Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 7
rasa Meyasa Daddy yayi tunanin haɗamu aure dashi. Lokaci ɗaya Daddy ya rusa dangantakar dake tsakanina da yaya Abba."ta ƙarasa maganar cikin shesshekar kuka dan ko kaɗan bata hango shock din dake kwance cikin fuskar Hafeez sale ba. Hafeez ya haɗiye wasu busassu miyau a hankalinsa ya yi mugun tashi "Sadiya kin fara shaye-shaye ne daman?"Hafeez ya faɗa cikin rawar murya, girgiza masa kai kurum ta shiga yi ga baki ɗaya abirkice take. Tasan labarin mutuwar Yaya AB ya riga ya zagaye duk wanda yake da alaƙa dashi "kisan kai ki kayi akan wani banza tunani naki."Hafeez ya faɗa sounding so very harsh duk da ya fahimci ko kaɗan bata cikin natsuwarta lokacin jin yake kamar ya kwaɗawa Sadiya mari kifa kansa yayi jikin sitiyarin mota yana ambaton Allah a ransa yama rasa kalar tunanin da ya kamata yayi a wannan lokacin Sun fi minti goma a haka babu mai magana a cikinsu sai shesshekar kukan Sadiya dake tashi a motar mai ciked a danasanin abinda ta aikata tare da hango makomar rayuwarta, ta tabbatar itama kasheta za ayi tada motar Hafeez yayi batareda ya sake yiwa Sadiya magana ba, ya harbata kan titi bai tsaya da ita ko'ina ba sai cikin harabar Bon hotel ya kashe mota Sadiya ta ɗago rinannun idanuwnta tana ƙarewa harabar wurin kallo, duk da bata cikin natsuwarta ta gane hotel ne Hafeez ya kawota wani irin mummunan faɗuwa gabanta yayi. Tunda take a rayuwarta ƙafarta bata taɓa tako cikin hotel ba tun tana budurwa, ballantana yanzu da aure akanta ace ta shigo hotel da tsohon saurayinta ganin bata motsa daga inda take ba sai bin Hafeez ɗin take da kallo cike da gajiya a muryarsa yake faɗin."muje mu kama ɗaki Sadiya mu samu mafita kinga yanzu dare yayi ban san inda zan ajeki ba bayaga nan, Jiki sabule ta balle marfin motar tabi bayansa har zuwa cikin reception ɗin Ya kama masu ɗakin da zasu sauka su tattauna dan yasan babu maganar su kwanta suyi bacci daga ita har shi. Tana tsaye tana kallonsa har ya dawo da key a hannunsa ya kalleta yana faɗin suje babu musu tabi bayansa cikin wani irin sanyi jiki da kansa ya buɗe ɗakin ya shiga sa'anan tabi bayansa ciki da parlor ne ta nemi kujera mai cin mutum ɗaya ta sulale ta zauna tana jin tsoro da tashin hankali na cika zuciyarta lokaci ɗaya. Dafe kansa Hafeez yayi da duka hannunsa biyu ya rasa ma wane kalar tunani zaiyi tabbas mata duka ragaggen tunani ne dasu idan banda hauka taya zatayi kisan kai bancin tasan itama kasheta za ayi. "Sadiya ya zama dole gobe kije ki gurfana agaban iyayenki ki nemi gafarar su bamu da tabbas akan AB ɗin ya mutu ko yana raye. A wani irin razane take faɗin."Na koma kace Daddy ya yankani Nima?"meyasa baka fahimta saboda son da nake yi maka na kasa karɓar yaya Abba a matsayin mijina, na kasa karɓar ƙaddarar zama gidansa, idan har soyayyar da kake min da gaske ne bai kamata kace na koma gidanmu cikin wannan yanayin ba Hafeez."baki buɗe Hafeez ke kallonta to me kike so nayi?"so kike na gudu dake muje wani wurin muyi aure ko yaya?"ke idan zaki iya barin iyayenki ni bazan iya barin nawa iyayen ba. kallonsa kawai sadiya keyi a wannan lokacin tana mamakin kalaman dake fitowa daga bakin Hafeez din. "ke kin san dole idan aka wayi gari akaji mutuwar AB acikin garin Kano dole a shiga nemanki so ki ke ki jamin masifa Sadiya ina zaman zamana."na faɗa maki gobe da safe zan kai ki gaban iyayenki ko ki hau adaidaita sahu ki tafi da kanki kar ma aganmu a tare a ɗauka da haɗin bakina kika kashesa. Ki tashi ki shiga ciki ki barmin parlorn, kallon Hafeez take tamkar bashi ba duk yabi ya sauya shin ina soyayyar da yake ikirarin yana yimata? "Sadiya ki daina yimin irin wannan kallon. miƙewa Sadiya tayi ta nufi cikin bedroom ɗin gefen bed ta zauna ta dafe kanta tana tunanin makomar rayuwarta mai cike da na sani tasan 'yan gidansu yanzu sun tsaneta duka kannenta da iyayenta, duk akan Abba Bashir."tun farko ban amince da wannan auren ba Daddy meyesa kazo ka lalata komai sadiiya ta ƙarasa maganar tana danna kanta ciki pillow ta saki wani irin kuka mai girgiza zuciya da ruhi. Daga Daddy har Hajiya mariya wacce yaranta suke kira mami tsaye suke a bakin emagency suna ganin yadda likitoci ke kai da kawo, batareda an masu bayanin wane hali Abban yake ciki ba saboda tashin hankali suna wurin a tsaye har qarfe huɗu na a asuba, sauro kuwa duk ya gama canye naman jikinsu dan basu mabi ta kansa ba tashin hankali bai sa sunji cizon da yake masu ba. Hawaye na zuba a idanu Mami tana addu'ar Allah ya tashi kafaɗun Abba, idan suka rasa Abba batasan wane hali zasu shiga ba. wani babban likita ne ya fito daga ɗakin da Abba ,yake ciki da sauri Alh Bashir ya nufesa cikin sauri da rawar murya yake faɗin."likita ya jikin nasa?"girgiza kai matashin likitan yayi yace su samesa a office ga baki ɗaya har Abdulkarim da yake tare dasu suka bi likitan kowa jikinsa a mugun sanyayye, bayani likita yayi masu wanda da kyar da taimakon Allah Abba,ya tsira da rayuwarsa sai dai yaji mugun rauni acikinsa sun masa allurar bacci daga Daddy har Mami wata irin ajiyar zuciya suka shiga saukewa a boye shima Abdulkarim sai lokacin ya samu ya dawo cikin natsuwarsa banda tsinewa Sadiya babu abunda yake a aransa Abdulkarim ya kalli Daddy yana faɗin."suje gida kafin washe gari zai zauna da Abba ɗin, suna mota Mami taga kiran siyama ya shigo a wayarta daman ta fito da ita ne koda wani zai kira acikinsu, lokacin karfe biyar da rabi na asuba mami ta dauka cike da ƙarfin hali tana ƙoƙarin ɓoye damuwarta."Mami ina kika je keda Daddy?"meya faru?"Siyama duk ta ruɗe. "gamu nan kan hanya siyama da haka mami ta katse wayar har suka kai gida daga Mami har Daddy kowa da abunda ke cin zuciyarsa gashi har lokacin likita bai basu damar ganin yaron nasu ba, zaune suka tarar da Siyama a parlorn da kayan bacci riga da wando masu kauri ajikinta tana ganin iyayen nata ta nufosu tana tambayarsu lafiya.?"mami ce tayi ƙarfin halin faɗin.yayansu ne babu lafiya Amman da sauki siyama ta dafe kirji zuciyarta na bugawa take faɗin."meya samu yayanmu Mami?"nan take Siyama ta ruɗe "Na faɗa maki da sauki. Dama Daddy ko tsayawa baiyi ba ya nufi bangarensa kai tsaye yana tunanin hukuncin da zai yankewa Sadiya wannan lokacin, ba dai shi zata wulaƙanta ta tozarta ba."ina Aydah?"kema mami kin san tana can buɗe da baki tana baccin musamman yanzu da ba sallah zatayi ba. "To kije kiyi shirye-shirye sallah da kin gama ki tasheta kuzo mu haɗu kitchen mu haɗa breakfast na kaiwa yayanku."da haka mami itama ta nufi bangarenta suna gama sallah daga Mami har ya'yan nata kai tsaye kitchen suka nufa suka fara shirye shiryen dora breakfast da yar aikinsu a gefe. Aydah sai turo baki take ganin an katse mata baccinta daman yan biki tun Jiya kowa ya kama gabansa daman babu wanda ya faɗawa Aydah Ab na hospital har suka gama break fast kowa ya nufi ɗakinsa dan yin wanka tun kafin su wuce Mami ta kalli Aydah dan tasan tana iya komawa bacci dan tasan halinta da shegen son bacci "karki koma baccin asara wanka za kiyi ki fito muje asibiti. Sai lokacin Aydah ta dawo gaban Mami duk a tsorace take "Mami waye babu lafiya?" Ta faɗa tana ƙoƙarin fashewa Mami da kuka, Mami ta sakar mata da harara tana faɗin."kefa dadina dake sakarya ce. "To Mami waye babu lafiya?" Aydah ta faɗa hawaye sun cika idanuwanta lokaci ɗaya dama ita ce mai rauni acikinsu kuma ita ce autar Mami. "Yayanku ne. Kuka Aydah ta fashe dashi lokaci ɗaya duk tabi ta rikicewa Mami tana faɗin "meya same sa Mami? Duk Aydah ta rude ta fita hayyacinta daman duk cikin kannen Ab yafi shaƙuwa da ita tasu kuma tafi zuwa ɗaya idan kana son kaga bacin ran Ab a gidan to ka taɓa masa Aydah, komai Aydah ta samu yayansu shima komai ya samu na Aydah ne, haka Siyama da Sadiya ke jin haushinsa Mami tayi tai masa faɗa tace ya daina nuna bambanci a tsakani kannensa haka zai cewa mami ya daina gobe kuma ya ci-gaba. Aydah na wanka tana kuka duk tabi ta firgice tana ta tunanin wane irin ciwo ne zai kwantar da yayansu daren Jiya daren angwancinsa cikinsu daga Mami har Daddy babu wanda ya faɗa masu asalin meya samu Abba ɗin. Siyama ta daɗe da shiryawa tana zaune tana jiran fitowar Mami takun stairs taji ta dauka Mami ce sai taga Aydah ce ta fito sanye da hijab har kasa kallonta kawai siyama keyi har ta ƙaraso tana tambayar mami bata fito ba ?"Siyama ta tallabe cheeks ɗinta cike da matsananciyar damuwa dauke a fuskarta take faɗin."Nima ita nake jira. Juyawa Aydah tayi ta koma sama dan duba Mami idan ta shirya ga baki ɗaya ta ƙagu ta ganta asibiti wurin yayansu da Mami taci karo saura kaɗan su bugu Mami taja da baya a tsawace ta ce "wai meyasa bakida natsuwa ne ko kaɗan kina tafiya sharaf -sharaf bakya duba gabanki, Ko yaushe baki tafiya a natse. Mami ta faɗa tamkar zata rufe Aydah da duka. Baki Aydah ta turo tana bai wa Mami haƙuri ta juya ta koma parlorn, Mami ta ja tsaki tabi bayanta daman Daddy yana fitowa masallaci asibitin ya koma ,Mami ce take tuƙasu a mota har zuwa asibitin daidai su Mami suna fita lokacin kuma Hafeez ya ƙaraso da sadiya a ƙofar gidansu. #Love Story 2023/2024 #Jiddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only Zaki biya ta wannan account ɗin👇🏻 0020428430 Ishaq Fatima A GTBank KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k [11/22/2023, 3:17 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love Story) JEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU 003. #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye novels *RUBUTUN ƳAN TAGWAYE ZANGO NA BIYU.* *TAFIYAR BIYU TAFI ƊAYA* PAID BOOK *KIN TABBATA KIN CIKA MACE? BABBAR MACE DAKE JI DA KANTA? KINA CIKIN MATAN DA SUKA SAN KANSU? WANDA SUKA SAN MUTUNCI DA DARAJAR KANSU? KO KUWA KEMA KINA CIKI SAHUN SU O’O?* *INA KUKE MANYAN MATA? WAƊANDA SUKA SHIRYA DAN GYARA JIKINSU? AURANSU? DA KUMA FARINCIKINSU?” *KUYI MAZA KU GARZAYA GUN FITACIYGA KUMA INGANTACIYAR MAI MAGANIN MATA DA MAZA DAN AMSAR NAKU KU GYARA DA KANKU WATO MEERAH HERBS WACCE TAI FICE GUN KAWO MUKU INGANTATTUN MAGUNGUNA BA TARE DA ALGUS BA.* Mun gwada mun gani 💯 Mun gani mun shaida 💯 Anyi mun gani 💯 MAGANIN SANYI MAGANIN NONO MAGANIN HIPS MAGANIN SLIMMING MAGANIN NANKARWA GYARAN AMARE GYARAN MAIJEGO MALLAKAR MIJI KO MATA SUBULU DA SCRUB MAYUKA NA GYARAN JIKI TURAREN WUTA MATSI MAGANIN NI'IMA MAGANIN TSUMI INFECTION FLUSHER DA DAI SAURANSU…..Uwar gida, Amarya, Budurwa, Saurayi, Ango, Mai gida? Duk mai kuke jira? Kuyi maza ku garzaya Meerah herbs maganin dake ingantace 💯 08142800199 07068558096 Hafeez Sale ya yi parking motar ba tare da ya kashe ta ba ya mayar da ganinsa kan fuskar Sadiya wacce tayi wani irin zuru-zuru idanuwanta sun kode laɓɓanta sun bushe kallo ɗaya za ka yi mata ka fahimci a firgice take. "Ki shiga gida Sadiya idan Allah yasa ƙura ta lafa zan nemi ki. Amma Dan Allah Sadiya karki ambaci sunana a matsayin wanda ya ba ki mafaka, kin dai san bansan yaushe kika shiryar da wannan shiri naki ba. Ƙarfaffiyar ajiyar zuciya Sadiya tayi zuciyarta tana bugawa da ƙarfin gaske ta kalli Hafeez yayin da idanuwanta da basa gajiya da kuka suka fara ambaliya kwalla "Dan Allah Hafeez ka mai dani hotel ɗin wallahi ina tsoron haɗuwa ta da Daddy Hafeez kasan yadda mahaifina yake da zafi sh.... "Dakata mana Sadiya! Hafeez ya katse ta da sauri fuskarsa ta bayyanar da ɓaci ransa a fili "Ya kike so ki jefa rayuwata a matsala?" Kisan kai fa kikayi Sadiya sannan kuma kike so na cigaba da baki wurin ɓoya? Gaskiya ba zan iya ba Sadiya ki fita min kawai daga mota, ko taimakonki da nayi jiya na kai ki hotel nayi nadamar sa. Oya fita tun kafin wani ido ya ganni tare dake masifar da kika jawowa kanki ta shafe ni. "Hafeez Dan Allah... "Dallah malama fita! Nace ki fita min daga mota. Cikin tsawa da hargowa Hafeez ya yi mata magana, Hafeez ɗin da ta sani mai sanyi hali da rashin son haniya halinsa sak! na Ya Abba, amma yau shine yake buga mata tsawa da ihu irin wannan. Gani ta kasa fita sai kallonsa take ga baki ɗaya hawaye sun gama wanke mata fuska. A mugun fusace Hafeez Sale ya ɓalle murfin mota ya fito ransa a ɓace ya ɓalle wa Sadiya murfi tun kafin ya kai da magana ta fito da sauri tana kallonsa ya ja motarsa da gudu sai da ya ɓacewa ganinta kafin ta durƙushe wurin ta saki kuka mai taɓa zuciya, ta dau lokaci a wurin tana kuka kafin ta miƙe ta kwakwasa ƙaramar ƙofa maigadi ya buɗe mata yadda ya ganta sai da ya ja da baya hakan da ya yi, ya ƙara linka tashin hankali da Sadiya take ciki shikenan kowa ya gama sani ta'asar da tayi shikenan ta zama abin tsoro da gudu a cikin mutane. Tun da masoyinta ya gujeta wanda ta hakikance dashi take ikirarin shine rayuwarta to kowa ma zai iya gudunta. Mamaki da maigadi ke yi me ya kawo ta gida ita da jiya-jiya nan aka kaita ɗakin miji shine za ta dako wannan uban sammako "A'ah ikon Allah Halimatu! ke ce a tafe da sanyi safiya nan? Allah yasa lafiya to shi kuwa ango naki yana ina da yabarki kika fito ke kaɗai? Gashi kuma kin taki rashin sa'a ga baki ɗaya mutane gidanan sun fita hatta da Alhaji yana dawowa daga masallaci ya fice, da alama Halimatu akwai abinda ke faruwa a gidanan. Naga fuskar Alhaji kamar wanda aka yiwa mutuwa, to ko mutuwar aka yi muku tun da kema ga ki kin zo da taki fuskar tashin hankali gashi kuma kina hawaye? To amma da mutuwa ce aka yi ai bai kamata Alhaji ya ɓoye min ba ko ladar jana'iza na samu. Dukka maganganu da maigadi ke yi yana ƙara linka tashin hankali da Sadiya take ciki ne ji da tayi babu kowa yasa ta nufar cikin gida da wani irin sauri, maigadi ya bi ta da kallo baki buɗe "Ikon Allah to ko me ta zo yi ne oho! Wannan garsakeƙƙiya ba za a ce tana tsoron namiji ba sai dai in kuwa bata da cikakkiyar lafiya. Maigida ya yi magana a bayyane kana ya koma ɗakinsa zuciyarsa cike da tu'ajjabin dalili zuwan nata. Mami tayi parking motarta wurin da aka tanada domin yi parking a hospital ɗin, ta wuce gaba Siyama da Aydah suna bin ta a baya hannayensu riƙe da food basket. Mami ta tura ƙofar ɗakin Daddy da Abdulkarim Safana suna zaune akan plastic chair gaban gadon da AB yake suna kallon hawa da saukar numfashinsa. Mami da Siyama ne kaɗai suka yi sallama banda Aydah wacce tana hango AB kwance cikinsa naɗe da bandage ta fara kuka. "Ina kwana Alhaji ya jikin nasa?" Mami ta faɗa sa'ili da ta iso kusa da Daddy. "Al-hamdullilah! Daddy ya faɗa muryarsa bata fita sosai. "Ina kwana Mami?" "Lafiya ƙalau Abdulkarim ya jikin abokin naka?" "Jiki Al-hamdullilah sai dai har yanzu bai falka ba. "Zai falka da izini Ubangiji. Mami tayi magana da damuwa akan fuskarta. Siyama ta matso ta gaida Daddy da Abdulkarim tare da tambayar jikin AB Aydah na can rakuɓe jikin ƙofa tana kuka, shesshakar kukanta ne ya jawo hankalinsu izuwa gareta, murmusawa Daddy ya yi tun faruwar al'amari sai yanzu fuskarsa ta saki har ya sami yi murmushi, da hannu ya fito Aydah tare da faɗin "Zo nan Mamana! Da gudu ta zo ta faɗa jikin Daddy ta saki kuka a hankali Daddy ya dinga bubbuga gadon bayanta "ya isa haka ki daina kuka Mamana ki yi masa addu'a kin ji?? Aydah ta gyaɗa kai gami da barin jikin Daddy "Oya share hawaye mana. Abdulkarim ya faɗa yana kallon fuskar Aydah. Tasa gefen hijab ɗinta ta goge fuskarta "Yau kam akwai aiki kuka sai mun gaji dashi mun nemo auduga mu toshe kunnayen mu. Mami tayi magana tana kallon Aydah wacce ta nufi kusa da AB tai tsaye tana kallon fuskarsa ma'aɓociya kyau da kwarjini. Sai misali ƙarfe 11:15am AB ya falka bakinsa ɗauke da sallati kusan dukkan su a tare suka tashi tare da nufo wurinsa kowanne yana kokari yi masa sannu, kafin Daddy ya kama hannunshi ya riƙe gam! Yana kallon fuskarsa "Sannu Abba ya ka ke ji jiki naka??" "Al-hamdullilah Daddy! "ma-sha-Allah! Bara a kira likita ya zo ya duba ka ya gani idan babu wata matsala Abdulkarim kira likita. Abdulkarim ya amsawa Daddy tare da ficewa da sauri. Jim kaɗan sai ga Abdulkarim ya dawo tare da likita da wata nurse dake biye dasu hannunta dauke da ɗan ƙaramin tray silver mai ɗauke da tarkace kwalaben allurai da syringe A firgice Aydah ta ɗago tare da bin matashin likitan da kallo yana sanye da farar long sleeve shirt haɗe da baƙin wando ya ɗaura lab coat akai wuyansa na saƙale da Stethoscope, duk duniya babu abinda ke sauri haifar mata da tsoro irin allura ta tsani allura ko syringe bata so gani. Sai da likita ya fara duba bugun numfashin AB kafin ya miƙa hannu ya ɗauki bottle ɗin allura ya fasa kwalbar tare da ɓare syringe ya zuƙo ruwan da sauri Aydah ta runtse idanuwanta jikinta ya ɗauki rawa, zufa ya tsatsafo mata akan goshinta da ƙananu gashi yake kwance lub-lub. A hankali ta ɗan buɗe idonta guda daidai lokaci da likita ya ɗauki auduga wacce ya jiƙa ta daga ruwan spirit ya kama tsintsiyar hannun AB sake runtse idon nata tayi ta, hawaye masu zafin gaske suka fito daga kwarmin idanuwanta. Tambayoyi da ta ji likita yana ma AB yasata buɗe idanunta. Bayan fitar likitan Daddy da Abdulkarim suka taimakawa AB ya tashe zaune mami ta saka masa pillow a bayansa. Abdulkarim ya taimaka masa ya yi brush da alwala sai lokaci ya sami damar yi sallar asuba, sai da Daddy yaga Abba ya ɗan sha tea kana ya nufi gida ya yi wanka bayan fitar Daddy shima Abdulkarim ya yi musu sallama, aka bar Mami da girls ɗinta Aydah tana manne da AB ko nan da can bata kusa ba kuma lokaci zuwa lokaci sai ta tambaye shi ya aka yi ya ji ciwo me ya same shi ina Yaya Sadiya ko batasan cewa bashi da lafiya ba. Tambayoyi dai ga su nan birjik take masa sai dai ko guda daga ciki ya kasa amsa mata daga ƙarshe ma da yaga tana so ta matsa mishi sai kawai ya lumsashe idanuwansa tamkar ya yi bacci dole ta kyaleshi. Kaitsaye Sadiya ta wuce ɗakinta ta faɗa kan gado tare da yi rub da ciki cigaba rera kukanta nadama babu kalar wacce bata yi ba. A hankali Daddy yake driving tun jiya zuciyarsa take cike da mamaki ta ya aka yi ɓoyayyen sirrinsa ya fito fili, kuma bai tashi bayyana ba sai a ranar daurin auren 'yayansa. Sirri ne da aka yi haƙa rami karkashin ƙasa aka binne daga shi sai marigayi matarsa Maryam suka san dashi wacce duk duniya ta ɗauki cewa ita ce ta haifi Abba hatta da iyayenta basu san cewa Abba ba jikansu bane. Ta ya aka yi wannan sirri ya bayyana? A ina Alhaji Bello Madawaki ya sami wannan ɓoyayyen sirri? Ina son Abba tamkar raina ba zan taɓa barin fitar wannan sirri ya shafi gobensa ba. Zan iya kokarina naga na kare masa martabarsa, ita kuma Sadiya tabbas sai ta fuskanci hukunci abinda tayi ba zan kyaleta ba duk da kuwa ta kasance 'yar cikina. Da wannan zance zuci Daddy ya iso gida yana fitowa daga mota, maigadi yana ƙarasowa "Sannu da zuwa Alhaji. "Yawwa Balmo. "Ai Alhaji bayan kun fita sai ga Halimatu amarya ta zo fuskarta a kumbure idanuwa duk a kode alamar tasha kuka har ta gode Allah, babu kalar tam..... Kafin Balmo ya ƙarasa magana Daddy ya nufi cikin gida da mugun sauri har wani uban tuntuɓe ya ci da interlock amma ko a jikinsa muradina ya yi ido biyu da Sadiya, rai ɓace Daddy ya tura ƙofar ɗakin Sadiya wacce har zuwa lokaci tana kwance rub da ciki yadda Daddy ya tura ƙofar da ƙarfi yai sanadi da ta zubura ta tashi zaune, idanuwanta suka bayyanar da tsanani tsorata da tayi, cikinta yai wani kalar ƙugi musamman da idanunta suka sauka akan fuskar Daddy wacce ke ɗaure tamau. Sadiya bata ƙara shiga bala'in tashin hankali ba sai da taga irin mugun kallo da Daddy yake bin ta dashi, zance ta gudu bai ma taso ba idan ma tace za ta gudu to ta je ina? Sai kawai ta sakko daga gado ta zo ta zube guiwayoyinta biyu agaban Daddy ta sadda kanta ƙasa tare da fashewa da mahaukacin kuka "Ka hukunta ni Daddy Dan Allah ka hukunta ni daidai da laifin da na aikata ban cancanci afuwanka ba saboda I really really disappointed you Daddy ban kasan yarinya tagari ba nayi tarnishing image ɗin gidanan na jawowa zuri'arka bad record Daddy ka yi min duk abunda ka ga dama... Muryarta yai wani kalar sarƙewa duk maganganu dake fita daga bakinta tamkar tana ƙara gayyato wa Daddy fushi da takaicinta ne, idanuwansa sun ƙara rinewa yasa hannunsa ɗaya ya cakume wuyanta ya yi dragging nashi ya ɗauke ta da gigitatcen mari na fitar hankali wata irin razanannayar ƙara ta saki sa'ili Daddy ya sake wanka mata wani mari, ba iya mari guda ko biyu ba maruka ya ci-gaba da ɗauke tasu har sai da ji da ganinta suka ɗauke hanci da bakinta na zubda jini fuskarta da ta fara hayewa Daddya ya duba "meyasa za ki nemi salwantar min da rayuwar yaro? Me ki ka fi Abba dashi da ba za ki iya rayuwar aure dashi ba? Shin ban cancanci a matsayina na mahaifinki ki fidda ni kunya a idon jama'a ba? Ɗan uwanki bai cancanci ki sadaukar masa da farin cikin ki ba? Meyasa Sadiya meyasa za ki nemi kashe Abba? Ya ƙarashe magana da wani irin mugun fushi a muryarsa, ya sake ta ta zube ƙasa wanwar numfashinta sai ya yi sama ya dawo ƙasa, ko kaɗan Daddy bai damu da hali da take ciki ba ya fito da wayarsa ya yi dialling number CP (Commissioner of police) tare da faɗa masa ya tura masa da yaransa su zo gidansa ga suspect ɗin da suke nema, da yake tun da sassafe Daddy ya kira shi ya sanarda shi komai sai dai ya ɓoye masa bai faɗa masa cewa Sadiya 'yarsa bace. A fusace Daddy ya rufe Sadiya a ɗakin nata ya dawo downstairs parlor ya kai gwaro ya kai mari, shi kaɗai ne zai iya iya bayyana hali da yake ciki. After twenty minutes ya ji ƙarar jiniyar motar 'yan sanda ya koma ɗaki ya jawo Sadiya kamar kayan wanki sai gunji kuka take yi. Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [11/23/2023, 5:57 PM] Jiddarh Aliyu 2: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love story #Gwagwarmaya #team tagwaye novels 004. *RUBUTUN ƳAN TAGWAYE BIYAR KARO NA BIYU.* *TAFIYAR BIYU TAFI ƊAYA* *KIN TABBATA KIN CIKA MACE? BABBAR MACE DAKE JI DA KANTA? KINA CIKIN MATAN DA SUKA SAN KANSU? WANDA SUKA SAN MUTUNCI DA DARAJAR KANSU? KO KUWA KEMA KINA CIKI SAHUN SU O’O?* *INA KUKE MANYAN MATA? WAƊANDA SUKA SHIRYA DAN GYARA JIKINSU? AURANSU? DA KUMA FARINCIKINSU?” *KUYI MAZA KU GARZAYA GUN FITACIYGA KUMA INGANTACIYAR MAI MAGANIN MATA DA MAZA DAN AMSAR NAKU KU GYARA DA KANKU WATO MEERAH HERBS WACCE TAI FICE GUN KAWO MUKU INGANTATTUN MAGUNGUNA BA TARE DA ALGUS BA.* Mun gwada mun gani 💯 Mun gani mun shaida 💯 Anyi mun gani 💯 MAGANIN SANYI MAGANIN NONO MAGANIN HIPS MAGANIN SLIMMING MAGANIN NANKARWA GYARAN

Chapter 2 of 7