Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 10
suka sani suya shafa bake ba. Ke idan kikayi wasa akwai fa masu harinsa a cikin compound din nan ko maman soni ta fada min idan yana son yarta Blessing zata bashi ta musulunta aikinsan dama ita ba addini gareta ba. Me zaiyi da wanan mara fasalin ke mai fasalin aikin tsaya wasa a yanzu yau din nan zan je gidan koke fa yar nata ta fada nan barikine ba arewa ba da wani zai tsaya sa maki ido ga mekikeyi balle kuma sunga addinin ku daya ba zasu tsaya sa ido ba game kukeyi. In yaso daga baya sai muje muga juju man din nan na hanya Obana musan abinda makomar alakan naku zai haifar a garemu tace yayi anty shiyasa nake sonki Wanan huduban na yarta ta dauka wanka ta farayi kafin ta fito tana fadin ni yanzuma naji na fara sonshi har cikin raina da kika fitar min da komai nasa a fili sai nake ganin kamar na gama samunsa ma ko. Tsab ta gyara jikinta ta fesa kamshi ta nufi gidan kai tsaye tanayiwa antyn ta saita dawo suna dariya a tsakaninsu ta dumfari gidan nashi. Kofan a rufe ta sameshi don tun daga nisa ta fahinci hakan karasawa tayi tana tambayan makwabciyan mu ko wata yar igala musulmace su saidai addinin ne gaya nan dai. Ta tambayeta ko tasan inda ya aje key din part dinsa tace bai bar mata ba yanzu baban Jamal baya son magana da kowa a compound din nan da wuyama kasan dawowansa balle fitanshi a gidan nan yanzu tunda matarshi ta rasu. A yadda najima ance kamar zai tashi a gidan don ya sayi gida a by pass zai koma can da zama yanzu wani irin faduwan gabatan yayi amma sai ta dake tace ok tana duba roban ruwansa dake waje. Nan ta ari bucket din matar ta dinga debo ruwa ta ciki tagama ta dauki tsiyaya da tagani a waje ta share masa ko ina ta gyara har kitchen dake bude duk ta gyaro ko ina na part din nasa tacewa. Cike yake da kewar matarshi da diyanshi da babusu a tare dashi yanzu shi kadai ke rayuwansa a garin mutanen yana harkan neman kudinshi na black market din mai da yakeyi a can din. Koda ya dawo duk da darene bai hana ya gane wurin a gyare yake ba mamakinshi bai kareba saida yaje kwalfan dan ruwan daya rage ya watsa a jikinshi yaga randar ruwa a cike yake ga kitchen da ko ina a gyare. Maman semi da suke shiri da marigayiyan yasawa rai tayi masa hakan ya furta amma ta kyauta wallahi ta hutar dani tsaya yin wani aiki gobe ke nan . Wanka yayi ya fito da dan abinda ya sayo ya zauna yaci ya danyi abubuwanda zaiyi kafin ya kwanta ya gama ya hau gado cike da kewar matanshi da yayansa a zuciyar shi yana tuno zaman rayuwansu dashi a baya. Washegari bai fita da wuri ba yana son yaji maman semi ta bude koda yayi mata godiya kan abinda tayi mai na dawainiya kada ya zama butulu. Yanan zaune yaji budan kofan nata ya tashi ya shirya ya fito yana kallon lokaci ga agogon dake daure a hannushi na dama lokaci ya nuna shidda da rabi na safe. Ya rufo kofan ya nufo dayan part din da yake makwabtaka da nasu ya samu tana shara yace you na good morning wooo maman Semi matar ta dago tana amsawa cikin mamakin ganinsa har wanan lokacin bai fita ba. Yace i come to thank you for what you did to my compound yesterday to oh no be me do amm na that maman baby sister come do am for you . That you wife friend sister wasia do de work wani irin yaji har hakan ya baiyana a fuskanshi lokaci guda yace ok thanks for d help ya juya ya fice a gidan tana fadin bye bye bai tsaya ya amsa mata ba ya fice get din gidan. Ya fito yana tafiya yana mamakin hakan da maman baby ta turo akai mai sai kuma ya tuna zamanta da matarshi a baya ya dauka don hakan ta turo aka gyara mai wuri. A nan gaba dasu ya samu taxi din da zai kaishi inda zai shiga mota zuwa wurin sana,an su din don sai an shiga mota daga nan zuwa baban titin garin . Samu sosai yakeyi kamar me bakin uwa don idan uwa taiwa danta addua shi ake kira bakin albarka insha Allahu kome mutum ya taba zaiyi albarka. Kyautatawa iyayye koda kadan ne in an dace da iyayye masu yawan lafazin albarka a bakinsu sai albarkan nan ya shafi da a duk inda yasa gaba a duniya. Shiya wa yanda suka gane suke neman albarka a wurin iyayye ta hanyan kyautatawa a garesu mu sanman uwa tafi saurin sakawa yaro albarka a bakinta ko wani lokaci Allah ubangiji ya bamu ikon kyautatawa iyayyen mu amin yasa iyayyen mu mata su gane fa,idan abinda malamai suke fadakar da mu akullun amin ZAINAB IDRIS MAKAWA [7/25, 9:25 PM] +234 803 434 1977: KARAN DAFI 🌾 YAFI DAN DAWA AMAFANI 🌾 ZAINAB IDRIS MAKAWA 🌾 🌾🌾🌾🌾🌾🌾🌾🌾 5️⃣ GA MAISON BANI HAKKINA ZAI IYA TURA KUDI DARI BIYAR KACAL A WANAN LAMBAN 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO A KIRA WANAN LAYIN WAYAN 08036959257 NAGODE ALLAH YA BADA IKON BIYA MUN GODE NAKU HAR KULLUN YAR MAKAWA, , , , , , YAR UWA KADA KI RAINA NAUYIN HAKKIN WANI A WURIN ALLAH, DON MIN AMANACE HAKKI, GAREKI , , , , , , Haka rayuwa yake zuwa wa bawa da kaddaransa ba ruwanshi da babba ko yaro duk yadda lokacin da kaddaranka ya gitta sai ya faru dakai a lokaci. Rayuwana dai kan haka yake zuwa min don yan gidan mu gaba daya sun daukeni a matsayin manya mai bakin kaddara irin na uwana. Don mutuwan anty safiya da yazo mata lokacin ina hannunta a take suka juya maganar suka dagwara laifin mutuwan nata a kaina wai zama danine ya ja mata mutuwa a lokacin. Tun anayi iya yan gidan mu har zancen ya fara fita waje makwabta da yan unguwa suka dauka gaskiyace idan na fito sai kaga yara na guduna har manyan ma wani lokaci zasu kauce min a hanya suna tsegumina. Rufin asirina guda shine Allah ya taimakeni ya sakawa rayuwata natsuwa don na samu tarbiya a wurin anty safiya a rikon da tayi min dom haka ninake gani don sam ban daukeshi a matsayin horo ba a wurina. Saboda natsuwata har wasu suka fara fahintar gaskiya da cewa kazafi akai mun ba gaskiya bace ina maita tunda ga yan gidan mu nan da nake zama dasu lafiya kalau ai dani. A cikin hakan baba ya sakani makarantar boko dana islamiya a can kasan mu indan na dawo daga boko zan dan tsaya na gyaro dakina na wanke uniform dina nayi shirin islamiya sai gab da magariba zan dawo gidan in shige dakina. Har yakai na fara kwasan su jamal ina zuwa dasu islamiya saidai boko a yanzu an raba muna wurin karatu dasu. Don su na kudi suke zuwa niko ta gwaunatin jaha nake zuwa inda karatuna nacan yanzu ya amfanendin don basu yarda nakai ajin da nake ba saida sukai min gwaji suka gani suka yarda da nakai ajin da baba keson a sani din. Gashi kuma kusan nicema karama a cikin ajin namu na nan saukin abin kawai akwai bawa manyan wuta shine ya ja min mutuci ga yan ajin namu na nan arewa din don kokarina yaja min kwarjini a wajen malamai da dalibai lokaci guda. Haka yasa nayi farin jini sosai a makarantar don kokarina da dan turancin da nake yayi min amfani sosai a nan din yanzu har kowa ya sanni a makarantar . Gashi kuma nayi sa,a don baba bai kaini makarantar da wani dan gidan mu ke zuwaba nawa na can gaban unguwarmu sosai inda nasu baida nisa da gidasu hakan yasa na kara samun sauki da jin dadin karatuna don babu me matsa min a nan ko dinga nunani ana abantani da sunan maita anan. Haka kuma ko a nan din na kama mutuncina don ban shiga abinda bai shafeni ba ina iya taka tsantsan da kowa saboda bata min suna da yan gidan mu sukayi . Yasa bana shigewa mutum saidai idan kin kawo kanki keda kanki zaki barni don rashin sakin jikina da banyi da mutane. Ga kawayen yanzu da son zuwa gidan kawa suga kwan daga baya ka dinga jin kananan maganganu marasa dadi yana tasowa akan gidanjesu in ba ai hankali ba har yakaisu ga daga hamata a tsakaninsu. Toni da ban da gata a gida mu ga kowa ina zanje kwaso wata kawa can zuwa gidan mu dan dama dama yanzu mama lanto ce kadai nakan daji sanyi a wurinta wani lokaci. Koshi dalilin hakan shine tayi wani ciwone sosai ganin bata da lafiya yasa na kama mata aiyuka su wanki wanke, wanke da shara don yaranta basu iyawa sosai a lokacin da zaran nagama mata in tafi gun hjy mairo nayi masu aiki tunda kwanon abincin ranana yana gidan nasu. Don ba ruwana da abincin gidan mu tunda ba saka min sukeyi ba sai sunga dama balle ko abin dadi baba ya kawo aka dafa idan ba robonshi zai bani naci ba banda rabo a ciki gidan. Kiri kiri ina kallo zasu zauna suna cin abincin su a tsakar gida inta gittaiya amma babu mai min tayi akan abincin saidai in sun gama na dinga bin kwanoni ina tsunta na wanke. Wanan kan basu hanani irinsa wanke wanke da shara har da wankin tufafinsu dana yaransu da farko nike yinsa a gida. Amma yanzu na daina na mama Lanto kawai nakan danyi koshi ba kullun ba sai idan naga aiki yayi mata yawa zan tsaya in kama mata tunda tana dan kulani ita. Sai kuma suka sakata a gaba wai munafunci yasa take kula dani ai don ta moreni tayi fari kuma a wurin baba tunda ta iya kisa da makirci jin hakan itama tayi sanyi da kulani sai idan basu kusa zata dan ban wani abu nata. Ganin haka yasa gidan ma bana wuni a cikinsa koda yaushe ina gidan su hjy mairo duk da can ma aikin wahala nakeyi sosai amma yafi min kwanciyan hankali . Don ba hattara ba zagi saidai aikinta kaf dana kishiyarta kusan nice meyinsa kuma ban taba wani tsegumi da kowa ba kan hakan wanan yasa banda lokacin zaman gidan mu ma sai dare. Hakan yasa suka fara kirana da yar iska sai barnan sunan ya karu gareni din kawai su bata min suna idan banda lafiya kuma kinsan jiki da jini babane zai kashe aikinshi ya kulla dani. Ire iren hakan yasa na bushe fitilata a gidan kowa yai min zan tsaya in masa kai tsaye in fice abina dama abinda suke nema a gareni ke nan suga na lalace su samu na fadi a ciki unguwa. Saidai duk wanda suka fadawa zaice hassada suke min donsun ga ba uwata a gidan haka kuma mutans basuga wani mugun hali na assha a gareni ba banda sherin da suke kulla min kawai na hassada. Ganin yadda baba ke wahala nayi dabaran tara kudin da yake ban na tara sak nasai dan garin kwaki da suga shi zanyi kwana biyu ina ci har yakai kudi ya dan taru a inda nake boyewa a cikin jakkata. Na dauko na kirga naga sunkai min dubu biyu da yamma da baba ya dawo daga kasuwa nasameshi dakin shi na gaisheshi ya dago kai yana fadin a, a Fadimatu kina gidan ashe ? Eh baba an dawo lafiya ya kasuwa yace Alhamdullahi baba na kirasa ya dago sai kuma na kasa fadin abinda nayi niyar fada a lokacin nayi shiru. Baba yace yi magana mana don naga kamar akwai abinda kike son fada min ko kuma kinyi shiru sai nayi kasa da kaina ina fadin a,a baba dama dai nace nayi maganin dan zaman banzan nan da nakeyi. Na dan fara suya a kofan gida idan na dawo daga islamiya don mu rage wahalan kudin lalurata a nan tunda ba kudi kake dashi ba ga kuma laluran gida duk akanka yanzu. Shiru yayi ya kura min ido na dan lokaci yace Fadimatu idan nayi hakan ashe ban gaza da luluraki ba duk da nasan cewa ke natsatsace in Allah yaso ba zan samu wani matsala na asha a wurin ki ba. To amma barinki a yanzu ki kafa tukunyar suya a waje tankar gazawane a wurina ko dan abinda nake bakine zuwa makarantar baya isan ki ? Da sauri nace a,a baba daga cikine ma aina tara har na samu kudin da zanja jari a wurina kawai dai ina son ya zamo ina wani abinda zai debe min kewan zaman kadaicin da nakeyi ne yanzu. Kai ya gyada min yace inda wanan kan da wanan amma gidansu hjy da kike zuwa can din akwai matsalane a yanzu kuma ? Da sauri nace a, a baba babu matsalan komai alhalin boye masa nayi don gaskiya zuwa dai nakeyi amma yau da gobe sai Allah don a yanzu ko naje wani lokacin har in dawo banci komai ba. Dama kuma don abincin da debe kewa nake wuni a can yanzu saina fahinci kamar anyi amfani danine aka samu har jikokin su suka sake jiki dasu shine aka fara nuna min bambanci. Shiru baba yayi yana tunane kafin can yace to fadimatu banki ba amma kada in gani ko inji ba daidai a kanki kan wanan sana,an don ranki ba zaiyi dadi ba gaskiya. Na barkine don bansan dalilin ki nayin hakan ba kuma nasan ba fada min zakiyi ba Allah yasa albarka a ciki nawane yanzu a hannunki ? Dubu biyune cif baba na hada yayi murmushi yace dubu biyu ina zasu isheki jan jari nasan matan gidan nan dan dama dama Lanto idan tana dashi zata iya baki aron kwanon suya da murhu ko kin manta dole sana,an naki saidashi za ayi. Nan kuma gabana ya fadi don sam banyi wanan tunanen ba ko kadan yace to zan kara maki dubu uku sai ki fara juyawa Allah yasa maki albarka a cikin sana,ar taki da sauri cikin jin dadi na amsa da amin . Har zan daga naji yana fadin mutaneme basu da alkawari da farko na dauka wanan yaron kamar da gaske yakeyi da yace zai dauki laluranki kamar yadda suka fara da yar,uwanki. Amma sai gashi tun kudin daya turo sau daya a sakaku makaranta bai kara turo komai ba a kanki alama ya nuna ashe dama bada gaske yakeyi zaiyi maki hakan ba. Allah dai ya rufa asiri aiko a hakan ma yayi kokari tunda bamu san uzurin sa ba yanzu don ko mahaifinshi naji yana min korafin rashi waiwayo gida da baiyi a yanzu. Jeki Allah ya tsare ya kare yasawa rayuwa albarka na amsa da amin ya miko min kudin na karba na dunkule a hijabina zan fito mukaci karo da mama uwa wace tabi hannuna da kallo saboda taga baba na mayar da dan ragowan kudinsa da basufi dubu goma ba a cikin aljihunshi. Saidai na rigada na tura hannuna a cikin hijjab dina a lokacin don haka bata ga ko menene ya bani ba nidai na fita na barta tana masa kallon zargi tace Allah dai yana ganin ku ai. A cikin daure fuska baba yace da akayi mefa tayi shiru yace yanzu dai yuka ya saura ku samu ku dora kan wuyan yarinyar nan tunda ukubanku bai kasheta ba ina shike nan. Malam ai bakaji ance gidan mu sun gaji kisan kaiba ko yace amma sun gaji kula sheri ga dan wani tunda yar nan ita kadai kun dauki kiyayyar duniya kun dora a kanta. Wasa wasa tun yana daure fuska har ya kai ga sakewa ga irin abinda suke masa din sai ya dauka kyautatawane a gareshi don rashin matansa dayayi kuma ita din maman baby aminiyar matartasace ai. Har yakai ya fara sakin jikinshi dasu komai dare ya dawo zai biya can ya dauki abincin da maman baby din tayi masa tayi shi kuma yana dan sayo masu dan abubuwa yazo masu dashi gidan a gidan. Idan yazo da takan fito da kanta su gaisa ko mijinta amma yanzu ta daina haka saidai ta turo mashi wasil har yakai shakuwa ya shiga tsakanin su da ita sosai. Wasa wasa kuma hakan ya koma soyayya a tsakaninsu har wani baison dan uwa yayi nisa dashi baiga dan uwa na wani lokaci ba. Ga ya habibi yanzun kamar an buda masa bakin aljihunshi har yakai ya tashi daga wanan gidan da mukai zama a cikinsa ya koma wani dan gida mai kyau daya saya. Ga kuma mota don rage jigila ya saya kasuwa dai a yanzu tasan dashi don gaskiya anayi dashi sosai a yanzu don yakai matakin da duk wata mota idan tayi loading zata shigo arewa dolene a ware masa dubu talatin na loding wanan motar. Sai ga kudi cikin dan lokaci guda ya budo gareshi yana samu fiye da tsamanin mai tunane shida yaje suna black market yanzu ya samu shiga ya kutsa cikin company NNPC din ana cabawa dashi. Allah ke nan sai dai wanan samun na ya habibi a yanzu yasashi shagala akan komai inka debe masoyiyarshi gaba daya yanzu ko yana son ya tuno da gida da yaran shi sai kuma hakan ya gagareshi. Gashi dai bawai ya manta dasu bane kwata kwata ya kan dan tuno dasu amma kuma yadda zai samu time yayo masu sako shine abu mai wuya a wajenshi. Tun abin yana damun hjy har ta kasa barwa zuciyanta hakan yakai tayi maganan da mijinta tace waiko ni nace ko yaron nan yana kiranka kai yanzu don ni an dauki lokaci mai tsawoma bai kirani ba gaskiya. Murmushi Alh yayi kafin ya dauki ruwa ya kora yana fadin a yanzu gaskiya zamu iya masa uzuri tunda hakan ba halinsa bane tun farko kinga dole yanzu mu daga masa kafa djn bamu san uzurinsa ba gaskiya. Iyakar mu dai mu bishi da adduan nan da muka saba binsa dashi na alheri shine abinda yafi bukata yanzu a wajen mu tunda yana cikin mutane kabilu iri daban daban suna gwagwalmaya dasu. Ajiyan zuciya hjy ta sauke tace addua kan muna kan yinsa kullun saidai mu kara a wanda mukeyi amma shirun ne nasa yayi yawa wanan karon gaskiya . Ina mairo tace gani zaune ai yace shine hikimar manyan da suke sa mutum aure a gida da can in kin natsu ai yana da mata a nan lokacin baya ko ? Yanzu ko fada min wa yake dashi da zai tunatar dashi zancen gida kedai Allah ya gyara kawai zamuce tunda ya riga ya shiga cikin arnaku ya saba da can yanzu saidai addua kawai gareshi. Wallahi abinda nakewa tsoro ke nan jin shirun nan nasa ina gudun yaje ya dauko muna yar kabila muzo a gaurayu dasu gudun haka ai kikaga nasa ya dauki matarsa suka tafi can Allah kuma baiyi zaman nasu mai dadewa bane ashe. Shiru hjyn tayi tana tunane halinda dan nata zai iya kasancewa a ciki yanzu kafin ta nisa tana fadin Allah dai ya kyauta zan sa gobe in Allah ya kaimu kannensa su kira min shi muji jn lafiya kalau yake can. Ai kaji matsalan ku mata baku iya hakkuri da yaro aga iya gudunshi babu dai inda zaije da tafi masa nan ga kuma yayansa nan yanzu a tare damu don haka ni banga abin damuwa tunda dole yazo nan din. Ta karasa mikewa tana fadin da wai mu kirasa muji bawai don ya bamu wani abu ba dai yace yanzu idan kin kirasa ai kamar tuni kike masa ke nan akan ki kyaleshi kawai zaifi a yanzun don bamu san uzurinsa ba a yanzu. Shike nan tunda kace hakan zan barshi ba zan kirasa ba insha Allah mu kwana lafiya ta fada ta nufi kofan fita can ta daga labule taji muryanshi yana fadin waini ko yar nan tana garin nan na kwana biyu banji muryanta ba a gidan nan ? Dan tunane ta tsayayi kafin yace yar wurin malam habu mana ai ana gane tana gidan nan ko bata nan don na kula tun shekaran jiya ba a shere min filin nan da nake zama ba. Wai bintu kake nufi ta fada cikin murmushi wallahi dazun nan nima na gama maganan ta don kwana biyu ke nan bata shigo gidan nan ba ko kuma sun hanata zuwa nan din ne oho ? Kai anya hakan zai yuyu kila dai akwai abinda ya hanata zuwa din ko kuma halin jiki da jini wata kila kuma bata da lafiyane ya dai kamata ku aika aji idan tana lafiya. Nima idan mun hadu da uban masallaci zan tambayeshi inji ko lafiya don gaskiya yarinyan tana da kokarinta gata kuma abin tausayi sosai zan aika yanzu a tambayo min ko lafiya bata shigo ba. Mijin yace haka dai tafi don ku mata baku raina abin tsegumi ko yaushe dan karamin abu sai amayar dashi babba rashin nuna kulawan naku zai iya jawo wani magana kuma. Yanzu zan aika idan na fita a duba muna ita dadai yafi ya fada yana kokarin jawo wani littafi a gefen shi ya jawo glass din shi na ido ya kafa a fuskanshi don gani. Hjy tana dawowa daga wurin Alh taci karo da kaya kumshe a buhu ta tsaya tana kallo tare da tambayan wanan kayan meye kuma a nan aka ajemun ? But na fito daga dakin ina fadin hjy ina wuni a,a bintu kece yanzun nan ko muka gama maganan ki da Alh ai yace a aika a duba ko lafiya bakizo ba. Nace lafiya kalau nake hjy kwana biyun nan ban dawowa gida da wurine kafin na dawo dare yayi shiyasa bana samun shigowa da sauri tace dani keko ina kike zuwa haka har dare ? Nace kasuwa nake zuwa wurin baba na sayo abu tace oho wanan kayan kuma na meyesu nace kayanane na kawo nan na aje gobe idan Allah ya kaimu ba islamiya zan fara suyar awara da yamma. Awara kuma bintu shi malam habu din ya yarda kiyi suyar awara kuma nace eh hjy aiba yawo talla zan tafi ba a kofan gida zan dinga soyawa kuma ba yawa zanyi. Kaiya wa yan nan tarkacen awaran ke nan dai ashe nace eh hjy sune na kawo nan don gudun tsegumi a gida ina son saidai su ganni dasune kawai inayi . To Allah ya kyauta nace amin ta sakai zuwa cikin daki nima nabi bayanta muka shiga daga cikin dakin a kusan lokaci guda na koma na zauna

Chapter 4 of 10