar cikin jin haushinta.
A jiyar zuciya Fadeela ta yi , tasha jinin jikinta cikin kwalla ta kalli Ruma tana cewa, " Wanne sharri kuma Ruma , ni ce fa Ruma."
Ummi baby cikin fusata ta kalli Fadeela tana cewa, "Ai wallahi kin bamu kunya kin yi asara."
Cikin tashin hankali Fadeela ta sake cewa , "Wai mene yake faruwa ne dan Allah."
Amina Salisu da babu tausayin Fadeela a ranta ko kad'an ta fara cewa , "Ku fad'a mata mana shegiya mahaukaciya mun gano ke KARUWA CE".
Duk sai da sukaji maganar ta ratsasu duk da ba sabon abu bane .
" Wa iya zubillah Amina Salisu, karki mini 'kazafi saboda kin tsane ni."
Ta fashe da kuka ,
"Wato 'kazafi ko macucuya munafuka."
Amina Salisu ta sake fad'a
Fadeela ta daure ta tashi daga gadon asubiti ta ri'ke hannun Zainab tana cewa, "Yanzu ke Zainab kin yarda da wannan."
Zainab ta janye hannunta ta kau da kanta .
Fadeela tace , "Na shiga uku ni , Yanzu mutanen da nake son shiryay dasu su ne zasu tozartani .".
Aliyyu ya kwashe Fadeela da wani mari da sai da ya yi sanadin komawarta gado ta zauna ,
" Kin yaudare ni , kin cuci rayuwarki ."
Ya ciro wayarsa a aljihu ya nuna mata bidionta da wani gashinan an rufe masa fuska .
Sauri tai ta Kalli Ambassador ta rushe da kuka mai 'karfi .
Alaji Mansur bai ce komai ba , haka Zainab
"Innalillahi wa innailaihir raji'un, kin yi asara Fadeela."
Amina Salisu ta fad'a
cikin izza da kuka Fadeela ta mi'ke tana cewa, "EH nayi nayi karuwanci, amma ni sam banyi don neman kud'i ba , naji na yaudare ku amma idan na sanar daku mene hakan zai amfane ku."
Fadeela ta zauna cikin kuka ta durkusar da kai tana cewa, "Yanzu na tabbatar da nayi asarar duniyata ,
akwai wata rana wajen shekaru 7 da suka wuce , mun je biki Kaduna tun daga nan komai ya fara .
Wani daga cikin abokan angon ya nuna mini yana sona , hakan yasa na yarda , domin ni Allah ya sa mini saurin sabo da yarda da mutane,
Ranar da zamu dawo kano ina cikin motarsa , ya fara mini wasu irin maganganu na rashin tarbiya, hakan yasa kawai naji shed'an ya shiga zuciyata kawai na sumba ce shi , tun daga lokacin hankalinsa ya tashi ya tafi hotel dani ,
ya yi duk yadda ya gadama dani yayin da ni kuma na ba shi had'in kai , a ranar ban dawo ba saida na sake kwana biyu, na sake ne man wasu mazan."
Fadeela ta share hawayenta tana cewa, "Bayan na dawo naji bazan iya jure zama ba tare da maza ba , kuma a lokacin sam bana san aure , naci gaba da yi a nan , wanda nake fita duk lokacin da naso , sai baba Aminu ya sa mini ido, hakan yasa ya mai dani gidansa ,
nayi cuta sosai saboda bazan jure zaman gidansa ba domin bana fita , lokacin da Inna ta ga na rame sosai tace ya dawo dani
bayan na dawo na yi matukar farin ciki, hakan yasa na yanke shawarar fita da dad dare,
nake zuwa nai abin da naso babu wanda ya sani ,
bayan shekara biyu sai na had'u dasu Farida, da farko na yi tunanin fad'a musu nima irinsu ce , amma nai tunanin nai shiru kawai zai fi na samu kwanciyar hankali, gudun ace tunda ina tare dasu nima irinsu ce, yasa na farai musu nasiha."
Kuka Fadeela ta sake rurucewa da shi tana cigaba da magana, "Yanzu babu Inna babu baba Aminu, na yi zaton zan ci gaba da watayawata ashe ni ma na gama rayuwa, yau tsawon shekaru na 7 cikin wannan rayuwa, amma a yau gani ckin tozarci ."
Ta dauko takardar da dactor ya basu tana nuna musu , "Yanzu likita ya tabbatar mini da ciwon cancer ya kama mahaifata , yace ta kai matakin da dole za a cire ko kuma komai ya iya faruwa."
Ta sake fashewa da kuka , Aliyyu yaja dogon tsaki yana cewa, "Sam banji tausayinki ba , azzaluma mayaudariya ."
yasa kai ya bar asubitin baki d'aya
Sadiq ya kalleta yana d'aukar wayarsa a cikinta yana cewa, "Nima na tafi ."
Ya tafi tana kuka
Ambassador ya kalli Ruma yana cewa, "mu ma mu tafi ko."
Ummi baby ta kalli Fadeela tana cewa , "Zamu tafi saidai muce Allah ya sake shiryamu abin da yafi miki ki koma Kaduna wajen family d'inki."
Amina Salisu taja hannun Zainab tana cewa, "Taho mu bar nan."
Suka fice Fadeela na kallonsu da bakin cikin rayuwa ,
Ummi baby ta kalleta tana cewa, "Sannan kuma video wanda ki ka yi mun watsa shi a duniya, yanzu babu sauran biyo-boye kowa yasan wace ke ."
Kuka ta sake fashewa da shi tana kallon su cikin tashin hankali, yayin da sukai tafyarsu sai Alaji Mansur kawai a Cikin d'akin .
Su Ummi baby suna fita , Ambassador ya kalleta yana cewa, "Tom yanzu kuma sai ki cika alkawari , tun yanzu zamu tafi gidana ."
Ummi baby wani tashin hankali taji ya ziyartar mata zuciya, ta kalli Ambassador cikin masifa tana cewa, "Sai kace baka ji abin da yake faruwa da Fadeela ba , gaskiya muna cikin tashin hankali Ruma
ba za mu bar asubitinnan ba sai munje an yi mana gwaje-gwaje munsan cututtukan dake tare damu."
Ruma ita ma cikin tashin hankali ta amshi maganar
Ummi baby taja hannunta suka koma cikin asubitin.
Ambassador cikin ranshi yace, "To ni mene matsayin."?
Share_____
'KAWAR KARUWAI💃💃💃
BY
AUTAR MARUBUTA
_________________________________
Page 31&32
Alaji Mansur ya kalli Fadeela dake kuka yana cewa, "Kin yaudari kanki , kin kuma b'ata rayuwarki, yanzu ke nan ba daban wa'yannan Karuwanba shi ke nan idan na aure ki na fad'a cikin masifa Fadeela, kinga rayuwa ke nan ba ki da kowa yanzu duk sun guje ki ,harda al'umar gari ,kinga yadda KARUWAI💃💃💃
sukai wasa dake, daman idan ba ka iya kamun 'barawo ba to shi zai kama ka , yanzu kina cikin mummunan yanayi a cikin garinnan .
Sannan kuma har yanzu ina sonki ."
Fadeela ta d'ago kai tana kallonshi cikin kuka
"Amma bazan iya auren ki ba , yanzu ke abin gudu ce Fadeela."
Ta sake rushewa da kuka
ya cigaba da cewa ,"Ko kad'an bazan aure ki ba , amma ba zan so rayuwarki ta tagayyara ba , dan haka zan mai dake Kaduna ,zan kuma d'au nauyin yi miki aiki ki samu lafiya , wato a cire miki mahaifa".
Kuka ta sake rurucewa da shi tana kallon Alaji Mansur ta kasa cewa dashi komai .
Cike da fargaba su Ruma suke jiran sakamakon gwaje -gwajen da akai musu , hankali ya matukar tashi
bayan wani lokaci ne aka bayyana musu cewa babu wata babbar cuta a tare dasu , amma suna d'auke da cutar sanyi mai muni a tare dasu, nan likita ya rubuta musu magani da matakan kariya , suka koma gida .
Suna zuwa kofar gida suka sami Kalid yana tsaye , aiko suka gaisa cikin girmamawa, yake musu nasiha
Nan Ruma da Ummi baby suka rungume suja suna wani kuka mai gwanin ban tausayi,
"Wallahi tun rasuwar Farida jikina ya yi sanyi , sannan yanzu naga yadda rayuwar Fadeela take tagayyara, a halin yanzu bani da burin da ya wuce na koma mahaifata Nijer wajen iyayena."
Ummi baby tai maganar cikin tashin hankali da kuka , lokaci guda kuma tana sake rungume Ruma a jikinta,
ita ma Ruma cikin gawurtaccen kuka ta fara cewa , "Allah ne abin godiya Ummi, ki dubi yadda ya kare mu daga cutuka masu had'ari da muni, ko dan wannan ya ishe mu ishara mu koma ga Allah domin babbar da ma ce ya bamu."
Kalid jikinsa ya yi sanyi duk tausayinsu ya kamashi , ya yi godiya ga Allah tare da yiwa Farida addu'a .
A lokacin ya kallesu yana cewa, "Tunda yanzu Allah yasa kun gane komai , gobe idan Allah ya kaimu duk ku shirya ni zan mai daku gidan iyayenku insha Allah."
Sake rungume juna cikin farin ciki .
Kalid yace , "Insha Allah gobe kuna farin cikin ganin 'yan uwanku ."
Ruma ta kalleshi tana cewa, "To amma ita fa Ummi baby tana Nijer ne Kalid, koda yake idan ba zaka damu ba , sai duk mu kwana a gidan mu , idan yaso washe gari sai a tafi Nijer d'in domin nima zani ."
Kalid yace , "To shi ke nan Allah ya kaimu goben ."
A halin yanzu su Alaji Mansur sun isa Kaduna zuwansu ke nan 'kanwar Inna , wato baba Laure tace Allah wadai Fadeela ta zauna mata a gida , sakamakon ta sanadin Zakariyya sun sami labarin komai
baba Laure d'amara taci da gyalenta ta kare kofar gidansu, dake babban gida ne da duk 'yan uwa suke a ciki.
"Ai wallahi zaki ga ma sakamakonki yadda Allah zai wajugaki , haka kika ki auren Zakariyya ashe akwai abin da kika 'boye tsinanniyar banza , wallahi kin 'bata mana zuriya , kuma ba zamu yafe ba , kuma kika sake kika shigo gidannan yau kwanan lahira za ki ."
Baba Laure tana maganar kamar zata rufe Fadeela da duka
sai da kyer da sutin goshi tare da taimakon wasu manyan cikin gidan , baba Laure ta amince da Fadeela ta zauna a Kaduna
a karshe Alaji Mansur ya yi musu sallama tare da ba wa Fadeela d'imbin kud'ad'en da zasu ishe ta ai mata aiki har ta samu na kashewa , nan yace mata iyakar abin da zai mata ke nan , ya tafi sai wata rana .
Ta shiga sabon tashin hankali kuwa , a cikin Daren suka tafi asubitin sakamakon motsawar ciwon nata ,
Nan Fadeela ta ga ne duniya ba sa ar ta bace ,ta wuce tunaninta , yanzu abin dake yawan fad'o mata mutuwar Inna kalmar ta da tace bazata yafe mata ba , tabbas baba Laure idan taji labarin ta haka Inna ta rasu , Fadeela zata fuskanci sabuwar tsana a cikin family, hakan yasa tai shiru tana rokon Allah yafiya.
Washe Gari
Duk sun zuba kayansu a mota sun bawa mai gida mukullin gidansa ,
Ga Zainab ga Amina Salisu da Ambassador, duk bayan sun yi sallama , sai Ruma ta shige mota , Ambassador idanunsa cike da hawaye yake kallon Ummi baby,
ita ma da tausayinshi ya kamata tasha gabansa tana cewa, "Ambassador ka yafe mini duk wani abu da nai ma na rashin kautawa, ni 'ya mace ce , kuma tsohuwar rayuwata zan koma yanzu a gaban iyayena , abin da ya kamaceka ka tuba ka koma ga Allah tunkafin duniya tai maka zafi ."
Ambassador ya rike mayafin Ummi baby yana cewa, "Dan Allah karki tafi."
Ta fisge mayafinta tana cewa, "Ummi baby nake a karuwanci, amma a yanzu Zulaihat ce , ya rage naka shiryuwa ko sa'banin haka , Allah ya had'a kowa da rabonsa."
Ta shige ta hau mota , Kalid yaja mota suka tafi , yayin dasu Zainab suke musu bye bye , suma su Ummi baby suna d'aga musu hannu .
Kalid 'karamar hukumar bebeji suka nufa cikin wani gari mai suna cutar biki .
Zuwansu ke nan wani Farin ciki ya rufe Ruma , wani irin zumud'i take jikinta na rawa, kallo guda taiwa gidansu tasan kwarai arzikin babansu ya karu, sai dai Allah yasa wannan azzalumin yayan baban nasu ya mutu wanda ya yi sanadin shigarta wannan rayuwa,
Da gudu ta fad'a cikin gidan tana kuka , taci karo da wani dattijon mutum yana alwahar azahar , tabbas shekara shida ba wasa ba , dattijon da sauri ya mike yana kiran sunan Allah cikin mamaki yana kallon Ruma , da gudu ta rungume sa cikin kuka tana cewa , "Baba ni ce , ni ce baba ."
A lokacin su Ummi baby suka shigo suna kallon yadda duk mutanen gidan suke rungume Ruma cikin tsananin kewarta,
bayan komai ya lafa Ruma ta gabatar da su Kalid, nan babu 'boye-boye ta sanar musu irin rayuwar da tai ,
ita dai mahaifiyar Ruma farin ciki take sosai da ganin yarinyar ta , bayan Ruma ta tambayesu ina baba Salisu, suka tabbatar mata da yana gidan yari , sakamakon laifin da ya aikata na yiwa yara fyade a cikin kano , aka kaishi kotu,
Wani farin ciki ne ya sake lull'be Ruma , yau kwanan zaune sukai cirrr ana labarin abubuwan da suka faru .
Washe gari mahaifin Ruma wato Alaji muhd ya yi musu bizar zuwa Niger a jirgi , da Kalid da Ruma da Ummi baby suka tafi .
Matukar zumud'i ke tattare da Ummi baby kan taje ta ga nata a halin ,
aiko da wajen la'asar suka sauka a Nijer , a halin yanzu Ummi baby matukar shau'ki take sosai ta ga wani cikin a halinta ,
bayan su isa kofar gidan ta ga babu abin da ya canza kawai sabon fenti ne da bai jima ba , wasu hawaye taji sun zubo mata kawai cikin takun 'yanci ta 'bude kofar gidan wacce ke had'e da gate , suma su Kalid suka bi bayanta
ba tare da ta yi sallama ba ta shiga tsakar gidan , kawai wasu hawayene da kasala suke biye da ita, idanunta takai kofar d'akin falon su ,wanda ta ga ta kalma da kuma tashin sautin hayaniya , kawai tasa kai tana kuka ta shiga falon ,
wata tsohuwa ce mahaifiyar babanta ta mike tsaye , mahaifinta da mahaifiyarta da 'kanwarta Aisha da taji wani arnen kitso da kunshi da gyaran fata , duk suka tashi tsaye .
Ummi baby kawai fad'uwa tai ta sume , duk sukai kanta .
Bayan ta farka kuwa sai murna ,"me yasa za ki tafi ki barmu aunty Ummi. "
Aisha ta fad'a tana kuka , Ummi baby ta basu labarin rayuwarta da kuma sanadin tafiyarta , har yanzu mahaifin Ummi baby yana sonta matuka , ya yi farin ciki sosai ,
A lokacin ake tabbatar mata bikin Aisha ake domin sauran kwana biyu d'aurin aure .
murna dai kamar ta kashesu suma makota da abokan arziki suna samun labari suka ltaho , harda saurayin Ummi baby wanda ya yi mata ciki , yazo da matukar murnarsa.
Washe gari
Su Kalid suka shirya , mahaifinsu Ummi baby ya tabbatar wa Kalid da yase masa mota tana kano tana jiransa, ya ba wa Ruma kud'i kimanin..........,tare da basu hakuri wai sun zo a ga'bar bikin 'kanwar Ummi baby, aiko sun yi matukar godiya , da kuka su Ummi baby suka rabu yayin dasu Kalid suka dawo kano .
Kalid yana isowa ya sami gallelitar motarshi mai tsada da kyau ya yi matukar murna .
BAYAN SATI
Yau kwanan Zainab biyu a Kaduna gidan Zakariyya, abin ya yi armashi da tsari .
A halin yanzu babu abin dake damun zukatan Ruma da Ummi baby suna cikin farin ciki da kwanciyar hankali tare da ahalinsu .
Saurayin Ummi baby ya matukar nadama da neman gafara , hakan yasa yake sanar da ita har yanzu yana kaunarta kuma zai aure ya