Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 7
sai dai kuma Daddy ya yi min gargaɗi akan kada na sake yi mishi zancensu kuma ba zan iya take umarnin Daddy ba. Sai da Aidah ta sauke numfashi kafin ta gyara zamanta ƙugunta ya ƙara mannewa dana AB "Ya Abba ka yi haƙuri ka ɗaure ka cire duk wata damuwa aranka Allah yana sane da hali da kake ciki a sannu zai warware maka dukka damuwarka, wannan abin zai zo ya wuce kamar ba a yi ba. "Haka ne Baby Aidah in-sha-Allah zan yi kokari na bi shawararki. "Thank you Yaya Abbana tashi mu tafi sport field mu yi wasa kwana biyu nayi missing buga wasa dakai, yaya Siyama bata iya komai ba a table tennis. Murmushi ya yi wanda bai wuce iya fatar bakinsa ba yasan Aidah tana yi haka domin ta kawar masa da damuwar da yake ciki, shiyasa bai mata musu ba ya ce ta je ta canza kaya ta sami shi a field, da gudu ta fice Siyama ta biyo ta zuwa field ɗin suna wasa tana musu tafi da sowa yayin da ihunsu ya kai kunne Sadiya da sauri ta taso daga kan gado ta nufi window ta leƙa ta hango yadda AB yake ta zabgar fara'a ga walwala akan fuskarsa, tun ba a je ko'ina ba farin ciki da walwalarsa sun fara dawowa jikinsa saɓani ita da take ji wani kalar ƙunci haɗe da baƙin ciki yana nuƙurƙusar zuciyarta. Sai da aka fara kiran sallar magarib kana suka dawo cikin gida. A washegari Daddy ya umarci AB ya koma bakin aikinsa wanda shine ceo na Kamfanin Daddy na siyarda motoci moon light Automobile industry, ba wai iya motoci kamfani yake siyarwa ba, suna sai da cars accessories da kuma abubuwan gyaranta Moon light Automobile industry kamfani ne da ya shahara saboda haɗin gwiwa ne da kamfanin whitepaper Automotive industry Germany, shiyasa motoci da suke kamfani suka fita daban da na sauran kamfanoni. Kaitsaye AB ya wuce ofishin sa dake hawa na huɗu secretary shi ta shigo ta kawo mishi schedule ɗinsa na yau ya duba firstly yana da meeting da employees na kamfani kana akwai online meeting da zai yi da whitepaper Automotive industry throughout bai huta ba saboda akwai sabuwar mota da kamfanonin nasu za su yi lunching sai around ten na dare ya dawo gida. #Love story 2023/2024 #Jiddah Aliyu #Asmy b Aliyu #team tagwaye novels #kurman Allo Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [11/25/2023, 8:27 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye Novels 006. Assalamu Alaikum Hajiyata kinada labarin kayan Egypt da muke kawowa kuwa to in baki saniba matso kusa kiji Ainam stockpile mun kawo muku kaya na gani na fada na gayu wainda sai wance da wance ake gani dasu ba kano made bane kunsan a koda yaushe burinmu mu kawo muku unique abu.Available ne ba jira zakiyi akawo ba muna bada sari muna kuma aikawa koina,duk abinda kike bukata hajiyata ki latsoni kawai wa.me/2348146766440 Ko baki siyaba yanzu kiyi saving number ta murika ganin status din juna Nagode jikinsa ga baki ɗaya ya yi masa nauyi tamkar wanda aka yiwa duka. Yana tura ƙofar parlornsa idanuwansa suka sauka akan fuskar Aydah dake zaune a ƙasa ta jingina bayanta ga soofa bacci ya ɗauke ta. Sai da ya ƙare mata kallo kana ya girgiza kai ya aje briefcase ɗinsa akan centre table kusa da wasu luxury warmers dake aje akan centre table ɗin ya nufi tv dake aiki wacce yake da tabbaci Aydah ce ta kunna ta ya rage volume, ya wuce ɗaki ya yi fresh up ya dawo parlor jikinsa sanye da pajamas sky blue in color ya zauna akan soofa da take jingine ya ɗan bubbuga kafaɗarta gami da kiran sunanta "Baby Aydah! Baby Aydah! Na dawo tashi ki je ki kwanta. A hankali ta ware matsakaitan idanuwanta akan fuskarsa da sauri ta gyara zamanta tana mutsitsika idanuwanta da bayan hannunta "lah! Ya Abba yaushe ka dawo?? "Yanzu nan. "Ka ci abinci? "A'ah amma zan ci. "Ga shi nan akan centre table na ajiye maka bari na zuba maka. "Dare ya yi Baby Aidah ki tashi mu je na raka ki idan na dawo daga raka ki zan zuba da kaina. "Shikenan. Ta faɗa da sanyi muryarta miƙewa AB ya yi ya miƙa mata hannayensa ta kama ta tashi tsaye suka fito compound ɗin gidan suna tafiya side by side, Aydah ta ɗaga kanta sama taga yadda taurari suka yiwa sama ƙawaiya gwani sha'awa ta dawo da ganinta kan AB "Ya Abba ɗaga kanka sama kaga yadda taurari nan suka haskaka sararin samaniya. Ba tare da ya tanka mata ba ya ɗaga kansa sama ya daɗe kafin ya dawo da ganinsa kanta yana faɗin "Tsalki ya tabbata ga Ubangiji da ya halicci sama ya ƙawata ta da taurari. Murmushi Aidah tayi tana gyaɗa kai kafin ta sake maida ganinta sama da sauri tayi pointing yatsanta akan wasu taurari guda uku da suka ware kansu sai dai ta tsakiyar su tafi haske "Ya Abba duba ka ga wadancan taurari guda uku. Idanuwansa ya kai gun da take nuna wa "Na gani. "Me ka gani?? "Taurari guda uku sai dai ta tsakiya ta fi su haske. "Ina nufi me ka fahimta akan taurarin?? "Bani da ilimin taurari. Ya yi magana yana kallonta tare da sakar mata murmushi saboda yasan shirmenta ne ya motsa. "Waɗancan taurari guda biyu ka ɗauke su a matsayin Yaya Sadiya da aunty Rumaisa. "Uhm! To ita kuma wancan guda ɗaya mai haske a matsayin wa zan ɗauke ta?? Yayi magana yana siririyar dariya dama yasan za a yi haka. Tsayawa tayi tare da fuskanta shi tana kwaɓe fuska gami da cuno baki gaba. "Ki faɗamin mana wacece mai haske nan?? Cikin shagwaɓaɓbiyar murya ta ce "Ka canka mana. "Kinsan ni ba kwararre bane a canka kawai ki faɗamin. Cikin zallan shagwaɓa take buga ƙafafuwanta akan interlock "Dan Allah ya Abba ka canka ina ji a jikina a wannan karo za ka canka daidai. "Ke dai in za ki faɗamin ki faɗa kawai idan kuma ba za ki faɗa ba shikenan sai da safe. Murmushi tayi haɗe da juyawa tana faɗin "Sai da safe Ya Abba. Har tayi taku biyu zuwa uku sai kuma ta juyo da sauri ta kira sunansa har shima ya juya saboda dauriya kawai yake yi amma yunwa yake ji kamar hanji cikinsa zai tsinke "Ya Abba ka biyo ni bashi amsar tambayar ka nayi maka alƙawari wata rana zan gayamaka wacce wancan tauraruwar da tafi yaya Sadiya da aunty Rumaisa haske. Bata jira ya yi magana ba ta buɗe ƙofar shiga main parlor da kallo ya bi ta dashi yana wani kalar murmushi. A washegari kasancewar Aydah tana da test na biology shiyasa bata jira AB ya tashi daga bacci ba ta wuce school. *ALHAJI BELLO MADAWAKI MANSION* Rumaisa tana kwance a ɗakinta tun daga ranar da aka fasa aurenta da AB ta daina fita ga baki ɗaya ta yi wata irin rama, kullum cikin kuka take musamman yanzu abin nata ya ƙara tsananta a dalili blocking ɗinta da AB ya yi, tana son AB fiye da komai shi ne rayuwarta rasa shi a gareta ba ƙaramin nakasu ne a rayuwarta ba. Mahaifinta ya kasa fahimtar irin ɗimbin son da take wa AB bata damu da rashin asalinsa ba. A haka take sonsa idan har bata aurensa bata ji za ta iya aure a rayuwarta. Mahaifiyarta ta turo ƙofar ɗakin nata ta shigo duk sallama da take yi Rumaisa bata amsa ba saboda tayi zurfi a tunani AB da irin soyayyar da suka shimfiɗa a can baya, kusa da cikinta Hajiya Nafisa ta zauna tare da ɗora hannunta akan sumarta a hankali take shafa sumar kan Rumaisa kafin cikin sanyi murya ta kira sunanta "Rumaisa! Firgigit Rumaisa tayi kamar wacce aka tasa ta hanyar watsa mata ruwan sanyi "Na'am Ammi. "Rumaisa har sai yaushe za ki daina wannan koke-koke naki?" Sanin Kanki ne Rumaisa mahaifinki ba zai taɓa aura miki Abba ba to don me da ba za ki cire shi daga zuciyarki ba? Babu kalar rokon da ban masa ba akan ya haƙura ya aura miki zaɓin ranki ko don wanzuwar farin cikinki amma ya yi biris dani jiya da dare har cewa ya yi idan na sake masa maganar Abba a gidanan zai yi mummunan saɓa min. Mahaifinki mutum ne mai matuƙar zafin kai da kafuwa wanda maganar fatar baki ba za ta iya canza masa ra'ayin sa ba. Saboda haka dan Allah ki cire damuwa aranki ki dawo da walwalarki nayi magana da yayarki Shema'u gobe za ki tafi Abuja wurinta ki kwana biyu watakila ki fi samu sakewa a can duba da nayi da irin shaƙuwar dake tsakanin ku. Har Ammi ta dasa aya a zancenta Rumaisa tana sharar hawaye kafin cikin dusashewa murya ta ce "Ammi ba zan iya nisanta da AB ba idan na tafi Abuja hakan yana nufi zan daina ganinsa kwata-kwata zuciyata ba za ta iya jure hakan ba. A halin yanzu ma zuciyata zafi take min Ammi zuciyata za ta buga taɓa ki ji Ammi watakila mutuwar zan yi soyayyar AB za ta kashe ni. Ta ƙarasa magana tare da ɗora hannun Ammi a ƙirjinta sosai Ammi ta firgita da jin yadda zuciyar 'yarta ke bugawa, da wani irin mugun ƙarfi da sauri ta jawo Rumaisa zuwa jikinta ta rungume ta wani irin tausayinta take ji ita kanta shaida ce akan irin zazzafar soyayyar da take wa Abba Bashir. Sadiya ta ɗauki wayarta dake aje a gefenta ta sake gwada kiran numbern Hafeez Sale a karo na ba adadi, tun ranar da ya dawo da ita gida idan ta kira wayarsa bata samu da alama ya yi blocking ɗinta. Tayi kuka har ta gaji tana son Hafeez Sale tamkar rai da numfashinta rabuwa dashi wani al'amari ne da zuciya da gangar jikinta ba za su iya ɗauka ba. Duk wanda ya san Sadiya ada a yanzu idan ya ganta da matuƙar wahala ya gane ta saboda ta rame ta yi baƙi sai ta yini guda curr batare da taci abinci ba tun Mami tana shareta har ta dawo rarrashinta kuma har izuwa wannan lokaci idan ta gaida Daddy baya amsawa hakazalika Siyama da Aydah basu shiga sabgarta. Cikinta da ke mata mugun ƙugin yunwa yasa ta fitowa ta shiga kitchen ta haɗa tea ta fito main parlor ta zauna, a hankali take sipping tea ɗinta AB ya turo ƙofa ya shigo bakinsa ɗauke da sallama, ta ɗago idanuwansu suka sarƙe tun faruwar wannan al'amari take wasan ɓoya dashi, kunyar haɗuwa dashi take ji. Sannu a hankali take bin jikinsa da kallo ya yi masifar yiwa idanuwanta kyau yana sanye cikin black blue color suit ya ɗura white necktie wanda ya yiwa three knot style ƙafarsa sanye da black men loafers sosai shigar tayi masa kyau ga ƙamshin turarensa da ya gama cika mata hanci. Kasa yi masa magana tayi shiyasa ta yi sauri sadda kanta ƙasa shima ya ɗauke kai tamkar bai ganta ba ya wuce dining area.sosai jikin sadiya yayi wani irin sanyi tamkar ba yayanta ba da tasani Acan baya sai wani shasshareta yake.lokaci ɗaya idanunta suka cicciko da kwallah gashi tunda ta dawo gidan babu wanda yayi mata maganar komawa makaranta tana shakkar tambayar daddy,dan har lokacin idan ta gaishesa baya amsa mata.ta qara kallon cikin dinning area din,yaya Abba ,kawai ne zaune a wurin har lokacin yana sipping Black coffee da wayarsa a hannu yana daddanata.qarfin hali tayi ta miqe tsaye ta nufi cikin dinning area din xuciyarta na wani irin bugawa tsaye tayi dan nesa dashi ko kallon wurin da take bai yadda yayi ba.xuciyar sadiya lokaci ɗaya ta kara qaryewa cike da qarfin hali take faɗin ."dan Allah yayanmu kayi hakuri wallahi sharrin shaidan ne."ta qarasa maganar cikin rawar murya nan ma dai AB.tamkar tana magana da dutsi haka yayi mata banza daman AB.badai miskilanci ba ,zata qara buɗe baki tayi magana ya dire cup tea din hannunsa ya bar cikin dinning area din da wata irin sassarfa da kallo ta bisa tana jin wata irin faduwar gaba wanda bata taɓa jinsa akan yayan nata ba.har dare abunda yayan nata yayi mata ya kasa barinta da irin yadda ya shareta tamkar bai taɓa saninta ba a duniya.kusan qarfe tara ta shigo dakin Mami ta sameta kan sallaya da carbi a hannunta akan doguwar soofa ta xauna tana jiran Mami ta gama azkar.jin tayi an turo kofar Sukayi ido biyu da AB.sai da gabanta ya fadi suna haɗa ido yayi saurin dauke idonsa cikin nata.sanye yake cikin cooffe brown din jallabiyya da tayi matuqar haske farar fatarsa. Shi bai juya ba shi bai shigoba still yana riqe da handling din kofar. Cikin rawar murya sadiya ta gaishesa babu yabo babu fallasa ya amsa ya juya Yabar kofar na Mami batareda ya jira mamin tagama ba.bayan Mami tagama sallah ta kalli sadiya da ta zama (Absent minded)sai da Mami ta kira sunanta fitgigit ta fado duniyar tunanin da ta tafi sai yanzu ta qara tabbatarwa watau yayanta yafi hafeez class da wani irin quality ashe idonta rufewa yayi?"gaskiyyar siyama ne da Take fadin zatayi na dama lokacin da bata da amfani ,to idan bazakiyi magana ba tashi kibarmin daki."Mami ta faɗa a mugun fusace da alamar sadiyar ta kaita bango cikin rawar murya sadiya ke faɗin."daman Mami akan maganar yaya Abba ne,da kuma maganar komawa school Dina nagaji da zaman.kuma yaya Abba,sai wani shareni yakeyi cikin gidan nan tamkar wata makiyarsa idan ina a wuri baya zama.shi bai san ƙaddara bane?"har hakuri na basa fa.maganar Abba,mu ajeta a gefe can tsakaninku lokacin da kuka bata ban sani ba,maganar karatu bana da iko akan karatunki kije ki samu daddy."hawaye lokaci ɗaya suka cika idon sadiya tana faɗin."to Mami kiyi masa maganar komawar tawa makaranta.idan dai ke zakiyi masa kije kiyi masa babu ruwana ki daina sakani a lamurranki sadiya."ganin dai da gaske Mami bazata saka baki ba yasa tabar dakin na Mami,a parlor ta tarar da AB Shida Aidah tana riqe da wayarsa tana bangalar Daria shi kuma sai murmushi yake wani irin kunci taji ya cika mata xuciya daga Aidah har AB babu wanda yabi takanta juyawa tayi ta koma sama tana jin idonta na cika da hawaye lokaci ɗaya. Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [11/26/2023, 3:44 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novel's *RUBUTUN ƳAN TAGWAYE ZANGO NA BIYU.* *TAFIYAR BIYU TAFI ƊAYA* PAID BOOK 007. *MOON LIGHT AUTOMOBILE INDUSTRY* AB yana zaune a office ɗinsa yana duba wasu car design da whitepaper Automotive industry suka tura masa yana selected ɗin wanda suke buƙata a kamfani nasu, secretary shi ce ta shigo tare da sanar dashi yana da baƙuwa amma ta duba bata da appointment dashi. Sai da ya kwaɓe fuska kafin ya tambaye sunanta "Rumaisa Madawaki! Secretary tasa ta faɗa. "Let her in. Ya yi magana kaman mai ciwon haƙora jim kaɗan da fitar secretary tasa Rumaisa Madawaki ta turo ƙofa tashigo tana sanye da turkish Abaya maroon in color tayi rolling da veil ɗin rigar sosai rigar ta karɓi fatar jikinta kasancewar fara duk da fari nata ta ɗan sirka shi da mayukan nan na zamani shiyasa skin ɗinta ya yi wani ɓauuu farinta har ci idanuwa yake. Tun kafin ta ƙaraso AB ya fara shigar ƙamshin turarenta a hankali ta tako yayin da idanuwansu suka sarƙe sosai ya hango ramar da tayi, nan take ya ji zuciyarsa ta karye amma sai ya yi kokari basarwa baya so ta silarsa su dawo da hannun agogo baya. Sai da ta iso gaban desk ɗinsa ta tsaya tare da rungume hannuwanta a ƙirji kallo-kallo suke wa juna shine ya fara janye ganinsa, gami da kawar da kansa gefe ɗaya. "Ban taɓa tsammani akwai wani dalili da zai zama sanadi rabuwar mu a faɗin duniya nan. Abba idan kai ka shirya haƙura da soyayyarta ni kan yanzu ma na ɗaura ɗamarar yaƙi da duk wanda zai kawo min cikass a soyayyarka. Ta ƙarasa magana tare da zama akan kujerar dake gaban desk ɗin tana kuma facing ɗinsa, ɗan bazawari murmushi AB ya yi shi kaɗai yasan irin raɗaɗi da yake ciki na soyayyarta sai dai bai ga amfani soyayyar ba tun da ba za ta kai su da mallakar juna a karkashin inuwar aure. "Ka haƙura dani ko Abba? Tayi magana hawaye na fitowa daga kwarmin idanunta. Sai da ya ɗan wargaza Sumar kansa kafin cikin raunatatciya murya ya ce "Ba zan taɓa iya daina sonki ba Rumaisa sai dai ya zama mana dole da haƙura da juna, duk wata soyayya da muke wa junan mu bata da wani amfani tun da mahaifinki ba zai iya mallaka min ke a matsayin matata, ta sunnah ba. "AB idan har da gaske ba ka haƙura dani ba to ka bani wani ɗan lokaci in-sha-Allah zan daidaita al'amurranan zan nemi hanyar da Dad zai amince da aurenmu. "Idan ma nace na jira ki Rumaisa ni kuma nawa mahaifin ya zan yi dashi domin na daukar masa alƙawari nisanta daga gare ki. "Wacce irin magana ce kake faɗa Abba? Ko dai dama ba ka ji soyayyata kwatankwacin yadda nake jin taka?" Rumaisa ta faɗa cikin muryar kuka. "Ba haka bane Rumaisa ke kanki shaida ce akan matsananci son da nake miki you're my first love how do you think zan daina sonki faratt ɗaya?? "Dole nayi wannan tunani Abba saboda hali da ka nuna min ka daina picking calls ɗina daga ƙarshe ma sai blocking ɗina ka yi, Abba wallahi ba zan iya rayuwa idan babu kai. Ka bani haɗin kai mu yi yaƙi kwatar soyayyarmu. Da girar ido ɗage yake kallonta yana ɗan shasshafa kwatatce sajensa, kafin ya ce "Rumaisa bana so mu yi abunda zai saɓa ra'ayin iyayenmu, mu yi haƙuri mu bi su yadda suke so a rayuwa ba komai kake so kuma ka same shi ba. After all this time Daddy yana ƙoƙarin ganin ya faranta min saboda haka ba zan iya abunda zai ɓata mishi rai ba. "Nima ban ce ka yi abunda za ka ɓata wa mahaifinka ba kawai i want my love back ka dawo da soyayyar da kake min Abba ka ɗaukar min alƙawari za ka jirani har zuwa lokaci da Dad ɗina zai amince da aurenmu. Girgiza kai ya yi tare da faɗin "hakan ba zai yiwuwa ba Rumaisa mu haƙura da juna kawai. "Ba zan iya ba Abba idan ban same ka ba mutuwa zan yi wallahi zuciyana zai buga.. Ta ƙarashe magana tare da saukowa daga kujera ta durƙusa on her knees ta haɗe hannayenta guri ɗaya cikin muryar kuka take faɗin "Dan girman Allah Abba karka bar ni rabuwa da kai zai iya cutar dani ka tausayawa rayuwata. Da wani kalan sauri AB ya taso ya kama kafanɗunta ya tashe ta tsaye hakan ya bata damar faɗawa ƙirjinsa hugging ɗinta ya yi tana kuka yana rarrashinta da daddaɗan maganganu hakan yasa ta daina kuka, ya ja ta zuwa kan ɗaya daga cikin cushion ɗin da ke cikin ofishin nasa ya ci-gaba da rarrashinta da kalaman soyayya masu sanyayya zuciya. "Da gaske nake yi AB idan babu kai ba zan iya rayuwa ba dan Allah karka sake juya min baya. Ka duba yadda na lalace tun daga ranar da aka fasa auren mu har kawo yau ɗinan rabon da na zauna naci abincin kirki iyakacina nasha tea shima sai naga yunwa za ta min illah nake ɗan kurɓawa sama-sama. Rumaisa ta faɗa tana ɗauke hawaye da suka sake silalo mata a kumatu. Sai lokaci da tai wannan magana AB ya ƙare mata kallon tsaf da gaske kuwa ta rame irin muguwar rama nan wacce da an ganka sai an tambaya ba za a shaida kana ciki damuwa, da sauri ya miƙe tare da nufar desk ya ɗauke car key gami da wayoyinsa yana faɗin "Tashi mu je mu ci abinci dama lokaci tashi na lunch ya yi. Rumaisa tayi murmushi tare da miƙewa ta ɗauki handbag ɗinta yana gaba tana bin sa a baya yayin da AB ke ci-gaba da faɗin "Daga yau duk abunda zai faru Rumaisa kada ki sake bari kanki da yunwa ina sonki sosai ba zan iya jurewa ba idan wani abu ya same ki. Ya ƙarashe magana daidai suna isowa parking lot kowanne su ya shiga motarsa suka fice daga kamfani. Alhaji Sanusi dake tsaye jikin window ofishinsa idanuwansa akan AB da Rumaisa wani kololon baƙin ciki ne ya dunƙule masa a kahon zuciya a fusace ya baro jikin window ɗin ya ɗauki wayarsa ya yi dialling numbern abokin ci mushe sa "Alhaji Umar kaga abinda naga ni kuwa?? "Me ka gani Alhajin Allah? Alhaji Umar ya faɗa har yana haɗawa da wata 'yar bazawarar dariya. "Alh Umar wannan shegen yaro tsintatce yanzu nan naga ya fita daga kamfani tare da 'yar gidan Bello madawaki?" "What?? "Wallahi nake gayamaka ai na zaci ka ga fitar su hankalina ya yi mugun tashi Alh Umar kada waɗannan shegun yara su mayar mana da aiki baya. "in-sha-Allah hakan ba za ta taɓa faruwa ba bari nayi gaggawar kiran Alh Bello madawaki na ƙara rura wutar al'amari. "Haka nake so mutumina. Alh Sanusi ya faɗa tare da hanging up yana saki murmushin mugunta, alƙawari ne ya ɗaukar wa kansa ba zai taɓa bari Alhaji Bashir da shegen ɗansa AB su sake farin ciki a rayuwarsa, shekaru 15 da kafa wannan kamfani shine silar hasassa shi duk wani cigaban kamfani shine ya kawo shi burinsa a ce yafi kowa damawa a wannan kamfani a matsayin sa na ƙani Alhaji Bashir da suke uwa ɗaya amma abin takaici sai da ya gama shan wahala kamfani ya haɓaka ya zama lamba ɗaya, Alhaji Bashir ya ɗauki babban matsayin da yake hari ya ba wa ɗansa AB duk da haka ya danne zuciyarsa ya cigaba da aiki a kamfani daga hawan AB kujerar CEO (Chief Executive officer) shegen yaro nan ya dinga bincike da bin diddigi shige da fice kuɗaɗen Kamfani har yai nasarar gano irin almudahana da suka dinga yi shi da financial director, AB bai bar su ba har sai da suka dawowa da kamfani kuɗaɗen da suka sata wannan abin da yai musu shine silar da yasa account ɗinsu yai ƙasa har yau basu farfaɗo ba. Sannan kuma ya bi ya tare gaba ya tare musu baya duk wani motsinsu akan idanuwanshi. Wannan shine silar da ya haifar da zazzafar ƙiyayya tsakanin AB dasu Alh Sanusi daga wannan lokaci suka shiga bincike hanyar da za su kawo ƙarshen AB a kamfani. Alh Sanusi ya yi nisa da tunani ƙarar buɗe ƙofa da Alh Umar ya yi ya dawo dashi natsuwarsa ba tare da ya ƙarasa tunano irin gada zare da suka ɗannawa AB da mahaifinsa. *GUSTO RESTAURANT* AB da Rumaisa suna fita kai tsaye Gusto restaurant suka nufa AB yana gaba tana bin sa a baya AB ya zaɓi Gusto restaurant a dalili ya yaba da daɗin abincinsu ga kuma wurin babu haniya, bayan an kawo musu menu kowanne su ya zaɓi abunda yake so yaci koda suka kammala ci abinci ƙarfe 3:00pm AB yana duba wristwatch ɗinsa sai da gabansa ya faɗi kasancewa da Rumaisa ya manta da Aydah da ya yiwa alƙawari zai je ya yi picking ɗinta a school agaggauce ya sha ruwa ko ta kai juice ɗin da aka kawo masa bai bi ba ya miƙe tare da kallon Rumaisa yana faɗin "Habibty I have to go bansan cewa lokaci ya tafi sosai har haka ba. Cike da zallan mamaki ta dire spoon ɗin hannunta ta ɗago "Habibi ina za ka tafi kake wannan saurin?? "Zan je nayi picking Aydah a school kinga lokaci ya tafi sosai sai mu yi waya. Yana ƙarashe magana bai jira jin ta bakinta ba ya nufar entrance ɗin fita da sauri ta bishi

Chapter 4 of 7