gano zuciyarshi ce ta buga,wanda hakanne yazama silar rasuwarsa.
Fahad da hydar kan gawar sukayi suna kuka suna kiranshi.
Dakyar aka rarrashesu.suka shiga yimishi addua.
Direba fahad ya tura yazo mishi da nana,dan batasan meke faruwa ba.
Kan kace me gaba daya kasar ta dauka sarki ya mutu.
Nana seda ta iso gidan tasamu lbr,kuka take kamar ranta ze fita anata rarrashinta.
A daren iyayen nana da sultan suka iso kano.
Sabida da safe zaa masa jana'iza.
Ranar kwanan bakinciki sukayi agidan kowa ka duba idonsa inbanda kuka ba abinda yake.
Gari na wayewa kofar fada ba masaka tsinke alumma sun taru domin yimasa sallah
Fahad da hydar ne suka shiryashi suka masa sutura.
Sannan aka fito dashi aka sallaceshi aka kaishi gidanshi na gaskiya.
Bayan an dawone jamaa suka fara tambayar ina hajiya babba.
Ba musu hydar ya bude kofar dakin da suka rufeta.dan yayi imani bakin cikinta ne ya kashe mahaifinsu.
Ayko da gudu ta fito cikin mutanen tana ta zage zage.gamida tonawa kanta asirin duk abinda tayi.
Kowa yashiga yimata tofin Allah tsine.itako se dariya take tana shewa.
Yar tace ta yi kokarin kamata amman ina tafi karfinta.
Tanaji tana gani hajiyar ta fice agidan da gudu cikin hauka.
Dan kowa be tausaya mata ba bare akamota.
Muje zuwa
Surbajo for lifeπππππππ
*DAN KARUWA*
πππππππ
*writen by zahra surbajo*
*page 22*
Haka suka ci gaba da zaman makoki cike da bakin ciki da takaicin rashin mahaifinsu.
Bayan sadakar Arbain din me martaba ne majalisar fada ta zauna domin nadin sabon sarki wanda kowa ya tsaida fahad kasancewarshi shine babba.
Ana gama tsaida magana daya aka sa ranar nadin sarkin.
Hydar sosai ya taya shi murna gamida fatan alkhairi agareshi.
Shide fahad jinshi kawai yakeyi yana amsawa.
Ranar nadin sarkin tazo dukansu sunci ado irin na sarauta.
Nan fa aka fara shirye shiryen nadin.
Fahad ne ya bukaci abashi abin mgn zeyi mgn,ba musu aka bashi.
Sannan yafara da addua kamin yace.
"Nayi matukar farincikin zabata da akayi dana zamo sarki awannan jiha tamu me albarka,sede inada wani uzuri dazan sanar da ku.nida Aliyu hydar duk dayane,yanada hankali da ilimi da zurfin tunani,Aliyu yayi muamala da talakawa yasan me sukeso yasan menene basa so sabanin ni da bansan hakanba,Aliyu in abu ya faru se yayi bincike kan yay hukunci sabanin ni dase nayi hukuncin sannan nake binciken,dan haka na janyewa Aliyu na yarda ba wata damuwa anada Aliyu amatsayin sarki,Allah ya tayashi ruko"yana kaiwa nan ya ajiye abin mgnr ya koma gurin zamanshi ya zauna ranshi fess dan shima so yake yayiwa kanin nasa irin sadaukarwar da yake masa.
Nam fa guri ya dauki kabbara,hydar ko gaba daya rudewa ma yayi,dan betaba zaton hawa kujerar sarki ba se gashi yayanshi ya yarje masa.
Haka aka kirashi aka nada masa rawani,gamida bashi sandar girma.
Nan akaita bushe bushen algaita.da kirari ga sabon sarki.
Nan aka shiga zuwa gaida sabon sarki,fahad ma mikewa yayi ya isa gabanshi yana shirin zubewa ya kwashi gaisuwa,se ganin hydar yayi shi ya zube agabanshi ya rike masa kafafu ya dukar da kai alamun girmamawa.
Fahad dagoshi yayi suka rungume juna.hawaye nabin fuskarsu.
Fatam alkhairi fahad yay masa sannan suka rabu kowa ya koma gurin zamanshi.
**************
*BAYAN SHEKARA GOMA SHA BIYAR*
Abubuwa da yawa sun faru aciki harda auren sarki hydar inda har matar tashi ta haifi ya tamace me sunan mahaifiyarsu amman suna kiranta da Sabrina,
Fahad ma da nana sun kara haifar yan biyu duka mata wanda suke saanni da sabrina,sunan su najwa,da jadwa.
Yayinda acikin shekaru nana itama ta rasa iyayenta duka biyu,se fayan Allah yay musu rahama.
Rayuwar duka gidajen biyu rayuwace me cike dajin dadi da so da kaunar juna
Tuni Sultan ya koma hannun hydar da zama,gata ba irin wanda be gani agurin uncle din nashi.
Wanda a halin yanzu yanacan kasar england ya kammala karatu afanni lafiya,amakarantar cambridge.inda kuma yasamu ayki acan.
Duba daya zakawa Sultan kasan shi me kyaune.
Matashine me matukar miskilanci,wanda in ze wuni beyi mgn ba hakan baya damunsa.
Sam bashida hayaniya,shiyasa ko aboki bedashi se guda daya,Safwan shine kawai abotarsu tai lasting dan ya karanci halayen sultan din shiyasa yaci maganin zama dashi.
Sultan dan kimanin shekaru talatin da haihuwa,ko kadan zina ba halinshi bace,dan aduniya ya tsaneta tsana me girma tunda iftilainta ya fadawa mahaifiyarshi.
Yana da kamala da tsoron Allah ga kwarjini bana wasa ba.
Muje zuwa
Surbajo for life.πππππππ
*DAN KARUWA*
πππππππ
*writen by zahra surbajo*
*page 23*
Fahad zaune shida hydar a lambun gidan fahad din suna tattaunawa,kai da ganin yadda suke mgnr kasan me muhimmanci ce.
Fahad ne ya gyara zama sannan yace.
"Yade kamata kayiwa danka magana ya fitar da matar daze aura,zamanshi haka beda maana kullum shekarunshi gaba suke yi"
Murmushi Hydar yayi sannan yace.
"Yaya insha Allahu zaa masa nafiso in tazo gida se muyi maganar dan a waya baze yiwuba"
"Hydar ay daga kai har shi din jirginku daya,kaima daya muka samu kai auren,nide kawai ka matsa masa yazo gida,"
Dariya hydar yayi sannan yace.
"An gama babban yaya,insha Allahu zanmasa magana kuma insha Allahu zaayi kamar yadda ka bukata"
Haka de sukai ta magana daga karshe fahad yay masa rakiya zuwa gurin motoci da fadawan da suka rakoshi.
Sallama sukayi ya tafi shi kuma yashige cikin gida.
************
Sultan zaune a dakinshi yana kallon wasan arsenal da bercalona kasancewarshi masoyi ga kungiyar arsenal shiyasa ya maida hankalinshi kan wasan.
Wayarshi ce tai kara.
Yana dubawa,yaga number uncle dinshi,da sauri ya kashe tv gaba daya sannan ya daga kiran.
Durkusawa yayi har kasa yana gaisheshi vikin nutsuwa zaka dauka agabanshi yake.
"My Boy,se yaushe zaka zo gida ne?"hydar yatambaya cike da kulawa.
Kara rusunawa sultan yayi sannan,yace.
"Daddy ban tsaida lokaciba,"
"Haba sultan yanzu fa shekarunka goma rabonka da kasar nan,sede mu muzo mu dubaka,ya kamata ka ajiye duk abinda kakeyi ka taho gida haka,muma munason ganinka,ga kannenka duk basu sanka ba ka daure kazo gida haka"
Ajiyar zuciya yayi sannan yace cikin nutsuwa.
"Daddy karshen watannan inanan zuwa insha Allahu,kuyi hkr"
Sosai hydar yaji dadin maganar sultan din,dan haka albarka yashiga sa masa sannan sukayi sallama kowa ya ajiye wayar.
Tv shi ya kunna yaci gaba da kallon wasan.
Hydar ko suna gama wayar fahad ya kira ya shaida mishi yadda sukayi,shima yaji dadi amman be nunawa hydar dinba sabida kara.
Tuni gidajen biyu suka rikice da murnar dawowarshi.
Kowa se shirin tarbarshi yake dan sunyi kewarshi.
Sabani Sabrina wacce hayaniyar da akeyi sabida ze dawo din ke bata mata rai,dan batason hayaniya ko kadan.
Suko su najwa ko ajinsu.
*************
Jirgin safe ze biyo dan haka da wuri ya isa airport,
Duk abinda yadace yayi yayi,ya gama jiran shiga jirgin kawai ya rage masa.
Ji yayi anzauna kusa dashi,da sauri yakai dubansa gurin.
.wata kyakkyawar budurwace sanye cikin shigar mutunci dake nuna ita musulmace kuma yar nigeria.
Dauke idonshi yayi akanta yaci gaba da danna wayarshi.
A hankali yaji tace masa cikin sanyayyan murya.
"Pls are you a nigerian?"
Dago kai yayi ya dubeta yayi murmushi sannan yace.
"Ofcourse,is something happen?"
Murmushi tayi sannan tace.
"Sunana hamra,daga kano state,nazo hutun makarantane nan gurin Aunty na,yau zan koma gida."
Murmushi yayi sannan yace.
"Sannu hamra,Sultan Fahad,my name from kano state, "
Murmushi tayi tashiga yimishi labarai ta kunsan halin gogan naku tun yana amsa mata har koma yaba banza ajiyarta dan ta soma sa mishi ciwon kai.
Ba abinda yayiwa hamra dadi gani kujerar su daya ita dashi,dan ganin farko da tai masa ta kamu da sonshi.
Dan haka zatai duk me yiwuwa taga ta samu numbershi.
Jirginsu na dagawa,sama,hamra ta fara surutuntaπ,
"Sultan a kano a wacce unguwa kukene?"
Yatsina fuska yayi sannan yace.
"Nasarawa"
"Wow nice to meet you,nima acan nike"
Murmushi kawai yay mata.
Can kuma se tace.
"Ka bani numberka mana mudinga gaisawa"
Kallonta yayi ido cikin ido akaro na farko da yaji wani abu ya daki zuciyarshi,dakyar ya furta.
"Na jima rabona da nigeria banida numbar nigeria,amman ki bani naki inna sauka gida zan kiraki "
Yana gama yimata bayanin ya tsinci kanshi da mamakin kanshi da yayi maganar.
Ba musu hamra ta bashi numberta yayi saving.
Da laasar suka sauka a malam aminu kano airport.
Duk family din sun hallara suna jiran isowarshi,
Yana fitowa ya hangesu,da dan saurinsa ya isa garesu suka rungumeshi cike da murnar ganinsa.
Nana da sabrina ne kawai basu zo tarbarshi ba.
Hamra ko bace mata yayi yasa bata ganshi ba,ba haka tasoba amman tarasa abunyi haka tabi yan gidansu itama ta wuce gida.
Sultan ma haka suka dunguma zuwa gida kowa na cike dajin dadi.
Gidan uncle dinshi ya sauka.
Nan yay wanka ya sauya kaya sannan yayi zaman cin abinci,bayan ya gama
Suka taba hira da mutanen gidan kadan,sannan ya mike yacewa matar hydar wacce yake kiranta,mummy.
"Mummy zanje na duba umma,abanj key."
Da sauri tasa najwa ta dauko masa ta bashi.sannan suka fice shida su najwa din dan sui masa jagora.
Suna isa gidan yayi parking.masu gadi nata zubewa suna kwasar gaisuwa har ya shige cikin gidan.
Zaune nana take,kan kujera yayinda sabrina ke kwance akan kafarta sanye cikin kayan bacci riga mara hannu sa gajeren wando wanda ko cinyarta be gama rufewa ba.
Muje zuwa
Surbajo for life.πππππππ
*DAN KARUWA*
πππππππ
*writen by zahra surbajo*
*page 24*
Kallo sultan yabita dashi,na mamakin girmanta.
Kauda kai yayi ya nemi guri ya zauna,sannan ya duka yagaida umman tashi cike da girmamawa.
"Idonka kenan sultan,haba kai har se an fada maka baka kyauta ba,taya mutum ze zauna akasar da ba tashi ba sannan ba tare da iyaliba,kayiwa kanka fada fa sultan"
Murmushi yayi ya sosa keya,sannan yace.
"Umma zanyi ne kinsan komai lokacine ki tayani da addua"
Harara tabishi dashi alamun ya raina mata wayo shide be kara mgn ba.
Sabrina ko ido take binsu dashi bata da alamun sakkowa ta gaisheshi.
Wanda hakan sosai ya bata masa rai yaji yarinyar sam bata masa ba,ji yayi zuciyarshi na mishi zafi.
Mikewa yayi yayiwa umman sallama yafice daga gidan yanufi gidan sarki.
Bangarenshi ya wuce,yana shiga daki ya haye kan gadonshi se huci yake shi kadai.
Sosai yaji tsanar sabrina acikin ranshi.dan shi mutum ne me shegen son girma.
Bacci ne yayi awon gaba dashi be farkaba se gab da magrib,da sauri ya fada toilet yayi wanka ya daura alwala ya fito ya kintsa cikin kayanshi da suka dace da kirar jikinshi.
Masallaci yaje yasamu jam'i sannan suka wuce falon hydar tare dashi.
Hirar yaushe gamo suka shigayi,kamin hydar yafara mgn cikin kulawa.
"My boy,kullum kara girma kake,shekarunka karuwa suke ba raguwa ba,yakamata babba kamarka ka ajiye iyali,hankalinmu be kwanciya, zamanka a can batare da iyali ba"
Murmushi sultan yayi yakara rusunawa sannan yace.
"Insha Allahu daddy zan nemo matar auren,inyaso kan na tafi se a daura auren mutafi tare."
Sosai batun nashi ya faranta ran hydar yashiga sa mishi albarka.
***********
Wasa wasa yanzu sultan kimani watanni uku kenan da dawowarshi,kuma tun da ya dawo sannu bata taba shiga tsakaninshi da sabrina ba,
A wannan lokacin sun shaku sosai da hamra wacce ta rikide ta zama budurwarshi,
Sosai yake sonta dan yanason mace me wayewa.kuma hamra na dashi dede gwargwado.
Soyayya suke me tsabta,inda takai kowa na gidan su hamra yasan da sultan haka shima gidansu ansan da ita.
Abokanshi da suke nace masa jin ya dawo yasa suka bibiyeshi.
Safwan kawai yakeba fuska dan yasan halinshi kuma ya iya zama dashi.
Sultan ganin sun fuskanci juna da hamra ne yasa ya shaida mata ta fadi agudansy ze turo iyayenshi.
Bayan hamra ta sanar agidansu se aka bashi dama.
Ba bata lokaci ya tura iyayen nashi,
Bayan sun nemamasa aurenta,iyayenta suka shaidamusu cewa zasuyi bincike akanshi kamin atsaida ranar auren.
Kudin gaisuwa suka bada sannan suka tafi da zummar in an gama binciken zaa kirasu.
Hamra diyace ga mininstan tsaro,Alh habu dogon karfe,so gidansu babban gidane itama.
Mahaifin hamra baza mutane yayi su binciko masa waye sultan.
Cinkin sati biyu shaidun komai suka bayyana,inda daga karshe de suka bashi final result da cewa.
"Ranka ya dade DAN KARUWANE FA, bashi da wata tarbiyya duba da wacece mahaifiyarshi,kasani ma ko can gurin yawonta ta samoshi,batun gaskiya bedace da hamra ba".
Ran mahaifin hamra in yayi dubu ya baci kasancewarshi me saurin fushi.
Kwalawa hamra kira yayi ya zayyane mata komai gameda sultan.
Sosai taji ta tsaneshi,kuka ta fashe dashi na bata lokacin kulashi da tayi.
Janta mahaifinta yayi se gidan su sultan .
Ranar jummaa ne duka suna harabar gidan azaune.
Fahad ya dauko nana sun kawowa hydar ziyara gidanshi,
Su sabrina kuma suna gefe ita da su najwa suma suna tasu hirar,hydar kuma yana tare da iyayenshi ana tsara yadda bikinshi ze kasance.
Turo kofar da akayi da karfine yasa duka suka maida hankalinsu gurin.
Hamrace tafe ita da mahaifinta cikin fushi.
Da sauri sultan ya mike ya isa gurinsu,yana tambayarsu lafiya de ko.
Muryar mahaifin hamrane ya katseshi.
"Dalla can munafuki kaida iyayen naka Allah ya tona muku asiri. Kunzo zakumin angulu dakan zabo,ashe kai din Dan karuwane!!!!! Dan karuwa ko taya ze kasance me tarbiyya"
Runtse ido sultan yayi,da karfi jikinshi na rawa.
Nana zamewa tayi ta zauna jagwab,wasu zafafan hawaye nabin idonta.
Fahad ko mutuwar tsaye yayi ya kasa magana.
Hamrace ta amshi maganar da cewa.
"So kake in aureka nima asamu karuwar acikin yayana to aniyarka ta bika Allah ya tona ma asiri wlh nafi karfin zama sirikar Karuwa,mata ga DAN KARUWA!!!!never wlh"
Tasss taji an dauketa da mari mw shiga jiki wanda seda taga wuta sabida hasken marin.
Da sauri takai dubanta kan wanda ta maretan.
SABRINA ce rike da kugu tana huci.
Cikin fushi hamra tace.
"Ke yar gidan uban waye da zaki mareni?"
Dauketa tayi da wani marin sannan tace.
"Gimbiya Sabrina ce agabanki ba sako ba,ke har kin isa keda wannan me dattin hular ku shigo mana gida kuci mana mutunci,wlh kunyi kadan,daga ke har uban naki duk shegen daya fasa Allah ya tsinewa uwarshi albarka,"
Daga hannu baban hamra yayi ze tsinke sabrina da mari,da sauri ta rike hannu,tace cikin fushi.
"Hattade dattijo,nasan darajar furfura shiyasa ban kwasheka da mari ba atun farkon shigowarka,amman wlh ka kuskura ka tabani senasa karnukan gidannnan sun farauceka,marasa mutunci kawai ku fice mana agida."
Hamra gaba daya tsorom sabrina ne yakamata yasa batayi yunkurin ramawa ba.
Kowa binta yake da ido cike da mamakin masifar tata wacce ba wanda yasan ta iya.
Baban hamra ganin take taken sabrina gab take da kifeshi da marine yasa ya wurga musu kudin gaisuwarsu yaja hannun yarsa suka fice cike da alwashin se ya dauki mataki.
Muje zuwa
.surbajo for life.πππππππ
*DAN KARUWA*
πππππππ
*writen by zahra surbajo*
*page 25*
Kowa bin sabrina da ido yake,an rasa me magana acikinsu.
Da gudu ta juya zuwa gurin Nana ta fada jikinta tana kuka tana fadin.
"Umma kice karya sukeyi,su dena ce miki karuwa ke ba ita bace su dena umma in suna fadi wlh zan iya mutuwa"tasake rushewa da kuka.
Rungumeta Nana tayi cikin matsanancin kuka itama.
Fahad ne ya mike ya usa gurinsu a hankali ya zare sabrina daga jikin nana ya ka ma nanar suka wuce gurin motarsu,kai tsaye ya zauna mazaunin direba,yajasu suka bar gidan zuwa nasu.
Hydar kasa cewa komai yayi ya wuce cikin dakinshi.
Matarshi tabishi abaya domin kwantar masa da hankali.
Sabrina kuka take iya karfinta,dan sosai ranta ya baci.
Jiki a sanyaye sultan ya isa gurinta yace cikin taushin murya.
"Kiyi shuru kaddarace kuma tana kan kowa,"
Afusace ta dago tana dubansa tace.
"Kaddara a ina,kode mugun son zuciyarka,taya zaka kwaso karuwa amatsayin matar aurenka,in kana dadironka kayi iya waje mana,taya zaka sa azo har gida azagar mana iyaye.to wlh ni ba ruwana duk wata yar kutumar uban karuwa data.... "
Tasss taji an dauketa da mari.
Agigice take kallonshi ranshi abace yace yana nunata da yatsa.
"Zaki iya zagin komai na kyaleki amman bazan taba bari ki zagi karuwa ba,karuwa nada matukar amfani arayuwata,ki iya bakinki"
A wulakance tabishi da kallo sannan tace
"Can ta matse maka in kai kana da alaka da karuwai mu bamu dashi kuma inde zagin karuwane agidannan yanzu na fara.kuma komai akaiwa shamuwa watan bakwai ne yaja mata"
Tana kaiwa nan ta juya cikin gida da gudu tana kuka.
**************
Nana ko amota in banda kuka ba abinda takeyi,kuka take kamar ranta ze fita,fahad nata rarrashinta har suka isa gida.
Ranar basuyi baccin kirkiba sabida bakin cikin da suke ciki da shi suka kwana.
*********
Mahaifin hamra ko suna fita hukumar yan sanda yay waya yabada umarnin azo akama mishi sabrina.
Yan sanda jin gidan sarki zasu kamota,yasa suka san dole se anbasu warranty na kamo tan daga sama wato ig.
Koda ya tuntubi saman se yasamu safwan abokin hydar shine ig din hakade safwan yay ta bashi hakuri ya hakura.
Maganar ta wuce.
***********
Wasa wasa seda acikin shekara guda sultan ya nemi auren mata uku yana kin yiwuwa sakamakon kalmar dan karuwa dake batawa.
Abun yaki ci yaki cinyewa wanda sanadin hakan yasanya sultan kamuwa da ciwon hawan jini.
Ga wata matsananciyar shaawa dake damunshi yarasa yadda zeyi da rayuwarshi.
Daga karshe de hakura yayi da neman auren ya fara tunanin komawa gurin aykinshi.
Sabrina ma na shiga tashin hankali mara misaltuwa sakamakon halin da familyn su suka tsinci kansu,ranta na matukar kuna gameda lamarin.
Kullum burinta ta nemo.mafita ga batun adena musu gorin.
Hankalin sabrina me taba tashi irin nayau ba bayan da wasu makwabtansu duka shigo har gida suka cimusu mutunci kan yar gidan tace ita sultan takeso wanda shi ko sanin da zamanta ma beyi ba.
Iyayensu basa son daukar mataki ne,gudun kar magar ta gama bazuwa agari yasa suke barin duk wanda yaci musu mutunci badan yafi karfinsu ba.
Sabrina kulle kanta tayi adaki tana kuka gamida tunanin mafita.
Zuwacan kamar wacce aka zabura ta mike da sauri tayi falon mahaifinta inda suke zaune shida fahad suna jimamin matsalar.
Muje zuwa
Surbajo for life
πππππππ
*DAN KARUWA*
πππππππ
*Writen by zahra surbajo*
*don Allah ina barar adduaarku kan Allah ya yayemin abinda ke damuna.π*
*26*
Ganinta kawai sukayi ta fado falon ba ko sallama.
Bin ta da ido sukayi cike da mamaki dan sun san ba halinta bane yin hakan.
Durkusawa tayi gaban hydar tana kuka tace.
"Abba tunda duk auren da ya prince ze nemo se an samu matsala har takai da ana zuwa har gida ana cimana mutunci ana tozarta mu ni na amince adauramin aure dashi.wlh duk tsanani zan zauna dashi"ta karasa maganar cikin kuka me tsuma zuciya.
Ba hydar ba hatta fahad jin maganar yayi kamar amafarki.
Sosai batun nata ya faranta ransu,dan ko kadan su basuyi wannan tunaninba.
Dago fuskarta hydar yayi yasa hannu ya goge mata hawayen dake idonta yace.
"My little princess kin tabbatar zaki iya zama dashi?"
"Na tabbatar Abba"ta bashi amsa.
"To tashi kije Allah yay miki Albarka"
Mikewa tayi ta fice afalon zuciyarta fess ji take kamar ta sauke wani kaya.
Fahad ko da hydar sunma rasa ta ina zasu fara dan gaba daya sabrina tasa su cikin shaukin farinciki mara misaltuwa.
Seda suka natsu sannan suka fara shawara gameda maganar.
"Yaya ni aganina mu nemi sultan muji ta bakinshi kar yaga kamar anmasa shigar sauri"cewar hydar.
"Ba wani jin ta bakinshi da zamuyi shi ya haifemu ko mu muka haifeshi,dolene yayi biyayya ga duk abinda muka zartar masa tunda de yarinya tayi tunanin ciremu acikin damuwa"cewar fahad.
"To shikenan yaya hakan zaayi yanzu semu tsaida lokacin bikin"
"Ranar jummaa me zuwannnan zaa daura auren,dan ranar monday daze wuce su tafi tare,sauran shagalin mata su fara shiryawa"cewar fahad hankali kwance.
**********
Duka family sun samu labarin auren Sabrina da Sultan.kowa yayi naam da auren.
Sabanin shi uban gayyar da sam abun be masa ba,shi aganinshi kawai gani ake yaki auruwa ne yasa akai musu hadin gida da yar kucakar yarinyar daya tsana.
Shiyasa duk wani shaani na bikin shi ba ruwanshi,abokinsa ake tuntuba .
Yau alhamis yau ne aka ajiye domin dinner.
Duk yadda sultan yaso daya rushe maganar zuwa dinner taki rusuwa.
Domin angayyato manyan mutane wanda shi be isa ya rusa ba.
Dole yayi wanka ya shiya awata gezner white colour tasha ayki da golding zare.
Takalmin kafarshi golding agogo da hula ma duk golding.
Sosai yayi kyau acikin kayan turare ya fesa ya nemi gefen gadonshi ya zauna,yana bin kayan da amarya zata sa da ido,wanda aka ajiye akan gadonshi,shi ya rasa dalilin kawosu bangarensa inde ba so ake abata ransa ba meyasa bazaa kai mata dakinta ba.
Yana tsaka da wannan tunani ne yajiyo sallamarta a falonshi.
Ji yayi kamar ya shaketa in yafita falon dan bakin ciki amman ya ya iya dole ya daure.
Amsa sallamar yayi ciki ciki,sannan yabata damar shigowa cikin dakin.
Turo kofar tayi ta shigo, bakinta dauke da sallama.
Kyan da tayi ya firgita sultan,dan angama mata kwalliya kenan aka turota tasa kayanta wanda aka kawosu tare da nashi.
Dubanshi tayi taga ya kauda kai daga kallonta,sema wani cika da batsewa da yakeyi.
Murmushin karfin hali tayi sannan ta taka cike da kirsa ta isa gabanshi.
Tsugunawa tayi agabanshi ta shagwaggwabe fuska ta dora hannayenta duka akan cinyarsa tace cikin shagwaba.
"Ya prince kaga mummy ko,kunshin da nace ayimin ta hana tasa ayimin wannan jagwalgwalon,yanzu dom Allah wannan yayi kyau kenan"
Yanayin da ta ajiye hannun nata akan cinyar tashi seda tsigar jikinshi ta tashi.
A hankali yabi zanen kunshin da kallo wanda yay matukar daukar hankalinshi.dakyar ya furta.
"Yayi kyau mana,ay tamiki zabi me kyau"
Wani murmushi ta sakar masa hadi da wasa da idanunta sannan ta mike tsaye tace.
"Nagode ya prince,ance kayana na gurinka suna ina in saka kar muyi latti dan kowa sun wuce mune kawai muka rage"
Da hannu ya nuna mata inda kayan suke dan koya ta motsa baki tana magana jikinshi mutuwa yakeyi.
Muje zuwa
Surbajo for life.
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels