da kallo wannan hali na AB dangane da irin wannan kulawar da yake ba wa ƙannansa yana bala'in ƙona mata rai duk wani abu da ya shafe su sai ya dinga wani rawar ƙafa more especially wannan brat girl Aydah, yanzu da tasan babu alaƙa ta jini a tsakanin shi da Aydah sai ta wani irin mugun kishi ya lulluɓe ciki da wajen zuciyarta, tsabar takaici sai ture abinci tayi ba don ta ƙoshi ba ta ɗauki handbag ɗinta a fusace ta bar restaurant ɗin.
*CRESCENT INTERNATIONAL SCHOOL*
Tun kafin AB ya yi parking ya hango Aydah tana ta faman kumbure fuska murmushi ya yi yasan yau sai sun yi daru da ita Aydah ba dai rigima ba har ta siyarwa tana dashi. Sai da ya yi mata horn kusan sau uku kafin ta nufo wurinsa duk da yasan ta ganshi tun ma kafin ya yi parking ita a dole fushi tayi fushi, tana zuwa buɗe backseat ta jefa backpack ɗinta kana ta zagaya ta buɗe front seat ta zauna, lulu eyes ɗinsa ya watsa mata yana sakar mata da tsadadden murmushinsa. Turo baki tayi gami da kauda fuska tana ci-gaba da kumbure-kumburenta cike da tsokana ya fara yi mata waƙar da yake mata sanda tana yarinya muddin yana so saka ta kuka a wancan lokaci ita yake mata "Aididi, Aididin ya Abba mai majina a hanci tayi k....
"Ya Abbaaaaa! Please stop that horrible song of yours na tsani wannan waƙa bana sonta.
Aydah ta faɗa tamkar cikin muryar kuka, yadda ta kwabe fuska yai masifar ba wa AB dariya sosai ya dinga yi mata dariya ita kuma ta ƙara hasale wa sai kawai ta kwaɓar da seat ta kwanta tare da lumshe idanuwanta "okay I'm sorry my little baby gayamin me kike so na siya miki kafin mu isa gida?"
Taƙi ta tanka masa sai rarrashinta yake tai biris dashi "Shikenan tun da ba za ki kula ni ba nima nayi fushi daga yau mun bata karki sake yi min magana.
Ya yi magana shima yana turo baki kaman ita. Aydah tana ji abunda ya faɗa tai sauri tashi daga kwance da take ta mayar da seat ɗin daidai fuskarta ya bayyanar da irin razanarwa da tayi na ji furuncinsa zuciyarta har wani kalar bugawa yake yi ba abunda ke sauri tayar mata da hankali irin Ya Abba ya ce ya yi fushi da ita "Ya Abba dan Allah karka yi fushi dani.
Tayi magana yayin da idanuwanta suka cicciko da ƙwalla, a natse AB ya juyo ya kalleta yaga yadda take danne hawayenta murmushi ya sakar mata yana faɗin "who touch my Baby??
"Ya Abba ne.
Ya faɗa sounding so childishness har wani kalar turo ƙaramin bakinta take yi wanda hakan ya daɗa ƙarawa fuskarta kyau, a daidai wani super store ya tsaya ya siya mata tarkace chocolate da biscuits, a bakin gate ya ajiye ta bai shiga gida ba yana kara jaddada mata ta tabbata taje islamiyya idan ya bincika bata je ba zai yi fushi da ita. Hakan yasa tana shiga gida ta wuce bathroom tayi wanka ta shirya cikin uniform ɗinta na islamiyya da yake Siyama bata dawo daga school ba dole ita kaɗai za ta tafi ko abinci bata tsaya ci ba ta fice direban dake kai su school ya kaita.
#Love Story 2023)2024
#Jiddah Aliyu
#Asmy b Aliyu
#team tagwaye Novels
#Kurman Allo
Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only
ACCOUNT NUMBER
0020428430
Ishaq Fatima A. Gtb
Or
8098456130
Fatima Ishaq
Opay digital services
Shaidar biya
08098456130
KATIN MTN Ta👇
07043079282
Shaidar biya ta 07065283730
Ko a tuntubi
08086207764
0816 114 6563
+234 704 040 2435
+234 903 056 9336
*ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU.
*BAQEER*
Ayusher Muhd
Umm Asghar
*KURMAN ALLO*
Asmy b Aliyu
Jidda Aliyu
*AKWAI SIRRI*
Zee Bawa
Hajja ce
*MUTALLAB ASAD*
Nana Diso
Billy S Fari
*KULUWA*
Zee yabour
Sadiya Dan
Duka Biyar ɗin akan 2k
Hudu 1600
Uku 1200
Biyu 800
Ɗaya 500
VIP💕🔥
Duk guda ɗaya 1k
NORMAL GROUP 500
VIP 1000
[11/27/2023, 10:24 AM] Jiddarh Aliyu 2: *KURMAN ALLO*
(A beautiful Love story)
NA
JEEDAH ALIYU
&
ASMY B ALIYU
#Love Story
#Gwagwarmaya
#Team tagwaye novels
*RUBUTUN ƳAN TAGWAYE ZANGO NA BIYU.*
*TAFIYAR BIYU TAFI ƊAYA*
PAID BOOK
008.
(FLASH BACK)
Alhaji Bashir Shamaki shi kaɗai mahaifiyarsa ta haifa tare da mahaifinsa tun yana da ƙaranci shekaru Allah ya yiwa mahaifinsa rasuwa sai dai yana da 'yan uwan su uku da suka haɗa uba ɗaya biyu mata namiji guda. Bayan rasuwar mahaifinsa, mahaifiyarsa ta sake aure idan ta haifi yara biyu Sanusi da Jamila. Matar Alhaji Bashir ta fari maryam ta rasu wacce duniya ta shaida ita ce ta haifi AB bayan rasuwarta ne ya auro Mariya ita kuma ta haifa masa yara uku Sadiya ita ce babba mai shekaru 25 a duniya Sadiya kyakkyawa ce sai dai ba irin matsananci kyau ɗinan ba tana da matsakaici tsayi, ga ta da jiki sosai 'yar lukuta ce kiwon parlor. Sai Siyama ita kuma tana shekara 22 Siyama da Sadiya tsayin su zai iya zuwa ɗaya sai dai Siyama bata yi jikin Sadiya ba, kuma kusan kamanunsu ɗaya sai dai Sadiya tafi Siyama hasken fata, dukkansu suna karatu ne a skyline university Sadiya tana shekarar ƙarshe yayin da Siyama yanzu ne farkon shigarta, sai auta kuma shalelen Ya Abba Aydah tana da shekaru 15 saura watanni uku ta cika shekara 16 tana SS two a crescent International school. Aydah duk ta fi su Sadiya kyawo nesa ba kusa ba, sai dai su nuna mata hasken fata saboda ita fatar jikinta chocolate color ce, bata jiki ko kaɗan gata gajera 'yar firitt da ita har yanzu da ta kai SS two ƙirjinta da kaɗan ya wuce na mai kirge dangi, su kan hips a bar ma maganar su, Aydah tana da wata irin baiwa ta ƙwaƙwalwa bala'in gifted ce komai aka faɗa mata ya zauna akanta, gata da bala'in shiga rai da wuya Aydah ta zauna a wurin ba ka ji kana sonta ba saboda talktive ce ta ƙarshen lissafi bata da saurin fushi sai dai akwai saurin kuka da shagwaɓa wannan kuma ya samu asali ne daga raino da Ya Abba ya yi mata. Duk girman laifi idan Aydah tayi indai Ya Abba yana nan ba a isa a dake ta ba.
Muhammad Bashir shamaki shi ne cikakken sunansa amma an fi saninsa da Abba schoolmate ɗinsa suna kiransa da AB saboda su saukakawa kansu fadar Abba Bashir ɗin. Abba matashi ne mai jini a jiki shekarun sa na haihuwa ba za su wuce 37 ba zuwa dai 38 Abba dogo ne sosai tsawonsa yasa har wani ɗan rankwafa ya yi yana da girman jiki don ba za a kira shi da ramamen ba. Yana da round face mai ɗauke da dogon hanci, Abba yana da wasu irin idanuwa masu masifar ɗaukar hankali gasu manya ne sosai eyes ball ɗinsa gray color ne, laɓɓansa pink kamar yana shafa lipstick sumar kansa baƙa wulik da ita, sajensa da ya bari mai haɗe da gejeren gemin ya ƙara ƙawata fuskarsa, Abba kyakkyawa ne ajin farko fatar jikinsa fara ce mai silke da ja, ja, tun kafin yasan cewa ba Daddy bane ya haife shi ya sha tambayar Daddy shi da wa ya yi kama domin Kwata-kwata ba abinda ya ɗebo daga kamanu Daddy ɓalle kuma Maryam saboda yana da hotunata sometime har saka hotonta gaba yake yi yana kallo ko zai ga idan ya ɗebo kamaninta. mutane sun sha tambayarsa ko shi half-caste ne(ruwa biyu) wannan tambayar har gobe ana masa ita Abba Yayi karatunsa tun daga primary har izuwa secondary school anan gida kano bayan ya kammala sakandare ne Daddy ya samar masa da gurɓin karatu a Kyiv national economic university ukraine ya karanci fannin ilimin kasuwanci da tattalin arziki anan ya yi degree sa har zuwa masters kana ya dawo gida Nigeria idan Daddy ya bashi matsayin CEO (Chief Executive officer) na kamfaninsa. Abba yana farko-farko dawowarsa Nigeria ya haɗu da Rumaisa Bello madawaki suka ƙula alaƙa ta soyayya wacce har takai su matakin aure wanda a ranar ɗaurin aurensu ne ɓoyayyen sirri da Daddy ya ɓoye akan Abba ya bayyana wanda shi ne silar da yasa mahaifin Rumaisa ya ce ba zai haɗa zuri'a da shege marar asali ba. Shi kuma Daddy saboda baƙin ciki da fushin zuciya anan take a wuri ya aurawa AB Sadiya.
(FLASH BACK END)
Koda AB ya dawo gida dare ya yi sosai ya tarar da abincinsa Aydah ta kawo masa da ya yi arba da warmers ɗin sai da ya yi murmushi saboda cikinsa a cike yake, ya kuma san gobe akwai rigima tsakaninsa da ita. A gajiye ya wuce bedroom ɗinsa ya yi wanka boxer kaɗai ya saka ya bi lafiyar gado.
*MASAURATAR KUDU*
Wata kyakkyawar mota ce kirar Mercedes Benz GLS 2023 fara tass da ita, ta shigo zuwa cikin masauratar daidai wurin da aka tanada domin parking mamallaki motar ya nufa ya yi parking da sauri murfin gefen direba ya buɗe wani matashin saurayi ya fito wanda da ganinsa kasan direba ne, ya buɗe backseat ƙafarsa ɗaya da ke sanye cikin takalmin sarauta halfcover ya fara sauke ta kan interlock, sai da ya kusan share 60 seconds kana ya zuro guda ɗaya nan ma sai da ya ɓata lokaci kafin ya fito da gangar jikinsa ya subhanalillah! Tsalki ya tabbata ga Ubangiji da ya halicci wannan kyakkyawar sura duk da shekarunsa sun tafi amma hakan bai ɓoye komai ba na daga kyau halittar da Ubangiji yai masa at least shekarunsa na haihuwa za su kai 52 l swear za ka zaci bai wuce 40yrs ba wani irin kyau gare shi mai fizgar hankali, gashi fari tass kaman ka taɓa skin ɗinsa jini ya fita. Jikinsa sanye da shadda milk in color dinkin babbar riga kansa ɗauke da rawani wanda ya yi matching da shaddar jikinsa. Alhaji Aliyu Mustapha na uku kenan ƙani ga Sarkin Kudu Alhaji Mahmood Mustapha na uku. Cike da izza mai ɗauke da zallan ƙasaita ya shiga takawa zuwa ainihin cikin faɗar ta mai martaba sarkin kudu faɗawa na hango shi suka fara zuba masa kirari yayin da bayi sai zubewa ƙasa suke yi suna kwasar gaisuwa ko kallo basu isheshi ba ballantana su saka ran zai amsa musu, fuskar nan tashi a maturƙe as usual. Faɗar a cike take da 'yan majalisar Sarki, irin su waziri, ciroma, wambai Galadima, jakadan Sarki da dai sauransu yana zuwa ya isa gaban sarki dake zaune akan kujerar sa ta mulki yasha naɗi da alkibba sai da ya zube ya kwashi gaisuwa kana ya nemi wurin ya zauna. Kallo ɗaya za ka yiwa mai martaba ka gano tsanani kamanin shi da Alhaji Aliyu. Sai da sarki ya ƙare masa kallo kana ya yi gyaran murya cikin izza irin ta sarakuna da suka amsa sunansu mai martaba ya ce "Aliyu mun aika maka saƙo muna so ganinka tun kwana biyu da suka gabata amma ba ka amsa kiran mu ba sai yau da ka ga dama, shin ko za mu iya sani dalilinka na yin hakan?"
Shima Alh Aliyu sai da ya gama shan ƙamshinsa irin na wanda jini sarauta ya gama ratsa shi kafin ya amsa wa mai martaba da cewa "Allah ya taimaki mai martaba Amma kasan da cewa tun inada ƙanunun shekaru bana da ra'ayin mulki, saurata kwata-kwata bata gabana.
A fusace mai martaba ke faɗin."wannan karon ba zan saurari uzurin da kake kawomin ba Aliyu nacewa baka son sarauta, kamanta sauratar gadonka ce jininka na zagaye da ita, wannan karon na rantse bazan saurari uzurinka ba kaje kawai ka fara shiri domin na saka sunanka a cikin jerin mutane goma da masaurata za ta yi bikin naɗin sauratarsu. Tashi ka tafi nagama magana.
Aliyu ya sadda kansa ƙasa yana bai wa yayansa haƙuri "Allah ya jada ranka ya ƙara ma lafiya da nisan kwana Allah ya huci zuciyarka."
Daga haka Aliyu ya miƙe tsaye ya fito daga cikin fadar wanda fadawa sai zuba masa kirarin da suka saba yi masa suke ko kallonsu bai yi ba shi wannan kirarin ma ciwon kai yake sakasa to ina ga ranar da yake mulki yasan sai ya kwanta gadon asibiti. Daga nan ɓangaren mahaifiyarsa ya wuce kai tsaye bayi mata tun daga kofar da zata sadaka da babban ɓangaren mai babban ɗaki bayi mata birjik ne ke kai da komawa kowa yana hidima bayyanar Aliyu a wajen yasa suka shiga zubewa gabansa suna miƙa gaisuwa ko kallo basu ishesa ba kai tsaye parlorn da mahaifiyarsa ke ganawa da 'ya'yanta ya nufa, wannan karon bai sameta zaune a Parlon ba kamar yadda ta saba zama ya kalli amintacciyar baiwarta ya faɗa mata tayi masa magana da mahaifiyarsa, ko minti goma bata yi ba ta dawo ta faɗa masa tana zuwa anan ta shiga hidima dashi ta cika gabansa da 'ya'yan itatuwa cima dai mai rai da lafiya irinta gidan sarauta kusan mintina goma sha biyar da zamansa sai ga mahaifiyarsa ta fito cikin babbar shigar alfarma wuyanta da hannayenta sun sha ado da gold tun kafin ta bayyana cikin parlorn ƙamshi ya gama cika ko'ina gami da zagaye ko'ina acikin Parlon,wannan ƙamshin mahaifiyarsa ce kawai mamallakiyyarsa, bayi biyu ne a bayanta tana shiga suka rufo mata ƙofar suka juya suka koma ganin bayyanar mahaifiyarsa cikin Parlon yasa ya miƙe tsaye har ta ƙaraso ta zauna bai zauna ba sai da ta zauna ya durƙusa gafda kafafunta yana gaisheta ta amsa cike da kulawa tana nazarta yanayin yaron nata. Kusan shekaru talatin harda doriyya haka yaron nata yake tun kafin ma yayi aure idan zata iya tunawa tun da ya dawo daga karatu, a haka kullum fuskarsa take babu kalar tambayar da bata yiwa Aliyu ba a lokacin sai dai yace mata babu komai idan tace rashin walwala yaron nata bai hanata sukuni za tayi karya. Jin mahaifiyarsa tayi shiru yasa ya ɗago ya kalleta cikin natsuwa yadda ta haɗe rai yasa gabansa yayi mummuna faɗuwa cikin wani irin yanayi yace "ummah.!"
"Mai sabon birnin.
ta kira sa da sunan da take kiransa dashi yana jin yadda muryarta ke shaking
A razane yake kallon fuskar mahaifiyar tasa yadda ta koma lokaci ɗaya "ba zan gaji da tambayarka ba meke faruwa da rayuwarka? Nasan akwai abunda kake boyemin tsawon shekaru talatin ko ka kashe wani rai ne da ka hana kanka walwala da farin ciki kamar yadda sauran al'umma keyi?"
Girgiza kai ya shiga yi ba tare da ya kalli mahaifiyar tasa ba ,cike da karfin hali ya furta "Dama wajen mai martaba na fito akan maganar naɗin sauratana ta Sarkin sabon birnin kudu.
Ki saka baki ummah,da gaske bazan iya daukar wannan nauyin ba duk yadda zan yi masa bayani ya kasa fahimta ta.
Aliyu ya ƙarasa maganar da respect a muryarsa, yana kallon yadda mahaifiyarsa ke karkaɗa ƙafa sunfi minti biyar a haka ba tare da kowa ya sake faɗar wata kalma ba.
Cike da izza mai babban ɗaki ke faɗin."tashi ka tafi naka gidan Allah ya bamu alkhairi. Jin haka yasa ya ɗan kalli mahaifiyarsa bai ƙara cewa komai ba ya miƙe tsaye yai mata sai da safe dama acikin gidan nasu aka yanki wani fili akayi masa gini irin na sarauta acewar mahaifin su mai martaba Sarki Mustapha na uku yafi son 'ya'yansa maza ko sunyi aure su zauna a tare dashi tunda akwai filaye manyya yanka kawai za a yi ayi masu ginin gida irin na sarauta. Duk da a ɓangaren Aliyu shi ba haka yaso ba
Ko kaɗan baya sha'awar komai na rayuwar sarauta, sam bashi da ra'ayi hakan ba haka tsarin rayuwar da ya tsarawa kansa yake ba.
Babu ranar da ba zai tuna ta ba ita ɗin ta zama jinin jikinsa duk iya ƙokarin sa na gani ya nemo ta har yau ɗinan ya kasa samun ta ko sai yaushe zai sake tozali da ita??
Tambayar da yake yiwa kansa koda yaushe kenan.
#Love Story 2023/2024
#Jeeddah Aliyu
#Asmy b Aliyu
#Team tagwaye novels
#Kurman Allo.
Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only
ACCOUNT NUMBER
0020428430
Ishaq Fatima A. Gtb
Or
8098456130
Fatima Ishaq
Opay digital services
Shaidar biya
08098456130
KATIN MTN Ta👇
07043079282
Shaidar biya ta 07065283730
Ko a tuntubi
08086207764
0816 114 6563
+234 704 040 2435
+234 903 056 9336
*ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU.
*BAQEER*
Ayusher Muhd
Umm Asghar
*KURMAN ALLO*
Asmy b Aliyu
Jidda Aliyu
*AKWAI SIRRI*
Zee Bawa
Hajja ce
*MUTALLAB ASAD*
Nana Diso
Billy S Fari
*KULUWA*
Zee yabour
Sadiya Dan
Duka Biyar ɗin akan 2k
Hudu 1600
Uku 1200
Biyu 800
Ɗaya 500
VIP💕🔥
Duk guda ɗaya 1k
NORMAL GROUP 500
VIP 1000
[11/28/2023, 3:51 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO*
(A beautiful Love story)
NA
JEEDDAH ALIYU
&
ASMY B ALIYU
#Love Story
#Gwagwarmaya
#Team tagwaye Novels
009
*RUBUTUN YAN TAGWAYE BIYAR KARO NA BIYU.TAFIYAR BIYU TAFI ƊAYA*
*ALH BASHIR MANSION*
Yau tunda tayi sallar asuba bata koma bacci ba ita ta taya Mami da yan aiki suka haɗa break fast. dama kuma Mami bata yiwa ƴa'ya ta horon rashin son aiki ba. Duk da tana da masu aiki bai sa ta sakankance da cewa yan aikin zasu riƙa yi mata komai ba. Sai ga 'ya'yan nata duka sun biyota da iya girki da son shiga kitchen idan ka cire Aydah acikinsu harta AB tun baida wayau yana taya Mami shiga kitchen indai yana a gida babu makaranta. Aydah ga ta mace sai dai bata aiki da rashin motsa jiki, idan kaji masifar mami a gidan na rashin son aiki to da Aydah ce, indai AB baya gida to sai ta shiga kitchen haka Siyama za tayi rantsuwa ba zata barsu da aiki ba ta taso ko ɓarar magi ne da yanka wani ganye tayi, haka zasu ta faɗa su ce yaya Abba, ya sangarta ta tana yiwa mutane yadda taga dama da anyi magana zai fara faɗin Aydah ai Yarinya ce duka-duka nawa take?" idan yana gida a ranakun weekend baya fita tasan a weekend idan ta dawo islamiyya dole ta shiga kitchen ta riƙa wani aikin.
To watarana idan tana jin halin nata dama da driver ya sauke ta in har bada Siyama suka tafi ba, ta balcony take bi zuwa ɓangaren AB A can za ta je tayi kwanciyarta a parlornsa tana buga game da wayarsa watarana har bacci take ,sai angama zata shiga cikin gidan taje ta ɗibi abinci taci.
Kuma daga Sadiya har Siyama babu mai magana tun da sun san yaya Abba, yana gidan baya dukansu baya zaginsu fushinsa shine punishment ɗinsu ,su kuma Allah ya ɗora musu azababben ƙaunarsa ko kaɗan basa so suga yayan nasu na fushi dasu. A kitchen tayi tsaye ta haɗa tea ta zuba soyayyen chips acikin plate ta shiga break fast ɗin da sauri kar mami ta ganta tsaye tana cin abinci tayi faɗa
tasan driver sai ya fara sauke Aydah kafin ya sauketa ita kuma tana da lecture karfe 8 daidai tasan shirin Aydah idan ma aka bibbiya yanzun za ta yi wanka kafin ta shirya ta ɓata mata lokaci gara kawai ya fara ajeta
Idan ya dawo ya kai ta tun da dama ita Aydah ta saba da shiririta tana gamawa
Ta wuce kai tsaye ɗakinta ta shirya cikin doguwar rigar Atamfa da ɗan ƙaramin mayafinta ta dauki kayan karatunta ta fito ta samu Mami a parlor ta mata sallama, da mamaki Mami ke faɗin."batare zaku tafi da Siyama ba?"
"Mami Siyama bacci take maybe batada lecture din safe.
"To ita Aydah fa??"
"Mami ya fara saukeni kin san shirin Aydah inada lecture ƙarfe 8.
"Amman dai zaku wahalar dashi.
Bata tanka Mami ba ta juya tana faɗawa Mami sai ta dawo."Mami ta bita da addu'ar Allah ya tsare hanya, sai da ta shiga ɓangaren mahaifinta ta gaishesa babu yabo babu fallasa ya amsa jiki sanyayye ta fito dama duk wata yana tura masu kuɗi a account ɗinsu, dashi suke cira suyi hidimomin makaranta da kuma lalurorinsu na yau da kullum. karfe 7:30 da rabi na safe Aydah ta fito cikin shirin zuwa school sanye cikin uniform ɗinta, Mami ta kalleta tana faɗin."Sarkin shiririta sai yanzu kika gama shirin ?"
Tun asuba, ban san ubanme kike ba yanzu ko gama break fast ɗinki wani babban aiki ne sai ki kama jiki ki je ki yi kafin driver ya dawo yaje ya sauke Sadiya."
Tamkar Aydah zata yi kuka take faɗin "shi ne kuma tace ya tafi Mami bancin tasan nima zani makarantar salon ta saka nayi latti.
Wani kallo kawai Mami ,tayi mata "ai ke senior student ce bakya gudun latti.
Mami ta ƙarashe magana tana dalla mata harara, maimakon ta nufi dinning area sai kawai ta wuce parlorn daddy tana kumbure-kumbure da turo baki
ta zauna kusa ga Daddy ta gaishesa cike da kulawa ya amsa yana tambayar "me akayiwa shalelen Ya Abba?" Hawaye har sun cika idonta cike da shagwaɓa tace masa "yaya Sadiya ce tasa driver a gaba suka yi ficewarsu bancin tasan nima zan je.
Ta ƙarasa magana tana wani matso ƙwalla.
"ke mamana shirinki ne sai hamdala yanzu ki je ki faɗawa Yayanku sai ya kai ki. miƙewa tayi ta nufi ɓangaren AB a hankali ta tura ƙofar shiga Parlorn wani irin sanyi ne ke tashi acikin Parlon, baya cikin parlorn Amma ya kunna ac ta rasa soyayyar yaya Abba ,da son sanyi komai sanyi da ake sai ya kunna AC kuma tana mamakin yadda baya mura, kai tsaye master bedroom ɗinsa ta nufa jikin ƙofar ta tsaya tayi knocking har kusan sau biyu jin shiru yasa ta tura kanta akwai duhu a ɗakin.
Haka ya saukar da duka labulayya.
Da hannunta ta riƙa lalubar switch ɗin bulb ta kunna haske ya gauraye ko'ina. Hangosa tayi kwance cikin italyn bed ɗinsa ya dunkunkune kansa cikin duvet, kai tsaye kan bed ɗin ta nufa ko fuskarsa ba a gani ɗan ɗaga duvet ɗin tayi tana kiran sunansa, can cikin bacci yake jin muryar Aydah a tsakiyar kansa ɗan buɗe idanunsa yayi masu cike da bacci yana kallon fuskarta, ta wani marairaice fuska tana kallonshi "Aydah menene?" Ya faɗa da Muryar bacci nan Aydah ta faɗa masa yadda Sadiya tayi mata gashi lokaci yana ta tafiya. "je ki parlor ki jira ni na saka kaya.
miƙewa tayi ta koma parlor mintina biyar ya fito da jallabiyya ajikinsa da car key sai da suna hanya ya tambayeta tayi break fast? tace ita batajin yunwa, faɗa ya dinga yi mata ita dai tayi shiru a hanyar dawo daga kai ta makaranta kiran Rumaisa ya shigo wayarsa, ɗauka yayi yasa a speaker ta gaishesa tana tamabayarsa yau tayi mafarkinsa shiyasa ma ta kirasa dan tashinta kenan ko kan bed bata sakko ba. Tana jin sautin murmushinsa ta cikin wayar bai dai ce komai ba ,tasan halin miskilancinsa sai ita ce tace "ba ka tambaya wane kalar mafarki bane.?" "ina tuki Rumaisa idan na isa gida i will call you back." Da mamaki a muryarta take tambayar inda yaje da safe nan? dan tasan idan zai fita office yana kai 9.
"Aydah na sauke a school ina hanyar komawa gida ya faɗa sounding so very free cikin muryarsa abu taji yana tsaya mata a wuya dakyar ta iya furta "driver ba zai kai ta school ba sai kaine za ka kaita.?"
Banza ya yi mata tamkar bai ji tambayarta ta ba, ta fara sakawa shaƙuwarsa da Aydah alamar tambaya ta fara jin tsoron kulawar da AB yake yiwa Aydah ɗin. Yana nufin ma idan sunyi aure haka zai rika yi mata?"katse kiran tayi ba tare da ta ƙara furta komai ba. ƙarfe biyu Sadiya tana tashi daga lecture ma'aikatar su Hafeez Sale ta wuce kai tsay office ɗinsa ta wuce sai da sakatariyar Hafeez ta shiga ta faɗa masa ya sha mamakin nacin da Sadiya keyi masa shi tun da tayi aure ta fita ransa baya sha'awar aurenta yanzu.
Idan ya auri bazawara yace me?" Yasan mahaifinsa da mahaifiyarsa ma Ba zasu taɓa yarda ya auri Sadiya ba a yanzu ba. tun da ta shigo cikin katafaren office ɗin nasa take binsa da kallo kona sakan ɗaya bata ɗauke kanta akansa ba tana mamakin kalar son da take yi masa tamkar ba Hafeez ɗinta ba duk yabi ya canja mata. Bai mata tayi zama ba sai ita ce ta nemi wurin ta zauna, da tulin files agabansa yana dubawa cikin natsuwa. Sai da ta kira sunansa cikin raunin murya sannan ya ɗago kansa yana kallonta ido cikin ido.
"Sadiya Meya kawoki office ɗina?" kina matsayin matar wani so kike ki ja min bala'i ne?" a raunane take faɗin."meyasa baka daga kirana koda sau daya ba kaji dalilin kiran?"karshe ma sai ka buge da blocking ɗina ina soyayyar shekaru huɗu da muke yiwa junanmu.
"Soyayya !"soyayyah!"daga ranar da kika auri wani na bani ba na tsinke wannan soyayyar acikin zuciyata Sadiya, ban taɓa yaudararki ba hasalima kece kika yaudareni.
kallonsa take tana mamakin kalamansa ,wani murmushin Sadiya tayi tare da faɗin "idan nace maka na kashe aurena saboda soyayyarka Hafeez za ka yarda?"idan nace maka naki yiwa mahaifina